Kishi Ko Hauka Hausa Novel Complete
Mata ne cike d falon ana daga kayan lefen d aka kawo, sai faman shewa d guda ake tare d yabon kayan d aka kawo, domin kuwa kaya ne n gani a fada, naira tayi kuka anan, duk wani abinda ke ciki ba na banza tun daga kan sutura zuwa sarkoki mayukane abindai sai wanda y gani, yan uwa d abokan arziki n fadin Amarya tayi goshi, Ana t sanya Alkhairi d fatan Allah y nuna mana ranar biki, can bangaren kuwa amarya ce cikin daki tare d kawayenta sai xolayarta suke daya daga cikinsu mai suna hafsa tace matar mutum kabarinsa, Aysha ba irin wulakancin d bakima Abbas ba y jure kamar karamin yaro lallai y cika jarumin maza gashi nan ynx y kamaki a hannu ta kare maganar ta sigar zolaya t dan bugi Amaryar acinya, ita dai kawai murmushi tai, a zuciyarta kuwa Allah Allah take bakin d suka zo karbar lefen su tafi take domin t ganewa idonta kayan d kawayenta suke t zuguguta wa ankawo mata.
Ita kam uwar amarya sai wani cika take tana batsewa tare d wurgawa kayan muguwar harara ita a dole kayan basuyi mata adalilin rashin sanya sisinan gwal, kasancewarsu yan bidiri wayo ‘yan maiduguri, Anty salma ce ta matso kusa d ita tai mata rada a kunne tace mata don Allah Anty kiyi hakuri ki saki fuskarki a gaban jama’a ne fah, kar ki ba da mu plx.. Kuma m ai bawan Allah nan yai kokari daga baya ai sai ai mishi magana. Sai alokacin t dan sakin murmushin d bai zuci ba, inda aka shiga tattare kayan ana maida su cikin akwatinan, har mutane suka fara watsewa cike d yabon kayan, y rage daga anty salma sai d kakar Amaryar wato uwar Amaryar d kannen amaryar a wurin, kawayen Amarya kam uwa jira suke su watse suka fito aka sakw baje kayan suma suna t santin lefen tare s Amaryar itama sai washe baki take tana duba kayan, inda kakar tace “OH ni hauwa yaran zamani ynx d ke ake duba kayan naki Rukayyah”
Goggo nikam kin sa min ido da yawa zamaninku da bamu ai ba daya bane, ko kishiru kike ne da kaya ta kare maganar d yi mata gwalo tare da mikewa ta ruga Daki a guje tana dariya, goggo tace ja’ira da kin tsaya sai na koya miki hankali.
Nan dai aka tattara kaya aka maida su cikin akwatunansu, mommy kuwa tashi tayi tabi Rukayyah Daki, ta sameta suna waya da Abbas, Rukayyah kuwa ganin yanayinsa mom din nata yasa ta saurin katse wayar tace masa ‘sorry I will call you back”
Ta cire wayar daga kunenta, ta tattara nutsuwarta Ga mom wacce ke ta jifanta d harara, tace momy Lfy kuwa,? Bansani ba ta bata amsa a gajarce, ina so ki gaggauta kiran Abbas kice ina son ganinshi!
Mommy me y faru ne don Allah?
in yazo kyaji a wajensa, Tunda na fuskanci kina neman xubar d darajarki a wajensa Tun kan ki shiga ciki gidansa, komai yayi a wjenki daidai ne kin Dora wa kanki son mai mata, sai Kace kin rasa masoya ne, ta juya ta fuce daga dakin.
Rukayya kam doguwar ajiyar xuciya ta sauke tare da fadin, mommy ban san ran da zata canja ba, bawan Allah nan kullum cikin mata biyayya yake kamar ita ta haifeshi amma bata gani?
Daukan wayar tayi tai dialing no shi, “hello”
Baby mommy tace tana son ganinka plx…
Ok insha Allah zanxo bayan magriba, ok sai kazo bye! Ta katse wayar.
DOWNLOAD HERE
Kishi Ko Hauka Hausa Novel Complete