🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* NA SAKE ZUWA DA SABON TSARI, SABUWAR TAFIYA, SABON AL.AMARI........ NI CE YAR MUTAN NIGER NA KAWO MAKU SABON NVL DINA WANDA A KASATA NAKE MAI TAKEN *BAK'A CE* bak'a ce na dauke da darusan rayuwa, dole ya nishadantar, ya baku mamaki, ya saka ku tunani..... *BAK'A CE* zai zo da kadan daga cikin al.adun yarena *BUZANCI* da kuma *TUBANCI* ..........ku biyo ni ku sha labarin *BAK'A CE* TALLAH TALLAH TALLAH *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣ *WANI YANKI NE CAN WAJEN AGADEZ CIKIN JAMHURIYAR NIGER mai sunna TIMIYA*, inda buzaye ne ke rayuwa a garin indai ka ga bakuwar fata to lale bako ne ya zo kuma juyawa zai yi , A kauyen nan basu da ruwan pampo sai fan take, wuta bata kai can ba , Gari ne mai tarin ni.ima , albarkar noma garake , sannan mota bata shiga domin can cikin sahara ne sai dai a hau rakumi a samu a shiga cikin Timiya Yan mata ne laye su hudu, Cikin ukun nan kowace ta kala tamkar ka lasheta dan kyau da daukan hankali sun sha digo digonsu na buzaye da katanga , sai daya a gefensu wace kanta ke sade kasa jikinta na dan rawa rawa hanayenta kawai ake ganni bakin kirin da yafen mayafinta na turkudi (tufafin buzaye ) Shigowa wani datijo ya yi yana dan dukawa dan tsayi ne da shi, da hannunsa yake yiwa mutanen dake bayansa nuni da su shigo domin bashida hausar kirki a bakinsa Yana dago kansa ya hangota a cikinsu, ya juyo da dan sauri ya ga mazan nan har sun zauna Rai bace ya nufi dakinsu wajen uwar yaran wato matarsa yana zuwa ya daga hannunsa ya dungurewa yar datijuwar kai ransa bace cikin yaren buzanci ya ce" ban hane ki turo min da wannan bakar yar taki ba? Na aurar da yaya hudu saura uku na cire wannan bakar a yayana, na sha fada maki ni a danginmu ba baki aman kika tashi kika haifo min baka? Na yi na yi ki fada min gaskiyar waye ubanta kin ce ni? Kuma dan bakin ciki an samu elhazawa masu son auren yaren kin tunkudo (turo) mini da ita ko? Bata ce komai ba sai sada kai da ta yi, har ya gama babatunsa ya juya Yana komawa ya damki hannunta ya jata kiiiii suna shiga ya hankadata ta tafi tagataga ta duke nan kusa da gadon karagar mahaifiyarta kanta sade, ya aibatata sosai kafin ya juya ya koma wajen bakinsa Kanta sade hawaye ya ziraro mata, ta dago a hankali ta kali mahaifiyarta da idannuwanta ke rufe ruf tana jin yanda zuciyarta ke suya Murya a raunane ta ce" *ANNA* (wato mama) Bata bude idannuwanta ba, bata amsata ba Ta dan jima a haka kafin take mikewa ta dage rufar da ta yi tana kallon mahaifiyarta da wani irin yannayi, a gaskiya a jikin wannan matashiyar budurwa banda idannuwanta ba wani abu mai hasken fari domin kuwa tana da baki ga kuma tufafinta mai rinar da fata ne wato turkudi Mamanta ta dago ta bude ido a karo na farko, murya shake cikin yaren buzanci ta ce" kal ki ce komi, ki yi hakuri kawai A hankali ta juya dan ruwa gidan baba tsoho.... Ku biyo ni garina, *TIMIYA* domin a Niger nake.... ......taku har kulun YAR MUTAN NIGERSAJIDA 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2⃣ A hankali take tafiya tana dan rabewa, da ta hango gugun yara sai ta labe har sai sun fice idan kuwa wasa ne suke dole sai dai ta canza hanya domin irin wulakancin da mahaifinta da wasu a cikin yan uwanta ya sanya har jama.ar garin ke wulakantata suma suna dubanta daban cikinsu.... A hankali ta karyo kwanar runfar baba tsoho Sanda take dan karasawa domin bata son haduwa da almajiransa tun bama Ali ba wanda ya so hada shi da ita ya ci mata mutunci yayi mata kwakwaran kashedi na koda wasa kar ta yarda ta nuna tana son sa domin shi dama ya shigo garin Timiya ne dan ya samu buzuwa fara ya aura..to tun daga lokacin sauran almajiran ke tsokanarta suna fadin ta Aliyu *BAK'A* zaune yake cikin bukarsa, rawani ne a fuskarsa kwaurin hannun sa da na kafarsa ake gani , hakan zai nuna maka tsohon mutun ne, domin fatarsa du ta yi yaba haka gashin dake kwaurinsa du sun yi fari sol sol da su Waje daya kawai yake kallo, a zuciyarsa kuwa ya afka tunanin yau ina ta yi? Ya aka yi bata zo ta dauki karatu da safe ba? Bata da kawa, bata da wani mai rabata a jikinsa, mahaifiyarta kanta bata mugun sake mata dan tana tsananin tsoron mijinta a kan yarinyar Shi kam yana cike da zulunmin abinda ya sa bata zo ba A hankali ta daga kasarin dakin ta yi masa salama Murmushi ne ya subuce masa yana kallonta kafin ya amsa salamarta karasawa ta yi tana dan tatare tataren dakin ta kai dubanta wajensa, cike da kaunar tsohon sannan idan tana tare da shi takan ji ta wani iri, bata jin tsoronsa sai soyayarsa, tsohon shi ne kawai mai yi mata murmushi a duniya, Dan murmushi ta sakar masa ta ce" SOFO (wato tsoho) Shima murmushin ya yi, ya dan nunota da yatsarsa, Ta karasa ta duka kasa ta ce" ta gode (gaisuwa kennan) Turkudin kanta ya shafa a hankali kafin ya ce" Alharasssss Mikewa ta yi ta gama tatare masa dakin ta dauko tsintsiyar kabar da ta yi da kanta dan share dakins ta shashare ko.ina ta dan dage kasarin ta dauki tulun ruwansa ta fice Murmushi ya yi, ya bi ta da kallo....a kasan zuciyarsa ya ayanna" Allah ya nuna min farin cikin ki kafin na koma gareshi Tafe take da tulunta cikin nutsuwa, tana zuwa ta duka wajen diban ruwan , wani dan kewaye ne aka yi shi ba rijiya ba, shi ba teku ba shi dai ruwan ana jayo masu shi ne, sannan kalar ruwan jajajir ne sai kanshin laka , akoy ruwa masu kyau sai dai idan ta yarda ta je wajen sai dai ta dawo ba ruwan ba tulun domin du yawancin yan matan garin can suke zuwa dibo ruwa su kuwa sun ki jinnin ganninta a wajen Sai da ta cika tulun ta mike ta gyara bakin zaninta da kyau ta daga ta dora saman kanta Yanda ta bar shi zaune haka ta dawo ta tarar da shi Ta nemi wajen Tulun ta ajiye tana dubansa cikin yaren buzanci ta ce" baka gajiya da kallon waje guda? Bai bata amsa ba sai mika mata allonta da yayi yana nuna mata wajen zama A hankali ta zauna ya ci gaba da koya mata karatu wanda sosai ta nisa kuma shine malaminta tunda ta san shi Suna gama karatun ya ce" menene tambayarki ta yau? Ta yi tsai tana kallonsa, can ta nisa ta ce" sofo, shin mutun mai bakar fata laifi ya yi aka halice shi baki? Da sauri ya kallota, ganni ya yi kanta a sade, tana faman murza hannayenta .....yarinyar akoy zurfin ciki sosai aman wani lokacin sai ta fadi dan abinda ke ranta domin tana gannin abubuwa masu firgitarwa a rayuwarta Hannunsa ya daga, murya a sanyaye ya ce" ko daya mutun baki da fari du daya ne a wajen Allah Dara daran fararan idannuwanta ta dago ta sauke kan nasa da sukai dan ja sannan du sun yi yaba irin na tsohon mutun, hawayen da ya taru a idannuwanta ta yi iya kokarinta ta mayar da su , daga haka bata kara komai ba, bata bari ta yu kuka ba ta mike tsam ta fice ba tare da ta kara kalma daya ba Ajiyar zuciya ya sauke, yana tir da halayen Agali, Agali bashi da hankali da tunani, dan kawai Allah ya yi yarinya an haifeta bak'a cikin y'ayanka sai ta zama abin kyama abin kyankyami abin wulakantawa? Ita ta halici kanta ne? Ta jima tana tafiya kafin ta karaso gidan iya mai siyar da nono Har kasa ta duka tana gaisheta Iya ta amsata kafin take cewa" kin ga nonon nan yana yi min wuya, ban san me yasa idan kin dauka cinikinki baya fice dala dari da ashirin .....sai dai ki maido mini shi haka du an motsa shi sannan in baki salama ni kam yau ki yi hakuri na sararma masu zuwa gida sara, kinga daman tausayin ki yake saka ni na baki dan ki samu dan kudin kashewa Kanta a kasa ta ce" ki yi Hakuri iya, zan kara kaimi wajen siyarwan ki zuba min kadan yanda zan iya siyarwa Kanta ta girgiza ta mike ta dauki kwarya ta zuba mata nono dan madaidaici ta mika mata, ita Allah yana ganni dan tana jin tausayin yarinyar ne aman tana da masu siyan nononta a hannu a hannu domin shannunta suna da yawa Dauka ta yi ta fice a gidan, tana tafe tana jin wata irin juwa na daukanta, bata karya ba, bata ci komai ba sai yanzu ta tuna Ajiyar zuciya ta sauke ta samu gu ta dan rakube ta daga kanta sama ta afka tunani Mu je zuwa ci kin labarin *BAK'A CE* 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3⃣ Suna tafiya ya shigo dakin, Yanda ya barta tunda ya dungure mata kai haka ya tarar da ita Ransa bace ya nunota da yatsarsa ya ce" ke, A hankali ta dago kanta ta sauke kansa tana kallon sa Y.ayana biyu sun samu miji yan albarkana Wani abu ta hadiye a makogwaronta, a hankali ta ce" wannan karon wa ka siyarwa yaran? Da mamaki yake kallon ta, mayar masa da magana ne ta yi? Shi? Da izgili ya karasa kusa da ita ya nunata ya ce" ke balagazar mace, ke har kin isa ki dube ni ki fda min cewar ni ina siyar da yara? A me kika dauke ni kennan? Matsiyaci? To bara na tuna maki a gidannan daidai da sansannin ( tabar buzaye) da zaki gumtsa sai kin taba tawa ba zaki iya siya ba dan bakya saye bakya saidawa zaune kike dabar ta.kar duwawu komai sai an yi maki, To yaranna sun samu mazaje sun yi min kyakyawan tayi! Kuma na fada maki idan har na aurar da yaran nan gaba daya ki kuka da kanki ke da yarki dan kuwa ba zai yiwu ya kasance ina ciyar da yar da ban yarda cewa tawa bace bama Har ya gama bata kara tofawa ba , ya juya ya fice a dakin A hankali ta zauna kusa da mahaifiyarsu, itama farinta har daukan ido yake, Hannunta ta kamo ta rike gam ta ce" zan so ki fada mana tarihinmu kafin muma mu tafi kamar su aunty a daina jin labarin mu, ba labari ba aike ba wani motsi.....Allah kadai ya san halin da suke ciki idan suna raye! Ba yace auren wata biyu kawai zan yi, idan na cika wata biyu na kwaso masa kudade na dawo ko ya sake ni ko bai sake ni ba sarki zai hana shi shigowa garin ........ ki daure ki fada mana tarihin rayuwarmu Anna (mama) Su waye mu? Ina ne asalin asalin mu? Su waye dangin mu? Bamu da kowa ne sai mu da ku? Idan muna da mai ya sa ba wanda ya taba zuwa inda muke? Ina son sani ANNA Jajayen idannuwanta ta sauke kan *Gaishat*, wai ita nan mai damar ce domin ita bata hantarar Bak'A, sannan tana kamanta bin iyayen su ba kamar sauran ba Kwace hannunta ta yi ta hade rai ta yi mata nuni da kofa Ta san kan zancen dan haka ta mike ta fice daga dakin Kallonta yake tunda ya kirayeta ta zo turakarsa tana zuwa ta tube du wani abin da sunnansa sutura a jikinta, ta tsaya masa a gabansa wato gashi ka yi ka gama na koma Kansa ya girgiza kafin yake tsareta da idonsa, ya juyar da kansa ya kuma kallota Can ya ce" Nadia, haka zamu yi ta rayuwa? Ke ba zaki taba saukowa ki bani kulawar da nake bukata ba? Saurin zubewa ta yi kasa ta ce" ka yi hakuri Uban gidana, ban san zan bata ranka ba kar ka hada ni da Ba (Aba) Idannuwansa ya lumshe, a gaskiya Allah ya jarabe shi da matsanancin son yarinyar, Yarinyar ce ko a cikin bugaje (buzaye) ta fita daban, ta hadu iya haduwa ko ba wanka Nadia mai kyau ce, dalilin haka ya amshi tayin aurenta da Ba dinta ya yi masa bisa sharudan kawar da ido da toshe kunnuwa kan karansa da za.a kawo a cikin garin kan yanda yana tafiyar da rayuwar gidansa, aman ya kasa samun nutsuwa da ita........ya kasance komai zatai masa tana yi ne dan tsoro ba dan soyaya ba A hankali ya dagota ya jata zuwa ainahin turakar domin yanda yake kwakwarta shi kansa mamaki yake, yanzu dai shekara biyar da aurensu bayanta ma ya kara auren mace biyu ya saki gudar aman har yanzu ta kasa fice masa a rai a kulun yana mai jin zumudin kasancewa da ita.....aman ita ta kasa kontar da hankalinta ko dan matsayinsa na sarkin garin ta murza mulkinta aa tana rabe rabe ne a gidan mijinta Nadia kennan babar yar *BA* Ke kin san nawa ne million daya? Jika dari dari har goma fa, an ce Gaishat har million goma sha hudu mutumin ya bada kudin aurenta, Ke ki rufe min bakin ki, ke fa haka birge ki yake ko? Kina ganni yanda yake aurar da yayan nasa daga sun tafi shikennan ba labari, kudin ya zo bai yi masa anfannin komai ba, daga an kwana biyu ya kashe sai kuma ya fara harin wata a cikin y'ayan nasa, ai sun kusa karewa zamu ga kuma idan wada ya tsanar zai yi shelar ya siyar Mahaifiyarsu da ta shigo da Buzu (salaya) a hannunta ta kale su ta ce" ke Amina, ki tashi maza ku je ku yi sallah, wannan maganar kun cika yinta bayan kun san ya zama abin gasa a garin nan, sai kun jaza min abinda ya fi karfina ko? Kuma da hakan bata faruwa da ku dan Ba din ku bai yarda da hakan ba, ku kun fi kowa sanni gidajen da basa haka basu fi a kirga a garinnan ba aman zaku zauna mamakin kwaya daya? Kowa ya yi da kyau kai nasa! Ku mike ku bace min a wajen nan kar ku yarda maganar nan naku ta yi tsayi ya zo ya tsige mu baki daya domin ku kun san waye shi ! Sumui sumui suka fice dan zuwa yin alwallah su gabatar da sallah Sai yama sosai ta kamo hanyar gida, Tana tafe ne tana dan jin dadin yannayin garin domin sanyin yama ya fara busawa sosai ita kuwa gwanar son sanyi ce sosai Ba ita ta kai gidan iya mai nono ba sai kusan magariba, ta kai mata cinikin inda iyar ta bata dala ashirin da biyar ta yi godiya ta mike Har ta kusa fita iya ta kirayeta ta dawo Ta ce" kin ga , ga abinci nan ki dauka ki ci mana ni na ci na rage, sauran ki yi min halin naki sai na tabatar kina kyankyamina ne na san irin matakin da zan dauka Fanata ce ta fito daga daki, kmar kulun cikin mahaukacin gayu mai gigitar da jama.ar garin ....Fanata dai y'a ce a wajen yar uwar iya wace ke aure a cikin garin agadez, mahaifin fanata Babarbare ne shi ya sa sunnanta ya fita daban , A da fannata ta kasance ita ba fara kar ba ita ba baka ba duda mahaifiyarta farar buzuwa ce, Aman kasancewarta a can cikin birni, da taraya da kawaye ya saka take shafa mai wanda ya mugun karbarta ta yi fari kar kar kar harma ta fi maman nata farin, Fannata akoy kyau ga iya daukan wanka Tana son garin timiya a rayuwarta domin gari ne mai cike da ni.ima Tunda ta fito take kallonta da mamaki, Dubanta ta mayar wajen Iya ta ce" iya, yarinyar nan mai maki tallah ce ta girma haka? Iya ta ce" eh ita dai ce Fannata ta yatsina fuska ta ce" to aman har yanzu sunnan da ake kiran nata da shi ne? Wato *BAK'A*? iya ta amsata da kai Fannata ta kallo wajenta ta kuma kallon iya ta ce" menene sunnanta na gaskiya ne ita wai? Iya ta kalli Bak'a, ta kalli Fannata, ta ce" sunnan Hajia ne da ita, karfi da yaji Ba dinta ya mayar da sunnanta Bak'a har ake mata kiranye da haka Da mamaki Fannata ta karasa kusa da ita tana kallonta, Yarinyar fa nata wani tsararan kyau, boyeyen kyau, duda mugun bakinta ga bakin turkudi na bugajen kauye🙈🤣, ga dati da take fama da shi, aman ita tana hango wani al.amari a tatare da yarinyar, to aman me zai hana ta shafa mai itama? A sanninta ba bakon lamari bane buzu farinma ya shafa mai, kai ba buzu ba yanzu abin ya zama larabawama mai suke karawa shi yasa zaka gan su wani farfarfar da su sunna daukan ido, ba sai dan duniya ke shafa mai a duniyarmu ba, mun dauki mai mun mayar da shi abin kmgyaran fata, ra.ayi ne shafa shi idan ka shafa ba mai yi maka kallon dan duniya a karkarar mu Abimcinta take ci kanta a sade tana ji yanda Fannata ke aikin tambaya a kanta, tsoro take kar a je mugun kyankyaminta kamar yanda mutanen garin ke yi ya saka take son sannin ko ita wacece dan ta kara samun damar ci mata mutunci, hakan ya sa take sauri dan ta gama cin abincinta ta kara gaba , so take ta siyarwa SOFO goro na dala biyar, ta saka dala goma asusun da take tarawa dan ta bawa Ba ko ya daina tsanarta, Gomar kuwa itama ta ci wani abin *AGAISHAT* ta ji sunnanta a sama sama yana yawo, sunnanta na gaskiya aka kiraya, Da dan sauri ta dago sukai ido hudu da Fannata, Fannata ce ta kirayi sunnanta na ainahi ba bak'a ba............. 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4⃣ A hankali ta kai idannuwanta kan Fannata dake kara matsowa kusa da ita A hankali fannata ta saka hannunta ta dago na Agaishat, kallon hannun take tana jujuyawa, fannata ta fahimci bayan bakinta na halitarta da Allah ya yi, akoy tarin dati ga kuma karin bakin turkudi, Da sauri Ta janye hannunta tana kokarin mikewa daga cin abincin cike da tsoron menene kuma Fannata ke taba mata hannu? Fannata ta ce" kin ga, ba abinda zan maki Kallonta take da mamaki domin da hausa radau Fannata ta yi magana bayan Agaishat kadan kadan take jin hausar itama baba Tsoho ke dan koya mata dan abinda ya iya, yakan ce ba.a san gobe me zatai ba Goshinta ta dafe ta kalli wajen iya ta ga sai faman gyara Sansanninta take(tabar buzaye), tana dan kukulewa da zare tana ajiyewa gefe tana yin kulin kadago kadago (dala biyar biyar ) Kurumci Fannata ta shiga yiwa Agaishat, Ta yi mata nuni da hannayenta da fuskarta gaba daya, Ta yi saurin taba ruwa ta nuna mata alamar bata wanka ne? Agaishat ta shiga faman saka tsohon takalminta na soso tana faman guduwa domin ta saka a kasan zuciyarta wannan abin zai kare ne a wulakanci da tozarci *WaRDUGU* Ta fada tana mai daga murya kamar zata kaiwa gabjejen mutumin dake tsaye a gabanta duka, Ta kuma cewa" WaRDUGU Odon jidu anna indahan yuna yugusnan gwa ( tun kana yaro yake fama da kai) Kansa ya dafe, ya kai dubansa kan agogon hannunsa, kallota ya yi ya yatsina fuska, can ya ce "Ayya (wato mama), Ayya inda medi mundu tam (wato mama ke rigimarki ta yi maki yawa) Hannunta ta dora a goshinta ta shiga kai kawo, kai take tana kawowa, can ta dauki wani ihu ihu tamkar tana buda, ta je ta dawo ta je ta dawo, ta kallo shi cikin yaren hausarta da bata fita da kyau ta ce" shikennan rayuwar bariki (gayu) ta lalata min kai, shikennan na zama uwar da ina fadi ba.a saurarena, ko nima zaka kula zazafar gabar da ni ne kamar yanda ka kula da Abbanka (mahaifi)? Hannayensa ya jimke ya daki garu da su, kafin yake juyowa wajen mahaifiyarsa, Taku ya yi zuwa gabanta kafin yake sada kansa, shima cikin yaren hausar sai dai tashi ta fi dan goguwa ya ce" Ayya ba dai saboda wajen wannan bugudin (tsofo) ne kike daga hankalinki harda hada kanki kike min da wannan Bugudin (wato mahaifinsa)? Kanta ta kawar ta ki bashi amsa hakan ya sa ya mike ya fito daga falon Yana fitowa ya nufi wani dankareran mashin *ROUTIER* jibga jigban nan masu shegen tsada domin daga million daya abinda ya kai har million shida ne, kuma mashin ne ba mota ba...gudunsu ma daban yake da kananun mashin Bakin gilas dinsa ya fitar ya saka ya tayar da mashin din ya yi masa wani irin ja wanda kana ganni tamkar dambe ake da mai jan da mashin din domin mugun karfi ne da shi ga kyau Hangame gate mai gadi yayi don kar ya jawa kansa bali wajen Wardugu Yana fitowa daga anguwa *Plateau* a birnin Niamey ya nufi *Francophoni* inda gidansa yake Yana karasawa shima tuni an hangame kofar ya shige da gudun tsiya ya silala wani waje da nan ne ma.ajiyar abinda ya shafi mashin da motoci Dira yayi ya juya da sauri sauri ya shiga hawa matatakalar bangarensa domin bangare daban daban ne da matarsa mai sunna *GALayn* Wata yar karamar carte ce ya dora mai dauke da hotonsa ya dora daidai wani detecteur ya bada dan kara titeeee kofar ta bude Caicaicaicaicaicaicai wash, gidan tubawa kamshi, wayo gidan batube ni.ima, bale mai auren gimbiya hajiar hajia, sarkin tsafta, sarkin ado, kwaliya ba dai a nuna mata ba, ta kasance cikin kamshi wanda indai kai ka ce zaka kwaikwaya sai dai ka tashi da mura (gaisuwa yar baba) Sanyi mai hade da kamshi ne ya buso shi, sanyi mai sanyaya zuciya Terrace din dakin fara kal kal kal haka take daukan ido ta sha guga, Tafka tafkan salon ( kujeru) ne irin na zamani masu kalar fari kal kal sai dan coussin kananuwa sosai su kuwa masu kalar baki kamar yanda mauquette (capet) Rido (wato labulaye) yen dakin suma kalar fari ne, sai dai farin ba kar ba kamar yanda kujerun suke , shi ya fi ruwa da kalar peinture (colern) dakin, shima an saka abinnan na daure labule baki wanda kana ganninsa ka san ba karamin kudi bane dakin ba wani tarkace aman komai ka kai dubanka ka san karshe ne sannan ya bada kala ta mamaki, Nan ya yada zango, ya daga kansa sama , Iska ya furzar yana jin yanda takalmin matarsa ke tahowa kwaskwaskwaskwas Kamshin da take fitarwa shima na daban ne, ta shafa turaruka har ta gaji, Tunda ta fito take kallon yannayin fuskarsa, a cikin ranta ta ayanna" wani masifafe kuma ya hargitsa min yannayin miji? Bata yi kasa da gwuiwa ba ta karaso kusa da shi ta daga damatsunnan hannayensa ta shiga masaging a hankali tana kara kallon yannayinsa Murya can kasa ya ce" *ADIBIRA* (Matata) Tsai ta yi tana kallonsa kafin ta ce" qu'est-ce qui ne va pas mon Bb? (Me ke faruwa Baby?) Kansa ya kawar gefe kafin ya janye hannunta a hankali ya mike ya nufi uwar dakansa Bakinta ta tabe, Galayn akoy saurin fushi, mace ce iya mace aman bata tunnanin zata tsaya tana wani bibiyar namiji ko waye shi balatanna wardugu? Wardugu zuma ne ga zaki ga halbi, wardugu ko a cikin tubawa tsoronsa ake, mutumin da idan ransa ya baci idan bai samu ya damki mutun ba yake suma? Mutumin da ya wawuri ogansa ya daga sama ya nana da kasa ogan nasa bama na niger ba domin a niger ba marichal, bako ne da kowa ke tsoro yana shayi, gardama kadan ta hada su General Wardugu ya daga shi ya nana shi kasa a gaban yaransa da kuma yaran general, wannan abin ya jaza masa da mukaminsa da komai shugaban kasa ya tsaya kai da fata aka tura shi daji can wajen mali sai da ya yi wata hudu ya sauko, aman maimakun abin ya yi sauki sai kara gaba da yayi, mutumin dake gaba tukura da mahaifinsa , fada yayi gwa da gwa cewa abansa ya kiyayi hanyarsa kan laifin da ya boyewa kansa sai shi sai mahaifiyarsa suka sani, ita a wa zata tsaya ta bi bayan wardugu da idan ransa a bace ka bashi hakuri yake hucewa kanka? Du irin yanda yake ikirarin shi yanzu ba ruwansa da fada da mutun na gugar jiki karya ne ! Ka yarda ka yi gigin kai masa wargin baya ce masa komai ya ciro daya daga cikin wukaken dake jikinsa ya burma maka idan ya so a kashe shi, Wardugu nada zuciya ta ainahin tubawa.... Mu je zuwa labarin *BAK'A CE* 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 5⃣ Mikewa Galyn ta yi ta fice itama ta bi ta babar kofar danma ya san ta yi tafiyarta ta je ta kara bada turaren ruwa a jikinta ta fito ta je wajen da kys din motoci suke ta dauki guda ba tare da ta tsaya zabe ba domin kuwa kaf ciki manya ne Tana fitowa ta shige motar ta tayar ta fice abinta wajen auren kanwar kawarta tana mai duba carte dinta ta bank dan ta tsaya ta ciro yayan banki na kari a wajen wasa.... Wannan kennan Ya yi kai kawo ya fi a kirga, ya dafe kansa yana tunanin irin nacin mamansa kan abu, ita yanzu dan wani tsoho can daban zata dame shi kan sai ya kaita, shi ya san wani bai isa ya bashi lafiya ba aman har fadi take shi ya taimake shi yana yaro, an dai dudura masa itatuwa haka kawai za.a kashe masa kwayoyin jiki Tsaki ya ja mai karfi, ya mike ya shiga cire kayan jikinsa masu nauyi ya rage masa culotte kawai Da dan gudugudu yake kara taka matatakalar benen bangarensa har ya karasa bangaren da piscine dinsa take Ba tare da wani tsaye tsaye ba ya fada cikin ruwan nan ya shiga iyo tamkar wani kifi yana kai yana kawowa ba wani alamun gajiyawa a tatare da shi Ba ita ta kai gidansu ba sai can dare har wajen karfe tara abinka da jeji shiru garin sai kukan tsuntsaye sai jefi jefin samari da yan mata ana tadi domin sukan kai har goma suna tadinsu A hankali ta shige gidan nasu ta samu ta leka kanta Fitilar kwai a kunne, sai dai tana jiyo minsharin Abansu dan haka a hankali ta kutsa ta nufi dakinsu yan matan gidan Mahaifiyarta ta gani zaune saman abin sallah, da alama ita take jira duba da irin yanda ta tsareta da ido Jiki a sanyaye ta karasa kusa da ita kanta duke ta ce" ANNA Bata amsata ba sai kureta da ta yi da kallo, Ta jima duken nan, aman bata mike ba domin ta san wani abu guda da mahaifiyarta keda na buzaye tamkar wata yar gidan sarauta koda yake du buzuwa ko buzu haka ne dadaya ne basu da shi wanda mutane ke jifansu da sun cika *Ashak* , Can kamar ba zatai magana ba ta ce" kin ga, ko wani hali zaki shiga, ko wace rayuwa zaki fuskanta *AGAISHAT*, ki guji sabawa mahalicin ki, ki rike mutuncin ki , ki ci gaba da hakuri watarana sai labari Kanta take gyadawa, kuma wani dadi ta ji har cikin ranta, ko ba komai ta san a duniya bayan baba Sofo Annartama bata kyamatarta, tana kawar da kai a lamuranta ne dan gudun fitina, irin yanda Abanta ke binta da shari kwararo kwararo ya sa mutanen garima haka, ba mai kulata da daraja, ko magana za.ai mata ba.a mata ita a mutunce, ya kasance ko gaishe da mutun ta yo sai ya yi mata yatsina domin Abanta bai barta haka ba har shari ya yiwa annarta kan cewa ko dai wajen baba Sofo take zagayawa gannin irin yanda ya damu da ita ? Wannan wutar kafin ta mutu sai da aka sha tashin hankali, baba tsoho ya yi kuka sosai aman bai daina kula Bak'a ba domin tana da mutunci yarinyar, shi Allah bai azurtashi da yin auren bama domin bashi da lafia ko ya yi ba anfani hakan ya sa yake jin yarinyar tamkar yar da ya haifa, itama tana mutunta shi tamkar mahaifinta Mamanta na gama fadar haka ta yi shiru kanta itana a saden tamkar tana gaban sarakuwarta A hankali ta mike ta nufi dakin su Tana zuwa ta tarar du sun yi baci abinsu dan haka ta dauro alwallah ta shige ciki ta tayar da sallah ta shiga ramuwar wa.inda batai ba , tana so du rintsi ta ringa samun gurin sallah sai dai tana tsoron mutane da kwagirar su, yanzu za.a wulakantata dan haka take bari idan ta zi gida sai ta yi wanda bata samu ta yi ba Tun karfe takwas na safe Aba ya fice bayan ya canza rawaninsa daga baki zuwa maroon turkudi sabo fil, ya sayi tufafi ya sayi rawanininka harda waya, ya fito sabo kudi sun fado shikennan a haka zai fada su tamkar wuta shima ya dankaro aure daga an cinye kudin shikennan ta gudu abinta Bai jima sosai a wajen ba ya dawo, Daidai lokacin Anna na fitar da dawar masararsa a ruwa wace ra jika dan tana son yin garin tuwo Bai yi mata magana ba ya zarce dakinta dake baban daki idan ka cire nasa a gidan, daman dakuna uku ne, da nasa da na Anna da na yan matan gidan Bai yi wata wata ba ya shiga kwasar kayanta yana kaiwa dakin yan matan yana jibgewa gefe guda, Ba wanda ya tanka shi ko ya yi mamakin lamarinsa domin sun san halinsa, haka yake du idan zai yi aure dakin mahaifiyar su yake fitar da ita ya hadeta da su ya kawo amarya, bama zai barta a dakinta ba sai dai ya hade su ya kawo amarya su sha shagalinsu ba wanda ya isa ya yi magana yanzu zai cici masa uwa ko waye Ko kallo bai isheta ba, don ta daukarwa kanta alkawarin in dai ba mutunci ne lamarinsa toh ba zatana kai kanta yana wulakantata ba gaban yayanta. Sai da ya gama fitar da komai kafin yake fita ya shigo da magini Sosai aka gyara dakin ya yi tas da shi Tare suka fita , sun jima sosai kAfin yake dawowa Wannan karon kuwa masu shigo da kaya ne Mariama dake wanke fuskarta bayan ta shafa kurkum ta yi tsai tana bin kayan da kallo, A gaskiya siyayar idan ka yita a kauyen ka isa ne, tun daga gado har kayan abinci na gayu ya kwaso abinsa sai dai abin haushin babu rabonsu a ciki na amarya ne, domin idan ka auri jar buzuwa ko duniya zaka kai gidansu nasu ne ba za.ai mata komai ba sai dai a kawo maka ita daga ita sai butarta (a kauye fa kar a ce inji sajida🤣) Sai da suka gama kawo kayan tsaf Mariama ta je faban mahaifinta ta tsaya masa kerere a gabansa, somin kuwa in dai haihuwar rashin mutunci ne ya haifa Mariama ta isa ta iya tsayaya tamkar mahaifinta Ido tar cikin nasa da yaran buzanci ta ce" Aba ya haka? Na ga ka fara kwaso kaya alamun aure zaka yi? Ya baka fitar da mu ba? Baka ba anna kudin siyayar kayanmu ba? Kun san wasu iyayen sun fi son yaya masu tsayayar nan, domin Aba yana dan shayin lamarin yar tasa domin a yanda yake gani tama fi shi rashin mutunci dan haka ya dan gyara rawaninsa irin zai yi magana ya ce" wani siyaya kuma? A sanina cikakiyar buzuwa ba.a yi mata kayan daki? Ta yatsina bakinta ta ce" sai kuma cikakiyar buzuwa ana yi mata sutura Karya ne Mariama, ya fada yana matsowa kamar zai doke ta, ya ce" ku ne yayan zamani kuke zuwar mana da abubuwan da suke neman fin karfin tunanin mu, ko uwarki haka aka bani ita, haka ake kai ku daga ku sai turkudin amarci da buta, kudin auren ku kuwa mu iyayen ku ke siyan maku kadara mu ajiye maku a nan wanda idan kun waiwaya zaku ji dadin su Wani malalacin murmushi ta saki tana kallonsa Ya ci gaba da fadin" ke da kin ga minister ne ya turo a nemi aurenki, ya saya maki komai, sannan ke da auren wata shida ne zaki yi ki kwashe komai ki dawo mini mu more da kudi? Tar ta kara saka idannuwanta cikin nasa kafib take juyowa ta ga mahaifiyarta ta fara daka dawar da ta wanke ta baza a rana ta sha iska tana so ta mayar da ita gari kennan , ta kuma kai dubanta wajen yayarta *BAK'A* dake ta dirzar wankin yan matan gidan harda na su kanenta ita dai burinta idan sun tashi su bata konce, ta kuma kallon mahaifinta dake kokarin shi dole sai ya yi mata wayo, wai wani harda cewa wai ya siyar masu kadara, shi? Kudin aurwnsu bai taba wata a hannunsa ba komin yawansu zai kashe su ne ya dawo talakansa marar mutunci, yan yatsunta biyu ta hade ta yi tap tap da su suka bada dan sauti kafin ta ce" ka kirga kudi, ina so ka bawa Anna kudi har million shida a cikin kudin da ka karba na auren mu domin na sani cinikinmu kake tamkar abin siyarwa baka amsan kasa da goma, ka bamu shida mu je birni tare da Anna mu siyo kaya mu dawo idan baka yi haka ba zan shiga duniya na saka ka a matsala kai da wanda ya kawo kudin aurena, ka san ni horonka ce Yana tsaye bami bude har ta fice a gidan, kallonsa ya dawo wajen Anna, da sauri ya karaso ya ce" kina jinta kika yi tamkar baki gani bayan kin san tana jin nauyin zuciyarki? Ko ke kika kitsa mata a taru a cuce ni? Har million shida? Ai kudin sun kusa karewa idan na baku haka! Bata bashi amsa ba ta ci gaba da dakanta , nan ya juya wajen Agaishat ya ga shi take kallo Ke dan ubanki daina kallona da wasu tula tulan idannuwanki masu kama da na mayu, shegiya da aka kwaso cikin ki a waje aka yayaba min, dan bakin jini ko almajiri na yiwa tayi guduwa yake, zan zo in kwakwale miki idannuwan nan in baki a hannayen ki ki je ki kaiwa tsohon dan iskan nan da kike zuwa kina wuni wajen shi wama ya san ko me yake maki a bukar nan Da sauri Annan ta juyo wajen shi, ta kai dubanta wajen Agaishat da ta sada kanta jikinta na bari, tausayin yarinyar ya kara dirar mata, nan ta kara gane shi ya sa idan ta fice take cika dare dan kar ta hadu da mutumin dake mahaifinta aman ya zamo makiyinta , ta rasa da wata kalma zata kirayi mutumin dake miji a gareta, ta san ya yi karatu, sai dai son kudinsa ya fi imaninsa yawa A hankali ta ce" ki je kawai zan idasa maki aikin Da sauri ta ajiye wankin ta warware mayafinta na bakin turkudi butubutu da shi ta yane jikinta gaba daya ta fice har tana hardewa tana waiwayen gidan nasa Bakin wata bishiyar mangwaro ta zauna ta fashe da wani matsanancin kuka mai karfin gaske Ku mu je a labarin Bak'a ce na sajida 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 6⃣ Kuka take tana murza goshinta a kan cinyarta dake lulube da turkudi, hawayen nan ya jika turkudin ya yayakune sannan ya gogun mata a fuska ya kara rinar da fuskar ya kasance wani waje ya fi wani wajen duhu sosai fuskar du ta yi jirwayi da ita Sai da ta ci kukanta har kanta ya fara ciwo kafin take yin shiru, mangwaron nan ta kuma kallo gannin du ya yi jajajir ya nuna ya saka ta mike ta gyara zaninta da kyau ta kama kokarin hawa , Da kyar ta hau bakibakin ta kamo wa.inda ke kusa ta tsintsinka ta diro ta zauna nan tana gogewa da hannunta sai kuma ta sha abinta, yau bama zata iya zuwa wajen tsoho ba ta san yana da ruwa goronsa kuwa ta kai masa gobe sai ta yi safiya ta je wajen shi Wardugu, yanzu yanzu? Kansa ya dafe ya ce" Ayya ko kin fasa tafiyar ne? Da sauri ta mike ta nufi dakinta tana dafe kanta, yaron nan akoy kagauta , bashi da hakuri yanzu in ba rigima ba a kai tsayen nan ya zo yace su yi tafiyar da a yanda ake bata labari garin can cikin jeji ne? Aman ba komai irin yanda take mafarkin mutumin nan abin ya tsaye mata a rai, tana tune sun yi da shi idan yaro ya samu lafiya sai ta bashi salama da abinda ya sawaka sai dai ta zo tana yiwa Wardugu magani da magungunnan aka tashe su daga garin aka maido su Capital tun daga shi bata kara ganninsa ba domin ta neme shi sosai, sai kwanan nan take jin lanarin yanzu tsufa ya kama shi sosai baya yawo yana garinsa na haihuwa harma an fada mata sunnan garin , tana son sauke nauyi domin kuwa tun daga kan maganin wajensa Allah ya aminta wardugu bai kuma Huka ba sai tana gannin haki ne ta je ta sauke ba wanda ya san gawar fari Nade ta fito da lifaya mai ruwan ja da kyalkyalin zaiba, lifayar sai baza kanshi take , Ayya ta kwana biyu a duniya aman karshe ce, akoy iya ado da sannin hakin turare, idan ka ganta sai ta birge ka gata da saka zinare tamkar ba da kudi take siya ba, danta ya bata damar murza mulkin da ta ga dama Tafiyar manya ba.a kwasan tufafi, mai aikinta baturiya ce ta fito da wata yar valise (yar akwati) yar karama wace a ciki ta saka du wani abin bukatarta ta nufi kofa dan kaiwa cikin mota Gaba ya yi yana amsa waya da aminiyarsa, kawarsa, wace du duniya itace babar kawarsa sai wa.inda ba za.a rasa ba, itace basa fada, ta iya tafiyar da lamarinsa ta iya zama da shi , sannan du irin yanda ya ki jinnin jajayen buzaye ita wannan baya iya kyamatarta , ba.a shaifar mutun aman shi zai bigi kirji da halayen *ALHINAYETT* Kana nufin yanzu yanzu? Bama zan yi maku bankwana ba? Wardugu ya ce" Alhinayettt bafa wani jimawa zamu yi ba, ke dai ki yi mana adu.a Yana fadin haka daidai yana zama cikin motar Hilux tamkar wani daki tana fa fadin waje, Sai fa ya gama wayar ya dubo AYYA da ta tsura masa ido Kallonta yake da alamar mamakin kallon domin irin kallon nan ne na tsare mutun idan ya yi karya Bakinta ta dan turo ta ce" kuma ka ce ba budurwarka bace, mutunci ne bakwa wata soyaya da ita, Murmushi ya yi do.in daman ya saka a ransa wannan ne, ya dan sasauto ya riko hannunta ya ce" Anna, aa, Alhinayett aminiyata ce, wace bani da amini ko aminiyar da ta kai ta Yatsina fuska ta yi ta ce" karyar banza wai aminci mace da namiji ? Ai ba shi sai idan soyaya ake Kawar da kansa ya yi ya ce" kin ce a lokacin da ya baki magungunnan da aka dura min ma tsofo ne, kuma har yanzu kina da tabacin yana raye? Ni din ma fa na jima a duniya Murmushi ta saki ta mika hannayenta masu saye da zobunnan zinariya ta dankwashe masa kansa dan ta san yana so ta yi zuciya ne ita kuwa ba zata yi ba, halayensa tana gannin sai dai ta fada masa domin tun bai san kansa take tafe da shi ba Sun Dauki hanyar airport dan zuwa garin Agadez daga nan kuma ya nemi abinda zai kai su garin da suka nufa Mali yaro ne ke wasa a wajen auren kawar Walyn , Tunda ta shigo wajen wasan yake kofata da kiran General wande, Walyn kin fice yaro (Matar general), Tunda ta nemi wajen da tana iya gannin kowa kowa na iya ganninta ta hakimce ta dauki kafa daya ta dora saman daya, ta karkace kadan ya kasance dankareriyar sarkarta ta zinari ta fito sosai, ta dora hannunta guda saman cinyarta awarwarayenta ma suka fito radau da su, takan dan saki dan murmushi hakoran makarta su bayanna, ta dan juya ta kuma juyar da kanta tana karewa mata da yan matan wajen kallo tana auna su daya bayan daya, Kari ake masa na hauka aman hankalinsa du ya karkata kanta, ya sani ne udan ta zuge bakin wannan jakar nata mai shegen kyau sai ya yi kwasa, jakar a yashe take kusa da kafarta tamkar ba komai na anfani ciki bayan kuwa a cikinta kudane da dankara dankaran wayoyinta na kece raini A haka har aka fito daga salar isha.i bata mike ta je ta yi sallar ba suna zaune sun zagaye mawakin da yakan silalewa ya bar yaransa da basu san ciwon kansu suma ba ya je ya gabatar da sallah ya dawo ya dora daga inda ya tsaya Wannan dawowar da ya yi bai zame ko.ina ba sai gabanta domin ya lura yau yan mulkin ne, yan na isan ne, tana son nuna bambanci tsakaninta da sautan matan wajen, Yana zuwa ya shiga kodata, yana waketa, yana wake jarumtar mijinta Kanta ya fashe , ya yi gingirigin Ai kuwa ta dauki jakar nan ta yage bakinta ta shiga zuba masa masu aku wato jika goma goma tana dangalar masa tana yi irin bata san ciwonsu ba sai da ta karar da jimki biyu wajen ya cika da ihu wata kawarta guda na daukanta vidio dan ta tura mata A wannan rana an jima ana wasa wanda Walyn bata bar wajen wasan nan ba sai da aka gama sai da ta ga karyar ko wace yar karya kafin take mikewa ta dauki jakarta kawayenta masu mata fada suka biyo bayanta har sai da ta shige dankareriyar bakar motarta bayan ta wankesu suma da kudi ta tayar ta halba bakin titi a lokacin har karfe goma sha daya ta buga na dare Garin niamey capital ta niger du wanda ya taba shigota ya san gari ne dake baje ta ko.ina da polisai Basa wasa kame suke tun karfin su, in dai ka kuskura ka taka doka toh fa zasu damke ka ne ba sasauci Tukinta take cikin nutsuwa, Danja ce ta tsayar da ita bakin inda polisai shida ke tsaye suna duba takardun mota na mashin, da kuma takardar shedan kai wanene Hankalinta konce take jira danja ta saki domin ta san sun san number motar general ko sun kurbi giyar bera ba zasu tunkareta ba koda kuwa ta taka dokar domin ta tsira tunda ta hau motar *DOKA* gabadaya Kwonkwonkwon karar kwonkwasa motarta, Da mamaki ta dubi wajen Wani saurayin police ne fuskarsa daure tamau ba alamun wasa a tatare da shi Da yannayin rashin mutunci ta sauke gilashin motar ta sauke masa idannuwanta masu nuni da baka da wayo Shima fuska a daure ya ce" madame vous etes en état d'arrestation, veillez sortir calmement nous nous occuperont de la voiture (Madame mun kama ki ki fito cikin nutsuwa zamu kula da motar) Da mamaki take yi masa kallon sakarai, baki bude ta nuno shi da yatsarta ta ce" kai aman kai sabo ne ko? Waye kai? Ka san ko wacece ni? Sadowa ya yi sosai ya saka idannuwansa cikin nata ya ce" eh mun san ko ke wacece, umarnin mijinki ne in dai kika kai karfe bakwai a gari du wanda ya hadu da ke ya kai ki cel ki kwana da safe karfe goma a sake ki daidai gari ya cika kuma a rubuta a jarida! Dum dum dum take jin maganar tamkar saukar aradu, quoi? (What), ita? A cel? Prison! Ita Walyn? Wardugu wardugu ta fada tun karfinta tana dukan sitiyarin motar ta ......... Ohk 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 7⃣ Ita Wardugu xai yiwa wannan wulakancin? Ta kwana a cikin kaso, batai sata batai komai ba? Dan kawai ta cika dare? Wayarta ta warta a cikin jakarta ta shiga laluben numbersa wace ta sam zata same shi Ta yi kira ya fi a kirga daidai lokacin polisawan sun zagayeta tamkar dai ta yi wani gagarumin laifi Hanjaki kwonce ya daga domin lokacin yana hakimce kan gadon hotel din da ya sauka ita Ayya tana can gidan sarkin Agadez matarsa uwar gidan ce kawarta ta kusa sosai, shi kuwa ya ki sauka a nan ya je hotel , bayan ya gama harkar kasuwancinsa ne kiran Walyn ya shigo wayarsa, domin Wardugu na sana.a.o.i ya san dadin nema , yakan ce ba dole ya nema ba shi mai Ayya da Walyn Murya irin ta yan duniya ya ce" adibinira (wato matata ) (readers kar ku manta a wannan nvel yare hudu ne, buzanci, tubanci, french da kuma hausa ) Murya ta sasauta tana tura hannunta cikin kannanuwan kitson da ta sha domin dai tubawa basa wasa da kitso ta ce" Haba mijina ya haka wannan tsatsauran hukuncin? Murmushi ya yi jin yanda ta sasauto, kennan dai sai yanzu ta nufi gida ko? Muryarsa yanda take ya ce" hukuncin ya yi tsauri ne? Ko bai kai daidai da laifinki ba? Idannuwanta ta lunshe tana jinsa har cikin ranta ta ce" matarka guda a prison? Ko laifi na yi ina tunanin na fi karfin nan sai dai ka hukunta ni a gida a dakin mu a saman gadon barcin mu ka rungumeni ka matseni ka haukatani da lamuranka , na san ina cika dare kuma baka so aman mutun ai ajizi ne, ka yi mini uzuri Wardugu Murmushi mai sauti ya sakar mata, ya ce" bara dai mu gwada wannan idan ya so na dawo daga tafiar da baki tsaya kin ji ina zan je me zan je yi ba zamu yi magana Fashe masa ta yi da kukan kisa , ta ci gaba da lalaba shi dan ya yarda ya yi masu magana su sakar mata hanya ta karasa gida dare na yi Lumfashi ya sauke ya ce" ki bani daya daga cikin su Cike da murna ta mikawa wanda ya fi kusa da ita tana zabga masa harara Yana kara wayar ya kame yana sara masa tamkar yana gabansa Murya a kausashe ya ce" wasu sutura ne a jikin matata? Murya a ladafce ya ce" aa oga, mu mun isa mu kali matarka? Bamu kala ba bamu san irin suturar jikinta ba A ransa ya ayana han, kafin yake cewa" idan ta ki ta fito ku zauna da ita a nan har safiya ta yi , har karfe goma sha biyu na rana kowa ya kasance ya ganta, sannan ku gayaci jarida ku bada cikaken labarin abinda ya faru, kar ku taba jikinta aman bata wahala, ka rike wayarta a hannunka sai goben ka bata! Sannan kar ku nuna mata wasa idan ta so kawo maku tsayaya ku tsoratata da bindiga Da " a vos ordres ya amsa kafin yake katse layin ya saka a aljihun rigarsa Wa ya ga zafi biyu 🤣 Karfe uku ne fa na dare aman ji kake gam gam gam ana dukan yar kofar gidan nasa Da sauri *Tibillal* wato mahaifiyar su Agaishat mata a wajen *ALGABIT* mahaifin su Gaishat ta zabura ta kai dubanta wajen *AGAISHAT* dake zaune tsuru tun bugawar farko ta fara tana kallon kofar shigowar su Mayafinta ta ja da kyau ta fito ta nufi dakin mijin nata Tana zuwa ta tarar da shi a kwonce tamkar mai baci bayan ya farka ya yi tsuru daga kwoncen yana tsoron mikewa ma Girgiza kafafuwansa ta fara ta ce" Algabit, Algabitt, ka tashi ana ta buga gidan nan Hannunsa ya saka ya bige nata ya ce" naki na tashin, bayan a gari an san na amshi kudin auren yaranna , in na bude wani mugu ne fa? Koma waye ya yi hakurin safe mana aman a wannan tsofon daren? Ba zan bude ba! Gannin ya tashi sai balbaleta yake da fadan da hujojinsa na karya ta mike ta nufi kofar wanda ya saka ya hantsilo ya rarumi wukarsa ya ja tunga yana fadin" kar ki bude mana, koma waye a daren nan ba bakon alkhairi bane! Janye sakatar ta yi ta bude kofar, Fado mata ta yi a jiki tana kuka, jikinta du sai rawa yake, ga sanyin garin aman wata yar ficiciyar riga ce a jikinta, mutumin da ya kawota a rakumi ne ya ce" na ga gidan zan dawo da safe a bani salamata! Da tashin hankali Anna ta janyota cikin gidan tana ta kokarin kara dagota tana duba fuskarta dake da balshe ko.ina a tsannanin tashin hankali ta ce" *FATIMATA* fatimata , fatimata Gaba daya mutanen gidan suka fito jin muryar Anna cikin tashin hankali Da sauri Algabitt ya karaso ya janyota ya ce" Ke Fatimata, meye haka? Daga ina kike? Ya haka a tsiyace jiki a lalace? Ina mijin naki yake???? Dago kumburanrun idannuwanta ta yi ta sauke su kansa, da haushi haushi ta budi baki tun karfinta ta ce"'""" Aba, sai na kashe shi, kuma ko zaka kashe ni sai na hana ka kara bada kannuna a irin auren da ka yi mini! Idannuwa ya zaro ya daga wukar nan nasa ya. Nufota ya saro daidai ita sai aka yi rashin sa.a Anna ta saka hannunta ta tare wukar ta yi mata muguwar sara a gefen hannunta ta yanketa sosai nan da nan jini ya bale Ihu yayan suka kwasa, da sauri mariama ta karbe wukar ta yi jifa da ita ta hayayako masa da mugun bacin rai da nuni da zata iya aikata komai ta ce" ka je, kar jini ya biya jini! Juyawa ya yi da sauri yana mamakin Kaf yayansa idan ya yi magana a da jiki na bari suke aikata abinda yake so aman kwanakin nan yana haduwa da hari kala kala da wajaje daban daban a cikin yayansa bale Mariama yarinyar na da zuciya ........ Labari bak'a ce labari ne kirkirare bisa lamarin da ba kirkirare ba, labarin yana tafiya ne bisa gaskiyar lamarin abinda ke faruwa , tabas na shiga kuma sai na fada......ku mu je zuwa a labarim bak'a ce in sha Allah 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 8⃣ Yana fita Bak'a ta cire daurin dake kanta ta daure hannun mamansu da fan kwalin du suka zauna jigum jigum suna kallon Fatimata A hankali ta dora kanta kan cinyar mamansu da take jin zuciyarta na yi mata nauyi sosai ta ce" a ranar da aka dora ni saman Amale (Rakumi) daga ni sai mata hudun da suka zo a matsayin fagin mijin da aka aura mini muka tafi Mun shiga garin agadez daga nan muka dauki hanya muke tafia tamkar ba zamu tsaya ba Sai da muka je Damagaran daga nan muke mike muka dauki hanyar kano Muna zuwa kanno muka kwana guda muka dauki motar asuba suwa Abuja Tafiyarmu tamkar ba zata kare ba, tsakanina da su ido ne su basa jin yarena nima bana jin nasu ya kasance muna tafiyar kurame ne sai dai abinda na lura da shi tamkar masu jin haushina domin ko abinci zasu bani sai dai su wulo mini su fadi wata kalma sannan su yi mini nuni da in ci Ba mu mu isa garin nan ba sai da safe domin da mukai dare muka tsaya muka waye a wani garin kafin mu karasa Gida ne tafkeke, ya tsaru, ya hadu iya haduwa Muna zuwa kowace ta yi tafiyarta aka barni a wani tankamemen falo ina zaune ni guda Ban jima sosai ba na fara gannin wasu mata masu kyau suma kowace ta sha kwaliya sai baza kamshi take sun fifito sun layu saman kujera gefe da gefena hakan ya saka na takure waje guda Ba.a jima ba wanda aka aura min da sunan mijina ya fito ashe yana cikin dakin du zaman nan da na yi ya zo ya zauna saman kujerar dake kallon tamu ya dora kafa daya kan daya Walahi Anna mutumin sam ba annuri a tare da shi, mumuna ne, garjejen kato ne fuskarsa ba anuri ba fara.a ba haske ko kadan a nan ya kuna taba domin ba sigari bace taba ce ya kuna ya shiga ja wace nan take wajen ya garwaye da warin kwaya Wasu maza ne suka fara shigowa, suka zauna suma inda suke hangen mu da kyau abin mamaki matan nan sai su ringa mukewa daya bayan daya su jujuya gaban mutanen nan wasu har su dakan masu duwawu su mamatsa a gabanmu a gaban kowa shi kuwa yana hakimce idan mace ta yi maka sai su hau ciniki cikin jarshen turanci a dauki mace a tafi da ita kwana wato Bariki Nan wani yace wannan fa? Wato ni domin sun ga sabuwa ce a wajen Da sauri na mike domin nunoni ya yi kafin yake yin maganar, koda ban ji me yace ba idannuwana sun nuna mini abubuwan da suka faru na ga komai na gane komai Magana ya yi masu wace ban san me yake nufi ba suka gama kasuwancinsu ya cashi kudinsa sosai kafin suke tafiya Sai da ya gama shaye shayensa ya taso kusa da ni sosai da muryar mashayi ya ce" ke fa sai na yi maki filafila dan kuwa an caje ni kudi kafin a bani ke kuma dan iskanci aka kawo ki daga ke sai wannan bakin kayan Tashi ki tube Da mamaki nake kallon shi, in tube, wai ina ne nan? Me hakan ke nufi? Matan nan su waye? In tube haka kai tsaye ai ko matarka ce ni koda mun saba da sannin juna fitsara ne gatsal ka kale ni ka ce mini tube Mikewa na yi da yarena na rufe ido na shiga zazaga fitsara ina son sannin inda ya nufa Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya kafin take kara sakin wani kukan mai karfi ta ce" Anna matan nan da suka fita bayan ya amshi kudaden karuwanci da zasu fita su kwana da karti ashe gaba dayan su suna zaune a matsayin matansa mace har bakwai ni ta takwas cikinsu ba daya ta yarwa sannan ba daya da ta san hanyar gidansu A wannan ranar da katsa ya dake ni kafin yake zuwarmini da wata irin sufa yayi anfani da ni ba imani yana gamawa ya wawatsa kafafuwana ya goge gaba daya najasar nan ya shafe a fuskarsa harda jini jinin nan ya side hannayen nasa ya fice Anna a wannan ranar.kafin gari ya waye sau tara yana zuwar mini Mariama ce ta dauko kwan fitilar sosai ta haska wajen kafafuwan Fatimata, ruwa ne ke yawo wanda ya saka Mariama cewa" Anna ruwan nan kuma na menene? Fatimata ta ce" fitsarina ne ba ruwa ba, haka fitsari ke zubar mini bama na sannin yana binna Anna ta fashe da wani irin kuka kafin ta ture kan Fatimata ta mike ta yi dakin yaren da sauri hannayenta duka biyu saman kanta, *YoYo, YoYon fitsari Fatimata ke yi*! A wannan rana yanda suka ga rana haka suka ga dare inda suka cure gaba dayansu waje guda ba mai yiwa yar uwarta magana sai dai suna bin juna da ido , nan Mariama ta mike ta dauko wata leda baka baba ta shinfida ta dauko zani ta shinfida ta kallo yan uwanta ta ce" ke fatimata taso ki kwonta saman nan, ke Agaishat(Bak'a) tafi wajen Anna, kuma ku taso mu kwonta dare na tafiya kar safiya ta yi mana a nan A hankali ta samu ta lalaba ta hau, suma du suka samu waje suka kwonkwonta ba dan zasu samu yin bacin ba, sun dai yi zuru ne domin Fatimata bata gama basu labarin irin ukubar da ta sha ba aka ga fitsari na binta hakan kuwa ya tayarwa da Annar hankali bata ma tsaya ta ji sauran zancen ba Anna ce duke kanta kasa ta kai sujada tana ta sheka kuka ta ce" ALLAH ka san wacece ni, kai ka halice ni, ya Allah ina cikin jarabawarka tun daga yannayin aurena har zuwa yau, na rasa me ke daure da ni da wannan mutumin ainahi Allahna idan ba a cikin sallah ba bana iya tuna wacece ni, menene tarihina, ina da yan uwa ko haka nake ni daya? Bana son a yi min maganar ko wa ya kawo min zancen zan nuna bacin raina ne, Allah yayana, ka bayannar sauran, wa.inda basu da lafia ya Allah ka basu lafia, wa.inda yake niyar aurarwa dan samun abin duniya Idan da alkhairi a cikin auren ka tabatarda, idan kuwa ba alkhairi bane Allah kai ka yi shi ka hana, ka hana ya Allah Allah sannan ka yaye min duhun dake cinkushe min ganina Ta jima tana kai kukanta wajen Allah kafin take mikewa ta yi tahiya ta salamce ta dora adu.a tana ta yawaita istigfari domin ba abinda ke saurin yaye kunci irinta Da safe tana tashi ta dauki sansani (tabar buzaye) a cikin nata ta matsa a bakinta ta yane jikinta ta buga safiya ta fice a gidan Zugum suke ba mai yiwa dan uwansa magana har wajen karfe tara Anna bata dawo ba, Aba daman tun cikin daren nan ya fice basu san ina ya kwana ba sannan bai dawo ba, sun zubawa sarautar Allah ido ne kawai A hankali Bak'a ta kali gorin tsofo, ta mayar ta kule a harshen zaninta a ranta take ayanna bawan Allah ko a wani hali yake? Ko an dauko masa ruwa? Tabas yana cikin damuwar rashin ganninta yau har za.a kwana biyu, sai dai ba zata iya fita ta bar gidansu a wannan halin ba, a hankali ta rike goron ta ce" sofo ina nan lafiata klau, ka ga na saya maka goro ma kar ka damu ina nan tafe wajenka ..........inna Anna ta tafi????? Gyara kimtsi, mai zamani dan sarki jikan sarki, Buzu jinnin sarauta, yaro mai zamani, taka lafia bijimin sarki, taka lafiya gagara gasa, kai ne na uku baban Rabatima, ka shigo a hankali yarima, taka sanu sanu sarkina , Kirarin da jakadiya ke yi masa kennan tunda ya tunkaro dakin mahaifiyarsa, dan dakatawa ya yi har ta yi gyaran murya kafin yake saka kai da salama a bakinsa Dago kanta ta yi tana murmushi ta amsa shi, a hankali ya karasa yana wata irin tafiya idan ya daga kafa daya kafin ya daga dayar sai ya jima Dukawa ya yi har kasa kansa kasa ya ce" ta gode Anna, ta gode Amy (Wato mahaifiyar Wardugu aminiyar matar sarki....da Amy suke kiranta bisa umarnin mahaifiyarsu,) Murmushi take sakar masa kafin ta ce" oh son tashi mana, amynka ce fa ko dan ka daina zuwa wajena ne? Yana murmushi ya mike ya zauna saman kushin dake wajen cikin nustuwa suka shiga gaisawa da harsen freinsh domin ita ce kawai yaren da zasu yi su jima suna hira cikib gane abinda suke fadawa juna Dan jim ya biyo baya kafin yake cewa " Amy ya labarin Oga ne? Na yi na yi ya siyar min da wata mota aman da yake yan rigimar a kansa cewa yayi aa motar ba ta yara bace, ki ji fa Amy Dariya suka saka gaba dayansu, Ayya ta ce" Wardugu, Wardugu baya jin magana Aghali, sai hakuri da murdaden halayen Wardugu Mahaifiyar Aghali matar sarki ta ce" Kawata, wai ina labarin aban Wardugu ne? Ni kam ina mamakin lamarinku, kawai daga wannan dan laifin? Ayya ta dago tana kallonta, a ranta ta ayanna ban ga laifinki ba, ku baku dauki haka a matsayin laifi ba, A fili kuwa ta ce" manta Murmushi Mahaifiyar Aghali ta yi, Ayya akoy mulki wannan da gidan sarauta take da an ji jiki domin mace ce mai mulki da isa, ga jan aji, da yake an dauko hirar da bata so daga haka ta katse hirar ta mike tana yi masu salama dan tana son shiga ciki ta kirayi number Wardugu rabonta da shi tunfa suka karaso jiya ba shi ba labarinsa ...........rashin Comment ne kawai zai saka ni daukan matakin siyar da novel din nan ko na tsayar da shi, 😊 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 9⃣ Ayya na zuwa dakin da aka sauketa zauna ta jinginar da bayanta jikin kujera ta daga kanta sama, Ta jima tana tunani, kafin take sauke ajiyar Zuciya a fili ta ce " *MARAHUT*, ina ka shiga? Ka san komai ka tarwatsa rayuwarmu, Marahut ina tausaya maka sai dai mutuncina darajata ba zan yarda ka zubda mini ba! Ka zabi wancen rayuwar ko? Ba komai ka je sannu duniya zata koya maka hankali, Ranta ne ta ji yana suya, yama aka yi ta tabo mata wannan mikin, ta sani da gangan ta tuno mata da maganar domin ta fi kowa sannin abinda ya faru, ita kadai sai Wardugu suka san takamaimai abinda ya faru aman zatana tuno mata da shi , ita so take sai ta yi hakuri bata san ta rufe babinsa ba kuma ko da jaraba sai ya saketa dan bata fatan idan ta mutu ya kasance shine alwalin gawarta (Toh fa😳 tubawa akoy zuciya) Aghali, dan me ba zaka kara aure ba? Matanka biyu yarka daya mace sai matan daki , ko a cikinsu har yanzu ba wace ta samu ciki bayan ina kula da irin zubin da ake maka ana canzawa du wace ta kwana biyu, ko dai baka zuwa inda suken da gaske? Domin na ji kishin kishin cewar wannan matar taka ta shanye min kai, Mahaifiyar magajin sarki ce ke fada kan ya ki karo aure bayan tana son ya tara yaya Murmushi ya yi ya ce " zan kara aure, ki kwontar da hankalinki, Ajiyar zuciya ta sauke kafin take miko masa yar akwati tana murmushi ta ce" ka ga Amynka ta kawowa wannan mumunar ( wato yarsa jikarta) Hannu ya saka ya bude ya gani, sarka ne da yan kunaye na zinari masu kyau sosai kirar yara, murmushi ya yi ya ce" zata je ta gaisheta sannan ta yi godiya........ wannan kennan Sai da ta bude lulubarta suka ga mace ce bayan ta fada masu ita mahaifiyar Gaishat ce , suka je suka shaidawa sarki ya bada izinin a shigar da ita bangaren Gaishat din yana mamakin zuwanta da fadawa zuciyarsa ba lafia ba domin shekara kusan takwas da aurensu bata taba takowa ko aiko da kannen Gaishat din ba duda tana yarta ta fari, itama bata wani zuwa gidan du ta takura rayuwarta da tsoronsa ta mayar da kanta ta daki duda kuwa irin yanda yake daukaka martabarta fiye da iyayen yayansa Tana shiga dakin ta nemi waje nan kasa ta zauna ta sada kanta , da kujeru da komai aman ta fi fanewa zama a kasan nan Da sauri ta fito jin sakon Sarki wai mamanta ce ta zo Tana fitowa ta karaso da gudu ta riko hannayenta a rikice ta ce" Anna lafia? Anna wa ya mutu? Anna na shiga uku me yake damunki? Anna me ke faruwa? Me aka maki Anna? Anna..... Shiiiiit anna ta fada tana dora yatsarta saman leben Gaishat, itama tana kare mata kallo, yarinyar bata wani karu ba a jikinta na da, sai dan girma daga fuska da ta kara, duda jikinta bai nuna alamar wahala ba aman tana da rama, kanta daure , Kunyar Gaishat din ta ji ta kamata, dole ta rikice domin bata taba zuwa alkhairi ko tashin hankali ba, itace ma ke yin kokari idan ta san Abansu baya gari ta leko a tsaitsaye ta koma shima ba wani zantawa suke sai dai su bi junna da ita Tunani ta afka shin fada mata zata yi ko kawai ta yi shiru ta juya A hankali Gaishat ta dago habar mamanta, dara daran idannuwanta na gado ta saka cikin nata ta ce" Anna, me ke damunki? Ki fada mani kin ji? In sha Allah ko bani da maganin damuwarki zan taya ki da adu.a Anna ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Gaishat, Algabitt ne....ya samarwa su Mariama mazajen aure wa.inda bama a niger din suke ba, kin san bani da labari tghmass ita a niger din ma aka bayar da ita, jiya Fatimata ta dawo, mariama fatimata ta kamu da cutar rashin rike fitsari , kin san ba maganinsa a kauye sai asibiti, baki ga fatimata ba, ta dawo wata iri, Ga irin tsanar Agaishat (BAK'A) , ya sako yarinyar a gaba tamkar ya kasheta dan ya san gardawan da yake zuwa da su dan zaben mata ba zasu zabeta ba, shi ya sa nake kara barinta da datinta, mai yiwuwa ita ta tsira daga muguwar rayuwar da yake saka mini yaya Shiru ta yi kanta sade tana gursheken kuka daga ita har Gaishat din, Ajiyar zuciya Gaishat ta sauke ta ce" Anna zan zo gidan kin ji? Sai mu samo abinda ya samu mu samu shiga asibitin Ido Anna ta zaro ta ce" ta yaya zaki fita Gaishat? Gaishat ta yi murmushi ta ce" Anna, ki daina damuwa da damuwata, ni na dorawa kaina, tabas Aba ya yi auren dole da mutumin da bana so, mai mulkin garina aman shi mutumen jira yake in nuna bukatata a wani abin jiki na rawa yake yi min ko menene , bana tunanin fita zata zama damuwa tsakanina da shi Anna ta sauke ajiyar zuciya, ta dago habar Gaishat ta ce" me ya sa toh ba zaki kyautata masa ki kontar da hankalinki ba? Shekarunnan ba fa kwanaki bane, ya ci ace kin zubar da komai kun fuskanci juna, ke Allah ya taimake ki kina cikin konciyar hankali kar ki bijirewa Allah mana Gaishat ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Anna na kara nade jikinta da fuskarta wato dai tafia zata yi, ita ba zata ki su dawama a nan suna hira da mahaifiyarta ba Tana ji tana gani Anna ta yi mata salama ta fice a gidan tana fatan kar ta hadu da wani a kusan gidan yarta ta fari , haka kawai take jin kunyar haka ....... Da dare, bayan ya gama salama da kowa ya nufo dakin mai motsa zuciyarsa, ya sani ne ta san sarai itace da shi aman taga damar ya tarar da ta rufe kofarta Ga mamakinsa yana taba kofar ya tarar da ita a bude, Turawa ya yi a hankali ya shiga da salama a bakinsa Kanta ta dago duda tana jin kunya , ta yi kokari ta amsa salamarsa cikin nutsuwa tana dubansa Da sauri ya karasa inda take zaune, da alama har wanka ta yi, na menene? Taba jikinta ya fara yi hankalinsa a dan tashe ya ce" GAISHAT baki da lafia ne? Me ke damun ki? Dan bakinta ta turo, kafin take dauke hannun nasa ta kara turo bakin, murya a matukar kasalance ta ce" me ya sa ka zabi aurena ta hanyar baiwa Abanna damar ya ci gaba da tafka tsiya a cikin garinka? Dakatawa ya yi, ya yi tsai yana kallonta, a hankali ya rungumeta a jikinsa ya ce" ba dai za.a yafe min ba du irin hakurin da nake bayarwa? Ki gane dan adam nake mai cike da izgili da sabo a doron kasa, Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" ina so ka bar ni na je gida Da sauri ya zabura ya cikata yana kallonta, muryarsa na rawa rawa ya ce" zaki tafi ki barni kennan? Yau kin fitar abinda ke cikinki shine zaki yi nesa da ni? Me yasa ba zaki yi mini adalci ba? Ina sane da du ranar da zan zo gare ki sai kin sha madaciya dan kar ki haihu da ni, na so daukan mataki a kanki aman bana iyawa Gaishat, ki yi mini adalci mana Dora dan yatsarta ta yi saman lebensa jajaji abinka da jan buzu ruwan sarauta ko na kauye dawisu ne, ta ce" zama da kai yanzu na fara, ina son zuwa gidanmu ne dan kanwata ba lafia, muna son kaita asibiti, ka bani dama da ikon da zan yi bajinta a lamarin Ajiyar zuciya ya sauke, ya rungumeta sosai har kamar ta yi ihun zafi, ya mikar da ita yana kallonta ya shiga warware lafayar da ta yane jikinta yanai mata kallon maita, haka ya idasa shigar da ita uwar dakanta cike da zumudi, wa ya isa in ba ita ba? Ita kadai yake tardowa har dakinta, hajia Gaishat mai sarkin garin *TIMIYA* Kamar yanda ya yi alkawari haka ya bayar da rakumi har goma, ya bata kudi masu yawa ya lamunce mata zuwa gari dan kai kanwarta asibiti inda gari ya dauka ana ta lale lale gimbiya ta karbi soyayar sarkinsu, abinka da kauye har yar salah aka yi ta murnar hakan ................... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣1⃣ ........Niamey....... Gidan Wardugu Kawata, dan Allah wai da gadke kike? Gaki ga yan kaso wa.inda suka aikata mugun laifi? Gaskiya oga ya san kan mugunta Walyn ta ja tsaki ta ce" ke, a dakin nan a nan suke fitsari, mata sai kawai ki ga an dage buje an tsirara fitsari a tsaye, basa kunya basa kyankyamin wajen , kai gaskiya Wardugu ni da shi akoy tashin hankali, ba ni ya wulakanta ba, walahi sai na rama! Me zaki yi masa? Wardugu ne fa? Kin manta waye shi? Ko mu da muke gari bama rayuwa da shi mun san waye shi, koda kina kema jinnin tubawa ba lale ki iya da rigimarsa ba, ya hada abubuwa da yawa ne, kin ga shine da daya kwalin kwal a wajen iyayensa, shine Wardugu mai sunnan rikitatu a cikin ku, shi ne Batube, kuma shi ne Soja! Wardugu kakarfa, tsayaye, isashe, hamshakin...... Ke meye haka? Walyn ta fada tana kallon kawar tata, Ta ce" ya zaki tsaya kina koda min miji sai kace wata mai son min miji? Toh bara ki ji mu a yarenmu ba.a yiwa mace kishiya sai ta cika wa.adin yin hakan, duka duka shekarana biyu da aure da mijina, ko na kai shekarun da yana iya kara wata Wardugu haramiyar wata mace ce a nan duniya, ban ki ba lahira idan ya dace da aljanna! Murmushi ta yi tana kallonta ta ce" dadina da ke saurin hawa , toh yi hakuri ni ban kai abin can ba .......... Bakinta ta tabe ta ci gaba da shafa cream dinta kan kurajen cizon sauron da suka yi mata cin balaki a cikin cel din nan, rabonta da ta saka kafarta kofa tunda abin nan ya faru, gashi ta rasa Wardugu a waya kwata kwata, ! Dogo ne fari kar, datijo ne christa sunansa Docter Lucien, kwararen likitan mata kennan wanda ya karanci abin kuma ya lakanta, Allah ya taimaki su Anna sun samu gannin Docter Lucien a dasha kuma tausayin irin ciwon da ya gani bayan ya sha fada ya karbe su ya shirya shiga tiyata da ita a washe gari wanda cikin ikon Allah sai da ya dauki awa shida kafin yake fitowa daga dakin tiyatar da ita shi ya hada zufa hakama masu kama masa wanda ba.a jima sosai ba aka gurgurota a gadon mararsa lafia aka kaita dakin da ake kontar da masu yoyon fitsari Jigum suke zaune suna mamakin wai asibiti ce haka, su kam tunda suka shigo garin a tsorace suke da yannayin tsarin gari, gini ne kala daban daban bene kai kasa na cin kudin masu kudin birni .... A hankali ta shiga bukar tana dube dube kafin take kallo shi, a kwonce yake , idannuwansa a rufe kamar marar lafia Da sauri ta karasa ta ce " Sofo? Firgigit ya buda idannuwansa ya sauke saman kanta, Kokarin tashi yake wanda da kyar abin tsufa ya samu ya zauna yana kallonta, murya na rawa irin ta tsufa ya ce" ina kika shiga? AGAISHAT zuciyata ta rikice na rashin gannin ki, na damu na kasa baci, kin ji har zazabi nake dan bana ganninki yata, ina kika je kwana biyu? Kin san ke nake gani ina jin dadi, kece mai daukana tamkar mahaifi, zo zo na ji me akai maki? Wa ya taba min ke ? Karasawa ta yi tana sakar masa murmushi ta kamo hannunsa ta damka masa goron da ta siyo masa tun wancen ranar, murya a nitse ta ce" mun fuskanci matsaloli ne a gida Sofo, aman yanzu alhamdulilah mun gode Allah, Su Anna sun tafi birni Sofo, muma watarana zamu je? Zaka tafi da ni nima na ga birni? Ajiyar zuciya ya yi jin ba abinda ya sameta na tashin hankali, ya lalubo karfen gurza goronsa ya mika mata ta mike ta darwaye ta dawo ta raba goron hudu ta maida hankali ta gurje masa shi tas ta mika masa ai kuwa ya hambuda yana tsotsa yana dan juya kai irin ya ji dadin goron Can ya ce" Birni garuruwa, A birnima akoy garin da dadi ne da shi sannan akoy wanda sam ba zaka so rayuwa ciki ba indai kai din bako ne Birni tana tatare da abubuwan firgitarwa, murane sun yiwa abin hawa irin mashin mota yarda, sun yarda da su suna halaka su Tagumi ta yi ta ce" suna halaka su kamar yaya? Ido ya dan zaro ya ce" zaki ga dan birni idan zai yi tafiyar da ba wata nisa ba, ba jeji ba, ba abin tsoro a hanya ba, dan tsabar sangarta da son jiki sai ya dare abin hawa abinsa ya tafi a dan kankanin lokaci in abin ya zo da karar kwana sai ya juyeka tamkar tuwon masara nan zigib ka mace shikennan sai kiyama Murmushi ta yi ta ce" toh ba kace ajali na tarda mutun du inda yake ba? Mutuwa ai kai ka fada min ba.a gudunta kuma ba.a boye mata, kuna Anna ta ce ita mutuwa lokaci ne idan lokacinka ya yi ba tsumi ba dabara zata daukeka ne ko waye kai ko me kake , kai ka ce min mutuwa mai yanke kauna, takan raba da da uwa, miji da mata, kuma kace min kowani bawa da ajalinsa a duniya Tsofo yama ta murmushi yana dan barin jikin nan na tsofafi ya dungure kanta ya ce" haka ne Agaishat, Mutuwa gaskiya ce, Allah ya sa mu cika da imani Ta amsa da amin...., ta ci gaba da fadin " ka ce a birni suna da wata kalar madara banda irin wannan tamu ta rakumi ko shanu? Ina so idan ka je birni ka kawo mini in kaiwa Anna ta sha ta ji itama Kansa ya girgiza kawai, domin ya lura yau du labari ne a kunshe a bakin Agaishat, wai shi zuwa birni, shi da a yanzu salarma baya iya zuwa masalaci kafafuwa sun kiya, ga tsufa me zai je nema birni? Sai dai idan har kadarar makwoncinsa a can wannan kuwa ya san ko ta wani hali Allah zai kai shi.............. Dago kanta ta yi ta ce " ka san me? Ya gorgiza kai alamar aa Ta ce" wankana sau biyu, su Mariama sun bani kaya suka saka na yi wanka Murmushi yake na jin dadi, bai taba yarda a duniya Allah na hada jinnin mutun da mutun haka kawai sai a kan yar yarinyar nan, Jinta yake tamkar jinninsa, sonta yake har bargonsa, baya son damuwarta, fatansa Allah ya bata miji na gari komai talaucinsa domin ba zata kasa ratuwa da talaka ba, a hakan rayuwarta ta ginu, gidansu ba laifi su ba talakawanan tukuf bane domin dadaya ne gidajensu ke zagaye a garin aman ita rayuwarta irin ta yayan talakawan nan tukuf ce masu wadatar zuciya, Tana ta zubar ta mike ta shiga dan totona dakin kamar yanda ta saba dan dudubawa da kyau ta kashe kunama, domin kunamu na cikin kasa bakaken nan wa.inda idan sukai cizo in ba.a yi gagawar shan magani ba dafin na saurin kashe mutun , sune a cikin kasar garin kamar me, yan garin sun iya rayuwa da su, domin sun san inda zasu same su sun iya kashe su tamkar yanda ake kashe cirnaku, Ta samu ta kashe wajen hudu ta cilar waje ta dauku tulu ta ce" sai na dawo Hannu ya daga mata yana murmushi ya ce" Allah ya tsare ki Yana kallonta har ta fice , ya samu kansa da zirarar hawaye, ya ce" ya Allah baka barin wani dan wani ya ji dadi, Allah ka sa , ka yarda, ka aminta , ka bani ikon gannin ta shiga hannu mai kyau kafin na koma gareka ....... *Niamey* Kan Anna kasa take tafiya domin bata son gannin irin yanda mutanen ke cuwa cuwa, a can kauye shiru ne, ba hayaniya , ba komai, sannan mutanen basu fi a kirga ba, hakan ya sa du idan ta fito daga dakin da Fatimata take koda dan ta leka ta ga safiya ce rana ne ko dare ne? Sai ta rikice Ji ta yi ta ci karo da mutun, da sauri ta dago dan bayar da hakuri sai dai me, gani ta yi ya zaro idannuwansa yana kallonta, a hankali ya nunota da yatsarsa sai dai wani abin ya ce masa Haba docter, haba docter, wacen koda jikin manyanta ya kamata ba zata koma haka ba, kuma ita batuba ce ba buzuwa ba, wannan kuwa buzuwa ce ta sha bakaken kayanta, kai bama zai yiwu ace ita bace, Da sauri ya ce" yi hakuri baiwar Allah Bata san ta ina ta iya hausa ba, bata san ya aka yi ta ce" Ba komai yi hakuri kaima Gaba ya yi yana dan waiwayenta, shi dai rabinsa da wancen dama familynta tunda aka hana masa aurenta, tun suna saurayi da budurwa, muryar wancen da wannan ba daya ba, sannan kai ka daina tunani kan matar nan mai yiwuwa matar aure ce Da sauri ya kawar da maganar a ransa ya nufi office dinsa yana dafe kansa a fili ya furta" ya dace na ajiye aikin nan, na jima ina fama har jikin tsufa ya zo.... Tunda ta koma dakin ta yi shiru tana tunani, Gaishat ce ta salame sallah ta juyo tana kallon maman nata ta ce" Anna me ke damunki ne?? Anna ta dan yi jim ta dago ta ce" wani yare na yi yanzu Gaishat, wanni mutun na kade ya min yare na bashi amsa tartar tamkar na iya yaren Da mamaki Gaishat ta taso ta zauna kusa da ita ta ce" me kuka ce????????? 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣2⃣ Cikin yaren buzanci Anna ta maimaita mata abinda suka ce Da mamaki take kara kallon Anna ta ce" kuma baki san sunnan yaren ba? Anna ta girgiza kai, da yannayin damuwa a fuskarta ta ce" ban sani ba, kuma da dukan alama ba yaren faransanci bane domin likita ya yi ta yinsa a gabana ba wani fahimta nake ba, sannan ba yaren nan da muke ji wajen masu siyar da abinci a garinnan bane wato Zabarmanci, wannan yaren shima daban yake Gaishat ta mike tana kallon ledar fitsarin fatimata ta ga bata cika ba ta ce" Anna, ko mu koma wajen mutumen ku kara yin yaren? Anna ko haka na da nasaba da asalinki? Nan da nan Anna ta ji ranta ya baci, asalinta? Kennan dai yayanta ba zasu daina daga mata hankali da wannan kalmar ba, rai a bace ta ce" ina ruwanki da asalina Gaishat? Ina ruwanki? Tana gama fada ta fice a dakin don ji take zuciyarta sai tukuki take mata na bacin rai Da kallo Gaishat ta rakata, haka ne, komai irin dadin da kake ciki da Annarsu in dai ka yi gigin neman sannin wacece ita? Zata fatatakeka ne ko waye kai komai kusancinka da ita, Ajiyar zuciya ta sauke ta karasa kusa da Fatimata da yanzu masha Allah sosai take samun sauki dinkinta ana kula da ita sosai, likitan karshe ne , du niger ta wannan fannin da shi muke takama! A yannayin nishadi ta fito a gidansu, Abanta ya santalo Amarya yar bariki, irin a nuna masa ana son yayansa har Bak'A bata kyamata tana bata abinci bayan ya cashewa maryama kudaden da ta yi rantsuwar ba za.a shiga da matar ba sai ya bada su ......Algabitt dai na rakashewa fa amarya , yayansa na gefe suna rayuwarsu , inda bak'a ta dan samu inci na kwana biyu a gidansu domin bashi da lokacin wulakantata yana malake da amarya yan uwanta kuwa sosai suka dan sasauta mata tsanar da sukai mata Yar waka take da yaren buzanci tana saka sunnanta a ciki, fadi take" ni bak'a yau wa zai so ni? Bak'a nake wa zai rabe ni? Yar bak'a haka ne sunana! Dala biyar babu mai kaunata, Ta yi dariya ta ce" ni ko a baiwa an rasa mai siyana a kauye da birni, Agaishat kij cika muni....ta fadawa kanta sai kuma ta yi murmushi tana girgiza kai kawai Algabittt, yar firit din yarinyar da ya auro ta furta kai tsaye Shi kuwa da yake saman gadon karagarsa ya yi dadaya ya kallota ya amsata da um? Tasowa ta yi tana juyi uwa bishiya ta karaso tana nuna masa gidan manta na shafawa ta ce" ka san yanzu muma a kauye mun yi ido, yarinyar nan jikanyar mai siyar da fura nake kawance da ita, ita na baiwa kudina ta siyo min wannan man, Na ga fatar Agaishat ta dameka, baka son yarinyar dan bakinta, ni kuwa na hango kyakyawar yarinya ce ta karshe kawai bakin ne ya yi mata yawa, dan haka ga shawara wace in dai ka yarda ka takurata ta yi a hankali zata dawo farar mace itama mu siyar mu samu kudinmu mu yi tafiyarmu birni mu je mu rakashe mu hau mota mu saka gilashi mu dangwali kaji Wata zabura ya yi daga konce yana kallonta, irin maganar ta fara shigarsa, ya fara aminta da shawarar amaryar tasa Kara jujuya masa ido ta yi ta mika masa ta ce" ka ga bude ka gani, ai dai ka san wannan uban farin da na kara ba nawa bane wanda har kake son samun irina ............. ka yi mini ciki na haifa maka mai kyau ko? To sai fa wannan, ka bada na je na kai mata a siyo mata ta shashafa ka ga yanda bak'arka zata dawo yar dagwasssssss Murmushi ya sakar mata ya jawota jikinsa ya ce" na yarda, in dai ta dawo fara sai in baki ki kai a siyo dan ubanta sai ta shafa ko bata so Dan ture shi ta yi tana jin haushi a ranta, dan jaraba sai ya kama ya jajagulata shi ba wani nisa yake yi da lamarin ba du ya hargitsa mata tunani ya barta, haba ta yi aure ta bar jarumin maza saurayinta, aman yau sai ta gayato sho gidan nan Dan dukan kirjinsa ta yi ta ce" ina so wani dan uwana ya zo mu wuni tare yau Algabiiiiitttttt Ta fada tana jan sunnan Da ido ya tsareta, wai itama nan ta iya bariki, murmushi ya yi, shi dai burinsa ta dauki ciki fa? Ina ruwansa inma 2a zqi dane mata ruwan ciki, shi dai in ta yi cikin ta haifar masa kace komin jaraba ya rike abinsa ko a shekara goma ne ya saida ya kara kama daloli, shi kam haihuwar yaya mata ta yi masa rana ( wani abu zai baku mamaki a lamarin nan, irin yanda Algabitt baya kishin matarsa? To bara ku ji readers , ban ce duka buzaye ba, ba zan ce duka ba domin mahaifina buzu ne dan tsananin kulle da yake yiwa matansa ko gidan mutuwa da ta shafi gidansu zasu je shi ke kai su da kansa ba direba ba kuma ya tsaya su fito rufrufruf uwa matan ninja baka gannin komai na jikinsa ko.ina a rufe ruf ba damar ganninsu komai kusancinka da su, sai dai kuma akoy buzayen da basu san darajar matansu ba, sam basa kishin matansu, sai su ga matarsu kwonce saman bed da kato su fice abinsu ko a kwalar rigarsu, baya hana suma in an jima su taketa abinsu doki ce dan haka suke zaune da ita ba wani abin ba! Gaskiya ce a fadeta🤷🏻‍♀) Murmushi Algabit ya yi mata ya matsota sosai cikin yannayin rada ya ce" ke , kar ki damu da fada mini fan yan uwanki maza zasu zo, in dai zaki zauna da ni ki haifa mini mata masu kyau? To na baki dama! Ai kuwa da murna ta rungumeshi ta shiga bashi kulawa daidai daukar hankalin tsufansa 🤦‍♀ Wannan kennan ................................................ A hankali ya jona wayar abinda zai dafa masa ruwan zafin dan ya kada madara ya sha Komawa ya yi jikin bed ya zauna ya shiga karanta messages din Walyn, daya bayan daya, Na farkon farkon du yannayin ranta a bace ne, harda baya jin kunyar a ce matarsa guda ta kwana a cell? Toh garin niamey ya dauka, ita yanzu kunyar zuwa auren da zata hadu da mata take, a jejefeta da habaici ya nuna ita ba kowa bace a fadin duniya Sai daga baya kuma ta fara nuna wai ina ya je ne? Ya haka zai yi tafiya bai yi mata salama ba? Ina ya tafi? Sai daga karshe ta sauko sosai ta yi ta turo masa alamun kuka da nuna ta yi missing dinsa yana ina ne? Tana son ganninsa ta yi missing dinsa Murmushi ya yi a fili ya ce" Hajia Walyn matar Wardugu, Walyn mai zamani, Girgiza kai ya yi, kai shi kansa ya sani da ace wani saunan namiji ne da tuni Walyn sai yanda ta yi da shi, kuma ba boka ba malan! Wayarsa ya kunna wace take kiransa, ya cireta a liste noire (Black list) ya kwonta yana sauraron ruwan zafin na karar ya dafu aman ya yi masa banza, tunani yake, wai shi shugaban revel zai yiwa haka? Ya fada masa gashinnan zuwa aman ya ki zuwa? Har ya je ya yi ta zaman jiransa wai sai daga baya ya yi masa message cewa ba zai samu zuwa ba,? Ya sani sarai waye shi aman ai shima ya san waye shi! In ba dan tsufansa ba da sai ta tafka masa ashar din da zai gigita! Wayarsa ce ta shiga kara , irin kukan bindiga ratatatttatatatatatattatatatatatatattatatatatatatatatatatatatatat Muka hannunsa ya yi ya dauko yana karanta sunnan mai kiran Sai da ta tsinke aka sake kira kafin ya daga bai yi magana ba Oga, bako ne muka yi, ahi kadai yake tafe cikin duhun nan, ya zo ta hanyar boye , ragar wajen nan ta shaida zuwansa domin ta kama masa hannun shine ya fito yana fada Kai waye ya zo? Wardugu ya katse shi da kakausar murya Murya na rawa ya ce" Shugaban Revel! Wardugu ya lumshe idannuwansa, a nitse ya ce" ku shigo da shi fallon farko, ku juya Da toh suka amsa suna masu mamakin mai gidansu, yana nufin daga shi sai shi zai ganna da wannan hatsabibin mutumen? Lale Wardugu bashi da tsoro, baya dar, baya tsoron uban kowa! Kwonciyarsa ya yi bayan ya ji wa ke jiransa, Can cikin tunaninsa wayar ta kuma daukan kuka, Da haushi haushi ya mike ya daga da kakausar muryar nasa ya ce" Hello! Wardu.........ta fada cikin sanyin murya Tsai ya yi bai amsata ba Kuka ta fashe da shi ta ce" tu me manque (i miss you) Ajiyar zuciya ya sauke a takaice ya ce" ki bi Nuger airlines gobe ina Agadez hotel din sojoji ki sauka nan ko bana nan ki je dakina Yana gama fada ya kashe kiran yana shafa gefen fuskarsa da sajensa DOGON wando ya dora saman gajeran ya saka riga fara kar ta ririke damatsunansa ya fito ya nufi fallon da aka sauke bakon dare (🤣) Yana zuwa ya shigo kai tsaye, Mutumen dake zaune ya sha rawani ya hakimce cikin shiga ta kamala mai daukaka darajar dan adam ya dago ya tsaida kallonsa kan Wardugu, a tarihin rayuwarsa dole ya sako wannan yaro, domin shi ne mutun na uku da ya ajiye shi jira Murya a kausashe ya ce" Wardugu ba.a tsayar da ni jira Shima Wardugu kai tsaye ya ce" *Rhissa agbula* ba.a ajiyeni jira! Murmushi Rhissa ya yi, ya mike tsaye suka gaisa irin gaisuwar musulunci suka baiwa juna hannu suna yiwa juna salama Wardugu ya ce" ya zaka zo wajena ni daya bayan ka san ya dace a tatauna da kai a bainar nasi kowa na da magana da kai harda mai zuwa da maganar shugaban kasarka Rhissa ya ce" shugaban kasarka dai, ka san ni ba nawa ba! Sannan ni kaima da na aminta ganninka dan na fafata da kai na yarda tsaurin kanka zai je da nawa, bana musanyar yawu da matsoraci, ba.a daukana a tv haka kyauta sai kace wani sakarai! Wardugu ya girgiza kai ya ce" ya ake ciki? Wa ke son tayarwa kasata hankali? Ina suke? Menene abubuwan yakinsu? Ana jitajitar kune kuka dawo bayan kun daina aiki a niger kace niger ta yi maka kadan sata yanzu? Me yasa ake samun gawarwakin bayin Allah a gidajensu? Masu aikata min haka baki ne! Da sun san idan na damke su zasuna kururuwar na kashe su da abinda nake masu da basu shiga gonata ba! Wardugu ya karasa yana dukan table din glass din dake falon ya yi wani jijiga aman bai fashe ba domin irin wannan mai masifar karkon ne, sai bindiga mai tsini ke tarwatsa shi Rhissa ya mike tsaye ya ce" ba ni bane, kuma ba yarana bane, abinda ya sa na tsayar da hankalina kennan har na baro aikina na garzayo dan ganawa da kai! Kar ka shiga yaki da ni ba ni bane! Na yi bincike tsageru ne, kan harkar siyasa ne, kuma na ga makwoncinsu, suna cancanza waje ne ina son sannin tsarin canza wajen nasu, Wardugu nima sai na yi maka maganninsu Wardugu ya girgiza kai ya ce..... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣3⃣ Wardugu ya girgiza kai ya ce" ka taba gannin na nemi agaji? Kokowa ai ya dace mutun yayi abinsa! Ka bani hanya kawai ka barni da sauran ai na san tsarin tsagerancin yan tsagera, idan ka yi yaki a kambacina kana so gobe su afko su aikata abinda ya fi haka? Domin sun san ba zan iya tarbansu ba? Aa ba dai Wardugu ba Haka tataunawar Wardugu da Rhissa ta kare, kowa na ji da kansa da kuma ikirarin kansa, Rhissa ya san abu guda Wardugu ba wai cika baki yake ba, yana fadin abinda zai iya aikatawa ne, ya san da in dai suka yarda ya ci masu kamar yanda ya fada ne sai sun gwamace mutuwarsu da rayuwarsu a hannunsa, Wardugu ya ga damar ya fitar da su jeji su fuskanci juna wanda hakan kuwa ba zai gyara su ba! Wannan kennan Bayan kwana biyu .......AMERICA Docteur Mu.azam ne ke zaune yana dadana computer, Can ya dago kansa ya duba time, A hankali ya ajiye ya mike ya nufi bayi ya sakarwa kansa ruwa Yana fitowa ya dauki kayansa ya saka ya saka vest dinsa ya dauki agogonsa ya daura ya fito fallonsa dan madaidaici ba wani tarkace sai kujeru da dan table da tv tankamemiya, sai hoton wasu fararan mutane mata da miji ga dukan alamu suna murmushi a hoto Kamar yanda ya saba zuwa ya yi ganan hoton ya tsaya ya ce" Abi, amy asalamu alaikum, yauma na tashi lafia, sai dai har yanzu ya kasa hakuri ya daina fushi da ni, gashi aiki ya taso min a kasarsa banda shi da mahaifiyarsa da mahaifinsa da suka dauke ni tamkar dan cikinsu bani da kowa, Zan kuma gwada kiransa ku taya ni da adu.a daga inda kuke, ina mai kara yi maku adu.ar Allah ya sa kuna cikin Aljannah Shi kadai ya tsaya ya yi zubarsa kafin yake zuwa wajen wayarsa ya zauna yana dan murmushi ya shiga doka kira Yana kallon wayar na haske ya ki dagawa, Walyn ce ta fito daga wanka ta zo ta mike abinta saman lafiyayan bed din hotel din itama tana duba saman screnn din dan gannin wa ke kiransa yake sharewa haka? Murmushi ta yi ta juya abinta ta shiga neman baci a kasan zuciyarta tana ayanna toh fa da shima yana gaba bare ni? Can dai ya daga ya saka a handsfree Soja kake Ya fada yana danne dariyar farin cikin ya daga kiransa Murya ciki ciki ya ce" Docter kake, kuma dan rainin hankali kake Murmushi ya yi ya ce" baka hakuri ne? Baka mantuwa ne??? Wardugu ya kawar da kansa ya ce" haka, ka san ba nine na watsa taron aurena ranar aurena dan wani gudiri nawa na shirme daga shiga ka ga amarya kafin a daura aure zaka fito ka watsa taro? Kai mahaukaci ne! Mu.azam baka da nutsuwa Mu.azam ya bushe da dariya ya ce" Wardugu, abinda ya sa na tsalako fararan fatar, na yi doguwar tafiya niger ba dan ina son na samu *BAK'A* bane?, ni bak'ar mace nake so, ita ce ra.ayina, ita nake son zaman aure da ita! Kar ka manta ni likitan mata ne, idan ka ga na kuke abu kaima ka gwada abokina Tsaki wardugu ya ja ya ce" kiran na menene? Mu.azam ya kuma yin dariya ya ce" kai ka dena jin haushina mana, ai ni ban shaki mahaifin matana ba Da sauri wardugu ya kai dubansa wajen Walyn wace ke kwonce, ta ji sarai dan haka ta yi saurin mikewa tana kallonsa, Fuska ya hade idannuwansa cikin nata ya ce" eh haka ne na shake shi, domin a lokacin ban san mahaifinta bane, kuma na tarar da shi ya zabgawa mamanta mari , idona ya rufe ban tsaya wata wata ba na shake shi, kai dan ubanka sai yanzu ka tina????? Ajiyar zuciya ta sauke, tana tine da ranar .....dalilin wannan action din da yayi na ta haukace kansa, wardugu jarabar duniya....komawa ta yi ta kwonta ta ja bargo tana rufe jikinta Wardugu ya fice a dakin , yana fita ya ce" Mu.azam?? Mu.azam ya amsa da na.am? Wardugu ya ce" kana son kashe min aure ne? Tana jinka fa Mu.azam bai ji dadi ba aman ya ya iya har ta ji, dan tsam ya yi kafin cikin yannayin mamaki ya ce" Wardugu yamzu tsareka ake idan zaka amsa waya ko me? Lale dole na auri batuba Kai banza ka nutsu ka ji!! Mu.azam ya yi murmushi ya ce" dadina da soja zagi, ni dai ka fadawa Ayyata in sha Allah ina nan ina faman gama abinda nake zan shigo Niger, ka san bani da masauki sai kusa da ita dan ita ta iya kula da cikina, zan zo ba zan dawo ba sai na samu macen aure na kuma gama abindq zai kawo ni Wardugu ya ji dadin haka dan haka ya amsa shi da murnar hakan Satin su wardugu hudu a garin Agadez yana faman aikinsa wanda tun Anna na fada har ta kawo ido ta zuba masa, gashi ta yi ta yi aminiyarta ta barta ta koma wani wajen ta kiya ta ki fir sai ma fada da ta dauka cewar masarautar ai girma ne da ita, ba ita ba ko baki ta kawo suna da wajen zama har lokacin da suke so a masarautar Agadez A yau suke saka ran komawa bayan ya fada masu su kiyaye, ya basu magungunna, ya kafa masu sharuda kan lafiar Fatimata, Jirgin da ya kawo su an basu takarda dan haka suka kai aka saka su a layin wa.inda zai mayar garin agadez bisa jagorancin docter Fannata Sun sauka lafia inda Fatimata ke dan takawa a hankali daga nan suka nemi abin hawa dan karasawa Timiya............ Timiya.....me aka kwaba? Me aka yi me ba.a yi ba? Me ake cikin yi? Timiya gari mai abin mamaki, Timiya garin bak'a, Duka na kawo wuka a yanka Algabitt ya yi mata bisa taki shafa man da ya fitar da kudi ya saya, Rai bace ya ce" sai na tsine maki in dai baki shafa man nan ba Cikin kuka ta ce" Aba, ka yi hakuri ka ji? Bana son canza kalar fatana ka yi hakuri Abanna Ni ban haifeki ba, ke ba abin alfaharinki bane yau har na yi hakuri na dube ki na nemi intaki aman ki butulce min? Uban wa ke hure maki kune ne ni? Aba ba kyau, ba kyau, mu ji tsoron Allah Hannu ya saka ya dake bakinta ya ce" ki rufe mini bakinkin nan mai bakin jaraba! Ke sai kin shafa Kokarin shaketa yake dan ya shafa mata Mariama ta fito da gudu tana ihu tana nuna dakinsu Dakatawa ya yi yana binta da kallon meye ke kuwa Hankali tashe ta ce" Ashta ce, ashta ce, tun da ta ce maka in dai ka yi mata auren nan sai dai a kai gawarta kai kuwa kace sai me ba dai ka daura mata auren ba? Ita ce gata can sai wani abu take daga baya ta fasa motsi Fancakalar da Bak'a ya yi, shi da amaryarsa suka nufi dakin da gudu Daidai wannan lokacin Su Anna da sukai doguwar tafiya suka shigo gidan da salama bayan su Dogarai ne da suka tarbo gimbiyarsu wace sarki yake hakimce yana ji tamkar ya zo ya tarbi abinsa Jin kururuwa ya saka gaban Anna ya yanke ya yi wani irin faduwa, cak ta tsaya tana sauraron magangannun dake tashi, ihun kuka yayanta biyu suke inda Bak'a ke jingine jikin garu ta daga hannunta ta dora saman kanta ta yi tamkar status tana kallon kofar dqkin nasu , Muryar amaryar Algabiitt ce ta tashi ta ce" ta kashe kanta, ta kashe kanta Wani irin luuuuu Anna ta yi wanda ba wanda ya ganta sai faduwarta da aka ji , nan mutanen gidan suka ankara da dawowarsu wanda nan da nan gidan kai dama anguwar ta cika da dukan jama.a ana ta daga maganar, tabas Ashata ta rasu, ta rasu ne da bakin ciki, tana da ciwon zuciya ne wanda ya yi mata tashin kai tsaye, wanda amaryar Algabitt ta yi kazafin ta kashe kanta, Tashin hankali! Mota ce katuwa irin ta sojoji, direba mai iya janta kawai ya dauka kai tsaye suka karasa gidan Sarki Ayya na zaune tana gyara akaifunta labari ya zo mata cewar ta fito su tafi Mikewa ta yi fa hanzari tana murnar yau kam Allah ya sa , Tafia suke cikin mota, Walyn na zaune tunda ta cewa Ayya ina kwana bata kara magana ba sai shanshan kamshi take domin da yar tsamarsu da Ayya, gani take Ayya ke zige mata miji yana wulakantata Tafia ce suka yi mai tsayi, cikin jeji ne sosai kafin suke shigewa sahara gaba da baya Wani kara motar take a cikin kasar nan tana cin tafiyar wace kana ganni ka san karfi ne ke aiki Duda a cikin mota suke aman sun yi budu budu da su domin kura sosai ke tashi sanadiyar gudun da suke a motar da kuma kasa A hankali ya ratsa yar gadar da ta kai mutun cikin kauyen, wato *TIMIYA*.............. YA RAYUWAR ANNA? ALGABITTTT FA? BAK'A????? SU WARDUGU DA AYYA DA WALYN ME YA KAWO SU TIMIYA??????? MU JE ZUWA ...........................................................na yi imanin da ba dan Allah na sakawa bawa hakuri da dangana a zuciyarsa a lokacin da ya rasa wani mutun mafi kusanci da shi da Anna ta samu tabuwar hankali ga wannan lamari na mijinta, kar ku manta na fada ba labarin mutun na dauko ba aa labarin abinda ke faruwa ne, (YA FARU!)...... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣4⃣ Bayan sun shiga garin timiya mutane suka ringa gudu suna kururuwa, wasu na fadawa gidajensu wasun kuwa na nufa gidan sarki wasu kuwa na kokarin neman hanyar da zata fitar da su daga garin ta barauniyar hanyoyi domin dai garin ba wani rufe yake ba Da mamaki suke kallon reaction din mutanen, Warsugu da sojan dake jansu ne kawai basu yi mamaki sosai ba duba da yannayin garin motar lafia dai bata shiga sai ta sojoji ko kuwa motar mugayen mutane masu zuwa su kai hargitsi su kashe mutane Kallonsa ya maida wajen Ayya wace ta dafe habarta ta wara idannuwanta tana mamakin nan yake mutumen kuwa? Aman gudun me suke? Labari ya kaiwa sarki a yar fadarsa, Tabas gabansa ya fadi da jin wannan lamari, ba a taba ba, mota har nan bata fara shiga ba, Mikewa ya yi da dukan kokarinsa ya tatara karfinsa inda dogarawa suka shiga kabara sunai masa kallon jarumi mai tausayin talakawansa da kuma kallon marigayi Du a bayansa suke inda yake daga kafafuwansa da kyar yana kara tunkarar motar, gannin motar ta sojoji ce hankalinda ya kara tashi, domin dai shi ya san motar tunda yana shiga gari kai gaisuwa fada, kai harma ya tafi kasa mai tsarki, me ya kawo motar sojawa Timiya? Shine tambayar da yake yiwa kansa, To ko dai sojojin ne a cikin motar ko kuwa mugayen mutane domin idan sun kai hari ai suna karbe motocin sojawan Wardugu ne ya bude gefen da yake zaune ya karbe hannunsa daga rikon da walyn ta yi masa ya diro daga cikin motar tsaye kan kafafuwansa Jibgi, dankari, in ba wardugu ba zaka shiga kauye sai ka je da wando tree Carter? Sai rigar sojawa irin body din nan damatsunnan hannayensa a fili, yar karamar bindiga marar karan sautin harbi ce a kugunsa inda ya rufeta da wannan rigar ta jikinsa ya saka belt kalar kayan sojojin ya daure tam abinsa Kansa sanye da hula baka kalar wandon sai takalminsa sandal wanda ya daura abinsa Sun karbe shi, sun amshi jikinsa, sun kawata shi Taku ya shiga yi da karfin jiki ya nufi Sarki da ya ja ya tsaya jikinsa na bari, ta faru ta kare, jita jitar Ashta kanwar matarsa ta kashe kanta wani ya kai birni an zo kama sirikinsa, mutuwar yau har kwana takwassss tabas wani ya kai, shikennan Alghabiitttt ya bani domin a hoto kuma a tv a birni Yana gannin wannan mutumen, an ce shugaban sojoji ne, shi da kansa ya zo kama algabiit? Algabitt ya ji haushin rayuwarsa, tunanin da Sarki ke yi kennan inda ya daskare da tare da bugun zuciyar ko wani taku na Wardugu dan nufo shi (🤦‍♀ in ba kauyanci irin na sarki ba, a rasa mai zuwa kama Algabiit karamin kwaro sai Wardugu? Za dai ka san waye shugaban sojojin nan hangensa kake!) Yannayin shigarsa ta tabatarwa da Wardugu shi ne magabacin garin, dama irin haka idan an zo sarkin gari ko mai garin gari ko kuwa tsageran gari wanda ya gagari uban kowa ke zuwa ya tarbi mutanen, in da karar kwana a kansu ake farawa Salama ya yiwa sarkin yana mika masa hannu sannan tar yana kallonsa ido cikin ido Jiki na bari Sarki ya karbi gaisuwarsa yana tambayarsa hanya da zarcewa da magana kamar haka" mai gida, na san ba auren iri ka zo nema a wannan jeji namu ba? Koma wa ka zo kamawa ka yi hakuri, a yi mana sasauci kar a kashe mu, a kama iya mutumen a tafi, ni kaina inada kankannan yara da mata, idan aka tsame masu ni wa zai ji da su? Da mamaki Wardugu ke kallonsa , aman da yake Wardugu dan duniya ne sai ya ce" Kai, baka san Allah baya barin wani dan wani ya ji dadi ba? Ai kuwa gaba daya sarki ya haukace, jiki na bari ya saki kuka ya duka kasa ya rike kafafuwan wardugu ya shiga magiya Ayya dake cikin mota ta dake lebenta na kasa ta kali sojan nan ta ce" ka karasa da mu, na san wardugu wani lamarin ya shiga na tsawatar masa tun kafin abin ya birge shi Walyn ce ta juyo da sauri ta kalli Ayya, a ranta ta ayanna wai ta tsawatar masa, sai son ta nuna ita kadai ta isa ta juya shi, ta ja tsaki a ranta a fili kuwa ta ce" Hum tana tabe bakinta sosai Sojan ne ya juyo ya ce" Hajia, ki yi hakuri, nan ya ce na ja na tsaya idan na matsa bai bani umarni ba ni da shi ne Da haushi haushi ta shiga bude motar wanda sojan bai ankara ba har sai da ya ji ta bude ya juyo da sauri , har ta sauke kafarta guda ta ga Wardugun ya dawo da saurinsa gefen da take Yana zuwa ya ja ya tsara mata ya ce" Ayya maman Wardugu, kece ikon mai sanya Wardugu cire wando ta kai, Ayyana kar ki yi fushi kin ji? Koma motar mu karasa sai ki yi masa tambayar ai sarkinsu ne Da mamaki ta saki baki tana kallonsa, sarkinsu? Aman me ya saka shi kuka da dukawa ya kama kafar wardugu? Dan murmushi ya yi bayan ya saka mata lafayarta ciki ya rufe ya bada umarnin su karasa inda sarki yake Suna karasawa Ayya ta bude tana shirin fitowa sarkin na karasowa ya dan risina yana gaisheta, Ayya ta kalli wardugu ya dan sakar mata murmushi Kai ta girgiza ta sauka sosai ta gaishe da sarkin kafin take fada masa abinda ya kawo su Wata ajiyar zuciya ya sauke a bayane, ya ce" A garinnan Sofo mai bada magani kwaya daya mukeda, ya sufa sosai, gidansa da dan nisa da kasuwarnan sai mun shiga gari sosai Ayya ta amsawa sarki da ba damuwa su je A cikin motar nan sarki ya shiga inda yake dan hangen Wardugu ta madubi lokaci zuwa lokaci, ya yarda da ake cewa sarkin sojojin fa masifafe ne , bashi da dar, in ba rashin tsoro ba du irin yanda ake tsoron abzinawa da asiri shi a gabansa sai dai ma shi sarkin ya ji gabansa ya fadi maimakun na wardugun ya fadi, lale yaron ya sha ya jiku ya tada kai , rabonsa da kuka tunda aka zo masa da sakon Gaishat ta tafi baban birnin niger inda ya yi tunanin shikenan ta gudu me ta bar shi.....(wani lamarin dan gyara nvl dina ne fa, sarkin abzin ba wasa walahi🤣🤣) Basu zame ko.ina ba sai anguwar baba Sofo Suna tsayawa mutane suka cika wajen, tunda sun ga sarkinsu a tare da mutanen ai shikenan sai suka sakin jikinsu da su harma ake matsowa a shafa motar sai a kwala ihu da yaren buzanci a ce" nima na taba, mota mota a garinmu, mota har gidanmu, Du ja sukai a lokacin da mutanen ciki suka fito gaba dayansu, suna masu binsu da kallo, girma da yannayin tsarin halitar wardugu ta basu mamaki, suna da mutane dogaye sosai sai dai ba masu fafadan kirji da manyan damatsuna haka ba, sai kuma matan dake tare da mutumen da dayen sojan, kun san dai Ayya gwadar ado ce, bale Walyn farar mace alkyabar mata, walyn farar batuba ce tas tas tas, Ayya ce ma baka domin Ayya baka ce mahaifin wardugu ne farin batube shima tas tas tas , sai sojan dake saye da kayan sojoji komai harda bindigarsa da katon takalmin nan nasu da komai sai muzurai yake Sarki ne ya amsa gaisuwarsu kafin yake kai dubansa bukar Sofo, Bukar kanta ta tsufa du ta zuzube sai abinda ba za.a rasa ba, ga dati sosai a dan nesa da wajen domin an yi rasuwa baka bata samu zuwa ta share masa ta gyara masa ba, Ruwa kawai take zuwa ta dauko masa ta koma Nuna masu wajen ya yi bayan ya samu ya shiga ya tarar yana zaune saman buzunsa da carbinsa yana ja ya kurawa waje guda ido yana ta istighfari(Allah ka bamu nitsatsen tsufa in muna da rai wanda zai kara kusanta mu da kai ya Allah) Gaishe shi ya yi ya juya inda sofo ke bin kofar da kallon mamaki, me ya kawo Sarki har wajena? Kuma hayaniyar me nake ji haka? Ku shigo; Sarki ya fada yana dubansu wardugu ya ce" anya kuwa? Me zai hana ya fito??? Ayya ta kallo shi ta ce" Wardug..... Da sauri ya yi gaba ya fara nufar yar bukar sofon a ransa yana ayyana ai idan Ayya ta nadaka toh fa tana yi da kai Shishiga sukai banda sojan nan, Walyn na saka kanta ta yi baya tana kakarin amai da coshe hanci, a fili ta furta" kai ina , ba zan iya ba! Ayya ta karasa a hankali kusan tsofon dake zaune ya zuba masu ido gaba dayansu yana mai binsu da kallo, ko gezau bai yi ba daga zaman da yake sannan yana jan carbinsa cikin nutsuwa A hankali ya amsa salamar Ayya da ta nufo shi cikin nutsuwa ta tsugunna dan nesa da shi aman suna facing din juna A hankali ta ce" lokaci mai tafiyar da abubuwa, lokaci mai bayanna abubuwa, lokaci mai rarabe abubuwa, Baba tsufa ya zo haka? Allah ya sa mu cika da kyau da imani Murmushi ya yi na gano wacece ita, tabas ya ganeta, idan ba zai manta ba shekaru sun kai talatin da suka shude ya sha kai mata magannin athsma na yaronta da bai fi shekara hudu a lokacin ba tana karbar masa aman ya ki karbar komai da sharadin sai yaro ya samu lafia Murya na rawa baba tsoho ya ce" y'ata ke ce a garin timiya? Ya jikin yaronki? Na koma ban same ku ba sai na yi adu.ar Allah ya sa ya warke Ayya da murna ta janyo hannun Wardugu dake tsaye kikam ta ce" baba ai gashi, kana ganni soja ne, cikin ikon Allah magannin nan mun ji dadinsa, nima a raina kake, na nemeka Allah bai yi ba, kwanan nan na yawaita mafarkinka, a sifarka ta da hakan ya daga hankalina na saka aka nemo min inda kake, shi ne na zo na yi godiya sannan na yi salama kamar yanda na dauki alkawari, Baba na murmushi yana kallon wardugu wanda shima zuwa lokacin ya risina, yana kallon tsohon yana kidaya shekarunsa a ransa, ya yi imanin a kadan ya linkasa uku da rabi, Baba ya maido kallonsa wajenta, kafin yake bin dakin da yake zaune da kallo, ya yi murmushi bai ce komai ba Ayya ta ce" Baba ka yi magana mana, Baba ya dago yana dubanta ya ce" kaya y'ata, ki dubi dakin da nake ciki a zaune a yanzu, me ya rage min? Me zan yi da arziki? Kyakyawan karshe kawai nake nema, shekaruna dari da ashirin da uku a duniya a hasashe mai yiwuwa na fi, Kallonsa kawai suke suna masu adu.a a ransu, adu.a suke da Allah ya datar da su da irin tsufan nan, wanda zaka yi ram da kai da carbinka, Jikin ayya ya yi sanyi sosai , a hankali ta zauna a kasar dake dakin tana kallonsa, murya a sanyaye ta ce" haka ne baba, Allah ya sa mu cika da imani...... Aman na so na yi maka wani abin da zai faranta maka, da zaka aminta ma da mun tafi da kai mun kula da kai Baba tsofo da kansa ke kasa cikin rawaninsa ya dago yana kare masu kallo, ya yi imanin wannan matar da muguwa ce da bata bi bayan alkawarin da ta yiwa talaka futuk kamarsa domin ta san bai isa ja da ita ba domin zamani ya zama mai abu shi ne sarki, shi ya isa shi ke da magana ya dora doka, aman du ta manta ta tako ta ci gari da gari, ta ratso sahara du dan ta yi masa godiya sannan ta cika alkawarin da ta dauka,? Sannan ya san ba yar yankan kai bace domin ba da kansu suke nema ba kawo masu ake har gida, shi kam ji yayi gaba daya ya samu nutsuwa a zuciyarsa da shawarar sa, Murya a sanyaye ya ce" tabas ina da bukata mau girma baiwar Allah, sai dai ban san ta inda zan fara ba, banma san ko za.a dace ba, Hankalinta ta maida kansa ta ce" Mecece ita?????????????........ 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣5⃣ Baba cikin yannayin damuwa ya ce" me zai hana na baki auren y'a? A nitse ayya ta ce" Auren Ya baba? Baba tsoho ya ce" eh, domin shi kawai zan nema a bada yarinyar dindindin , Aman baba wace yarinya ce wannan?? Baba ya sauke ajiyar zuciya ya ce" yarinya ce mai tarbiya mai ladabi da biyaya, yarinya ce mai nutsuwa, bata da kwaramniya, inda aka ajiyeta ta zauna kennan sai an ce ta tashi, yarinyar nan ina jinta a raina tamkar yar da na haifa, a kulun damuwana na mutu na barta a wannan hali, tana cikin halin matsi dan kawai Allah ya yita *BAK'A* sai dai ni murnar hakan nake domin fatarta ya sa har ta kai warhaka sai dai har yanzu bata samu mijin da zai aureta ba a kauye ta girma sosai shekarunta goma sha takwas a duniya , Jim Ayya ta yi tana kallonsa, kafin take cewa " me dinka ce Baba? Baba tsofo ya kalli Sarki dake kallonsa shima cike da rausayawa, da wani ne duda tsufanda in dai yana iya magana yana gane wasu abubuwan da gudu zai karbe makuden kudin da aka baza masa, sai dai shi bawan Allah ta yarinyar fake tare da shi tun tana yar shekara shida a duniya yake, irin tunanin da iyaye zasu kwana su tashi da shi na gannin yayansu sun samu mijin aure mai nagarta wanda zai kula da yayansu, toh haka baba tsofo yake kasancewa, du motsinsa itace a ransa, tambayar kansa yake ina? Ta yaya? Wanene wanda zai rike masa Agaishat mudin ranta cikin mutuntawa da kauna? Ya hanga ya hango bai samu ba, har almajirinsa ya tuntuba aman ya watsa masa kasa a ido, hakan ya saka shi dukufa wajen kai kukansa wajen Allah, yana rokonsa da ya bili masa da hanya ta inda baya zato baya tsamani, ya bilo masa da hanyar da zata zamo alkhairi gareta,,,, Sarki ya ce" kanwar matana ce, Sunnanta *AGAISHAT* Kana nufin farar buzuwa? Ayya ta tambaya Sarki ya ce" buzuwar ce tabas, sai dai ita wannan Bak'ar buzuwa ce, Ayya ta kai dubanta wajen Baba Tsofo da ya yi kododo yana kallonsu, kallonta ta maida wajen Wardugu dake tsaye ya tsareta da ido yana jiran jin me zata ce,? Ya san halin mamansa, ya san Ayya da daukarwa kai, ! Murya a sanyaye ta ce" Warduggggggggg.......... Fuskarsa a hade ya ce" Lalalalala, Daga haka ya tamke fuska yana kallon su Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon kasa ta afka tunani (Tabas a al.adar Tubawa ba.a yiwa namiji auren dole, bake Wardugu, sannan idan namiji ya yi aure sai matarsa ta yi haihuwa kamar uku zuwa hudu kafin ya yi mata kishiya idan kuwa bata haihun ba sai ta dauki shekaru kafin ya yi mata kishiya, wannan haka ne ba ja, haka al.adar garin yake, ) Ayya ta kuma kallon su, ya zata yi? A hankali ta ce" baba, wannan yaron shi daya Allah ya bani a duniya, Sannan bai jima da yin aure ba, Ban ki ba, ina so idan da hali a bani yarinyar a matsayin yar rikona, yar amanata, in sha Allah zata ci abinda na ci ta kwonta a makwoncin da na kwonta ko wani iri ne, kafata kafarta Har Allah ya bata miji, zan yi dukan abinda ake yiwa ko wace y'a na kaita gidan miji sannan zan bi dukan lamuranta a gidan miji mudin raina Baba tsoho ya jima yana nazarin maganarta, baya shakun za.a bada AGaishat in dai sarki ya yi magana, damuwar shi ne: Agaishat zata so bin bakin fuska duda irin matsin da take ciki? Gida fa gida ne, sannan mahaifiyarta zata yarda da radin kanta a rabata da yarinyarta budurwa ba da wani dalilin aure ba ko dangi na jini haka kawai a tafi da ita tare da mutanen da bata sani ba? Ko wannan karon ma isar za.a nuna mata a kuma kwace mata *Y'A*? Duda haka baba ya kai dubansa wajen sarki, Irin kallon da baba ke yi masa sai da ya saka ya ji kunya, ya ce" abinda za.a yi, zamu kama baba a je da shi da ku baki daya ga mahaifiyar yarinya da mahaifinta, du yanda hali ya kama zuwa ya fi aike Sun lamunce da hakan inda Wardugu ya kama baba a hankali ya mikar da shi sarki ya kama masa suka fito yana dan dingisa kafarsa har suka karasa wajen motar inda sojan nan ya bude wardugu ya daga baba a hankali ya saka shi gidan gaba sarki ya shiga suka shishige gaba dayansu Walyn da binsa da kallon meye kuma haka? Shima kallon Ayya dai yake, Basu zame ko.ina ba sai kofar gidan Algabiitt ...................... ................. Anna, ki yi hakuri haka kin ji? Ki daina damuwarnan kin ji Anna? Agaishat ta fada tana miko mata gurasa ta kasa da aka kawo sadaka gidan mutuwar Anna ta lumshe idannuwanta bata karba ba ta bude tana kara bin yayan nata da kallo, Mutuwar nan da aka yi bai saka Algabiitt ya yi sanyi a lamuransa ba, ya sako Agaishat gaba dole sai ta yi shafe shafe itama ya samo mata miji kamar yan uwanta tamkar damuwarsa ta yi auren ne, Yarinyar bata isa ta wulga ba sai ya dura mata zagi Ya hana a yi zaman makoki sai yayanta dake zagaye da ita Amarya kuwa idan yau wannan ya zo ta ce dan uwanta ne , gobe sai wancen ya zo ta ce kaninta ne, ta mayar da gidan filin kawo kwartayenta ba tare da wani dar ba domin mai gidan ya bata lamuni.... Anna murya a shake ta ce" bana so ya kashe mini wani cikin ku, Mariama ta juyo fuska du ta yi mata ja abin kuka ta ce" to ki biyo mu mu bar masa gidan mana, dan mi ba zaki bi mu mu yi tafiarmu ba? Kin san abinda ke daure mu a nan ke ce, Hankalinta tashe ta ce" a duk lokacin da kuka ambata mini abubuwan nan biyu asalina da barin Algabiit bara ku ji na fada maku yau abinda nake ji! Ji nake tamkar lumfashina zai tsaya idan na ji an ce na bar inda Algabiit yake in dai ba da yawunsa ba, ji nake zan fada halaka, ji nake duniyara shi ne, ji nake in ba inda yake ba ba ni! Wani duhu ke rufe mini ido kaina ya dauki nauyi idan na takura sai na tuno wacece ni? Nakan fada damuwa mai tsanani juwa ta ringa dibana du idan aka yi maganar dangina, kun ji damuwata Suke suke kallonta, Agaishat (Bak'a) kanta na saman cinyar Gaishat, Mariama na zaune gefensu, Fatimata na jingine da garu tana facing dinsu, Jiki a sanyaye Fatimata ta ce" me ke damunki haka Anna? Wannan ba soyaya bace, Mariama ta kallota ta ce" wace soyaya? Ai koda an yita a baya a yanzu Ya kasheta da kansa, Me ke damun Annarmu? GAISHAT ta buda baki zatai magana sai ga Algabiit bugum ya fado dakin yana dan dudukewa dan tsayi Direct ya zarce gurin Anna bakinsa na rawa ya ce" sai dai su tafi da ke da tsinaniyar yar ki! Ba wanda zai kama ni, ba abinda na yi! Da sauri ta mike tana dafe kirjinta, tsinaniyar yarki ke mata yawo a kwakwaluwa, wacece kuma? Me aka yi? Su wa zasu tafi da su? Bata kai ga tambaya ba ya duko ya dago Bak'a da gashinta ya mikar da ita, Yawun bakinsa ya tatara mai cike da warin Sansani ya tofa mata a fuska ya ce" ga dan iskan tsohon da kike wuni wajensa tare da sojoji, to ki sani sai dai su kama uwarki Janyeta Anna ta yi da karfi sannan ta yo fallon nasu da sauri dan jin lafia? Gaba daya yayan nata suka biyota inda Algabitt ya labe yana leke yana kuma sauraron abinda ake fadi Da kallo Anna ke bin su, sukai mata salama suka shiga gaisar da ita da yaren buzanci, Ayya ta kalli wardugu dake karewa kowa na wajen kallo, ta ce" ban san bama da wani yare zamu tatauna da ita da alama buzanci kawai take ji Anna dake tsaye ta ji komai abinda aka fada da yaren da ba zata ce ga sunansa ba, kuma ba yaren da suka yi da likitan nan a asibiti bane............................................ 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣6⃣ Bata kai ga magana ba dogarai ke sanar da shigowar sarki falon sirikan nasa , daman da baba tsoho ma shi ke fasara tsakaninsu domin ba komai yake ganewa ba shi kuwa sarki ya zauna da tubawa Tunda ya shigo Anna ta sada kanta dan kunyar siriki, shima du a wani takure yake inda Gaishat ke binsa da kallo tana tambayar kanta me ya kawo shi ko bakinsa ne? Gyaran murya ya yi ya ce" Anna, ina fatan kin san baba tsoho, wanda Agaishat ke zuwa wajensa babanta kennan Daga inda yake ya daga murya da irin abin haushi haushi ya ce" ya zata manta kwartanta uban yarta? Ai ni dama na san dubunki sai ta cika munafuka, yau dai ga zance zai bude Da wani irin yannayi Wardugu ya kai dubansa daga inda ake maganar, wa ke magana ta rashin da.a haka? Shine abinda yake tambayar kansa din wardugu na jin yaren buzanci kai bama buzanci kadai ba wardugu irin mutanen nan ne masu kwakwaluwar kwashe yaren da ba nasu ba, yana jin yaruruka da dama, hakan ya bashi damar jin abinda ake fada harma wanda Algabiit ke aikowa daga daka Sarki ya girgiza kansa kawai, ya san wanene Algabiit farin sani, kuma fa ya san harma gudumuwarsa wajen Algabiit ya tsula tsiya a garin aman ba komai zai dauki mataki ne tun kafin ya saka a tarwatsa su baki daya Anna da ta kasa hada ido da shi ta gyada kanta, ya zata kasa gane mutun mai daraja a idannuwanta? Wannan mutumin ko dan tsufansa a girmama shi aman Algabiit ke aiko masa da zagi haka? Ta yi imanin ba ita ba ko Algabiit din baba tsoho ya haife shi Bak'a kuwa tunda ta kyala ido ta ga baba tsoho ta samu ta rakube jikinsa tana dan jefo masa tambayoyi a hankali da alamun tsegumi Hannunsa ya saka ya dungure mata kanta yana murmushi, a ransa ya ayyana idan kika tafi,....nishadina, murmushina, zai tafi da ke Sarki ya ci gaba da fadin" wadinnan mutanen da kike ganni, wannan baiwar Allahm mahaifiyar wannan bawan Allahn ce, sannan ta taso tun daga garin da kuka kai Fatimata rashin lafia ta zo Agadez daga nan sun dauki hanya sun zo garin nan dan neman baba sofo da ya baiwa dan nata maganin huka tun yana yaro bisa alkawarin idan an samu lafia sai ta bashi abinda ya samu Toh Sai aka tashe su Allah bai yi sun kara haduwa ba, tun daga lokacin take nemansa domin mutun ce mai son cika alkawari abin na tsaye a ranta sai yau Allah ya yi Dan numfasawa ya yi, ya ci gaba" kin ga, ba a niger ba, ko a kasar waje masu fada a ji ne, Sun zowa Baba sofo da alkhairi na mamaki sai dai abin mamaki baba ya ce sam shi yanzu ba ta abin duniya yake ba, ya yafe sai dai damuwarsa *AGAISHAT CE* Anna ta dago da sauri ta ce " AGAISHAT? Sarki ya ce" kwarai kuwa, Baba ya nemi alfarmar......................................................gaba daya sarki ya kwashe yanda suka yi baba da su Wardugu ya fadawa Anna dake zaune kanta na kallon kasa sauran yayanta na zagaye da ita Bak'a kuwa na jikin Baba sofo Da sauri Bak'a ta dago ta kai dubanta wajen Anna da Sarki, ta maida dubanta wajen baba Sofo, Baba Tsoho ya yi gyaran murya ya ce" shakuwa, da tunani ya hana ni sakun nutsuwa Annar Agaishat, na sani bani da ikon zartar da hukunci kanta domin ban haifeta ba sannan ni ba wani shakikikin dan uwa ba A duniya adu.ata biyu ce, Allah ya sa in gama da duniya lafia Aljanna ta zamo makomata , fatan Allah ya nuna min ta zama mutun mai cikaken inci, ta samu nutsuwar zuciya , ta samu zama itama mutun, Anna Agaishat ta yaya hakan zai faru? A timiya mu duka bamu fi kirgo da yatsu ba, nan da kike ganina har limamin garinnnan na nemi alfarmar ya aure man ita mana aman ya nuna aa ba zai iya ba Almajirina ma ya kiye min, Gashi yau da gobe sai Allah, Agaishat girma take, mu kuwa gajiyawa muke kara yi, Idan ta fito daga nan ina ta fada? Me ta ci? Ya ta yi ta samu Allah ne masanin gaibu, ni kam a matsayina da wanda take zuwa wajensa sannan ta daukeni tamkar uba nakan yi mata nasiha, nakan tsoratar da ita, nakan nuna mata karara rayuwa da abinda Allah ya bani ikon sani Annar yara , Ba zan tirsasa maki ba, ba zan saka ki daukan abinda zaki yi ta nisawa zuciya bata da tabas, aman ina so ki yi tunanin gaba da bayan lamarin, in da hali ki dauki Agaishat ki baiwa wannan mata riko da zuciya daya, ki yi kyakyawan zato, ki saka a ranki alkhairi ne sannan ki bi da adu.a, na yi imanin koda mugaye ne Allah zai saka mata kaunar yarinyar shari ya juye wa khairi Wardugu ya yatsina fuska ya dubi Ayya dake zaune tana kallon su, da yaren tubanci ya ce" Ayya, yarinyar nan fa wannan mahaifiyarta ce , kuma ina jin shegiya ce shi ya sa wancen yake zazaginta haka! Ayya me ya sa suke faman rabuwa da yarinyar? Ayya Wardugu ya isheka haka , Ayya ta fada tana zaro masa idannuwanta, murya a kausashe ta ce" baka lura da abinda ke faruwa ne? Ba zato ba tsamani muryar Anna, cikin yaren Tubanci ta ce" ba shegiya bace, wannan da ka gani ya shige daki ya labe shine ubanta, yana kyamatarta ne dan ta zo duniya *BAK'AR FATA* Da mamaki du suke kallonta, Ayya ta taso ta karasa kusa da ita, hannunta ta kamo tana kallonta ta ce" batuba ce ke????? Anna ta lumshe idannuwanta sai ga hawaye sharsharshar ta dan jijiga hannun Ayya ta ce" ban sani ba, ban san ko mecece ni ba, Damko hannun Ayya ta yi da dan karfi ta saka idannuwanta cikin nata ta ce" ban san ko dan ina jin yarenki ba? Sai kawai nake ji zan iya sadaukar da y'ata wa ke, zaki rike mini yarinya da gaskiya? Ayya ta ji gabanta ya dan fadi, matar na tare da wani banban lamari, Ayyan ta jijiga hannayenta itama tana kallonta ta ce" mudin raina Algabiit dake ciki sai zaro ido yake, ya shiga ukunsa, ya aka yi Anna bata manta yaren nan ba? Aman abinda ya yi mata *Harta sunnanta ta manta*! Domin kafin ya lulo timiya da ita sai da ya tabata ta iya yarensa, ta iya saka kaya irin nasu, ta iya yan dabi.unsu, shigewa ya yi ciki ya zauna jikinsa na dan rawa rawa Anna ta lumshe idannuwanta, ta ce" thank you, Wardugu dake tsaye ya kalo su , Inglish kuma? Inglish ta yi? Hai san ya karasa shigowa dakin da kyau ba sai da ya karasa, inda shigowarsa ya saka du yan matan suka tsaya kallonsa da mamaki, Bak'a kuwa ta lafe da tsoro jikin baba tsoho jikinta du yayi wani sanyi tana son fahimtar maganar tafiya da wa wai ake? Ina ai ita ba inda zata, ba zata bi wasu mutanen da bata sani ba bata taba gani ba ta je a kasheta, ya zata iya tafia ta bar yan uwanta da annarta da baba Sofo? Wa zai ringa kawo masa ruwa? Wa zai ringa saya masa gogo yana gurza masa a karfen gurje goro? Wa zai ringa koya mata karatu? Wa zai ringa ce mata itama mutun ce dan tana baka Haka Allah yake son ganninta ? Wardugu yana karasowa ya dan duka yana kallon Anna ya ce" di u speak Inglish? Anna ta dago ta kale shi, ta amsa masa da kanta, a ranta tana nanata inglish? Wani yare ne shi kuwa? Ba irin wanda suke yi da matar bane kennan? Wardugu da mamaki ya ce" ya aka yi kika iya inglish? A ina kika koya? Wa ya koya maki? Daga wani gari kika zo? Anna da kanta ya fara sarawa ta dafe kanta da sauri , muryarta ya fara rawa rawa ta ce" i...i...i don't know ! Ta fashe da kuka tana rungume hannayenta da sauri Gaishat ta karasa tana rungumo Annarsu itama tana kukan za.a kuma raba su da yar uwarsu? Domin ta sani ne , a yanda anna ke jin zafin irin abubuwan da ake yiwa Agaishat , a yanda aba ya tasota a gaba da man bleating kan sai ta shafa ya yi kudinta itama , anna na neman koma waye ta bashi aurenta ta tafi ta huta, ta gwamace ta tafi ta auri koma waye da aba ya yi kudinta itama kar a je ta fada irin rayuwar da fatimata ta fada ko ma wace ta fi ta Sai da Anna ta yi kuka mai isarta, suba bata hakuri kafin take share hawayenta ta yafito Bak'a sake kukan yan uwanta da mamanta na kuka A hankali ta taso ta nufo Anna Tunda ta taso suka sauke idannuwansu kanta Wardugu ya tsura mata ido, a ransa ya ayyana " Eh lale baka ce, tana da baki sosai da kuma kazanta, a rayuwar kauye dole su tsangwameta domin gari ne mai bambace bambance Kawar da kansa ya yi, jikinsa ya yi sanyi da lamarin uwar yarinyar, tabas akoy bamban al.amari a tatare da ita, da farko ya so ya cakula abin, ya kasance an watse su yi tafiarsu ba tare da Ayya ta kwaso masu wani jangom din ba, sai dai ina yanda matar ta yi yarensa tar tar tamkar nata, sannan ta shiga turanci tamkar yarenta shima, kuma ta furta bata san bama sunnan yaririkan da ta yi, harma ta shiga wani yannayi dan za.a takurata da tambayoyi ya saka shi yin sanyi, a hankali ya furta" sai na san su waye ku! Anna ta kamo hannunta ta zaunar da ita daf da daf, ta dago fuskarta, abinda bata taba yi ba irin kusancin nan da yar tata, tana so ta yi tana mugun tsoro da kunya Murya a raunane ta ce" Agaishat, Ina son ki Da sauri Agaishat ta kara kallonta, Anna ta sakar mata murmushi ta ce" sosai, ina son ki, kuma ina so ki samu canjin rayuwa, bana so ki kare a haka bana so ki kare a ciki duhun rayuwa Gaishat ta ce" Anna, Anna Anna ta kallota ta ce" menen Gaishat? Kar na raba ku da yar uwarku? Na san muna cikin jimamin mutuwa, muna cikin rudu, aman ku kun fi kowa sannin rayuwar da muke , mutanen nan na tafia in dai ba da ita ba na yi imanin ba zai barta ba tunda ya saka wannan lamarin a ransa sai ya aikata Da wa zai hadata? Ina zata fada? Mai yiwuwa idan aka tsilira da ita wani wajen koda ta so guduwa ishrwa ta kasheta a hanya, Agaishat ta fashe da kuka jikinta ya kwashi rawa ta ce" Anna aa, aa Anna, kar ki bada ni haka Anna, ku kadai na sani Anna, kar ki raba ni da ku, kar ki yi mini haka Anna, ki barni ina ganninki har in mutu, ki barni ina gannin baba Sofona ina kai masa ruwa yana kiya mini karatu, ni ba ruwana Aba ya yi ta dukan nawa ba komi Anna in dai ina ganninki ina gannin yan uwanna ina gannin Baba Sofo ya isheni Anna, kar ki rabani da abinda nakeda a duniya wato ku........ To jama.a ya zama kwashe ne? ............m 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣7⃣ Anna zuciyarta ta yi mugun karyewa Hawaye yana shatatar mata muryarta na rawa ta ce " Agaishat, ki yi hakuri ki bi su, ba mugaye bane Agaishat ta buda idannuwanta da kyau ta ce" kina da tabacin ba mugaye bane? Kina da tabacin su din mutanen kirki ne?? Jikin Annan ya yi sanyi ta sada kanta Gaishat dake hawaye itama ta matso ta dafa hannun Agaishat ta ce" Agaishat.... Anna ta dago ta ce" bani da tabacin halayensu, ba zan ce su din mutanen kirki bane kuma ba zan fadi akasin hakan ba Agaishat, ni da na haike ki, ni da na yi rainon cikinki, na haife ki , tunda kika ji na ce ki je, toh ki je din kawai....ba zaki fahimci girman maganana ba sai ranar da Allah ya nuna maki kin haihu, soyayar dake tsakanina da ke na iya cewa ki je to ki yarda da na yi imani na barwa Allah komai ne, a nan kike ko a wani wajen dama shi ya halice ki, ko wace rayuwa zaki fuskanta shi ya kadaro maki, ni ban isa na hana ko na saka ba sai dai na yi ta kai kukana wajensa ina neman jin sanyi daga wajensa Agaishat ta rintse idannuwanta, ita bama bin nasu ba, wannan mutumen da suke tare wanda yake tsaye tunda suka zo wanda fuskarsa bata ga saki ko tausayi a tatare da ita ba, shi take tsoro, in dai mugaye ne ta san shine mai yanka mutanen domin wannan da gani shine bamban mugun Algabiit dake daka sai sintiri yake, haka zata tafi? Ba.a bashi komai na kudin tafia da ita ba? Koda ba yarsa bace ai shi yake ciyar da ita tunda aka haifeta, ya isa a yi shawara da shi sannan a biya shi! Sai dai yana ganin yanda wardugu ya diro daga motar nan ya nufosu, tun a lokacin ya fara sakin fitsari domin shi yama yi tunanin an zo kashe shi ne, ba zai fita gaban wannan mutumin mai kwarjini ya yi wani abin ba, aman ta yarda ta bada Bak'a haka zata gane bata da wayo! Bak'a na ji tana ganni, tana gurzan kuka mahaifanta da rai ba babu ba, ba aure ba ba dangi ba aka fitar da ita tana waiwayen Anna da ta koma da sauri ta shige bayi ta rufe ta shiga rizgar kuka, aka shiga da ita cikin motar da bata taba gani da idannuwanta bama bale ta shiga, Tana ji tana ganni matar nan ta shiga ta riko hannunta tana dan murzawa Alamar rarashi Tana kallon baba Sofo har aka sako shi motar shima kafin da kyar sai da Wardugu ya yiwa Walyn tsawa ta shiga motar wai karni take ji na bak'a, ya shiga suka tayar tana ji tana ganni aka bar anguwarsu gidansu yara sai bin bayan motar suke suna ihun murna sun ga mota manya sai daga hannu suke har sai ta bace da ganninsu aka je kofat baba sofo aka tsaya suka sauke shi Agaishat ta kara rikicewa gannin da gaske sun bar baba Sofo wanda ya tsaya yana daga mata hannu idannuwansa sun kara kodewa alamun kuka yake na zuci sai dai ya fi farin cikin hakan da zamanta a garin Haka suka dauki hanya ba tare da sun huta ba ko sun sha ruwan garin ba suka dibi hanyar komawa garin Agadez Kukan take tana fadin"" Anna, Sofo, Anna, sofo Walyn ta ja tsaki ta ciro ecouteurs dinta ta saka a kune, Wardugu dake gaba ya rufe idannuwansa a tunaninsa zata gaji ta yi shiru ne aman ina sai kara boda Agaishat ke yi Ayya na tausarta tana bata hakuri da tubanci bata san ta dan iya hausa ba ita kuwa bata iya buzanci ba Juyowa ya yi, da yaren buzanci ya ce" Ke ki rufe mini baki a nan tun kafin na saukeki na yi maki dukan tsiya, shiiit bakin nan naki ya mini shiru ko na ciro maki shi a hannunki Wa ya ga hadiya, Agaishat hadiye kukanta ta yi, tana zaro ido tana kallonsu daya bayan daya tana sauke ajiyar zuciya, Ayya tana magana tana yi mata nuni da ta yi hakuri ta yi shiru ta daina kuka A hankali Agaishat ke ajiyar zuciya sannan ta damke hannun Ayya wace ke rike da nata itama, tana kallonta, a nan ita kadai ta dan hangi laushi a tare da ita Tafiya suke suna ratsa sahara har suka baro suka debi titi, Agasihat ko dis ba baci a tare da ita sai kallon titin da take , tsoro fal ranta haka idannuwanta suka nuna, mamaki take dama Shukoki na gudu? Domin yanda motar ke gudu sai take gannin suma shukokin gudu suke tun karfinsu Walyn dake takure tana sakin numfashi sama sama ta shiga yinkurin amai tana kakari Ayya ta kai dubanta wajenta da mamaki, lale walyn bata da mutunci, yanzu du irin yanda ta fafeshe su da turare tana jan tsaki kuma ta kai amai zata yi dan warin Yarinyar da suka dauko Ta girgiza kai kawai ko ci kanki bata ce da ita ba Wardugu dake zaune a ransa ya ayanna Walyn bata son zaman lafia, in dai Ayya ce ta isheki ba abinda ya dame ni! Ba su su karasa cikin gari ba sai can wajen karfe goma na dare Abinka da agadez ma ba wani banban gari sosai bane sai ya kasance shiru garin sai yan mata da samari wasu na tafe a kafa wasu a mota wasu a mashin suna dan yawansu na yau da kulun wasu sun nufi gidan rawa, wasu sun tafi gidan cin abinci, wasu suna yawatawa dan shan iskan gari kuma suna hirarsu Idan ta juya can sai ta juyo nan, kallo take irin na kauyawa sosai jikinta kuwa har zuwa wannan lokacin bata saki ba, sai dai ta rakube jikin Ayya wace take kara rike hannunta dan ta saki jikinta Direct gidan Sarki aka kai su Ayya, har ciki suka shiga da motar suka sauke su Ayya Walyn sai sauke ajiyar zuciya take ta rabu da alkakai Har sun juya motar Wardugu ya ce" tsaya Sojan ya ja ya tsaya , Wardugu ya juyo wajen Walyn ya ce" sauka ki kwana wajen Ayya Walyn ta dago da sauri daga kakabe kakaben jikinta ta zaro ido ta ce" me me ka ce? Wardugu ya tsareta da wani kallo na kar ki raina min wayo Walyn ta ce" aman Wardugu , wani irin na sauka na kwana a wajen Ayya bayan ga mijina wajenka na sauka kayana a wajenka komaina na tare da kai? Yama zaka raba ni da kai ka hada ni shakar iska daya da wannan mumunar yarinyar mai siffar aljannu Yatsina fuska ya yi, a ransa ya ce wai siffar aljannu, ko a ina ta san aljannun ita? A fili kuwa ya ce" Haka na yi ra.ayi Walyn ta ce" Wardugu kar ka yi min haka, me na maka? Kar ka yi min irin horon nan! Wardugu ya kalli sojan nan ya ce" sauka mu je Sojan dai bai ce komai ba ya bude ta fita da bindigarsa yana kallon ikon Allah Wardugu ma ya fito ya rufe ya tafi wajen sojan ya fara tafiya, sojan ya waiwaya ya ga a yanda suka ajiye motar a bakin hanya, bayan wannan matarsa a ciki, sannan tsakanin fadar da hotel din sojojin akoy tazara, kuma idan mutun ya tunkaro wajen haka kai tsaye daga bakin karfe goma na dare ordre da aka baiwa sojojin shine harbi ba ji ba gani in dai ba a mota ko wani abinda yake malakinsu ba wanda da ya tunkaro wajen akoy adadin odar da aka ce su yi dan shaida su ne wada kowace safiya ake canzawa Shi dai biye yake da shi da sauri yana hadawa da fan gudugudu suna tafiya har suka fita daga gidan suka dauki hanya (🤔 sisi kika ce zaki iya da wardugu ko?🤣) Walyn wani ihu ta saki a daidai lokacin da ta fahimci wardugu bara mata ya yi motar gaba daya ya tafi a kafa da ya je da ita, Wardugu ita yake wulakantawa? Toh ita kuwa ba zata shiga wajen wannan uwar tasa da wannan yarinyar mai karnin jini ba! Sai dai ta kwana a motar! Haka ta takure a motar nan ta ki kunna hasken waya dan a gaskiya tsoro take ta kunna waya wani abin ya lura da mutun tun bama dare da ya tsala maguna suka fara kukan jarirai ba, Kawata, tsakaninki da Allah ke haka rayuwarki wata irin mace ce bahaguma? Yanzu yarinyar nan da kika kwaso kin san asalinta ne? Ayya ta yi murmushi tana kallon kawarta aminiyarta matar sarki, ta ce" mamanta ta iya tubanci Anna matar sarki ta dafe kai ta ce" dan ta iya tubanci sai me? Dan ta iya yarenki shikennan sai ki wani kwaso yarta? Kin ce a gidansu kuka daukota Ayya ta ce" ki gane kawata, lamarin mahaifiyar yarinyar da yarinyar ne akoy sarkakiya, wai kawai dan kalar fatarta shikenan take fuskantar tsangwama, ita kuwa uwar sai kawai ki ji tana yare kuma wai tace itama bata san sunnan yaren ba, kuma ni na yi haka ne dan cika alkawarin bawan Allahnan, baki ga yanda ya tsufa ba aman haka yake nisa lamarinta, Anna matar sarki ta dafe kanta da hannunta dake cike da zobunnan zinari ta kalota ta ce" ai idan kin lura yanzu wannan matsakar ta zama ruwan dare, a kauye suna kin bakar fata tare da jahilci a birni suna kiyaye bakar mace dan dogon buri irin nasu sannan suna hakan ne da dabara, kina ganni daidaiya zaki ga a yanzu mutun ya tashi ya dauko bakar mace, sai ki ji suna fadin Allah ya basu farar mace koda maya ce, banza idan ta cinye su fa? Ayya ta dora kafarta daya saman daya tana ajiye tufar da ta gutsura ta ce" ba ko.ina ba, ban ki maganarki ba aman nima nace maki ba ko.ina ba, Du macen da kika ga ana yi mata duban marar kyau ko anai mata wani gani gani ina mai tabatar maki ita ta saki kanta, Mace du muninta idan ta iya wanka ta iya kula da jikinta ta iya kwaliya daidai da yannayinta sai ta kara da adu.a kawai Sannan ita bakar mace da kike ganni baiwa ne da ita, bakar mace tana da kwarjini, bakar mace nada juriya a kowani fani, bakar mace na da kyau mai fuzga, idan bakar mace ta sakar maki tsararen murmushi zaki hangi haske ne a tatare da ita, ke kawata zaki sha mamakin yar amanata in sha Allah Anna matar sarki ta yi murmushi tana jujuya kanta ta ce" oho dai, kina kare bakar fata dan kina da ita bayan taki mai kyau ce, na rantse maki ko ni na samu taki ina so domin bakinki mai kyau ne, ba gashi ba Wardugu ya samu dan bakinki da farin mahaifinsa sai ya samu kalar fatar nan ta yan ethiopia baki ga yanda fatarsu take ba? To aman wannan yarinyar kina ganni da akace wanka ta saka kuka aman kika biye mata wai kika rakata ta yi baci a haka? Anya kuwa zaki iya wani gyarata? Ayya ta ce " ki saka ido kawai..... Sojan nan tafiya dai yake aman ba karamin gajiya ke tatare da shi ba, sai ya ga Wardugu daga kafa kawai yake yana jefawa yana kara kutsawa cikin duhun garin suna ta sauki su karasa hotel din Ba su su karasa ba sai kusan sha biyu na dare, Suna karasawa Wardugu ya saka kai kai tsaye ya nufi shiga wajen da idan ka shigo harbi ne zai salamo maka .................... Kadan ne ku yi maneji😍😍😍😍 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣8️⃣ *Godiya ta tabata ga Allah sarkin sarauta ubangijin talikai, godiya mai dumbin yawa gareku da adu.a Allah ya saka da alkhairi ya biya ....* *Khadijat tawa ta grup BAK'A CE* wannan page din naki ne Ja sojan ya yi ya tsaya bai san lokacin da ya ce " Oga, zone interdite ce fa Wardugu ya juyo yana kallonsa, ya yi murmushi ya ce " tsoro kake ka mutu sergent? Kansa ya dan shafa yana kallo Wardugu, wardugu ya kara cewa" mutuwa fa ko kana kan gadonka sai ta daukeka sergent ba gwara mu tunkareta ba? Kara kwalalo idannuwansa ya yi yana kallon wardugu Wardugu ya matso ya dafa kafadarsa ya yi murmushi ya ce" mu je ...... Haka suka kutsa gaban Sergen din nan tamkar ya bale ya fado dan tsoro, Sai dai ga mamakinsa sai ya ga sun kama wata yar raga a nan Wardugu ya bude ya shige Shima shiga ya yi yana ta waige waige yana biye da wardugu nan ya hango ashe har sun shiga balbalin hotel din sun fice hatsarin Wara wawar ajiyar zuciya ya sauke yana biye da wardugu Wardugu ya rage sauri ya dan rage sautin muryarsa ya ce" nima bana so na yi mutuwar bindiga fa Sergen, ina so na mutu cikin nutsuwa kai da zabi gareni in mutu ina sallah kuma ranar juma.a, Aman kawai yau ranar asabar gatsai gatsai sai mu tarbi mutuwa? Da juma.a ne ma, Ya dan yi murmushi ya yi gaba ya barshi nan tsaye yana murmushin shima, kai ogansa idan ya yi wani abin tamkar ba shi ba, wai shifa a nan wasa ya yi masa da rai🤔 Tun fa wuri ta farka daga bacin da ya saceta, sai dai ta ki motsawa tun a jiya da aka sauketa saman gado ta yi baci ta kasa ta sauko kasa ta kwonta saman farin tls din ta rufa da mayafinta na turkudi tana kallon yanda pankar sama ke juyawa har baci ya dauke, a yanzuma ta farka tun da wuri tana son tashi sai dai tsoro take hakan ya sa ta yi kuri da abin mamaki a fuskarta tana kallon pankar nan, mamaki take menene? Ya aka yi bai daina gudu haka ba? A gaban idannuwanta aka kunna , tunda ya dauki gudu bata ga ya tsaya ba, ita tsoroma take ya yo kasa kasa ya kasheta Ayya ce ta bude dakin ta shigo da salama a bakinta Firgigit Bak'a ta tashi ta zauna jikinta jikin garu tana bin Ayya da kallo Ayya ta yi tsam itama tana karantarta, a kasa ta kwana du sanyin nan na kasa, sannan da alama bata yi sallah ba Dukawa ta yi kusa da ita tana kallon yanda take jan mayafinta tana lulubawa a jikinta, Murya a sake ta ce" kin yi sallah? Da ido kawai Agaishat ke bin Ayya domin bata san me take fada da yaren tubanci ba Ayya ta yi dabara ta kamo hannun Agaishat ta mikar da ita ta jata suka nufi bayi Suna shiga Ayya ta dauki butar karfen dake wajen ta kunna ruwa mai dumi dumi ta cika mata ta nuna mata wajen da zata iya dukawa domin ta san ba wani gane lamarin wc zarai ba tukunnan dai, ta yi mata nuni da ta yi dagara ta yi alwallah ta yi sallah , ta yi mata nuni da har rana ta fito Da kai Agaishat ta amsata tana kallo sai da ta fita ta duka ta yi fitsari nan inda aka nuna mata ta wanke jikinta ta mike ta yi alwallah tana jin dadin yanda ruwan keda dumidumi Tana gamawa ta fito ta ga salaya aman ba kowa a wajen dan haka ta hau ta tayar da sallah ta yi abinta cikin nutsuwa kamar yanda Baba tsofo ya koya mata Tana gamawa ta zauna ta hade kanta da gwuiwarta tana zubar da hawaye, tunani take ya Anna ta tashi? Ya yan uwanta? Ya baba sofo? Wa zai kai masa ruwa? Wa zai gurza masa goro? . ..... Buda kofar aka yi aka kuma shigowa , Wannan karon matar sarki ce da wata baiwa buzuwa da kuma Ayya Ayya ta kali matar sarkin ta ce" so nake a fada mata ina so ta yi wanka ta shirya mu tafi garinmu domin Wardugu yace jirgin karfe daya zamu bi Matar sarki ta yi murmushi har yanzu tana mamakin daukarwa kai irin na aminiyarta, ita da ko hausar juna basu iya ba Ta kali baiwar nan cikin isa da dakewa ta fada mata abinda zata fadawa Agaishat wace tunda matar sarkin ta fara fadi take kallonta daga zaunen da take tana fahimtar yarenta Kafin ma baiwar ta fadi Agaishat ta kallo Ayya, a hargitse ta ce" ina zamu tafi kuma? Kar ki kaini wani wajen kin ji? Ki barni a nan ma Tana fada ne tana dan nufo su Ayya dake tsaye Baiwar ta yi saurin tareta , da yaren buzanci ta ce" ki tsaya nan, kin san ina ne kike a nan? Kina garin agadez, a garin agadezma kina masautar agadez, a masarautar agadez ma gaki gaban matar sarki uwar gida sarautar mata, Ki koma baya ki cika umarninta Rakubewa Agaishat ta yi tana kallonsu, ta shiga ukunta, ya zata yi? Matar sarki kuma? Ko sarkin garinsu talaka bai isa ya yiwa matarsa ko yayansa wargi ba bale na garin Agadez Kanta a sade ta ce" zan yi wankan Ayya dake tsaye ta karaso kisanta tana kamo kafadunta ta kallo aminiyarta ta ce" me ta ce mata? Sai nake gannin kamar ta tsorata? Kar ta tsorata min yarinya fa kar ta rikitata Anna dariya ma kawai yannayin Bak'a ke bata, ta fadawa Ayya abinda aka yi Ayya ta dafe kanta ta zabgawa matar nan harara ta ce" ku tafi abinku tunda dai ba zaku tausasa ba, idan ita sarauniyarta ce ke ni ai aminiyata ce, bana son irin yanda kike nunawa kan yarinyar nan, kina manta mutun ce itama ? Anna ta yatsina fuskarta ta ce" kin ga bara na je na ga in an kawo kayan da kika ce kina so, gaskiya ki yi hakuri ba zan iya wannan faman ba Ayya na kallo Anna ta juya baiwarta ta bi bayanta suka tafi Zaunar da Bak'a ta yi gefen gado wace ta takure waje guda, ta juya ta fauko wayarta ta zauna ta danna kira Ana dagawa ta ce" kana ina? Amsawa ya yi da" gani gefen aghali muna ratauna wata magana To ka bari ka zo yanzu yanzu nan bangaren da aka saukeni ina ciki ina jiranka Da toh ya amsa ya mike yana cewa Aghali ina zuwa 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 1⃣9️⃣ Shiga ya yi ya zarce dakin Ayya ya tarar bata nan sai ya fito ya shiga dayan dakin, daman falo ne mai daki biyu, Yana shiga ya tarar da ita tsaye , Bak'a kuwa zaune inda ta ajiyeta Karasawa ya yi yana tambayar lafia? Ta amsa shi cikin kulawa ta tambayeshi kwannan iyalinshi Ya yi murmushi dan ya san Walyn bata zo nan ba kennan wajen matar sarki ta je? Ayya ta ce" Wardugu, zo ka yi mana fasara da y'ata ka ji? Ina son yi mata magana yanda zata fahimta aman ban lamunce maka ka rikita min ita ba ka ji? Da mamaki yake kallonta, daman shine dalilin kiran nasa? Kai? Yanzu Ayya ya zata yi idan baya nan toh? Kai kawai ya dan girgiza ya karasa inda Agaishat ta kara rakubewa jikinta ya fara rawa ta nuna alamar tsoronsa take ji Ayya ta ce" Wardugu ka yi wani abin mana, ka ga tsoronka take ji, bana so dan Allah Wardugu ya sauke ajiyar zuciya ya kali Ayya ya kara kallonta, uwa uwa hummm Karasawa ya yi ya dan rage tsayinsa yana kallon yarinyar, kokari ya yi ya saisaita maganarsa ya ce" me ke damun ki? Kallonsa take ita kuwa, irin kallon nan na kana jiran gannin me za.ai maka Wardugu ya dan rontse idannuwansa ya bude ya ce" kin ga, mu fa ba mayu bame, ba mugaye bane kamar yanda kike tunani, mamanki tace mu zo da ke, idan kika kwontar da hankalinki kika nutsu sai ina kai ki kina gaishe da mamanki, kinga dai yanda kuka yi da ita ko so kike a mayar da ke ne?? Tsam ta yi tana kallonsa bata bashi amsa ba Ayya ta matso ta ce" me kake ce mata? Wardugu ya kali Ayya ya ce" ba komai Ayya ta ce" to ka ce mata ta tashi ta shiga ta yi wanka , ko na yi mata da kaina ma Ido Warsugu ya zaro, sai kuma ya basar, ya kaleta sosai ya ce" kin ce Sofo na koya maki karatu ko? Kai Agaishat ta shiga daga mai Ya ce" yawa, kuma sofo ya fada maki tsafta na cikin adini? Sai mai tsafta zai shiga aljannah fa Agaishat ta kara gyada masa kai, Ya fara jin haushin gyadegyadan kan nan, aman Ayya na wajen ta kasa ta tsare, ya tausasa murya ya ce" toh ki tashi ki shiga bayi, Ayya ta nuna maki kayan wanka ki yi wanka sosai kin ji? Kai ta kuma gyada masa ta mike tana kallon Ayya, tunda ta ji yace za yana kaita wajen Annarta zata gwada yi masu biyaya ...... Ayya da jin dadi ta rakata bayin ta kuna mata ruwa masu dumi sosai ta bata sabulu da soso sababi, ta bude bruch da maclean ta mika mata ta yi mata nuni da yanda zata yi , Har ta juya ta dawo tana nunawa ta ce" ki cuta jikinki lungu lungu sannan ki wanke tafin kafafuwanki kin ji Kai Agaishat ke gyadawa har Ayya ta gama ta fice A hankali ta tube kayan jikinta, ta yi tsaye gaban ruwan tana kallon yanda yake zuba Da tsoro tsoro ta tara hannunta ta janye, ta kuma tara ta janye hardai ta yarda da ruwa ne ke zubowa kuma ba zai konata ba A hankaki ta shiga tana bismillah a ranta ta yi tsaye ruwan ya shiga kwararun mata a jikinta tun daga kanta dake da kitso kwaya daya tal har jikinta Sai da ya gama dukanta ta dauki sabulun ta shiga gogawa a jikin soson tana jin yanda kamshinsa ke tashi tana jin dadin kamshin A hankali ta shiga cuda fuskarta da soson nan ta cudeta da kyau ta darwaye kafin ta shiga wanke wuyanta sosai da bayan kunnayenta da cikin kunnen ta gangaro hamatarta kamar yanda Ayya ta nuna mata ta daga ta kama dirza ta yi kasa ta wanke jikinta sosai ta bi ruwan nan ya shiga darwaye mata kumfar da har ta zama baka dan tsabar datin dake jikinta, tana kallo ruwan na bin yar magudadar ruwa yana tafiya Ta koma ta darwaye soson ta kara yin yanda ta yi , ta shiga saba sabulun a tufkeken gashinta na buzuwar usul ruwan nan na dareaye mata, Abinka da tufkeken gashi wani wajen ya wanku sama sama aman cikin kam da datinsa daskare, haka Agaishat ta yi ta wanka tana sakewa tana jin kanta wani sakayau tana kara balbaluwa a cikin ruwan nan tana jin dadinsa abinka da ba sabanba ta wanke tafin kafafuwanta da abinda Ayya ta nuna mata nanma ta ga dati sai fita yake , har yatsarta ta saka ta debo datin tana kallo da gaske dati ne ta wanke da sabulu tana daga kanta sama ruwan na shiga idannuwanta yana kara ratsa gashinta da jelar ta sako tana yawo du idan ta juya kan Fitowa ta yi ta dauki kayanta wa.inda sai a lokacin ta ji suna wani irin bugawa da ta rabu da datin jikinta, har ta shiga tunanin ko ta wanke? Sai wani abin yace mata idan kika wanke ki saka me kuma? Mayar da kayan ta yi ta fito ba tare da ta kashe panpan ba domin bata iya ba Ayya dake zaune tana jiranta domin Wardugu ya tafi abinsa , ta mike tana fadin" eyah Agaishat ki cire kayan nan mana Agaishat ta yi kasakai tana kallonta Ayya ta dafe kai ta ce" wani yare kika iya Agaishat kin iya frencais? Angalais? Ko hausa? Agaishat dake kallon Ayya ta ce" Ayya, hausa kadan kadan Ayya cikin itama dan yaren hausar nata ta ce" ouf , mun samu na gaisuwa, ki fida kayan nan ki canza wasu kin ji Agaishat ta gyada kanta tana kallon wa.inda Ayya ta nuna mata, sannan ta juyo dan gannin a gaban Ayyan zata saka sai ta ga Ayya ta nufi kofa abinta Ajiyar zuciya ta sauke ta tube kayan ta dauko wa.inda aka ajiye mata Tsayawa ta yi tana kallon doguwar rigar abaya baka wace bata san ina ne gabanta ko bayanta ba sai dogon wando wanda ta daga tana ta jujuyawa irin na maza ta ayanna a ranta sai dai ba irin na mazan garinmu ba domin wandunnansu tamkar buhu........ Da daurin kirjinta tana tsayen nan Ayya ta dawo ta ga bata saka kayan ba Nufota ta yi ta ce" aa ya baki saka ba? Agaishat ta mika mata ta ce" Anna ban iya ba Ayya ta yi murmushi ta shiga nuna mata ta juya ta saka wandon da kyar domin ya yiwa jikinta kadan duda fadinsa da yanda kuma yake jayuwa, Ta dora rigar ta kule yar igiyar dake ciki Ayya ta juyo tana kallonta, ba laifi kayan sun amsheta sai dai sam wankan nan bai yiwa ayya ba , gani take bata wanku ba da saura duda yanda du wani jirwayi na turkudi da fari fat din nan ya fita Mai ta miko mata ta shafa , ta miko mata turare ta tayata shafawa Agaishat bata san tana sakin murmushi ba sai da ta waiga wajen madubi A hankali ta taka ta karasa, hannunta ta mika ta taba madubin tana kallon kanta, a hankali ta juyo wajen Ayya ta ce" na gode Anna Ayya ta karaso da dan kalabin rigar ta kama kanta da bai karasa bushewa ba ta saka mata ribom ta daure mata sannan ta nada mata dan kwalin ya zagaye fuskarta Kwali ta dauko ta nuna mata da ta shafa , Agaishat ta ce bata iya ba , hakan ya sa Ayya ta saka mata idonta ya fara ruwa ruwa abin rashin sabo Ayya tace ta jure karta murje ta kuwa juren Abin maskara ta dauka ta fitar da shi ta saka wani mouchoir (kyale) ta goge bakin jikin tas tas, ta dauki jagira mai ruwan baka ta gogoga a jikin abin ta samu ta caje girar bak'a, girar ta kwonta tsaf a inda ya kamata ba kamar da farko yanda take wawatse ba Ayya ta juyata wajen madubin ta ce" Agaishat, Tsafta, kwaliya, ya zama wajibi ga macen da ta san ciwon kanta, ki rike wanka , ki kasance mai tsafta kin ji?? Kai Agaishat ta daga tana kallon kanta da mamaki, tamkar ba ita ba, ta sawaya hancinta ya wani tafi zuwat, wai a nan Ayya bata gamsu da wankan ba jira take dai su karasa Niamey ta dauki lamarin a hannunta.......... Karfe sha biyu da minti arbadin suka fito daga masarauta suka nufi aeroport, ita dai Ayya bata san yanda wardugu ya yi ya samawa Agaishat waje ba bata tambaye shi ba Sauran minti biyar suka karasa, suna zaune Ayya na kallonsa yanda ransa ke bace, bata ga Walyn ba bata tambayi inda take ba domin ba wani shiga lamarin juna suke ba, bata san zuwanta ba sai da ta ganta daga ina kwana wani abin bai kara shiga tsakaninsu ba sannan dan yanzu bata ganta ba itama ba zata wani tambayi inda take ba , Allah ya basu zaman lafia ita da mijinta ba abinda ya shafeta da zamansu haka kuma ba zata shiga dan wani gyara ba! Ba.a jima ba suka mike domin an fara kiraye kirayen sunnaye, Ita dai agaishat tunda aka haliceta bata taba gannin jirgin bama bale wai har ta shigeshi Ta dai bi bayan Ayya da ta kama hannunta ta shiga nuna mata yanda zata taka matatakalar ta hau suka hau tare tana kara rike Ayya da kyau dan kar ta fadi har suka shiga Kallon tsarin cikin jirgin take a ranta ta ayanna ba irin na mota ba , Nan Ayya ta tsaya sai da Wardugu ya shige kusan madubin domin sam ya hannata zama a nan in dai tafiar jirgi zata yi, ita dai sai dai ta yi murmushi kawai irin yanda yaron nata ke sonta ke kokarin kareta har mamakinsa take , Yana shiga sai ta saka Agaishat ta shige tsakiya , shi kam bai yi magana ba domin ransa a kololuwar bace yake, wai Walyn ta bi jirgin damagaran gobe ta bi na niamey ta karasa, shi zata nunawa zuciya ko? Han...... Ayya ma ta zauna ta ja ceinture ta sakawa Agaishat sannan itama ta saka bayan ta kashe babar wayarta ta android Ba.a jima ba aka shiga fadin a daura ceinture a kashe waya da yarurukanmu na niger da kuma french da inglish duka , bayan an gama jirgin ya fara tafiya wace suuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu ne saman doguwar hanyarsa har ya zo wajen hatsarin wato tashi da saukar jirgi ba, Cikin adu.a a bakin Ayya Nan fa ake yinta domin abin tashin jirgin nan, kun san ko wanda ya saba sai ya ji cikinsa ya yi kasa bale wanda shigarsa ce ta fari kuma sha.af Ayya ta sha.afa da fada mata abinda kan iya zuwa sannan tace da ita tashi zasu yi sama, ita kuwa a kauye baba sofo ya taba gaya mata akoy harda wani abin mai tashi sama a birni sunnansa jirgi , Ai gaba daya ta shiga jijiga ta damki cinyar wardugu dake gefenta na dama ta damko ta ayya ta bude baki ta........ 🤣🤣🤣🤣 ku taro su kauyawa a birni🤣😂😂😂😂😂 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣0️⃣ Ido Wardugu ya zaro, ya kai kallonsa kan hannunta wanda ke dauke da dogayen akaifu domin ba wani cire su take son yi ba sai baba sofo ya sakata gaba take yanke akaifunta sai tace nai ai susa take da su, Wardugu bai gama tantance meye haka ba ya ji wani irin ihun da ya yi barazanar tarwatsa masa dodon kunne, A tare suka juyo wajenta shi da Ayya ...... Ayya cikin yannayin tashin hankali da yaren tubanci ta ce " Wardugu Wardugu tsoro ne take ji na manta ban fada mata ba, kuma ban riketa ba , mai yiwuwa bata taba ganninsa bama bale ta shiga; Bak'a da jikinta ke bari gaba daya ta kwalallo idannuwanta, daurin dan kwalin nata ya kunce , hawaye tuni sun kama zarya, ihu kawai take tana ambatan innalilahi wa.ina ilaihi raj.une! Mutanen dake kusa da su harma wa.inda ke dan nesa da su ne hankalinsu ya fara tashi du aka fara jiyowa wajen su Ayyar da ayyar tambaya da alamun tsoron a fuskokin su.... Daga can kofar masu kula da passenger wata mata mai kulawa da bukatun passenger ta fito da sauri da dan sket dinta, ta sha kwaliya, tana dan sauri tana fadin kowa ya zauna kowa ya kwontar da hankalinsa ba komai bane , sannan tana nufo wajen su wardugu; Hannunsa ya daga na dama ya shafa sumarsa, a kasan zuciyarsa ayannawa yake wannan wani irin tashin hankali ne? Shi Wardugu da girmansa da irin yanda duniya ta san shi, shine za.a yiwa taro da yar kauyen nan! Merde! merde! merde! Juyowa ya yi wajenta, hannunsa na hagu dake kusa da ita ya saka ya janyota jikinsa, ya sakata a jikinsa da hannun nasa ya karkata fuskarta gefen hannunsa na dama , ya saka hannun nasa na damar ya yiwa bakin nata mai ihu wata damka ...ai kuwa shiru kake ji ba ihu ba di kira da salamcewa sai dan mutsu mutsu wanda shima da ya kara riketa sai laf tamkar ta lafe ne a jikinsa. (WARDUGU kan keta) Tambaya matar nan take lafia ? Me ke faruwa?? Wardugu gannin bakuwa ce yar amerika, sai ya ciro carte dinsa da hannun hagu dinsa ya nuna mata mai shaidar ko shi waye, sannan da lebensa ya yi mata nuni da mahaukaciya ce kar ta wani damu........🤔 Ai kuwa ta shiga bada hakuri da iya yi, ta juya ta koma. Ayya sai faman ya cika yarinya take aman ya tsareta da ido ya ki yin maganama; Nauyin da ya ji ta yi ne ya saka shi sasauta rikon, ba.a wani dauki lokaci ba Agaishat ta yi baci sai kace wata baby, bacin tsoro da tashin hankali, bacin wahala, gashi daman daren jiya ba wani bacin kirki ta yi ba dan tsoro da zulumi, sai ajiyar zuciya take saukewa du ta goge hawayenta a jikin rigar wardugu. A hankali wardugu yake kokarin kwontar da ita jikin kujerarta, Ayya ta zabga masa harara ta jinginar da Agaishat a jikinta tana kara tabata dan tabatarwa in ba suma ta yi ba. Murmushi Wardugu ya yiwa mahaifiyarsa na alamun bada hakuri kafin ya jingina yana duba agogon hannunsa domin tafiar idan Allah ya yarda ba wata mai tsayi bace a jirgi tsakannin Agadez da Niamey. Allah ya sauke su lafia, Wardugu da kansa ya tuka motar da ya je da ita ya ajiye aeroport , Bai zame ko.ina ba sai gidan Ayya. Suna zuwa Ayya ta yi hamdallah ta kamo Hannun Bak'a wace ke kallo da baki da hanci da ido gaba daya Fitar da ita ta yi ta ce" mu tafi yar gidan Ayyarta A hankali ta fito itama kamar yanda Ayya ta koya mata ta bi bayan Ayya tana waiwayen Wardugu da ya fitar da kafarsa guda waje yana ta faman yamutsa gashin kansa, wayarsa ya ciro yar karama ya dannawa abokinsa kira wato docter DOCTER MU.AZAM Yana dagawa ya ce" Ranka ya dade oga *Wardugu Marahut* Wardugu ya ja tsaki ya ce" Mu.azam ni za ka yiwa rashin mutunci? Yaushe ka fara karya? Mu.azam ya yi shiru, ......tamkarma ya kashe kiran. Wardugu ya duba ya ga kiran na tafia, ya kara karawa a kunnensa ya ce" kai! Mu.azam ya sauke ajiyar zuciya ya ce" abokina, ka yi hakuri ka ji? Jikina ne ya tashi aman yau nake fita asibiti in sha Allah da na huta sai na kamo hanya. Wardugu da ya gama jin abinda ya fada, cikin mutuwar jikin da bai san ko na meye ba ya ce" me ke damun ka ne harda kwonciya hopital? (HOSPITAL) Mu.azam dake kallon karin ruwan da aka saka masa ya lumshe idannuwansa, jiki a mace ya ce" idan Allah ya kawo ni zan fada maka koma menene, Wardugu ya sauke ajiyar zuciya, bai bashi amsa ba ya katse kiran ya rufo motar ya tayar dan ya samu ya karasa gidansa ya huta .......................... TIMIYA Rana ce, karfe biyu na rana ne, aman da dan lulumi kamar yanda garin ya saba, A kasan innuwa suke zaune su uku suna yamutsa garin kwakwi da mai da yaji da manda (gishiri), Fatimata ce mai kwadawar, Ayya na yiwa maryama susa a kanta Mariama ce ta dago ta ce" Fatimata kar ki hade yajin nan duka ki ware min a robar nan kuma kar ki zuba mai iya shi din sai mandan ya isa kin ji? Fatimata ta amsata da kai, Ayya dake mata susa kuwa a ranta take tambayar kanta Mariama ko ta daina cin yaji ne? Kai ina Mariama da yaji ai akoy amana. Fatimata na gama warewa, Maryama ta mike ta dauki dankwalinta ta daura, ta dauki robar ta nufi wajen tulun Anna kwaya biyu dake cike da ruwa ta dauki guda ta dora saman kanta ta kama hanyar fita, Kallonta suke da mamaki, Fatimata ta ce" Mariama ina zaki tafi kuma? Ki bari mu ci mana. Mariama ta juyo ta ce" ki ware min nawa, zan je wajen Sofon nan na Agaishat na dubo shi ne, Murmushin da Anna ta jima bata yi ba ta saki, sanyi ta ji a ranta daman tana ta tunaninsa halin da yake ciki mutumen kirki Mariama oga kennan, Mariama ba daukan raina, Bata zame ko.ina ba sai majalisar mahaifinta, Tana zuwa ta mika masa hannu ba alamar wasa ta ce" kudi nake so Aba, Bakinsa ya yatsina, Mariama fa ta fara isarsa da wannan ya bata ya batan, tunda ya karbi kudin aurenta take tatikarsa, idan ya nuna ba zai bada ba kuwa a ji su, Rai bace ya saka hannunsa a aljihun rigarsa ya ciro dala dari ya mika mata a ransa yana adu.ar Allah ya sa ta karba kar ta ce ta yi mata kadan! Karba ta yi ta maida tulunta da robar saman kanta ta juya ta nufi gidan mai goro.... Nan ta sayi goro har na dala Ashirin, ta sayi man zafi na ciwon jiki ta sayi yar tsintsiya, dauka ta yi ta nufi runfar baba Sofo. Tana zuwa ta yi salama har sau biyu kafin take jiyo muryarsa can kasa yana amsawa; Shiga ta yi tana wara idannuwanta dan ganni da kyau domin ta biyo rana idannuwan nata duhu suke ganni. Yana kwonce fuskarsa na dubinta, ya takure ya kara yamutsewa da cazbaharsa yana ja kuwa, Bata yi masa magana ba ta karasa inda ta ga tulun ta jawo ta fitar da shi ta wanke shi tas ta juye ruwan nan na cikin tulun Anna, Ledojin da suka shihigo da kararuwa ta tatare ta fitar kafin take juyowa ta shiga share bukar inda baba sofo ya samu ya zauna yana binta da kallo da mamaki a kasan zuciyarsa; wannan ai yayar Agaishat ce, mai fadan nan, ikon Allah kawai yake fadi a kasan zuciyarsa. Tana gamawa ta dauko robar abincin ta debo ruwa ta dawo ta darwaye hannunta ta zauna, ruwan nan ta kara yayafawa garin dan ya kara yin laushi sosai, tana yi bata ko kallonsa dan ta yi imanin ya tsareta da ido ne,............ Sai da ta kai bakinta ta ji idan mutun yace tsotsama zai yi tsaf zai tsotse abinsa ta dago da dubanta a hankali ta kai wajen baba Sofon dake kallonta ta ce""" 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣1⃣ Ta ce" ga abinci, ina magurjinka? Hannunsa dake dan rawa ya saka ya fitar da magurjin ya mika mata yana kallonta dai, Mikewa ta yi ta wanko magurjin da goron, sannan ta dauko wata yar roba mai marfi da ta amso wajen mai siyar da goro ta kara darwayeta itama, ta dawo ta zauna ta saka yar farar leda a kasan abin gurzawar ta shiga gurza goron nan manya har uku; Robar ya saka hannunsa ya janyo, bismillah ya yi har zai fara ci maganar Bak'a ta dawo masa inda take cewa < ka ringa wanke hannunka Sofo, ka ga jiki na iya daukan dati mai yawa banda ciki ka ji sofona? > Dubansa ya kai wajen Mariama, a hankali ya ce" Mariama? Dagowa ta yi tana dubansa bata amsa ba, Baba tsoho ya ce" ina kwana, Mariama ta kifta idannuwanta ba wani dar ta ce" Lafia, still tana kallonsa Murmushi ya yi ya yi mata nuni da kofin ruwan dake hannunta sannan ya nuna mata hannayensa. Tasowa ta yi ta karasa, dukawa ta yi ta kamo hannun nasa ta wanke masa da kanta sannan ta kuma ciko kofin ta ajiye masa ta koma ta ci gaba da gurza goron ba tare da ta furta masa kalma daya ba. A hankali baba ya fara cin garin nan, yana ci yana dan kallon yannayin Mariama, Mariama ikon Allah, Mariama mai albarka, A hankali ya ce" nima ina jin rashinta sosai, Mariama ta dago kanta ta zuba masa ido, murya a cinkushe ta ce" dan me ka rabata da danginta? Sai da baba Tsoho ya hadiye wanda yake dan tsotsa a hankali ya dan kurbi ruwa ya ce" dan ta rayu cikin nutsuwa, ta samu inci kafin ta yi kaura zuwa lahira Mariama ta ce" a wajen danginta, a kusa da mahaifiyarta ta fi samun inci Sofo! Idannuwansa ya dan lumshe kafin yake budewa ya ce" ta yaya? Ta hanyar ta kare rayuwarta a bakin titi? Ita ko arzikin mazan zamanin ta kasa samu idan sun shigo gari da gari dan jar fatar yayanmu ne da gashi da kyau! Ba ruwansu da tarbiya, usuli , da halaya! Burinsu shine au samu iri mai kyau ....bayan su kansu idan suka kalli kansu a madubi zasu gane cewa a da ba haka Allah ya halice su ba, kwonci tashi kuma fatarsu sai ta dawo irin tawa idan Allah ya nufa masu tsayin rai ne, Su da ka hadata da su din kana da tabacin a inda zasu kaita ba.a kyamar bakar fata? Mariama ta maido masa da amsa du a hargitse da yannayin bacin rai tamkar a lokacin ne za.a tafi da Bak'a, Baba tsofo ya ce" birni da kike ji ana fadi, wata duniya ce a cikib duniyarmu mai cike da abubuwan al.ajabi, A birni mutane basu da lokacin dan kina da fata baka ko dan kina da muni ya kasance du idan kin zo waje za.ana kwagirar ki ko a hantare ki! Sannan birnu cike take da mutanen da kwakwaluwarki ba zata iya hasaso maki ba, idan wani ya tsana wani zai so.......Mariama, ku yi hakuri. Kanta ta mayar ta ci gaba da aikinta, tana gamawa ta ware masa wanda zai ci a lokacin sannan ta zuba masa sauran ta kai kusa da dardumarsa ta ajiye masa ta ajiye tsintsiyar a gefe, ta fitar da sauran canjin kudin ta ajiye saman dardumar ta dauki robar Anna da tulunta ta juya, Har ta fita ta dawo ta duka kusa da shi kanta a kasa da yaren buzancinta ta ce" ta kasance abokiyar fadana, wace idan na tashi itace kanwata ita nake cin zali, takan kwaso kayana ta wanke min, idan dare ya yi can tsakiyar dare in na je juyawa sai in jita nanake da jikina, sai in rungumeta sosai a jikina ita da marigayiya, sai gashi lokaci guda a cikin kwana goma na rasa su! su duka biyu, ita wace ta rasu ina binta da adu.a baba wace kuwa take raye inai mata adu.a sannan zan yi iya yina dan gannin na kyautatawa wa.inda take so take kyautatawa, haushinku nake ji ku duka har Annar! Tana gama fada ta mike ta yi gaba abinta . Baba sofo ya yi murmushi har cikin ransa ya ji dadin haka, ashe dai Mariama na tare da ikon allah, Mariama kennan Allah ya sa ranar da zaki hadu da yar uwarki ki bini da adu.a koda na mutu. NIAMEY Doguwar riga fara kar ce a jikinta mai siririn hannu aman tsayinta har kasa, irin mai laushin nan ce bata da kwaliya ko das ta tafi ne ta bi tsarin halitar jikinta, Kamshi take bazawa du inda ta gota sai fai fuskarta ta cabe da hawaye tana biye da shi, Murya a raunane ta ce" WARDUGU, nice ya dace na yi fushi irin yanda ka wulakantani, ka banzatar da ni a cikin duhu a garin da ba nawa ba , a garin da na je dominka, ka fice ka barni, sannan da safe da ka dawo ko ka kali motar da ka bar ni a ciki, ka yi tafiarka wajen mamanka ni kuwa ko oho! Shine dan na tafi zaka dauki zafi da ni haka? Wardugu da ya gama saka mabalin rigarsa ya juyo ya kare mata kallo, a ransa ya ayyana '''''rainin hankali kennan, ta dawo daga tafiarta wace ta isa da kanta , shine aka sha karamar riga aka sha wankan turare aka zo ni ga maye ga mai jira aka kawo min na karbe ko? Murmushi ya sakar mata kafin yake binta da wani mugun kallo irin na rainin nan, ya dauki yar karamar wayarsa ya bar ta chating din nan ya dauki ky din mota domin garin da hadari hadari baya son ruwa ya foke shi yau, ya fice ba tare da ya furta mata ci kanki ba; Da kallo ta bi shi kafin take zama bakin bed din tana shafe idannuwanta, bakinta ta zumburo a fili ta furta" zaka sauko ne, haka kawai ka wani hada ni shakar numfashin wannan uwar taka harda wata karin malatin? Naki din wardugu! Na ki na shirya da mamanka duda baka tambaye ni ba na san hakan kake so sai dai ni a gaskiya ba zan iya jure mulkinta ba sai kaceatar wani sarki dan tana uwar General! ........hum Wardugu bai zame ko.ina ba sai aeroport, yana zuwa ya ajiye motarsa ya shige ta wajen sojojin dake tsaron kofar bayan sun sara masa ya shige ciki ya haye wajen tarban baki Bai kai ga karasawa ba ya ji muryarsa ya ce" mek (men), Juyowa ya yi, arba ya yi da amininsa, abokinsa, Mu.azam zaune saman kujera, gilas a idannuwansa ya saka costume kafarsa sanye da takalmi sau ciki baki sai sheki take.....sai dai abinda bai masa ba irin yanda ya rame Yana kallonsa har ya karaso inda Mu.azam ya mike tsaye yana murmushi ya bude hannayensa irin ya zo ya rungume shi , Ido Wardugu ya zaro ya nuno shi da yatsa ya ce" kai ko? Mu.azam ya saki dariya yana kara kure Wardugu da kallon yaushe rabo ya mika masa hannu ya ce" Asalamu alaika amini Wardugu ya karbi musabaharsa yana mai furta" amen wa.alaika salam amini, Murmushi suka yi kafin suke gaisuwar larabawa, Wardugu ya yatsina fuska ya ce" kai dai ka cika naci, gaisuwar nan ta wani runguma ba wani sonta nake ba aman sai ka wani damki mutun kato da kai! Mu.azam ya bushe da dariya yana biye da shi inda soja guda ya karbi jakar Mu.azam dake hannun wardugu ya shiga ja har wajen mota ya bude ya saka masu ya juya bakin aikinsa, Wardugu ke jan motar yana dan kallon Mu.azam jifa jifa, a kasan zuciyarsa yana tare da damuwa na abubuwan da ya gani a tatare da Mu.azam wannan zuwan, ya rage magana, ya rage fara.a, ga dan cazbi a hannunsa yana dan dadanawa, ga rama da ya tafka ta mamaki sai dai fatarsa ta gyaru ta yi fresh aman ba alamun yana jin dadin rayuwa..... Haka har suka karasa gidan Ayya wada rabonsa da gidan kwana hudu kennan tunda ya kawo su bai samu aiki ya barshi ya zo ba , aman ita Ayyar ta ue har wajen aikin ta amshi carte dinsa ta banki wai zasu je shopping ita da sabuwar yarta, ya yi murmushi da ya tuna irin kudin da suka kaso, Ayyarsa uwarsa Ayya manya....... Zaune Ayya take saman kujera tana kallon yanda Agaishat ke dan turo baki tana kallon Ayyar da yannayin abin tausayi, Daga ita dai gajeran wando da yar rigar da Ayya ta yi mata jan ido kafin ta yarda ta zauna da su dan ta shafa mata gomage a jikinta da fuskarta tamkar amarya, gefe hijab dinta ne baki dan kar kalar abin madarar ya bata hijab din Ayya ta dauko ko dan idan an yi baki, wani irin kulawa Ayya take baiwa Agaishat (Bak'a), kudi ta kashe na mamaki wajen siyen mayuka masu gyara fata ba canza kalar fata ba, sannan ta shiga kasuwa da kanta tare da Agaishat tana nununa mata abubuwa nasu na tubawa na gyaran jiki ta kwaso itacen magarya ta kwaso kayan gyaran jiki suka dawo gida, wata irin shakuwa ce ta shiga tsakannin Ayya da Agaishat, domin Ayya wayayiyar mace ce ta yo anfani da irin yanda ta waye ta ja Agaishat a jiki tun tana tsoro tana baya baya har ya zamana sun shaku tana dora kanta saman cinyar Ayya ta yi baci ba tare da wani dar ba. Yauma sun tashi da niyar yin gyaran jikin ne, Ayya ta dadaure mata gashinta da abin nan na saloon wanda idan an wanke kai ake sakawa a dadaure gashi da shi dan ya nanade ya bushe, ta kwaba abin gyaran jikin nan ta samu ta shafa mata ta yi mata hayakin mai mugun zafi wanda fuska kawai ake fitarwa, tana gamawa ta sakata ta yi wanka ta shafa mata na madarar nan suka zauna a fali sunna kallo aman ta hanata magana dan kar na fuskar ya saka fuskar ta yakune........ Mai gadi ne ya fara shigowa da jaka, Wardugu na biye da shi sai Mu.azam wa.inda shigowarsu ne ya ankarar da Ayya ta warci hijab din Agaishat ta ...... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣2️⃣ Da sauri Ayya ta samu ta rufa mata hijab din inda Bak'a ta yi mutuwar zaune a ranta tana ayana Ayya wayo daman sai da na fada maki Ayya ........... Karasowa suka yi, Mu.azan na kallon inda aka rufe da hijab yana son sannin ko waye, Wardugu kuwa kallo daya ya yiwa wajen ya kawar da kai a ransa fadi yake" me Ayya ke son yiwa fatar nan da ta rine? Da murna Ayya take kwalawa mai aikinta kira da ta zo ta dauke akwatin Mu.azam sannan ta kawo masa tarba, Ayya ta tarbo shi tana murna ta kamo shi ta zaunar da shi sai murmushi take tana kallonsa ta ce" yarona, yaushe gamo? Mu.azam dake jin wata nutsuwa na saukar masa ya dube duba irin na mahaifiya, a hankali ya duka kasa ya ce" Ayyana ina yini Ayya ta kuma kamo shi ta tayar da shi tana kallonsa, yannayinta ya fara canzawa ta kai hannunta wajen wuyansa ta ce" me ke damunka? Ya haka ka rame har haka? Ko dai ka je ka sakawa kanka ayuka ba hutu ne?? Dariya ya saki yana kallon Ayya , kafin yake maida dubansa wajen Wardugu ya ce" freind Ayyana har yanzu akoy yannayin nan? Wardugu ya yi dan murmushi yana kallon su, Ayya ta yatsina fuska ta ce" ba wani nan, yanzu tashi ka je ka yi wanka ka fito zan fara yi maka dura ne tunda abin haka ne! Yana dariya ya mike ya kalli Wardugu ya ce" mu je ko? Wardugu ya gala masa harara ya ce" a matsayin matarka ko dan jagorarka? Mu.azam ya yi murmusho yana ji a cikin ransa ya yi missing din abokinsa da mahaifiyar abokin nasa, Juyawa ya yi ya nufi dakin da ake sauke shi wanda yake a matsayin nasa, Ayya ce ta dubi wardugu, da idannuwanta ta yi masa nuni da ya tashi mana shima baya gannin mutun? Wardugu ya daga kafadu ya ki tashin yama mayar da dubansa wajen tv inda ya dauki commande ya canza tasha ya kai Canal plus sport ya shiga kallon ball. Ji take ta fara gumi , ga kuma ta kage a yannayin zaman nata, ba.a jima ba Mu.azam ya dawo daga wankan da ya tafi ya zu suka kara kasancewa mutun biyu maza kennan, Ayya ta tashi da yannayin jin haushi ta dunguri kan Wardugu ta ce" ta yi maka kyau! Wajen Agaishat ta karaso ta kamata ta mike kafarta ta yi mata tsami sosai, ta samu ta saka mata hijab din ta ce" je ki yi wanka Agaishat ki sauko mu ci abinci . Da toh ta amsa ta bi ta bayan kujerun ba tare da ta gaisar da su Wardugu ba, Mu.azam da ayar tambaya ya kallo Ayya, bai yi nauyin baki ba ya ce" Ayya ina kika samo wannan? Ayya ta karasa kusa da su sosai ta zuba jus ta mika masa shima kamar yanda ta mikawa Wardugu ta ce" Me ke damunka tukunnan yarona?? Mu.azam ya shiga dan sosa bayan keyarsa, ya kallo wajen Wardugu, ya kuma kalli Ayya. Haka kawai wardugu ya ji gabansa ya fadi, shima kure shi da kallon yake kafin ya ajiye yar wayar dake hannun nasa ya zuba masa ido, Murmushin dai ya kara yi masu, ya ce" na yi rashin lafia ne Ayya, kuma yanzu alhamdulilah na samu sauki, Ayya ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa ta ce" na tsorata da yannayinka, ka wani rame, ba komai haka ne idan jiki ya tabu sai a hankali aman yanzu ka zo kennan sai na ga yarona ya koma yanda yake da koma ya fi haka kafin ka bar gidannan, Wardugu dake kallonsa ya shafa kansa shima kwata kwata bai yarda da maganar Mu.azam ba! Kai haba a irin yanda suka san juna Mu.azam ba zai layance masa ba Mikewa ya yi ya nufi kofa da wayarsa a hannu inda suka bi shi da kallo, Mu.azam ya ce" Ayya ya tafi fa kennan?? Ayya ta daga kafadunta ta dan yatsina fuska ta ce " ya gaishe su! Mu.azam ya yi dariya yana kallonta, a ransa kuwa dadi yake ji yannayin, kai yana jin dadin zama da su, Wardugu rikitace, mahaifiyarsa ta iya zama da shi, ta kai ta kawo ne idan tama da bukatar ganninsa a wayarsa ya yi mata activen localization, du inda yake idan ta shiga nema za.a nuna mata kawai sai dai ya ganta kuma sam baya gigin kashewa doka ce! Suna tsaka da tataunawa mai aikin Ayya ta shinfida ledar cin abinci ta kawo abincin ta ajiye, ta kawo kayan zubawa da na sha, ta kawo su jus na gida da Ayya ke yin abinta da kanta ta saka a frij du ta ajiye, Ayya ta umarci Mu.azam da ya sauko bara ta dubo yarta..... Wardugu ya dawo, bayansa *ALHINAYET* kawarsa ce ke biye da shi, Salama ta yi ta shigo dakin inda Ayya ta tsaya ta saki baki tana kallon Wardugu da Alhinayet din, Alhinayett na zuwa ta shiga gaisar da Ayya cikin yannayin ladabi da mutunta mutun, Ayya ta dan kebe baki, ta amsata ta juya dan dubo Bak'a Mu.azam dake zaune ta juyo ta dafe habarta ta ce" su likitoci ne a garin namu??? Mu.azam ya sakar mata murmushi ya ce" lauya, lauya, lauya mai kunce mai laifi , zamani lauya iko, lauya mai saka kato ya duka, Kai ta dafe ta ce" wace ni, rufani ka sayani, ai ba dan an san ni aminiyar *Aboki* bace da an fige ni a Niger! Mu.azam ya ce" kai ai rigimama ta san waye *Oga* Wardugu ya girgiza kai yana zama ya ce" *ALHIN* ki zauna mu hau wannan abubuwan kafin ku ci gaba da kirar da kuka koya! Alhinayettt ta je kusa da Wardugu ta zauna tana fadin" General ka duba lamarin nan je ten conjure................(plz) Wardugu ya kaleta zai yi magana sai ga Ayya ta dawo da Agaishat, Doguwar riga simple irin ta zaman gida ce Ayya ta bata, bayan ta saka ayya ta bata Dan kwalin rigar nufin ta yane kanta sai dai suka hau rigima kan aa dan Allah ta bata hijab, Gannin sai su bata lokaci ne ya saka Ayyar bata hijab ta zumbula suka sauko, Sai a lokacin Agaishat ta duka ta ce" ina yinin ku, Alhinayettt da Mu.azam ne suka amsa inda Wardugu ya kebe bakinsa bai wani amsa ba aman yana yi mata kallon tsaf, a ransa yake ayyana black, but ko a baki *BUZU MAI KYAU NE* 😂😂😂😂🤪😜😜😜😜😜😜😜😜😜🤪🤪🤪 na fada a zo a dake ni🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐🧐 May be 23......zuwa dare in sha allah, idan comment ya birge ni😄😁😆😅😂🤣 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣3️⃣ Waje Ayya ta samu ta zauna , nan Agaishat ta je kusa da ita sosai itama ta zauna ya kasance an saka baban plateau din a tsakiya, Ayya ce ta bude inda abincin yake, tuwon tsaki ne da miyar kubewa wace aka yita da naman shanu ta sha dadawa da kayan miya 😋..ga kuma man shanu na kirki a gefe, Sai su fruits da aka hi masu yanka mai kyau aka sasaka cikin plat plat, sai jus da ruwa, A hankali Ayya ta dauko abincin, Agaishat ta dauko abin zubawa, Cikin wannan banban plateau din Ayya ta zuba abincin ta daidaita miyar, ka.ida ne in dai ka zo gidan Ayya daidai cin abinci bata raba assiete, sai dai a hadu a ci a abu guda ....... Bayan ta zuba ta kare Agaishat ta kawo abin wanoe hannu da kuma cokula a wata yar roba, Gaba dayansu cokulan suka dauka banda Agaishat da Ayya , hannayensu suka wanke .... Ayya ce ta fara saka hannunta, sai Wardugu, sai Mu.azam, sai Alhinayettt, sannan Agaishat dake karamar cikinsu, hakane gidan Ayya baba ke fara saka hannu cikin kwanon cin abinci sannan yaro ke rike kwanon dan kar ya ringa yawo, ba.a magana idan ana cin abinci, ba.a dane danen waya, ba.a wani kale kale sai an gama, sannan bata yarda ana tsaka da cin abinci ana shan ruwa ko jus, sai an gama ake sha, sannan ana cin abinci daidai ne ba.a matsawa ciki a yi mugun koshi, lamarin gidan Ayya sai yayanta (🤣), Abincin nan ake ci cikin nutsuwa, Alhinayettt ta kure Agaishat da kallo, sam batai mata kama da tubawa ba, sannan ba bahausa bace ko daya duda hijabin dake kanta gaban goshinta lufluf yake kwonce da gashi, girartama wani irin gazar gazar da ita, du bakinta lebenta haske ne da shi tas tas, ga girar ido ga manyan idannu, wannan cikin biyu daya ce ko bakar balaraba ko bakar buzuwa! Alhinayettt dai ba wani yawan zuwa gidan Ayya ba take ba, sukan hadunsu ne da wardugu a wani wajen, yanzuma zuwa ta yi da rigimarsu ta kansu wace ta zo su yi kan irin yanda ake cece ku ce a gari na matarsama idan ta cika dare kwanan cel take bare wani banza! Alhinayettt kwata kwata ta manta zancen ba.a magana idan ana cin abinci gidan Ayya dan haka ta kali Agaishat da kyau, haka kawai ta yi niyar yi mata magana da buzanci dan ta gaskata zatonta, *ABZIN?* , ta fada tana kallon agaishat, Agaishat da ta hadiye abinci ta kaleta itama, itama ta so ta ayanna hakan cewa wannan buzuwa ce, gannin yannayinta sai dai bata fadi ba dan ba wajen fadin bane, Ai kuwa Agaishat ta washe baki itama da yaren buzancin ta maida mata cewa" eh , ke fa?? Alhinayettt zata maida mata maganar Wardugu ya tsimki hannunta na dama dake kusa da shi, sannan ya zabgawa Agaishat wata muguwar harara wace ta sakata sada kanta hannunta na rawa rawa, Ayya yatsina fuska ta yi bata yi magana ba, Sai da aka gama mai aiki ta shiga kwashewa, Agaishat na tayata kaiwa komai wajensa ta dawo ta zauna kasa kusa da kafar Ayya, Wardugu ne ke kallon wayar Alhinayet tana nuna masa hotunnan birthday dinta da ta yi baya nan yana dan murmushi kasa kasa ya ce" Alhinayettt , ina tunanin kin girma ashe dai na daina tunanin nan? Alhinayettt ta yi dariya ta dora hannunta saman nasa ta ce" na baka ka sha? (Irin su taba zata bashi wani labarin) Ai kuwa Wardugu ya dan cafke hannunta yana sauraronta, inda ya bata hankalinsa suna ta hirar su, Ayya ce ta dan ja tsaki, ta girgiza kai tana kallon Mu.azam ta ce" kana ji? Zamani ya zo mana da abubuwan mamaki, sai ka ga mace na tafawa da namiji, tana raba jikinta da nasa wai a zuwan mutunci kawarsa, ! Mu.azam ya zaro ido yana kallon Ayya, a fili kuwa ya furta" Lah, yana dafe bakinsa, Wardugu da ya gama jin komai ya saki murmushi yana kallon Ayya, ya ce" Ayya, qna abota mace da namiji, abota sak ba wani soyaya ba kuwa, Ayya ta juyo bangaren su a takaice , daman jira take wani abin ya hada su ta ce" wardugu ba abota ba dai yayan awaki! Nace yayan awaki, Ke yanzu Alhinayettt kike ko wa? Aman ke marainiya ce ko? Ina nufin mahaifiyarki ta rasu? Alhinayettt dake kallon Ayya a dan tsorace ta ce" Aa Ayya, Ayya ta dafe habarta ta ce" Toh abin mamaki, aman ita baku rainata kamar yanda kuka rainani ba ko? Ina nufin Wardugu baya zuwa gidan ku a matsayin aboki sai saurayi? A tare suka kalli juna Alhinayettt da Wardugu, suka maida dubansu wajen Ayya, Ayya ta ce" to in ba haka ba, ya za.a yi ni ina mahaifiyarki , kato ya ringa zuwa wajenki a matsayin aboki kuma na zuba ido yarinya kin kai kin kawo min a gida? Wardugu ya shiga gyada kai yana kallon mahaifiyarsa, ta jima tana son aikata wannan aika aikar wa zumuncinsa da Alhinayettt, yau dai ta yi hankalinta sai ya kwonta kuma ko? Ayya kamar zugata ake sai magangannunta take son ranta karshe ta ce" to ni ba tsohuwar banza bace, in sonta kake ka fito a mutun ka fada ku daina boyewa Allah kadai ya san tsakanin ku! Dan haka tun wuri a fasa daukana a wata marar ilimi ana ce min wai kawa! Aa abokiyar tagwaitakarka ce Wardugu! Wardugu kallon Ayya kawai yake, inda Alhinayettt ta dan sada kanta kasa, a ranta ayannawa take ita bata ga laifin zumunci da suke da Wardugu ba, walahi da soyaya suke da ba haka ba, kwata kwata ba wani zance wai shi soyaya tsakaninsu, haka kawai Allah ya hada jininsu suke mutunci, Wardugu bashi da shamaki a gidan su, hakama saurayinta wanda zasu yi aure suna mutunci da Wardugu, aman haka ne itama kakarta ta sakawa zumuncinsu ido har sun mayar da ita tamkar mahaukaciya domin idan sun ga zata fice sai su shiga magana kasa kasa da yaren french ai kuwa ta kama zage zage tana fadin ita za.a munafinta? Toh gashi itama maman Wardugu kallon masu soyaya take masu bayan ita koda bindiga ba zata iya soyaya da wardugu ba domin ta san waye shi, Wardugu dan yana son ki ba zai hana ya yi maki dukan mutuwa ba, dan yana son ki baki fi hukunci a wajensa a gaban koma waye ba, hum soyayama da wardugu ai tashin hankali ce, ita mai ya kaita? Ta fi son namiji marar rigima mai bata damar ta yi rayuwarta cikin aminci........ Wardugu dake kallon Ayya tar, ya maida dubansa wajen Mu.azam ya ga sai gumtse dariya yake, Kansa ya girgiza ya maido dubansa wajen Ayya, da hannunsa na dama ya daga ya sara mata, sannan ya yi mata nuni da ta ci wasanfa , ta more abinta, Hannunsa na hagu ya mikawa Alhinayettt ta mike itama ya ja hannunta tana waiwaye tana so ta yi hira da agaishat aman ya jata kiiii sukai waje Kusan motarta suka tsaya, Alhinayettt bata bi ta kan fadan Ayya ba, bata nuna damuwarta ko a fuska ba, ta ce" Wardugu, rigingimunka sun isheni haka, ya isheka malan! Wardugu ya shiga gyada kai yana kallonta bai bata amsa ba, Ta ci gaba da maga domin ta san ba amsar zai bata ba, ta ce" ta ya zaka saka Walyn kwana a cel? Wardugu ina jin zafi idan na ji ana fadin baka da sasauci, baka wasa, baka sulhu, Wardugu matarka ce fa? Ya kake so mutane su fasaraka?? Wardugu ya tsura mata ido kawai, Ta ci gaba murya a sanyaye" ka daina Wardugu, ina so idan na zo waje na tarda ana fadin alkhairi a kanka, ina so idan ana maganarka ta kasance ana yabonka Wardugu, ka ringa sasauci freind, Wardugu ya yi mata dan murmushi ya miko hannunsa ya dungure mata kanta bai ce mata komai ba, Alhinayettt ta ce" Wardugu ina kula samu buzuwa?? Wardugu ya yatsina fuska ya ce" hum, Ayya ce ta daukota wai ta yi y'a, Alhinayettt ta ce" yarinyar ce ta birge ni, irin yanda tana buzuwa , bakar buzuwa aman bata bata bakinta ta hanyar shafe shafe ba, ina son mutun haka walahi..... Wardugu ya daga kafada ya ce" daga kauye, can cikin kauyen kauye fa ta fito, inama ta ga man bale ta shafa? Allah dai ya sa idan ta dan waye ta zama dan kauye ya fi na birni shegantaka.... Alhinayettt ta ce " sai dai idan ba tare da Ayya take ba, Ayya ce zata wani bari haka ya faru? Yarinyar ce innocente, dan Allah ka hada ni da ita mu zama kawaye, Wardugu ya waro ido, a fili ya furta" kawaye? Ki kirani aboki kuma ki yi kawance da wannan? Aa! Alhinayettt ta yi murmushi tana kai masa dan dukan wasa ta ce" ina son ta zama kanwata ne Wardugu, ina son na kara nuna mata shafe shafe karma ta saka kanta, sannan na kara wayar da ita...... Kafadunsa ya daga irin ita ta gano, kafin yake bude mata motar ya yi mata nuno da ta shiga Dariya ta yi ta shiga , ta kunna wato dai ta ishe shi da magana ko? Hannu ta daga masa, ya yi mata nuni da sai ya zo , ta tayar da dankareriyar motarta ta kama hanyar makarantar kannenta dan ta dauko su ta mayar da su gida Komawa Wardugu ya yi, yana shiga ya tarar da su sai labari suke suna dariya abinsu, Mu.azam kuwa ya kasance du motsi sai ya kali Agaishat dake zaune tana kallon Tv kuri, ita har yanzu mamaki take mutane a cikin wannan allon suna ta magangannu suna komai abinsu, har bayan take lekawa wai ko zata gansu ta nan ta sha yiwa Ayya tambayar kuma yanzu idan suka fito fa? Yanzunma Ayya ta kuna mata wakokin dandali, kalo take tana ta sakin murmushi kumatunta na lotsawa dimple har biyu a fuskarta, wani wajen sai ta rufe fuska idan namiji ya fara rawa, sosai take dan gane hausar da suke tana kara koya ta nan, shi kuwa abin na birge shi, sannan ya yiwa Ayya tambayar wacece ita? Da french, ayyarma ta shiga kora masa bayanin komai.....ya sha mamaki, ya ji wani lamari a tare da yarinyar, yana son inganta rayuwarta...... Wannan kennan. Wardugu na zuwa ya ce" tashi mu je, Mu.azam ya mike ya bi bayansa suka nufi dakin Mu.azam din , Ayya ta yatsina fuska a ranta ta ayanna mai yiwuwa ya yi fushi🤣. Suna shiga Wardugu ya ce" c'est bon, maintenant tu me dit la verité sur ce qui t'arrive ( ya isa, yanzu sai ka fada min abinda ke damunka!) Mu.azam ya tsare shi da kallo, a hankali ya zauna saman kujera yana kallon Wardugu, Wardugu ya karaso ya zauna shima, ya ce" ka san dai kana iya yiwa kowa karya banda ni! So ka fada min tun kafin na hasala Mu.azam, wata irin cuta ce wannan wanda baka taba yi a gabana ba ta zugeka haka? Me ya samu kasan gashinka ? Kana tunanin ban lura ba? To gashinan kasan gashinka a aske! Sai ka janyo sauran ka rufe, du ka zama wani iri? Ka duba fa ka gani wandon vest ne a jikinka ka dauko riga rose (pink) ka saka sai kace mace? Hannunka ba agogo, yannayinka na nuna kama tare da damuwar da ta fi karfin furucinka, ina hawa aiki karfe goma na dare, ka fada mani na juya! Mu.azan da wata irin murya ya ce" Cancer du cerveau ke damuna..... (cancer ta kai) Wani irin tsam Wardugu ya yi, ya kaste maganarsa a lokacin da bai shirya ba, Zurbat ya mike yana duban Mu.azam, hannayensa duka biyu ya saka ya dafe kansa, baya baya yake ja ya...... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣4️⃣ Wani irin tsam Wardugu ya yi ya katse maganarsa a lokacin da bai shirya ba, Zurbat ya mike, duban Mu.azam yake da wani irin kallo, hannayensa duka biyu ya kai saman kansa ya shiga yamutsa gashin kansa , baya baya ya shiga yi da kafafuwansa, bai fi taku hudu ba ya tsaya ya juya ya juyo, hanunsa ya jimke ya daki dayan da shi, A hargitse ya dawo wajen Mu.azam, so yake ya zauna aman ya kasa...... murya a cinkushe ya ce" yaushe, yaushe? Yaushe ka sani? Ya aka yi ka sani????? Mu.azam ya mike yana dan sakar masa murmushi yana kokarin ganin ya saka shi ya dan nutsu aman ya kasa kama shi, dan haka ya tsaya yana kallonsa ya ce" Wardugu, har na kai wajen da gashina baya zama fa, ya jima a jikina ciwon ....nima ina gannin alamu a matsayina na likita sai dai ina turewa na ki maida hankali, ya kai ni sai na suma na yi awani a sume, na daina shiga tiyata ba yau ba, ina zuwa asibiti ne dan kar imanina ya yi rauni, ina zuwa ne dan haduwa da wa.inda suka fi ni damuwa, ina yi mana adu.a a tare, Wardugu idan na jima a gabannan na kara shekara hudu a duniya,... "C'est faut!,(KARYA NE!) Wardugu ya fada tun karfi yana nuno Mu.azam da yatsarsa, Taku ya yi wajensa ya ce" idan kai ka fada, idanma wani sakaran likitan ya fada na fada karya kuke, karya ne Mu.azam, ku baku isa ku fadi abinda Allah ya boye ba, ba wani mahalukin da ya san ranar mutuwarsa , mutuwa bata shawara, bata fadi sai an ganta, mutuwa na zuwarwa bawa a lokacin da bai sani ba, sannan a lokacin da bai shirya ba domin a kulun bawa baya cikin shirinta, Wardugu ya yi shiru, gaba daya ji yake jikinsa ba karfi, a hankali ya kai kasa ya zauna nan kasa, waje guda ya tsurawa ido kafin ya ci gaba da fadin" sannan Allah kadai ya san gawar fari, ba wai dan wane bashi da lafia wane lafiarsa kalau za.a ce sai marar lafiar nan ya rigayi mai lafia rasuwa, Mu.azam da ya karaso , a hanakli ya duka ya dora hannayensa saman na Wardugu, murya a raunane ya ce" ban taba tunanin wani abin zai girgizaka haka ba Wardugu, menene a ciki? Ko dan abin ya shafeka ne baka so ka ji? Wardugu ka yi hakuri, ka daina tayar da hankalinka kan maganar nan, nima na fada maka ne dan na ji sanyi sannan na samu wanda ya san ciwona, Wardugu ka.... Bai tsamaci lamarin ba, sai jinsa ya yi jikin Wardugu, Wardugu da dan ya tsokane shi yake ce masa sai sun yi gaisiwar larabawa, yau gashi da kansa ya rungume shi, Murya a cunkushe wardugu ya ce" bana so bana so..... Kasa karasawa ya yi kuma ya saki Mu.azam ya mike ya fice da wani irin sauri ....... A hankali Mu.azam ya hade kansa da gwuiwarsa, , tabas mutuwa Aya ce, duk mai rai mamaci ne, tabas ba karamar ni.ima bane da Allah ya boyewa bayi ranar mutuwarsu, shi gashi, hasashe ne aka yi, likitoci sukai a kansa, rayuwar turai da za.a fada maka komai kwaro kwaro ne, sun kiyasta lokacin da suke gani zai kai a raye a doron kasa sun fada masa, wai basu fada masa rana da lokaci bama aman gashi du ya firgice ya fice a hayacinsa, Idannuwansa ya lumshe yana jin saukar zazafan hawayensa, zuciyarsa ce ta ci gaba da fada masa" ka zo kasar nan je dan ka kara ninninka ibadunka, ka kara yawaita sadaka da aikata abubuwan alkhairi, ka zo kasar nan ne dan ka samu ka raya sunnar ma.aiki idan Allah ya nufeka, mutuwa kowa yi zai yi Mu.azam, ka daina karaya ka yi hakuri har Allah ya yi ikonsa a kanka, Wayarsa ce ta dauki kuka ya kai dubansa wajen wayar ya mike daga tsugunnin nan ya daukota ya daga, Docter me ka yi kennan? Na zo wajen aiki na tarar da takardar barin aikin ka? Saboda ni kake son yin nesa da aikinka ko saboda na fada maka ka yi hakuri a yi maka aikin nan? ...... Kansa ya shafa yana sauraronta, masoyiyarsa wace ke nuna masa kauna, tana son Mu.azam tamkar nama daya na cikin miya, tana son kasancewa da shi, labarin rashin lafiarsa ya gigitata har itama ta kwonta, nan ne ta yi ta fadi tashi har ta gano ana iya yi masa aiki a cire wajen, aman aikin ne keda hatsari sosai, yana iya samun tabuwar tunaninsa, ko ya kasance ya shiga coma wace shigekan daga ita ba zai tashi ba, ko idan Allah ya aminta ya yi jinya sumul ya samu sauki aman shi ya kara kai da kasa ba zai harda a wani buda kansa ba a dawo kuna ba wani succes, MU.azam ya ce" Aisha, Aisha ta ce" ka dawo na roke ka, ka dawo tun kafin lokacin a iya yi maka aiki ya shige, Ki yi hakuri ki daina kirana Aisha, Mu.azam ya fada da sanyin murya, ya ci gaba da fadin" nawa kuka yiwa aikin? Nawa suka fita? Karshe dai du yawanci daga dakin aikin za.a fitar da su basu san inda kansu yake ba, zasu dawo kulun a jone da inji yana taimaka masu wajen numfashi, da na.urori masu basu abinci, da masu jan fitsari da masu karban kashin su, zasu dauki lokaci a wannan yannayin har ya kasance ko a cire masu na.urorin ko dare daya su tsaya sun daina aiki, su basu dauki kadara suka yi ta ibada suna shinfida a makwoncinsu na gaskiya ba, su basu san a inda suke tsakannin duniya da lahira ba, Aisha, Allah ya dora mani, ba zan kai labari ba! Ki yi hakuri...... Yana gama fadar haka ya katse kiran, Docter Aisha dake kai kawo tsakannin dakinta da falonta ta dafe kai ta fashe da kuka, yar balaraba kyakyawa da ita, a fili ta furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Mu.azam, in sha Allah zaka warke, sai mun rayu da kai Mu.azam....... (😔😔😔😔😔😔) Bayan sati uku Ayya ce zaune tana nunawa Agaishat yanda ake gyara lale ja domin tana son kunsa mata ne, Bayan ta tankade shi lukui ta kawo mahanabiya ta zuba masa sannan ta zuba dan madaidaicin ruwa ta kwabe shi sosai ya yi shar da shi ta zuba dan ruwa gefe ta ajiye tana kallon Agaishat ta ce" yi ki wanke kafar mana Agaishat, kin ga yayanki Mu.azam ya ce zaku fita ku zaga gari , ni kuwa na fi so idan mun gama kunshin nan sai ku tafi.... Agaishat ta yi sauri ta shiga darwaye kafar nata ta cire ta dauke ruwan ta kai ta zubar ta dawo ta dauki abin goge kafar ta gogoge ruwan kafin take zama ta tankwashe kafafiwanta Ayya ta shiga daura mata iskwace tana fadin"ki lura dan gobe ki daura abinki kin ji Yar Ayya, Agaishat ta gyada kai tana murmushi, a kowani lokaci a kowani yannayi ta tsinci kanta tunda ta sauke kafarta a gidan Ayya sai iyayenta da yan uwanta da baba sofo sun fado a ranta, bale yanzu Wardugu kansa da yake yawan hararata a farkp ya daina, shi dai baya shiga lamarinta aman baya hana wani shiga, Alhinayettt ma tana lekowa wani sa.in idan Wardugu na gidan su sha hira da yaren buzanci domin tana jin dadin jin yaren raurau ana hira da ita ba wani kyama, sosai Alhinayettt ke dan gwada mata wasu abubuwan, da hikima take nuna mata wasu yan al.adun yan birni sannan Mu.azam na mugumugun sakata a jiki, yana sakar mata fuska fiye da tunanin mai karatu, idan ta kali kayayakinta, suturun da suke malakinta a yanzu, sai ta ji hawaye na neman zubo mata, tunaninta me yan uwanta suke sakawa a yanzu? Wani hali suke ciki? Jiya i yau ne ki Baba ya canza halayensa? Sai dai takan bi su da adu.a kawai, itace kadai abinda take iya yi masu a yanzu, kuma tanaiwa iyayen rikonta adu.ar gamawa da duniya lafia, ba.a wani sakata makarantar boko ba domin shekarunta sun tafi shekara goma sha takwas har ta kusa cike sha tara, aman a gida Ayya na koya mata abinda ya sawaka sai karatun islamiya da ta kara zurfafawa sosai tana kara neman ilimin adininta. Ayya na gama daura mata kunshin ta mike tana leka windows, mamaki take irin yanda yanzu wardugu ya ajiye kafarsa a gidan, duda ta san amininsa na nan dole za yana yawan zuwa aman abin na bata mamaki, bai jima da fita ba fa aman har ya dawo, sannan yanzu basa fada da mu.azam akasin da da sai ta shiga tsakani ko ta gindaya masa doka kan Mu.azam din kafin yake barinsa ya huta, yanzu kuwa bini bini ya shigo ya haye wajen Mu.azam su yi ta hirar da ita bata san ko ta meye ba, yanzun ma tsaye suke su uku, da yar jajar nan Alhinayettt sai hira suke suna dariya, Rufe windows din ta yi ta juya ta fice ta bar Agaishat na zaune tana jira ya bushe ta wanke kamar yanda Ayya ta fada Bayan kunshin Agaishat ya bushe, ta mike ta saka takalminta silifas ta yi bayi, Wanke kunshin ta yi, jan kunshi yayi jajajir, ga mamakinta ya fito sosai a fatarta har ya haska mata fatar kafar da hanayen, Da sha.awa take kallon kunshin ya yi kyau a idannuwanta, Ta dauki lokaci a bayi domin sai da rmta yi wanka ta fito ta je bakin madubi tana goge gaban goshinta inda ruwa ya taba kannanuwan kitson da Ayya ta dage akai mata wa.inda sai warwarewa suke dan kansu , Turarukanta ta zauna ta shafa na madara masu sanyin kanshi, ta shafa mai kadan a jikinta, Kwali ta dauka tana adu.a domin har yanzu ta kasa sabawa da saka shi da dadi sai ta yi ta fama, bayan ta saka ta caje girarta, ta dauki wani jan baki mai ruwan lebe wanda Ayya ta fada mata kadan za tana shafawa a lebenta na kasa, Hakan kuwa ta yi ta shafa kadan kafin take tsurawa madubin ido, tunda ta zo garin nan ka.ida ne a wuni sai Ayya ta tsareta yin wanka sau biyu wataran har sau uku, idan kuwa ta yi wanka dole ne ta zauna ta kula da du wata gaba ta jikinta, tun tana kallon haka a wani iri har ya kasance idan bata yin ba itama bata jin dadi, sannan ta yarda da mutun sai da gyara, wannan mugun bakin da take gani a jikinta a ruwan wanka ta ga yana sauka daga jikinta, tsabar rashin wanka na kirki ne da kuma karin bakin turkidi(tufafin buzaye), yanzu fatarta ta kasance bak'a mai haske, irin bakin nan mai kyau mai birgewa, ga gyara yana kara samu yau da kulun, har santsi santsi take ji fatar tata ta fara yi mata, Mikewa ta yi dai ta shiga fitar da riga da siket din da Ayya ta rataya jikin abin turaren wuta tun da safe kan su zata saka, Wani ni.imtacen kanshi suke na turaren tubawa, A hankali ta saka slipe (pant) dinta, an ta kasa saka breziyar domin har yanzu bata iya aiki da ita ba, kai ita bata ma sonta ne , Kayan nan ta saka sket da riga, sun amsheta sun mata cicif a jikinta dinkin zamani , Tsaye take tana kallon lufayar da Ayya ta bata, ta nuna mata ta koya mata daurawa sai dai bata iya ba har yanzu (daura lufaya sai a slow), Gashin kanta kawai ta sakawa ribom ta saka yar bakar hular da Ayya ta hada mata da kayan ta luluba Lufayar ta fice da takalman a hannayenta dan Ayya ta nada mata da kanta, Alhinayettt karfe nawa ne zaki je wajen auren? , Agaishat ta tsinci muryar Wardugu da bata da siri tana tambayar Alhinayettt dake zaune tsakiyarsu Ayya kuwa na wajen table din diner tana gyara shirin da mai aikinta ta yi mata domin bai mata ba! A hankali ta sauko, ta karaso tana hangen yanda Mu.azan ke sakar mata murmushi, Karasawa ta yi sosai kafin take gaisar da su a jimila ta hanyar fadin" Ina kwanan ku, Alhinayett ta amsata tana yaba kunshinta da harshen buzanci wanda Wardugu ya ji me take fada ya yatsina fuskarsa yana girgiza kai. Mu.azam ya kai dubansa wajen agogo ya maido wajenta ya ce" Agaishana, yanzu ne safiya, duba karanto min karfe nawa ne? Na ga ko kin gane yanda na koya maki, Ai kuwa ta juya wajen agogo ta shiga nunawa da hannayenta tana irgawa tana faman fada masa lokacin Ayya ta karaso ta kama hannunta ta ce" a bar y'a na gama shiryata, ita da bata yi safiyar zuwa wajen namiji ba ai ba lale ne ta gane safiya ce ko rana ko yama ! Ayya ta karasa tana murguda baki irin na tsofafin nan masu rigima ta kai dubanta kan Alhinayettt, wato dai da Alhinayettt ake, Wardugu ya mike ya karasa wajen Ayya, ya kasance sun saka Ayya a tsakiya shi da Agaishat wace hannunta ke cikin na Ayya tana so ta warware mata Lufayar nan ta nada mata, Sosai ya so rage muryarsa, sosai ya yo yaki da muryarsa ya ce" kin ce baki tsufa ba? Da yaren tubanci, Juyowa ta yi ta murguda masa baki ta ce" eh da saurana, Wani tsadaden murmushi ya sakar mata yana dan juya kansa, ya kamo dayan hannun nata cikin nasa ya ce" kin san du duniya ba a yi ba ba kuma za.a yi ba macen da zan so kamar mahaifiyata ko? Ta kawar da kanta bata bashi amsa ba, ya ce" in dai kina irin abin nan sai in fara tunanin na bani Ayyana ta fara tsufa, Hannunta ta warce ta dungure kansa kamar yanda takan yi idan ya hasalata ta ce" ni ba wani tsufa ko rashin tsufa bane, ina jin haushin irin yanda kuka dauki al.adar yahudawa kuka mayar naku, tun da safe take gidan nan Wardugu ya ce" Mu.azam ya gayace mu baki daya mu raka shi ya ga gari, Ayya ta yi tsam tana kallon sa, Mu.azam ya gayace ku? Wardugu ya gyada mata kai, Hannunta ta kai wajen wuyansa ta taba wai ta ji da zafi, Kalau ta ji wuyansa, ta saki ta dafe habarta da mamaki, ta ce" yaushe mage da bera suka fara shan innuwa daya har shawararsu ta fara zama daya? Me ke damunku? Shirin naku kuma ya fara bani tsoro, Wardugu ya saki hannun nata yana murmushi ya karasa ya ce" ku fice mu je ta fito idan an gama shiryata, kai yama zaka hada mana fita da karamar yarinya? Yanzu fa dole ka saka mutun ya rike bakinsa gaban yara! Mu.azam dake biye da shi yana dariya Alhinayettt kuwa da naci ta zauna sai da Ayya ta nadawa Agaishat ta saka takalminta plat, suka kamo hanya Agaishat ta mugun yi mata kyau a idannuwanta, sai ta fito kamar wata chocolate color din balaraba, ta hade ta yi wani sihirtacen kyau Haka suka karaso suka bude bayan suma suka shiga, ita dai Agaishat kanta a kasa, irin kalon da mu.azam ke jifanta da shi ke bata kunya, sai ta rasa me ya sa yake irin kallon nan,? Alhinayettt ta mika hannu ta dauko wayar Wardugu ta dawo ta shiga nunawa Agaishat hotuna suna dariya, Wardugu ya ce" ina muka nufa oga? Mu.azam ya ce" ka kai mu Bienvenu a Wardugu place, Wardugu ya taka wani wawan birki, ya kalo shi ya ce" wasa kake? Mu.azam ya ce " aa can nake son zuwa, yana mai hade rai shima ya mayar da dubansa gefen titi (BIENVENU a Wardugu place, waje ne da mahifin Wardugu ya buda da sunnansa tun suna tare suna ganewa juna kafin abinda ya hada su ya hada su su bar shi da mumunar rantsuwa a tsakani, an ce yanzu matarsa da ya aura take kula da wajen wai ita Aisata ,......mugun tsama ne tsakanin wannan family masu matukar kaunar junansu a da, kuma har yanzu da daya kwal da ya malaka dai Warsugun ne..........)..... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣5️⃣ Wardugu da ya mayar da dubansa gefen titi ya kai hannunsa yana shafa kansa a hankali, tabas Mu.azam yana tako shi kwanakin nan, in sha Allah shi kuwa zai yi iya yinsa dan gannin ya faranta masa... Motar ya tayar ya dauki hanya, tafiya ce suka yi mai dan tsayi kafin suke karasowa wajen, Daga mu.azam har Alhinayettt sun yi mamakin yanda ya yarda ya zo wajen, Mu.azam ya ji wani girman Wardugu ya karu a idannuwansa , kaunar aminin nasa ya linku a zuciyarsa, adu.a ya yi masa da fatan alkhairi ... Sai dai me, suna shiga da motar suka fara hango wasu abubuwa, Yan mata ne da muguwar shiga, shiga ta kananun kaya sosai, da samari suna kai kawo suna dan badalar su, Gaba dayansu kalon wajen suke da mamaki, Wardugu ya jinjina kansa a ransa ya ayanna, *Abinda ka zabarwa kanka kennan Uban Wardugu!* Mu.azam ya yi tsam ya ce" Wardugu , ko mu juya dai? Domin wajen shi har ya fara bashi tsoro irin yanda ake shiga ana fita ana wasu abubuwan, Wardugu ya juyo bangarensa, ya saki dan murmushi ya ce" ai mun zo sai kun shiga, Ya bude ya fice bayan ya dauki hularsa casquette dan baya so kowa ya gane ko waye shi, Jiki a sanyaye suke bin bayansa har ya karbi tikect din su hudu wanda zai basu damar leka ko.ina sannan su ci abinda ransu ke so, du tiket daya jika talatin ne, a wajen ba abinda babu, a da da aka bude shi an bude shi ne dan yara da iyayensu ranar weekend kawai ake bude shi, sannan ka.ida ne sai ka zo da mahaifiyarka ko da mahaifinka zaka shiga, ba.a barin budurwa da saurayinta shiga domin wajen an kawata shi da su piscine, su kayan lilo na zamani wajen game, wajen hutawa, da wajen cin abinci, Aman a yanzu sai ta canza zani tunda ta karbi wajen da nufin zata kula masa da shi ta canza komai banda sunnan wajen, domin dalilin sunnan da ta bari doka ke tsalake su, Wardugunma bashi da labari , a yanzu wajen ba.a barin yaron da bai kai 18 shiga ba, sai gaga gagan yan duniya, sannan ba abinda ba.a yi a ciki, kan masu bushe bushen su, sai masu aikata zina a fili (wa.iyazubillah) shi kansa mahaifin wardugun bai san takamaimain abinda ake aikatawa a wajen ba, hasalima baya zama tunda abinnan ya faru da iyalansa ya ji niger din ta fice masa a rai, dan haka yake yawonsa yana kasuwancinsa a duniya, idan ya zo niger ba dan ya jima bane, koda an kawo masa korafi bai wani dubawa dan kuwa baya so ya baiwa yan tsunguri tsoma damar kawo masa korafin gidansa, Jikin Agaishat haka yake rawa, gannin irin abinda baba sofo ke fada mata cewar ba kyau yawo jiki a bayane haka sannan ba kyau aikata zina, Ayya ma ta yi mata fadan ko a tv ta ga sun saka mace na namiji na rungumar juna ta canza tashar ba kyau aikata zina sannan ba kyau kallon tsiraicin wani banban zunubi ne , Wajen cin abinci Wardugu ya zame da su, domin daga nan du wani abin hange zai hango shi. Suna zuwa suka zauna a tsararun kujerun wajen, kamshi sai tashi yake, yayan sangartatu , yayan masu hannu da shuni, da kuma masu hannun da shuni, yayan talakawan da suka zabi rayuwar hutu da zama a inda Allah ya ajiye su, sai bushasha ake ana tafiyar da lamarin cikin tsarin yan gayu..... Menu ne aka kawo masu aka aajiye masu, nan Wardugu da kansa ke a dan duke dan kar wani ya gane shi ya dauki menu dinya kare fuskarsa da ita, Alhinayet da gabanta ke faduwa na yannayinsa, jikinsa ya nuna ya hau, yannayinsa ya nuna ransa a bace yake, Ta kali Mu.azan da ya rapka tagumi bai taba Menu din ba ta kuma mayar da dubanta wajen Agaishat ta ga du a firgice take sai sada kanta take bata son kallon mutanen wajen , abin bako ne a gareta, Hannunta ta kama ta ce" Agaishat, tashi mu je, Ai kuwa tamkar jira take ta mike ta bi bayan Alhinayettt suka fito daga dakin cin abincin suka zauna a wata farar kujera inda suka baiwa wannan lamari baya. A hankali yake karanta menu din, harda porc, da giya kala daban daban, sannan abinda ya fi daukan hankalinsa wani abu da aka zana fari shi kuwa aka rubuta masa kudi , shi idan dai ka dauke shi dole sai ka biya, kudi masu yawa haka, Kiran serveuse din mai dan bingilin sket ya yi da hannunsa, Tana zuwa tana wani irin juyi fa tafia ta karaso , Ta saman gilas dinsa ya kare mata kallo, kafin yake mika mata menu din ya nuna mata abinda yake so, Kallonsa take dan gane idan har dan hannun ne? Ko kuwa? Domin sunna taka tsantsan sosai bisa umarnin hajiarsu, dan ta fada masu au kula fa, kar su yarda wani mai bakin cikinta ya yi masu rami su afka, domin abin nan hoda ce, hoda ta shaye shaye, Jikin wardugu wando ne wanda ya dan dara gwuiwarsa, sai bakar riga wace bata da zanen komai a jikinta, sai hular baka itama wace bata nuna ko ta meye ba ya dorata saman gashin kansa wanda yake da dan tsayi kadan ba dayawa irin na samarin nan dai na zamani, yannayinsa ta karewa kallo, girkeken namiji, bai yi mata kama da police ba, in ba police ba kuwa wa zai zo masu leken asiri? A tunaninta, dan haka sai ta ce" oga, ka kawo carte din ka ko kach zaka biya? Wardugu dake zaune a aljihunsa ba kudi, sai dai a mota, carte dinsa kuwa idan ya bada za.a iya gane ko waye shi tun kafin ta karasa wajen, Yana tunanin mafita Mu.azam ya mita tasa carte din ta bank, Karba ta yi ta karanta sunnan, Kallonsa take shima, a take ta ayannawa ranta yan hannu ne, wani lokacin likitoci na zuwa siyen abinnan su dai basu san ko me suke da shi ga, Juyawa ta yi ta tafi dan kawowa , Wardugu ya hade jimkaken hannunsa da wanda yake bude ya shiga murza su a tare, Sannan yana kara bin wajen da mutanen wajen da kallo, Table sun kai biyar da ya hango suna fan dukawa su ja wani abin da yake kyautata zaton hodar maye ne a saman plat dan karami mai ruwan zaiba mai shegen kyau kafin su dago su dora daga inda suka tsaya, Abin mamaki harda yan mata, kananun yan mata wanda a cikinsu sai ya yi rantsuwar akoy wace bata kai 18old din ba! Wajen a da kafin ya dawo haka yake etablissement privé, wanda etat gwomnati ta san da zamansa ta bada amanar a bude shi, bisa takardun fa aka gabatar a da an gabatar ne kan irin wancen tsarin na wajen hutun yara da iyayensu ranar da ba.a karatu, aman a yanzu ta sauya zani wanda shi dai da hannunsa bai saka hannun a bude haka da shi ba, Kansa ya girgiza, yau ko uban wa ya daure masu zasu ci ubansu! Dubansa ya kai waje, nan ya hangi su Alhinayet suna fan taba hira da Agaishat, Idannuwansa ya tsaida kan Agaishat wanda bai ma san ya yi hakan ba, kallon me yake mata? Sho kansa bai sani ba ko yannayinta ne ya fi yiwa idannuwansa dadin kallo? Yana tsaka da kallon nan nata aka gabatar masa da harakar gabansa harda abin ja, Ajiye carte din ta yi ta juya, Wardugu ya dago hannunsa ya shiga dubawa da kyau, lale kwarai ita ce, ta ina? Ta ya aka yi take shigowa kasar? A ina take samu? Ita ke oder ko mijinta ya canza yake samo mata? Wa yake basu? Ta wace hanya ake bi a kawo har nan? Ina polisawan dake bincike a bakin titi ba dare ba rana?, ina tsaron da yake takamar ya baza a sauran garuruwa ma bale a garin da yake ciki?, ya aka yi ya yi sake haka har wannan lamarin ya cin masa da ransa da lafiarsa? Yana tsaka da tunanin ne sai gata ta shigo, Mace har mace, farar buzuwa mai shegen kyau, ta sha wasu mahaukatan sket da riga kanta ko dan kwali babu, ra sha wani dogon takalmi mai tsini, tana tare da wani balarabe ya sha jalabiyarsa hannunsa rike da makulin mota , Wani na biye da su da jaka baka suka shige tana dan dadagawa mutanen da sukai sabo hannu, A hankali Wardugu ya mikowa Mu.azam ky din motar da suka zo da ita, Murya a bace ya ce" ka tashi ka dauki yarwn can ku koma gida, minti talatin na baku ku shige gida da abin hawan nan, ko ku je gidan su Alhinayet dan ya fi kusa da wajen nan, domin idan kame ya ritsa da ku sai kun kwana a cel! Ido Mu.azan ya zaro, kame a karfe uku na yama? Gashi ranar asabar ne ranar da mutane da yawa kan fita dan shakatawa, aman me ya sa zai yi kame har cikin gari bayan a cikin nan ne ake badalar? Yar karamar wayarsa ya dauka ya dana kira, Daga dayab bangaren aka daga ana mai fadin' Chef👮🏻‍♂️ (Sir), Wardugu ya ce" ina so yanzu ka yi kira wajen Gn na Gendaremeri, sannan ka hado min mahaukatana, ina son motoci masu yawa su cika gari, ina son mahaukatam su karaso nan Wardugu place, kana jina da kyau, polisai su kama du wani wanda ya yi masu shige da suspect, ba zancen takardunka ko wani abin yau kamun yannayin mutun nake so a yi! Na fitar maka da iyaye mata wa.inda suka bayar da kwakwaran hujar daga inda suke, sai wa.inda suka kai yarensu wani wajen, bayan su a kama a cike mani cel! Da a vos ordre ya amsa yana katse kiran ya mike ya shiga aikatawa ba jira, Mu.azam mikewa ya yi da sauri ya fice ya tisa su a gaba da adu.ar Allah ya kai su inda zasu je lafia kar abin nan ya ritsa da su , duda motar Wardugu ne, da lambar shaida shi ne, ba zai hana a bincike su ba domin matarsa ta saka ya dora dokar ko motarsa a ringa bincikawa a gari! ......... Toh fa, An tabo Wardugu, an tabo tashin hankali🤔 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣6️⃣ Bayan tafiyarsu da kamar minti ashirin, Wardugu dai na nan zaune yana bin kowa da kallo ta kafurin bakin glass dinsa, Mintuna tsakani sai kukan jiniyar sojoji ta fara yin salama wajen, Da farko tunaninsu ficewa zasu yi, sai dai abin kara yi masu salama yake, Hajia Aisata dake zaune saman cinyar karuwinta suna shagali aka dokowa waya, Dagawa ta yi da yannayin duniyanci ta ce" Ya? Masu tsaron kofar Wardugu Place ne daya ya yi kiranta a tsorace ya ce" Hajia me motocin sojoji ke yi a kofar nan? Na ga sai jeruwa suke suna didirowa da alama wani suke jira, Ai bata san lokacin da ta diro daga saman kafar mutumen ta ce" me me me ka ce? Sojoji? A nan? Bata tsayin jin amsarsa ba ta fito da wani irin gudu ta ce" du wanda ya san da hoda gabansa ya yi gagawar rabuwa da ita ga arnawa a kofarmu! Nan fa wajen ya rikice, mutane du suka tsorata, Aka fara kokarin guduwa wasu na nufar motocin su da gudun tsiya wasu na auna tsayin katangar sai dai ba halin dirawa domin ga tsayi ga abin kama barawa an zagaye wajen da ita, Du masu jan mayan nan suka aniya gudu suna boyewa wasu na watsawa cikin ruwa wanda kadan ta rage masa ya janye abinsa, manya manyan masu fada a jin wajrn suka fara nufarta suna tambayarta me hakan ke nufi? Dama ba da lamuncewar gwamnati ta bude wajen raba masu eh yane ba? Ba wanda ya daure mata a gwamnati?! Ita dai ta cire dogon takalmi sai bi take table table tana kara goge dan sauran hodar da wani farin tishu ita da yarenta masu aikin wajen, Du sun haukace sai ihu take yiwa mutane kan wa.inda tsiraicinsu ya bayanna sosai sai fadi take su yi maza su saka kayan da ya fi wannan, Sannan da gudu wata bagwariyar yarinya ta fito da abaya ta kawo mata ta luluba mata daidai nan tuni sojojin sun cafke masu tsaron kofar sun fara tura su cikin motar wasu kuwa na tsare masu bi ta hanyar da wa.inda ke zuwa a lokacin, Wani sergent ne ya kali abokinsa ya ce" yau fa akoy buro.uba a wajen nan, domin lamarin na gida ne, fadan gida ne, Kai ya girgiza ya ce" ai ba na gida ba, ko na waye ta tarowa kanta dan oga ya yi mata tashi daya! A guje ta karaso table din wardugu tana babala botiran rigar tana zuwa da mamaki mamaki haushi haushi ta ce" kai waye mai hular nan ne wai? Kai ana a yi maza a kawar da komai kai kana zaune kikam , to walahi bara ku ji kaf wajen nan dan na lura hoda ta coshe tunanin ku! Du dan iskan da aka kama da ita ba ruwana, tawa kaf ta wajen nan ta bi Wc! Ta hannayen ku kuwa ban sanku bama bale na san me kuka shigo da shi, kun kuwa san wajen da girma ba lale ne sojojin su yarda da ina iya control din kowa! A hankali ya dago yana hangen yanda ake shan tsere da mutanen tsakar wajen fa sojoji suna yi masu cafkar fara suna yin waje da su, Ransa ne ya kara baci , me ya kai su kokowa da su? Su saka lasifika su yi magana kan du dan akuyar da ya nemi gudu za.a watsa masa tire a gaz! Aman sai wani guje guje suke da juna harma su yi tunanin mu tsarensu ne! Gilashin idonsa ya cire a hankali ya dago da jajayen idannuwansa ya sauke saman fuskarta , murya a dake a dage ya ce " aman kuwa da kin ci amanar clients din ki *AISATA*, na ji kuna fadin client sarki ne ke kuwa kina ikirarin ba ruwanki dan an kama shi da hoda yana zuka, Mutuwar tsaye ne Aisata ta yi, mutanen wajen kuwa gannin mai maganar sannan ya karasa mikewa tsaye du ya saka suka rude abinka da mai laifi suka fara neman hanyar fita, A rikice ta nuno shi da yatsarta ta kusan baba ta ce" Wardugu? Wardugu! Wardugu, Ya ce" ki ajiye yatsarki da nuna da ita, ko ki hade yatsutsanki ki nuno ni da hannun baki daya, rashin tarbiya ne nuna baban mutun da yatsa Aisata! Wani irin juya ta fara ji, hankalinta tashe ta ce" aman kai da kanka zaka tonawa wajen nan asiri? Ka fa san mamalakin wajen, Sergent Kabir da ya shigo da sauri ya zo dan jin me Wardugu zai fada kiran da ya tura nasa ya ja ya tsaya ya sara masa, Wardugu ya juyo wajensa ya ce" ankwa! Da sauri ya mika masa, sannan ya kara ja ya kame, A bainar jama.a Wardugu ya ja hular kansa ya cire ya nufota ya ce" Madame *MARAHUT AISATA* iko ya kama ki bisa laifin buda gidan badala, yada mugayen ayuka a boye, da siyar da hoda a fili kuma a bayane, ki yi shiru ko dukan abinda kika fada zai yi aiki kan ki, kina da damar tsayar da lauya dan kare kan ki ko kwato incinki......... Yana fada ne yana sarkafa mata ankwa irin na an kamo barawo, kafi yake turata gaba da kansa ransa bace , Suna fitowa ya daga murya ya ce" lasifikha sergent! Ai kuwa da gudu aka fita aka kawo masa, Ana kawowa tuni yan jarida sun halarta sun fara dauka abinsu, Wardugu na amsa daidai kunenta yana rike da ita hannunsana dama ya daga, a dake kalamai a rarabe ya ce" Duk wanda ya yi gigin guduwa daga wannan waje zai jawa kansa rigima, zamu saki batkonon tsohuwa (🤣🤪), koda kana da rashin lafia kan ka! Ku hade gaba dayanku tsakiyar wajen nan minti biyar na baku, du wanda bai zo ba tawa ce ni da shi! Ji kake wajen ya dan lafa da iface iface, nan fa dan koke koken yan matan ya fara tashi,, wasu na dora hannayensu a kai suna ihun sun mutu sun lalace yau asirinsu ya tonu, wasu na kaico da tunanin mai tsaya masu domin dama ba wani abin iyayensu gare su ba , irin sun samu dan masu kudi ne suka zubar da tarbiya aji daraja irin ta ya mace suke bin su ana shan kida, wasu samarin sun sato motar gida ne an zo a more da yan mata haka ta ritsa su, wasu manyan mutane ne masu iyalai a gida suka baro suka dauko wata yar shilar suka zo a cashe, waje dai ya fara daukan kimtsi, waje ya yi tsit sai iza keyarsu ake ana waje da su, Murya kasa kasa Aisata ta ce" Wardugu, ka bar ni na kirayi abanka, Bindigarsa karama ya daure a kugunsa kafin yake turata itama ya yi mota da ita, A wannan rana Wardugu bai nufi gidan su Alhinayettt ba sai wajen karfe bakwai na dare, Yana zuwa bai fita a motar su ta sojoji ba kira kawai ya yi suka fito ba tare da ya yiwa kowa magana ba suka duru a motar ya ja, inda Alhinayettt ta bi su da kallo ta koma tana shan dariyar mahaifiyarta na fadin" yau fa akoyta, Alhinayettt yau ana rigima a garinnan, kina ji shiru ? Ba galama basu fara kade kadensu ba Alhinayettt ta yi dariya ta ce" Anna (Matar babansu ce), ai sai adu.a kawai, Wardugu Wardugu Kowa Wardugu, ni dai zan yi ta yi masa adu.ar Allah ya tsare shi........ Gidan Ayya ya kai su, wace ke zaune tsakar gida da waya a hannunta sai dokawa wardugu kira take aman ba.a dagawa, Ai tana gannin sun sauko ta nufo wajen su sai dai bai tsaya ba ya yi gagawar juyawa ya fece abinsa, domin ya sani ne yanzu har an fara zuwa wajenta, bayan ta sani shima bai isa ba , shima yana bin dokar ne ! Gidansa ya yiwa tsinke, Nan ya tarar da Mota uku a ciki bayan na kofa da aka hana shiga, Mita daya dai ta mahaifiyar Walyn ce, biyun ne bai gane ba, dan haka ya shige bangarensa yana haharde kafafuwa yana so ya je ya zauna ya kashe du wata waya dake yi masa kuka a kunne ta hana shi sakat sai doko masa kira ake shi kuwa ba wanda zai daga kiransa domin ba wanda zai saurara, ba tonon asiri ne ya yi niyar yi masu ba, ba huce haushi ne ya yi niyar yi wa mahaifinsa ko matarsa ba, abin ne ya daje shi, ya diro masa a lokacin da bai yi tunani ba, tashin hankalinsa shi ne...ta ina ake shigo da hoda har ta gama gari haka? Ya sani ne sai sun sha masifa fa lauyoyi, inda ya san ya shige gabansu harda dan gidan banban lauya baki daya, in ya yarda ya ce a saki mutane, iyayen yara da manya masu daraja zasu sako shi a gaba ace dan da yaronsa ne ! Kansa ya shiga shafawa ya bude bangarensa ya shige , Kamar koda yaushe, sansanyen kamshi ne ya taro shi, wannan fa ba.a wasa da shi, Agogon hannunsa ya fara kuncewa yana kokarin karasawa cikin dakinsa na baci dan ya samu ya yi wanka, Wardugu" ta yi kiran sunnansa tana mikewa ta nufo shi, Tsayawa ya yi yana kallonta, domin yanzu ya dan saka mata haushinta da yake ji na ta tafi ta bar su wai ba zata hada numfashi da yar gidan Anna ba, Karasowa ta yi ta shige jikinsa du da yanda yake tarewa, Murya a kasalance ya ce" Walyn bari na yi wanka , aiki na yi jikina ba tsafta, Kai ta girgiza ta kara shigewa jikinsa tana rungume shi sosai a jikinta ta ce" baka wari kuwa Wardugu, kamshin turarenka na nan, A hankali ya raba jikinsa da nata ya ce" aa tsaya na yi wanka, na yi zufa sosai kin ji? Ya karasa yana mai zaunar da ita saman tsareren bed dinsa mai ruwan zeba, Bayi ya zarce ya samu ya shige kasan shower, Ruwa mai sanyi ya sakarwa kansa a jikinsa dan yana son jin sanyi A hankali ya lumshe idannuwansa yana jin sanyi mai dadi na ratsa shi, Sai da ya gama ya yi wanka na kirki ya dauro alwallah ya fito daga bayin , zuwa wannan lokacin har karfe tara ta kusa cikewa, Yana fitowa , Walyn ta kara nufo shi Tsayawa ya yi yana kallon yannayinta, magana ke tafe da ita domin batai masa yannayin tana bukatarsa ba, Dan haka ya zarce ya dauko jalabiyarsa ya saka ya dauko salaya ya shinfida yana kokarin tayar da sallah, Wardugu mana! Ta fada da yannayin damuwa, Juyowa ya yi yana kallonta bai amsa ba,.. Ta karaso ta ce" su Mamanmu ne fa ke zaune a falona ka fito ku gaisa ,. Wardugu yana kallonta, mamansu, har wannan lokacin? Bai bata amsa ba ya tayar da sallarsa, dama dan ya yi shafa.i da wutiri ne, Zama ta yi har ya karasa, ya zauna ya yi doguwar adu.o.insa na tsari da komai ya mike ya cire rigar daga shi sai gajeran wando ya yi bismillah ya haye bed, Da mamaki take kallonsa, ranta ne ya baci ta ce" aman baka ji wace nace maka tana jira ba?, Domin ta sani ne, yana mugun daraja mahaifiyarya, ko gaisar da ita zai yi sai ya dan duka, aman yanzu ta fada masa ta ga ya wani kwonta abinsa, Wardugu ta kara kiransa tun karfi, A fusace ya dago zaune , murya a bace ya ce" ba zan je na gaisar da mamanki ba, na gaji baci nake son yi ki fice mani a daki! Ido ta kwalalo tana kallonsa, kafin take juyawa ranta in yayi dubu a bace yake, tana son tsayawa ta ja maganar aman wani abin na hanata, dan kuwa dukan alamu sun nuna idan ta yarda ta kawo masa raini komai na iya faruwa , Juyawa ta yi tamkar zata tashi sama ta fita a dakin, Karamar wayarsa ya bude, Sheik ibrahim ya danawa kira, An jima tana ringin kafin yake dagawa da salama, Wardugu ya gaisar da shi da tambayarsa jama.a, Sheik ya amsa yana mai tambayar Wardugu Aiki, Wardugu ya amsa shi a nitse ya ce" Malan, a kara saka mu a adu.a, Sheik ya yi murmushi ya ce" Wardugu , na ganka a tv, fatan Allah ya tayaka, Allah ya baka ikon yin aikin kirki, sai dai zan kara fada maka, a duniya karka ce sai ka birge kowa, ka yi lamarinka domin Allah, kar ka saka fushi ko gaba dan Allah ya baka dama mai girma ta jan wanda ka yi niya, ka ci gaba da kawar da kanka a kwadayi , sannan ka ci gaba da jan istighfari kana kaiwa allah kukanka ka ji? Wardugu ya amsa a mutunce sukai salama, A hankali ya lalubo cazbaharsa fara kar tana ta kanshin turaren ruwa ya shiga ja daga kwoncen yana ta jan astghfari, Me mijinki ke takama da shi a duniya Walyn? Ya rasa wa zai rufe sai aban iman? Ko dan yana auren yar yayata ai sai ya daga masa kafa, dan kawai ya kama da shi a wannan wajen, wajen ba na ubansa bane? Zance wajen sunnansa ma gare shi! Me yake tunani? Dan yana sanye da rigar iko shikennan ? Ai idan shine yau gobe ba shi bane zai ringa yiwa mutane rashin mutunci! Tunda haka ta faru muke gidannan aman ya zo ki wani zo ki ce wai ya gaji? Gajiyar kaniyarsa, mu da muke nan bamu gajin bane? To idan mijina ya kwana a cel nima na dauki alkawain sai na tozarta Wardugu sai na saka wardugu ya shiga uku, sai na Aunty! Walyn ta fada tana daga murya sosai, Da yatsarta daya ta ce" ke a wa? Wacece ke? Kike ikirarin tozarta Wardugu bayan Allah ya rike? Ke kin san da za.a shige shi da an shige shi ba yau ba Aunty! Wardugu baya zuwa maula, hukunci kuwa idan ya kama zai yiwa ko wani dan buro........ba, meye? Takamarki ki yi masa shari, ki hada shi da malame, ko ki same shi ta hanyar abin duniya? Ban ce sihiri ba zai kama shi ba domin wanene shi, sai dai na miki alkwarin tunda kika fadi haka , sai dai mu mutu baki daya,! Mahaifiyarta ce ta kasheta da mari, rai bace ta ce" kan namiji? Kan namiji zaki ciwa kanwata mutunci? Namijin ne ya kai dan goyo har haka? Ke Wardugun da kafin aurenku ma sai da ya karya maki hannu sau biyu shine kike daga jijiyoyin wuya dan ance za.a taba lafiarsa? Kin manta dan ya kauce ki malaki wannan daula na yarda yake tata maki rashin mutunci? Idan kin canza ra.ayi na sani da wuri dan Ubanki! Wakyn dake yashe tun marin magaifiyarta, jikinta a mace, takan mance du wani kudirinsu idan tana tsaye gaban gwarzonta, namiji ne Wardugu, can dama tana sonsa sosai, damuwar kuna tana son kudi sosai! Mu.azam, tashi ka kai ni ya sha maganin bakin nan , Ayya ta fada tana nuno masa wani dan kuli wai maganin baki ne dan kar baki ya fada masa Mu.azam dake zaune kafa tankwashe Agaishat na koyar da shi bakara ya dago da mamaki yana kallo Ayya, A hankali ya ce" Ayya, idan muka yarda muka fita a yau fa kama mu za.a yi a rufe, sai karfe takwas na safe za.a tsayar da kamen nan, ki rufa mana asiri Ayya kin j? Ayya ta zaro ido ta ce" dan ubansa a rufe mun, bafa zai yi baci ba sai ya sha maganin bakin nan yau yanzu yanzu dan haka tashi mu je Mu.azam, Mu.azam ya mike yana ayyana ta faru ta kare a ransa, dan ya san in dai suka fita titi za.a kama su ne, za.a rufe su, daga shi har Ayya har Agaishat din, ...........to fah🤣🤪🤪🤪🤪✌🏼 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣7️⃣ Mu.azam ya ce" Ayya, ki bani na je na kai masa, kin ga ko an kama ni kadai ne za.a kama, Ayya ta ce" yo kai na d'a bane, a hada har mu a rufe, ba yace doka ta hau kowa ba? Na tabata an hada da iyayen mutane a wajen, Mu.azam kam ya rasa ya zai yi da Ayya , ta kuwa coge kofar daki inda Agaishat ma ta fito tace ba zai yiwu Ayya ta tafi ta barta ba, Kallon agaishat yake kasa kasa, a hankali ya ce" idan aka rufe ki Agaishana, ba zan iya hakura ba, kar ki biyo mu na roke ki, Irin na yara ta yi masa da kafadarta irin ta kiya, tama rigayi kowa karasawa wajen motar bayan ta amshi maganin bakin na hannun Ayya, Haka Mu.azam ya fitar da motar dake da lambar Wardugu, ya dauko carte dinsa ta shaidar shi likita ne, da carte didentité dinsa, Fitowa ya yi da motar Ayya ta shige baya ta hakimce, Agaishat ta shiga gaba aman a ranta a tsorace take, tana tsoron sojojin garinnan, daman ba.a saka soja a lamari a niger sai abin ya baci, su fa ba ruwansu hade kowa suke, idan ka yi masu gardama su tataka banza su barka nan zubde tamkar kayan wanki, Tuki yake zuciyarsa kuwa sai adu.a yake, Agaishat ma adu.ar kawai take inda Ayya ke kara buga lambar wardugu aman a kashe, bata shigama bale a dauka, Danja na tsayar da su aka haske su da cocila dall a idannuwansu,, gaba da baya sojoji suka zagaye su har mutun uku, Na kusa da direba ne ya kwonkwasa kofa, Mu.azam ya bude yana dubansa, Mutumen ya ce" motar Gn ce Oga, Ya ce" eh na gane ai, Ya ce" malan daga ina , kuma ina zaka je? Wa ka dauko? Sannan ka bude mana bayan mota zamu yi bincike, Mu.azam ya fara bude masu motar, sannan cikin nutsuwa ya ce" ina tare da mamanmu ne, mahaifiyar Wardugu da kanwarmu Agaishat sai ni kuma amininsa ne, daga gida muka fito zamu je gida wajensa bisa umarnin mamansa, Menene shaidarka? Sojan ya tambaya ba alamun wasa, Mu.azam ya mika masa cartocinsa, sannan ya sauke madubin bayan ya dayan ya leka wajen Ayya, Kwarai kuwa itace, waye bai san Ayya ba? Mahaifiyar General, Gaishe da ita ya yi cikin mutuntawa ya ce" yi hakuri mama muna bisa aikin mu ne, ki tabatar mana da abinda ya fada, Ayya ta ce" eh haka ne, ina son gannin Wardugu me yanzu yanzu, Sojan ya gyada kai yana kallonta, Wanda ke bincika cikin motar ya shaida masu ba komai cikin motar, dan haka ya mika masa takardarsa ya basu damar su fice Cikin ikon Allah haka sukai ta haduwa da sojojin nan suna kara titsiye su , Harda wanda bayan dukan bayannan nan yace ai shi bai wani san Ayyar ba a bashi shaidar da ta fi haka, Nan fa aka sha rigima da kyar masu taya shi suka tsawatar masa ya batsu suka tafi, Tun abin karfe tara sai kusan sha daya suka karasa gidan Wardugu nanma suka tarar da wani balakin an hana iyayen Walyn fita sai dai su kwana a nan in kuwa suka fita aka kama su toh su suka gano, sun izata sai balaki take kan wardugu ya fito ya raka su ko ya basu shaidar da zata sakasu su tafi har gida lafia, Suma su Mu.azam sai da aka titsiye su kafin suke samun shiga gidan, Mu.azam na tsayawa ya sauke ajiyar zuciya yana kallon hajia rigima, domin Ayya ta hade rai ta yi kicin kicin da fuska tana kallon yanda suke tsatsaye suna ta magana suna tafa hannu suna balaki, Mu.azam ya ce" Ayya, kar ki kula koya na roke ki, Ayya ta yi murmushi ta ce" oh yarona, yanzu kai ke yi min gargadin kar na kula kowa, ai ka san bana kula mutumen da bai iya tsawatarwa zuciyarsa ba! Bude motar ta yi ta sauka, Ai kuwa tunkarar wajensu ta yi direct ba wani tsaye tsaye, Tana zuwa ta ja ta tsaya itama tana yi masu kallon da suke mata, Da yake akoy wuta ko.ina haske ya garwaye gidan kowa na gannin kowa ne, Ayya bata fita sai ta shirya ko fitar da a rikice take ne, dan haka yanzuma sai baza kanshi take, ga lufayarta ta nada mai ruwan ja da baki, ta sha awarwarenta na zinariya, Walyn ce ta ce" ina yini, Ayya ta kai dubanta wajenta ta ce" lafia, sannan ta mayar da dubanta wajen iyayen Walyn din tanai masu kallon ido cikin ido, Mahaifiyar walyn ta miko mata hannu ta ce" Hajaju ne, uwar gidan *MARAHUT* ke ce da tsakiyar daren nan?? Ayya ta sakar mata murmushi ta mika mata hannun itama ta ce" wa.alaiki salam maman Walyn, ke ce a gidan Wardugu da wurin nan haka, Kanwar maman Walyn ta kali Walyn ta kuma kallon sirikan biyu, ta juya bangaren Walyn tana ayyana taf, lale ana cakwakiya a gidan nan, Ita kuwa walyn kitson kanta kawai take sosawa, susar da bata san ko ta meye ba, Ayya ce ta fara cika hannunta ta kuma kallon Walyn ta ce" Aa, Walyn yaron nan yana nan ne dai ko? Bara na shiga na gani Wardugu sarkin aiki! Juyawa ta yi ta nufi bangaren Wardugun cike da isa, sai a lokacin Mu.azam ya lalaba Agaishat ya cire mata tsoro suka fito daga motar, Mu.azam ruwan sanyi sai ya nufi wajen su dan gaishe su, Walyn ta daga ta watsar da idannuwanta sannan ta zabgawa Agaishat wata muguwar Harara da kallon kyama ta juya tana riko hannun mamanta suka koma bangarenta, Agaishat dake dafe da kirjinta jin yanda zuciyarta ke dokawa Mu.azam ya kallo, Murmushi ya sakar mata ya ce" mu je Matar Mu.azam, Ido ta zaro kafin take daga kafa da sauri ta yi gaba tana jin wata kunya kunya da wani irin abu game da Mu.azam din, yakan mantar da ita wacece ita ta halin nuna mata itama mutun ce mai cike da cikeken inci, yana yaba kalar fatar jikinta ta hanya kawatata da kalamai masu tsari da sence, yakan ce Allah ya datar da shi samunta, ita Agaishat yar gidan Sofo? Tana so ta biye masa tana tsoron ko wasa yake mata? Tana son ta yarda tana tsoron yan birni, Ayya na shiga ta zarce har dakinsa na baci tana fadin" ina kake janyau, ka hargitsa mana gari ka lafe a gado, tashi tashi kaima ka yi kwanan zaune dan nema kawai! Da wani irin sauri ya mike ya diro ya warci doguwar rigarsa yana faman sakawa ta shiga dakin, Wardugu ya ce" Ayya, wai yaushe zaki dauna shigo min haka zaraf kawai? Me ya fito da ke a tsohon faren nan? Ya aka yi kika ratso sojawan hanyar nan? Wa ya kawo ki? Maimakun Ayya ta bashi amsa sai cewa ta yi" baka da sutura a jikinka ne kake kwonciya Wardugu? Wardugu ya dafe kansa ya furrta" Ya Allah, Bakinta ta yatsina ta ce" fito ina jiranka Sai da ya saka kayansa ya biyo bayanta, Yana fitowa ya ga Mu.azam, da bakuwar nan ta ayya da shi ba zai iya fadin sunnanta ba dan bai wani rike ba, Sai dai mamaki yake, yanzuma wasu kayan ne jikinta, shi abinda ke bashi mamaki yaushe ta iya saka kayan tubawa har yake bin jikinta haka? Yaushe ta iya saka kayan kansa nema ? Kawar da kansa ya yi da sauri yana yatsina bakinsa yana ayyana ina ruwanka yo, ba dai Ayya ta daure mata ba? Ayya ta karbi kulin maganinta ta umarci agaishat da ta bude frij dake nan falon ta fauko ruwan roba Agaishat ta nufi frij tana tambayar kanta ina wajen budewar yake? Domin ba irin na gidan Ayya bane, wannan wani glass nema a jikinsa ko.ina tar tar yake ana hangen abubuwan dake ciki tar sai dai ba lale ka san wajen kunawarsa ba, Ja ta yi ta tsaya tana kallo, Ayya dake jira ta kallo wajenta ta ce" Agaishta kawo mana, Agaishat ta juyo tana raraba idannu ta ce" Ayya, ina zan bude?? Wardugu ya girgiza kansa, Mu.azam ya mike ya je ya nuna mata ya bude mata, ta nuna masa wanda take tunanin ruwan ne? Mu.azam ya ce mata" wannan ai jus ne, gidansa da kamarsa yake yannayin ruwa, aman kin ga jerin ruwan nan, Nan ta dauko suka dawo wajen Ayya dake ta yiwa Wardugu fadan ya kwonta bai ci abinci ba dan ba sai ta tambaya ba ta sani ne kwonciyarsa zai yi, aman kwata kwata bata sako maganar matarsa ba ko iyayenta, bata da wannan lokacin, Wardugu dai kallonta yake, ta bude ruwa ta tsiyaye fiye da rabi ta zuba maganin ta girgiza ta mika masa ta ce" shanye, Wardugu ya cee" Ayya meye kuma wannan ? Ayya ta ce" Wardugu, magannin baki ne, bakin mutane, ka san baki fa ya fi maye mugunta, baki ai ba dan uwa bane, bare yau ka janyowa kanka maganar mutane Robar ya rike a hannunsa ya ce" Ayya, bayan walahaulan da nake yi kuma dai kin bani wannan jike jiken naki? Ayya ta ce" walahaula hanyarta daban, wannan ma nasa daban, kai harda garin hantiti nake tafe, maza shanye ka dauko min buta a bayinka na zuba maka ka yo wanka ka turaru sai mu juya, Ido ya zaro yana kallonta, kafin ya maido dubansa wajen Mu.azam da irin kallon kai ka kawota ko? Mu.azam ya juyar da kai wajen Agaishat dake zaune kasa yana kallonta, domin kallonta na saka shi nishadi 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣8️⃣ Bani da bakin da zan yi godiya a irin tarin kulawar da kuka nuna, da tashin hankalin da kuka nuna na wannan abin da ya faru, kunya ta kama ni, na ji kunyarku sosai na irin hada ni da Allah da kuka yi, wacece ni? Ni ba kowa bace da zan ki yin hakuri dan haka nake shaida maku ga *BAK'A* . Daga taku yar mutan niger Kun yi sake , kuna gani tana zuwa ta shige dan ta samu ganninsa aman mu tun da yama muke zaune, a matsayin mu na iyayen matarsa yace ya gaji ba zai fito ba, kina ganni da takama bayan ta fada mana magana ta shige abinta, Auntyn Walyn ke fada ranta na kara baci, Mahaifiyar Walyn ta ja tsaki , ta ce" koma me take takama da shi ai mijin ya nuna mata iyakarta, yanzu ba da kishiyarta bace yaronta ke fada? Banza ita har ta isa ta nuna ita wata ce? Bayan an ci mata mutunci kowa ya sani? Walyn dake zaune, gaba daya zuciyarta ke wani irin tashi, ta rasa me ke damunta kwanakin nan takan tsinci kanta a irin yannayin rashin jin dadin jiki, bata iya kara furta masu komai ba ta mike ta je dan ta saka a kara tsaftace masu wajen da zasu kwana, domin ba zata lamunci a rufe iyayenta ba, za.a samu matsala sosai, Sai da aka sha rigima da Wardugu ya shiga wankan hantitin da Ayya ta jika a butarsa ta karfe, Yana yin wankan ya fito yana jin yanda yake warin magannin, sai dai yana fitowa ta kuma tare shi da hayakin Hantitin nan yana ta bade shi , Jajayen idannuwansa kawai yake binta da su, in ba Ayya ba, wannan uwar gajiyar da ya kwaso ta zo ta tirke shi da wannan abubuwan? , Tana gamawa ta fita fallo da hayakin bayan ta debo turaren wutar dake jere saman coiffeuse din dakin tana tafe tana dan sakawa yana tashi a hankali, Kansa kawai ya girgiza, ya cire jalabiyarsa ya saka rigarsa mai karamin hannun wace ta baiwa jikinsa damar bayanna ya saka wandonsa dogo fari na jalabiya saman gajeran ya fito, Ayya dake kallon Tv, Mu.azam kuwa sai wani kara shigewa Agaishat yake yanai mata labari kasa kasa, wanin ta zaro dara daran idannuwanta, wanin ta dan yi murmushi, wanin kuwa sai dai ta rufe fuskarta da hannayenta wai kunya take ji, Galala ya yi yana kallon kusancinsu da kuma yannayin su, Ayya ce ta juyo wajensa , sai dai ranta ne ya baci gannin irin rigar da ya fito da ita, ita kam ya zatai da wannan sakarar dabi.a ta wardugu ta saka kannanun kaya? Sam ba al.adar batuben mutun bace, Batuben mutun yanda mace zata ji kunyar bayannar da jikinta haka shima namijin, sun fi saka manyan kaya sukan yi rawani ko su aza hula saman kansu, suna saka kananun kaya irin na zama aman dogon wando har kasa, riga mai mutunci su yi zanzaro abinsu, aman fa siri batube sai mata nai, shi ya saka take mamakin Wardugu, gatsai gatsai sai ya bi gari da wando daidai gwuiwa, riga mai yankeken hannu har yana wata takama, Rai bace da yaren tubanci ta ce" Wardugu ! Nigey medi nubazzu ? Ay kubu nukoy ? Anna gnuduro indi hadin ? ( Wardu! damme bakajin magana , wannan wane irin rigane ? Idan mutane suka ganka me zakace?), Wardugu ya kalli rigar jikin nasa, kansa ya shafa wanda haka kamar ya zame masa jiki, ya juya ya sako wata riga a saman wannan duda haka bai bala boturanta ba, Yana dawowa ya zauna yana kallon Ayya, Ayya ta girgirza kai ta ce" a gaskiya wannan abin sam bai yi ba, kai ba wani karamar kira ba , ka wani saka kananun kaya, yanzu haka a haka sirikanka suka ganka wardugu? Salon a fita da kai a baki ko? Wardugu ya lumshe idannuwansa ya bude ya ce" basu ganni ba, Me kake nufi da basu ganka ba?, Wardugu ya daga kafada ya ce" ai na gaji ne, sai idan na huta Ayya, Da kallo take binsa, a sanninta yana matukar jin kunyar iyayen matarsa yana darajasu, ko dan irin yanda sirikan namiji keda matukar daraja wajen mijin yarsu a al.adun tubawa, domin kuwa suna da dama sosai a kan mijin yarsu, aman yau yace wai ya gaji bai je ya gaisar da su ba? Ta so ta tsawatar sai kawai ta kyale, domin dai Walyn da Wardugu auren so suka yi, shi bai taba kawo mata karar matarsa ba, itama bata taba kawo masa karar rashin girmamata da Walyn bata yi ba, ai ido ba ma.auni bane abin duba ne, yana gani kuma yana sane, dan haka ta watsar ta mike tana duban Agaishat ta ce" ku tashi mu tafi kar mu kwana a gidan nan kun ji? Wardugu ya kaleta yana talabe habarsa, ya ce" Ayya, ai yau sai dai ki yi hakuri da gorin wai kin zo gidana, yau kwana ma zaki yi Ayyar wardugu, Ayya ta zaro ido tana kallonsa, ta ce" kai, ka rufamini asiri, ni na kwana a gidanka wardugu? Aa aa, ka tashi ka mayar da mu da kanka man, Wardugu ya dubi Mu.azam ya ce" kai, zaka bado hankalinka nan ne? Bakin karfe dayan dare dokar ba wani karbar uzuri, motocin yan tafiya kawai za.a bari su je masaukinsu, suma sai dai su waye a can, ba zai yiwu ni na karta dokarnan ba Mu.azam zaka saka baki ko sai na ... Mu.azam ya taso yana dariya ya ce" Ayya, karfe daya saura kadan, ki yi hakuri, mutuncinki, girmanki ya fi karfin ki je cel Ayyarmu, kuma ke ke fadin ya yi aikinsa tsakani da Allah a rayuwa, ki yi hakuri Ayya, Ayya ta yi shiru tana kallonsu, Dubanta ta kai wajen Agaishat, ta maido wajen Wardugu, Kanta ta girgiza ta mike ta karaso wajen Agaishat ta kama hannunta ta ce" tashi mu je bangaren mata, Agaishat ta mike tana biye da Ayya, Mu.azam ya dan yi taku dan raka su Wardugu ya riko hannunsa, Mu.azam ya dawo da baya ya ce" namiji, bangaren Walyn fa zasu je? Wardugu ya ce" eh na gani, Mu.azam ya ce" anya kuwa za.a kwashe lafia? Wardugu ya yi murmushi, ya maida dubansa wajen Mu.azam da kyau, kallonsa yake yana karantarsa, A nitse ya ce" me ke damunka da ita? Batai maka kankanta ba? Me ke jan ra.ayinka wajenta? Ko bakin nata? Mu.azan ya dago da sauri yana kallonsa, Wardugu, yanzu mutun yanzu ba mutun ba, Mu.azam ya ce" ban gane maganarka ba, ....... ........................ 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 2️⃣9️⃣ Wardugu ya shiga dan shafa sajensa, ya gyada kai ya mike yana dan nuna alamun zan kamaka ne ya yi ciki abinsa Mu.azam ya bishi da kallo, ya maida kansa yana duban wajen kananun fitilu fararen dake kara kawata dakin, Murmushi ya yi shima ya lunshe ido a ransa yake ayanna zan so na rayu da ita koda na yini daya ne Ayya na zuwa bangaren Walyn ta yi salama , ba wani hayaniya ko nuna isa ta ita mahaifiyar mai gidan ta samu waje ta zauna tana duban Walyn ta ce" Walyn muna son daki ni da y'ata , muma kwanan gidanki yau ya kama mu, Walyn ta mike ta nufi wani dakin ba tare da ta ce komai ba, inda mahaifiyarta kuwa sai ta fara hura hanci ance gidan yarta, Bata jima ba ta dawo ta ce" ga dakin an gyara Ayya, Ayya ta mike Agaishatma ta mike suka nufi dakin da aka nuna masu Suna zuwa Agaishat bayi ta nufa ta dauro alwallah, Da nadin nan nata ta shinfida darduma ta tayar da sallar nafila domin dare ya yi sosai ya raba, ita kuwa yanzun ta zame mata jiki sai ta yita take iya rintsawa komai dare, Kuri dai suke zaune suna kallon juna kowa da kudirinsa a kan dan uwansa, ita auntyn walyn mamaki take ashe wardugu har mahaifiyarsa, yo har mahaifiyarsa mana gashi itama dole ta kwana a gidan? Dare ya raba , karfe biyu da rabi yayi aman wardugu ya kasa rintsawa, A hankali yake sando ya sauka daga bed din domin nan Mu.azam ya zo ya kwonta bayan sun sha rigimar ba zai kwanar masa a gado ba yace shi kuwa nan zai kwonta, Yana kokarin fita ya ji muryar mu.azam ya ce" ina zaka je? Wardugu ya juyo da sauri, ganninsa zaune dare dare saman bed din ya saka shi zabga masa harara ya ja tsaki ya ce" matarka ce ni da zaka wani motsa dan na motsa? Wajen Walyn zan tafi Mu.azam ya zaro ido ya ce" aman Wardugu baka da mutunci, wajen Walyn fa kace, bayan ka garza rashin mutuncin nan idan walyn ta kaleka komai jarabarka lale lale bata da zuciya! Wardugu ya kama haba irin mamakin nan, ya ce" kai aman baka da mutunci, ohk dare ya raba kowa ya samu nutsuwa yana shara baci ni ina nan juye juye sai ta ki kulani dan na bata mata? Da a yau da asuba zan kara aure walahi talahi a masalaci! Mu.azam ya zaro ido yana kallo Wardugu ya fice a dakin yana wata irin tafiya na ya kumsa masa haushi, Kai ya girgiza ya koma kwonciyarsa Wardugu na shiga bangaren ya tarar da su still nan saman kujeru, Walyn sai gyangyadi take, mahaifiyarta ta fara bacin itama , auntyn kuwa sai dan kada kafa take , Dakewa ya yi abinsa ya dan yi gyaran murya irin bai ahigo din nan ba, kafin yake yin salama ciki ciki ya shigo gaba dayansa Su duka farkawa suka yi, yanzunma ya cire rigar ta sama sai mai karamin hannun hakan ya sa iyayen Walyn din saurin kawar da kansu, Da idonsa ya yi mata magana, da idonsa ya isar mata da sakonsa kafin yake juyawa ya koma bangarensa, Yana fita kasa kasa maman Walyn tace" Walyn, mijinki abubuwan da ya tara suna da yawa fa, shi ne rashin mutunci, shine fada, shine rashin kunya! Walyn ta lumshe idannuwanta ta mike ta nufi kofa bata ce da ita komai ba Auntyn walyn da ta kume da haushi itama bata furta su ci kansu ba ta kawar da kanta tana dan kada kafa , niya ne ta yi yau ba zata yi baci a gidan Walyn ba! Walyn na zuwa ta yi niyar nufa dakinsa sai dai ji ta yi ya riko hannunta ba tare da ya yi mata magana ba sun nufi dakinsa, Suna shiga ya shiga kokarin janye zip din doguwar rigarta ta atampa, Tana tsaye tana kallonsa ya janye ya cire mata tana kallo yake kokarin janta bayi domin mafi yawancin lokuta haka ne ida zai sadu da ita sai sun je sun salo wanka kafin yake baje kolinsa, Ja ta yi ta tsaya tana dubansa, kwarai ta so ta kiye masa sai dai ba zata manta wani lokaci da ta ki karbarsa ba irin yanda suka kwashi tsayin lokaci yana daure mata ba shi ba ita a harkar har sai da ta yi ta fama kafin ya sauko, Rai a dan dagule ta nuna ai ita ba sai ta yi wanka ba, Wardugu ya yi kalar tausayi ya ce" walyn wardugu, me yasa ba sai kin yi wanka ba? Kinga jiki da danshi danshi ya fi dadi tabawa😌, Kanta ta juyar ta shiga kokarin hana kanta garza masa rashin mutunci, a sama take kwarai take tausar kanta kar ta saki hanya ta hanyar karta masa rashin mutunci, Binsa ta yi suka yo wankan, Suna fitowa ya jata saman bed domin shima yana so ya yi ya jishi ya saku, Da sauri sauri ya shiga romancing dinta, sai dai ya lura bata bashi hadin kai domin sai dan zile masa take, hakan ya saka shima ya zo mata kawai kai tsaye wanda hakan na wahalar da ita ainun, idan a dadi suke yakan bita a slow da dabaru ne aman yanzun shima sai ya je ya darza son ransa, Yana samun nutsuwa ta shiga tura shi, A hankali ya dagata yana duban yannayinta Rai bace ta ce" sai yanzu ka san da anfanina ko? Bayan ka gama wulakantar da ni da iyayena? Wardugu yaushe zan yi daraja a idannuwanka? Yaushe zaka daina wulakantani kai tsaye ? Dan ana fadin kai rigimame ne ai na yi tunanin kana iya zubawa kowa rigimarka banda ni! Walyn, Ya fada a hankali, kafin yake cin gaba" ki yi hakuri kin ji? Dare ne ki daina daga muryarki, sannan ko ba dare ba na fada maki ki daina magana tun karfi har tana fice tawa amo, mace kike, yar kwalisa ba wai wata kara zube ba, sai da na yarda da class dinki kafin na dauko ki, ki yi aiki da iliminki mana? Nifa ba ni na yi kamen nan ba! Aiki ne , doka ce ta hau du wani mai laifi, To kawai dan nine sarkin son kai sai na ware mijin auntyn matata?, Wardugu, kana da ikon warewar, in ka ware ba wanda zai daga maganar , kana da ikon zuwa ka fitar da shi a yanzuma ba wanda ya isa ya ja da maganar, Wardugu ya tashi zaune, tuni hankalinsa ya fara tashi ya ce" kina nufin in na je na fido shi shikenan nine general Wardugu ba wanda ya isa ya ja da ni? Walyn ta kale shi ta ce" karya na yi ne? Wardugu ya girgiza kai ya ce" a niger, a duniya ba wanda ya isa ya zo ya titsiye ni walyn aman in fa a hanyata ta dawowa daga fido shi na mutu na tarda general din baki daya? Ya zata kare min? Shikennan dan ina tsoron bacin ranki da na iyayenki sai in bata tsakanina da mahalicina? Walyn wasa kike da lamarina, kina aurena aman baki san waye ni ba! Kema kin kwana a cel bare wani tsohon dan kacare! Kin san yana me na kama shi? Tare da wa? Ku kiyaye fitina sai ku zauna lafia walyn tashi ki bar min dakina! Rai bace ta diro daga saman bed din ta saka rigarta ta bar pant din a nan, sai da ta kai kofa ta ce" inma me yake yi shi a bayanne yake yi wa ya san me wani ke aikatawa da Alhinayettt! Tana gama fada ta yi waje da sauri abinta, Da mamaki ya rakata da kallo, Ya so abin ya bata masa rai sai kawai ya yi watsi da shi ya mike yana murmushi ya shiga ya tsaftato jikinta ya dawo falo ya kwonta Tun karfe bakwai aka farka a gidan Wardugu, Ayya ta fito da yarta su sai gida, Mahaifiyar walyn ta fito da kanwarta su mijinsu, Mu.azam ya fito cikin dakakiyar shadar wardugu sai kanshi yake bazawa, Walyn na daki tana ramuwar bacin da suka kwana zaune suna masifa da iyayenta, Agaishat dake zaune jikin Ayya, domin yanda ka san mage haka take, ta lafe jikin Ayya kanta a konce kan cinyar Ayya take hangen yanda Mu.azam ke aika mata da murmushi, ya aske gashin kansa ya yi irin askin nan na samari ya yi kyau abinsa sai daukan ido yake, a baza abubuwan kari a falon na wardugu hakama na walyn, Takunsa ya shaida fitowarsa, Tafiya ce yake cikin isa da takama, Yana fitowa du suka kai dubansu wajensa, Wani irin faduwar gaba ne ya samu Agaishat, a ranta ta ayana ya salam, Wardugu ya karasa direct wajen Ayya, Yana tafe ne yana kallon yarinyar dake kwonce saman cinyar Ayyarsa, wace irin gaisuwa zai yiwa mamansa ne? Yana karasowa ya ja ya tsaya, kaki ne jikinsa tun daga hular kansa har takalmansu na sojoji, sababi ne bugagu ne na manya da galolinsa a jiki na shaidar shi din waye, Gilashin idonsa ya cire ya saka idannuwansa cikin nata, Wani irin tsam ta ji a gaba daya jikinta hakan ya saka ta kankame hannun Ayya, Da ido yake nuna mata ta matsa ya yi hugin din mamarsa , aman Agaishat bata gane ba domin ba.a taba haka da ita ba, Idannuwansa ya lumshe, a hankali ya duka ya kai hannunsa ba wani dar ko tsaye tsaye ya kama hannunta ya aniya dagata daga cinyar Ayya, Agaishat da ta yi mutuwar kwonce🤣 ta zazaro ido tana kallonsa tartar A hankali ya bude bakinsa ya busa mata iska wajen idannuwanta ya karasa mikar da ita kafin yake yatsina fuska, Ayya dake kallon ikon allah ta ce" kai daina taba min hannun yarinya ita ba irin wannan kawar taka bace! Meye haka zaka hanata hutawa? Wardugu ya turo baki sai kace wani shagwababe ya duko ya dan yi huging din Ayya, a hankali ya ce" ni ni ne na wajenki kar ki manta Ayyana, ina kwana, Ayya ta rungume shi itama tana murmushi ta ce" sannu da tashi Wardugu , aman ka ga yarinyata yanzu na fi ji da ita kan ku, ai ku maza ne , Ya yi murmushi yana kallon yanda Ayya ke kokarin maido da Agaishat jikinta, Cika Ayya ya yi ya ce" amini abin kauna, Mu.azam dake danna waya yana faman blok din yarinyar nan docter, domin ta whatsup sai kuka take masa ta fame shi fa walahi gatannan zuwa nigeriar ta dawo da shi a yi masa aiki, ya dan dagawa Wardugu hannu, Wardugu ya girgiza kai ya ce" tashi ka ja ku bi bayana na raka ku, aiki ne da ni fa ka sani, Mikewa ya yi inda su Ayya ma suka fice suka nufi mota ba tare da Wardugu ya koma bangaren walyn ba domin ya san ko ya je wata rigimar ce zasu yi dan haka ya shige dankareriyar sabuwar rangrover dinsa ya ja gaba su Mu.azam na biyr da shi a baya, Du inda suka zo gilas kawai yake saukewa ya yi nuni fa yana tare da motar su mu.azam har suka karaso gidan Ayya Wata mahaukaciyar mota fara ce fake a kofar gidan, suna karasawa mai motar da ya juya keyarsa ya juyo yana kallonsu waya a kage a kunnesa Datijo ne dogo fari kal, cikin manyan kaya yake ya yi rawani aman ya bude habarsa, Gabansa ne ya yanke ya fadi gannin yaronsa cilo da ya malaka yanda ya fito daga mota ya zama cikenken namiji mai jini a hanci, A hankali ya hango matarsa, aminiyarsa, mai kaunarsa , ta fito daga bayan motar daya ta karaso wajen wardugu, A hankali wardugu ya rike hannayenta yana dubanta cikin ido ya ce " mahaifiyata, ban kama matar Marahut dan na hada ki rigima da shi ko dan daukan fansa ba, ta cancanci kamawar ne, ina rokon ki da kar ki biyewa kowa ciki kuwa harda Marahut! Ayya ta rike kuncinsa , ta sakar masa murmushi ta ce" na sani, kaida ba mace ba mai zai saka ka yi aikin mata? Na yarda da kai Wardugu, mahaifinka kai ya zo nema ba ni ba domin ya san wacece ni, ba abinda zai hada shi da ni , ka je aikinka, sai dai ina kara jadada maka ka kiyaye bakin mutane , ka yi aikinka domin Allah , Wardu ya gyada kansa ya mayar da ita mota inda tuni mai gadi ya bude mu.azam da ya sada kansa kar Aba Marahut ya gane shi ya ja motar ya shige gidan Ayya Agaishat dake zaune gaban motar a hankali take hangen Wardugu har ya shige tasa motar ba tare da ya nuna ya ga halitar wani a wajen ba ya tayar ya ja motarsa ya nufi wajen aiki Murmushi marahut ya yi bayan mai gadi yana kokarin rufe gidan ya dakatar da shi ya tura ya shige daidai Ayya ta fito daga motar, Kokarin tafiya take domin ta ga shigowarsa sai dai me, Muryarsa ta tsinta , muryarsa mai gigitata, a hankali cikin sanyi ya ce" *asalamu alaiki anmi Wardugu!* 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣0️⃣ Dan jim Ayya ta yi, kafin take dora kafafuwanta ta fara hawa yan matatakala kwaya uku dake sadata da balbalin bangarenta, A nitse a dake ya kuma furta" du musulmin kirki ya dace ya amsa salama koda iya abinda zai fada kennan, Ja Ayya ta yi ta tsaya tinawa da ta yi tare take da su Mu.azam, ko ba komai bata so yarinyar da ta dauko riko, ta dauka tamkar yarta ta cikinta ta yi wani tunani a kanta, dan haka ta ja ta tsaya ta juyo a nitse tana kallonsa ido cikin ido ta ce" amen wa alaika salam, A hankali ya kai hannunsa jikin karfen ginnin yana kallonta, matarsa uwar dansa, auren soyaya suka yi ba na hadi ba, auren fahimtar juna mai cike da nishadi, sai dai ya yi sake, ya yarda laifinsa ne hakan ta faru, a hankali ya ce" wa ya baki izinin yin tafia har kasar agadez kauyen agadez timiya ? Kika je kika yi har kusan wata biyu? Anmi wardugu banda fitar ta cikin garin Niamey yanzu kuma har kin fara yin ta nesa haka? Ba dai a so zuciyata ta huta ..... Ya karashe yana dan sada kansa, Mamaki take, al.ajabinsa take, uhum lalema, me yake nufi da ita? Kennan yana bibiyar rayuwarta ko me? Fuska ta yatsina kafin take fadin" gidan nan ban yarda Wardugu ya saka ko sisinsa ba dan kar watarana ka zo da takamar danka ya gina, Marahut ya ce" bayan Allah ya halita min ziyarta inda gonata take a duk lokacin da na yi niya? Haushi ne ya cika Ayya, yana nufin ita, dan kuwa ai matayenku kamar gonakinku ne, Dan juyawa ta yi ta ce" ka tarda shi inda yake ba gidana ba, Dan daga murya Marahut ya yi , domin ta tafi ya ce" ki kiyaye fita kai sake ko dan yarmu da kika dauko kar ta koyi yawo ba izinin miji idan mun yi mata aure! Wani irin bude kofar ta yi ta rufota da karfin gaske wanda da ba dan glas din mai nauyi kuma mai karfi bane da kasa zai zubo baki dayansa. Murmushi ya yi, a hankali ya sauko wajen su Mu.azam dake tsaye cirko cirko, Mu.azam ya gama yarda wajen wa Wardugu ya yi gadon abubuwa, Gashi mahaifinsa ya kai shekaru sitin da yan kai aman yana abubuwa tamkar wani bajimin matashin sarki? Yana karasowa ya saki fuskarsa sosai ya mikawa Mu.azam hannu, A mutunce Mu.azam ya gaisar da shi, Marahut ya amsa yana dubansa kafin yake kai dubansa wajen Agaishat, da yaren buzanci ya ce" ina murna da kasancewa Abanki yarinyata, Agaishat ta ji abin sabo, abin ya zo mata a bawai, ikon Allah, mutun ya wannan, ya kirata da yarinyarsa, gashi fari karkarkar ita kuwa baka kirin aman bai nuna kyamata ba, harma ya fada mata ya yi murnar kasancewarta yarinyarsa, Baki kawai ta saki tana kallon kama, kai har yannayin girman jikin domin Ayya bata da girman jiki irin wannan , Hannunsa da ya dora a kafadarta na dama ya ce" sannan ki yi ta kulawa da kanki ki yiwa Ayyarki biyaya, zan yi tafia sai na dawo ........... Agaishat da wata kwallah ta tarun mata a ido tana kallo ya fice a gidan a kafarsa domin a waje ya bar motarsa, Yana fita ta juyo wajen Mu.azam, da tsananin murna ta ce" ka ji me ya kira ni? *Yarinyarsa*, Mu.azam na kallonta shima da murmuahin a fuskarsa yana kallo hawayen murna ya zubo daga idannuwanta, Cike da zumudi ta ce" kuma kuma yace ya yi murna da kasancewata tare da su, yaya Mu.azam ni *BAK'A*, ai bai kai ga bata amsa ba ta cikashi ta shiga taka matatakalar da gudun tsiya dan zuwa fadawa Ayya cike da murna, Sai dai tana shiga ta tarar da Ayya zaune ta hade rai tamkar an yi mata mutuwa, yannayinta ya nuna tana cikin yannayin bacin rai mai tsanani A hankali ta shiga dan takawa dan karasawa kusa da Ayya, Tana zuwa ta dan duka tana kallonta murya a sanyaye ta ce" Ayya, lafia? Ayya ta dago ta yi mata wani kallo na ta barta, Agaishat bata fahimta ba ta ce" Ayya, *WANENE WANNAN?* Ayya ta zuba mata wani kallon, rai a hade ta ce" ki je dakinki Agaishat! Agaishat ta mike da sauri tana kallon Ayya kafin take juyawa da sauri ta nufi dakin nata a matukar tsorace, Tana shiga ta karasa bakin bed ta tsaya jikinta na rawa, Ayya bata taba yi mata haka ba, dan haka hankalinta ya tashi ainun,............ Wardugu dake tsaye kan kafafuwansa tun zuwansa wajen aiki yana fama da jama.a, tun daga manyan mutane masu fada a ji da suka biyo sahun nasu, da tsagerun mutane da suka zo belin yan uwansu ko abokai, sai bayin Allah talakawa da yayansu suka kai su inda basu taba tunani ba, suma sun zo da kokon bararsu kuma cikin ikon Allah wardugu na sauraron mutane du wanda ya ga abin ba wani bane a nan take yake salamarsa da kwakwaran kashedin idan suka kuma hadewa a irin wannan waje ba zatai masa da kyau ba, Daga karshe dai Wardugu na bincike ne cikin nutsuwa yana salamar mutanen da basa bushe bushen nan bisa kashedinsa wanda da kansa yake yiwa mutun ido da ido ba aike ba! A hankali ya fara kawowa wajen masu zuwa dan kawai su kwale, wani saurayi aka shigo masa da shi, yana zuwa ya zube kasa ya shiga gaisar da Wardugu, Warsugu dake kallonsa, kana ganninsa ka san ba wani dan mai shi bane, aman ya tashi ya saka kansa a rayuwar halaka idan an yi magana ace kadara, ace Allah ya dora, A dake ya ce" tashi ka zauna saman kujera, Da sauri saurayin ya tashi ya zauna sai sasada kai yake tamkar ya yi karya gaban sarki, tsoro yake a ransa domin a gaban idonsa akaiwa wata dukan tsiya wanda ya sa har ta sume dan kirikiri ta yi ikirarin ita ko wacece ta tofar da yawu ta dura ashar ta ci alwashin gyatiminta zai zo ya fitar da ita har sai uban gidansu Wardugu ya bata hakuri hakan ya sa su kuwa suka nuna mata da gidan maza ta shigo ba gidan yara ba, suka murza kwonji a jikinta har ta some, labarin da ya kaiwa Wardugu da ya fito a gaban mutanen nan na cel ya zuba mata ruwa da kansa wanda hakan ya farfado da ita, sai dai tana tashi ya wanka mata wani marin da ya mayar da ita duniyar suma sannan ya nunata da yatsa ya ce" ban so tonawa kowa asiri ba shi yasa na saka aka shigarmin da iyayenku daga wancen dakin wanda ba wanda zai gane in an shigo da kai wanene mahaifinka kuma me ka aikata ba, sai gashi kin tonawa mahaifinki asiri a matsayinsa na dan siyasa kin kama sunansa har kin nuna mana halin kodin! Dole mu kai kararki wajen alkali kin zagi soji! Haka aka kwasheta aka jefata cikin cel din ya koma ya ci gaba da aikinsa dan haka ne ya sa wannan saurayin kamar ya kwonta dan kadabi, Wardugu ya ce" yaya sunanka? Saurayin ya kalo shi kadan ya sada kai ya ce" sunana Murtala Tasiu, Wardugu ya gyada kai ya ce" tun yaushe kake zuwa wardugu place? Kai da wa kuke zuwa? A nawa kuke biyan kudin shiga? Du sati sati kuke zuwa? Da yan mata kuke zuwa? Murtala ya ce" ba.a fi shekara biyu ba,, Ni da dan gidan Elhaji Dahiru muke zuwa, Aa ba kowani sati ba dan kudin shigan da muke biya shima ba kulun yake da shi ba jika goma goma, sannan in mun shiga ga kudin kashewa , aa iya mu muke zuwa a can muke haduwa da yan mata kowani sati akoy a ciki, Wardugu ya tsare shi da ido ya ce " tun daga bakin lokacin ka fara busa kodin? Murtala ya shiga raraba ido, ya daga hannu zai fara rantse rantse Wardugu ya ce" murtala, ka fada mini gaskiya mai yiwuwa ka samu sasauci! Murtala ya ce" oga, ka rufa mani asiri dan girman Allah, mahaifina gajiyaye ne, sai na bi abokin nan nawa yake bani wani dan abin na je na ciyar da mahifina da kanwata, kanwata bata gani, mahaifina kuwa ya tsufa, ba a son raina nake saka kafata wajen nan ba, Wardugu ya ce" ban tambayeka labarinka ba Murtala, ban yi niyar wulakanta ba ina rokonka kar ka wulakantani, kar ka kawo mani shirme a nan , da farko dai du idan ka ga soji rikeken dan tasha ne domin tashanci koya mana ake mu shanye sai dai muna aiki da shi ne kan tsari, na jima a aikina hakan ya saka ana yi min karya nake ganewa, ka bani amsata ko mu baje basirar rainin hankalin ni da kai!............. 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣1️⃣ Da sauri Murtala ya ce" Eh eh , tun daga lokacin da muka je abokina ya siya ya saka na taba tun daga lokacin nima nake sha , Wardugu ya shiga gyada kai ya ce" kana iya fita, Dan mikewa ya yi, sai ya mike sai ya dan duduka sai da wani soja ya shigo ya finciko shi ya mayar da shi cel, Da mijin Auntyn walyn aka shigo, Mutun har mutun, sai sasada kai yake na kunya, Warsugu ya tsare da da ido, wai tun a nan duniya ka kasa hada ido da mutanen da basu baka ko cin wuni daya ba, ya zaka kare da wanda ya haliceka ya baka dukiya dan gannin ya zaka tafiyar da ita, ya ara mata lafia, gani da ji, ya baka ikon motsi, ya baka damar magana, ya kaika kasar da ba yake yaken yu da kulun wa.inda zasu iya tayar maka da hankali , ya baka isashen lokaci dan kawai ka bauta masa ka yi masa biyaya, sai gaka tsofai tsofai a gidan badaka tare da yar shilar yarinya ta tube kusan zindir tana maka rawa tana ciyar da kai gasashen kifi, shine zakana wani sada kai a gabana kai ga cikenken dan iska! Du wardugu ke jifansa da wani matsiyacin kallo sannan yana ayyana du haka a ransa, Wardugu ya ce" ya sunanka malan? Mijin aunty da mamaki ya dago yana kallon wardugu ya ce" haba haba wardugu, ai ko me ake a san na gida, a fitar da na gida, ka yi hakuri kure na aikata ba zan kuma ba , ka salame ni na koma ba tare da wani bama ya ji abin kunya ne ace ka rufe mijin kanwar babar matarka! Baki wardugu ya dan daga na mamaki, ka ji wani dogon bayani wai mijin kanwar babar matata, Kai ya girgiza a ransa ya yi murmushi, a fili ya kuma furta" ya sunanka malan! Yana mai dagowa da yanayin dakewa, Mijin auntyn walyn nan ya fara zufa, yana gagawar magana ya ce" tototo, sunana Lawali , Elhaji lawali, Wardugu ya ce" me ya kai ka Wardugu place? Kai da wa ka je? Me ka je yi? Tun yaushe ka fara zuwa? Me ka lura ana yi a wannan waje? Lawali ya ce" ni kam wannan waje na je ne bisa tsautsayi da rabon a yi, domin dai yarinyar nan na so na aura sai take shaida min na kaita mu sha iska, to da muka je shikenan sai muka mayar da wajen wajen zuwanmu lokaci zuwa lokaci yanzun dai an kai shekara uku, Sannan a wannan wajen gaskiya na lura ana abubuwan da bai dace irin ahaye shaye, wannan da ka ganni tana yi wai karamin ne, eh wanda muke yi shine karamin ba Allah ja da kwana.... Ya karashe yana jinjina Wardugu ya jinjina kai, ya ce" lawali kada daga Kokin ne? Da sauri ya dago yana duban wardugu, ya ce" bilahilazi ban taba ba, ai ni ko warinta na ji juwa ke kayar da ni, ka rufa mani asiri rashin jina bai kai can ba, Wardugu ya dago yana dubansa, wai rashin jinsa, kai ya girgiza da hannu ya yi masa nuni da ya fita, Yana kokarin kara magiya Marahut ya shigo inda sojan nan ya biyo bayansa yana dan kame kame ya rasa me zai yi, su dai ba wanda bai san oga Marahut mahaifin uban gidansu ba, shi ya isa ya masa iyaka ne? Tun daga babar kofa ya samu shigowa ya ratso du zone na control ba.a hana shi ba sai shi tal dake tsaye dan kula da bude kofa da kuma rufewa da kyau ne zai hana shi shigowa? Kallon Lawali Marahut ya yi kafin yake girgiza kai yana murmushi daga cikin rawaninsa,, Kai sade Lawali ya fice domin ya ji kunyarsa ainun Marahut ya bi tsararen tankamemen office dan nasa, bMarahut ya ce" ya aka yi ka canza kanshin turarenmu ne Wardugu? Kuma ya aka yi ba hotona a office dinka bayan kai din dan halal ne koda shege ai ado yake da ubansa bale dan halal , Wardugu dake ta cika takardu yana dan dana laptop bai ce da shi ci kanka ba, Marahut ya ce" Warsugu Abanka ne fa ni ? In ba ruwanka da mutane su ga kana min haka ba ruwanka da Allah ne?? Wardugu ya ajiye biron dake hannunsa ya dan shafa kansa ya dago da kallonsa wajen mahaifinsa wanda a kamaninsu haske ne kadan ya dan fi shi domin farin wardugu ba irin cancan din nan bane, Warsugu ya ce" Aban Wardugu ra.ayi ne ya sa na daina anfani da turaren da ka sanni da shi, sannan ni ba mace bane da zan kawo hotonka office na buga, kuma shegema mutun ne! Murmushi marahut ya yi ya karasa wajen kujera ya zauna ya ce" to ka fido mani matata mu tafi gida Wardugu, Wardugu ya yi murmushi a bayane shima ya ce" ba zan so shakar iskar da kuke shaka ba ko na second daya, sai dai ya zama dole ne, matarka mai laifi ce Meye laifinta wardugu? Me ta yi da tsanani haka? Ka san yara da kin ji suke,aman ai koma me ta yi ina gannin sai mu kashe mu birne abinmu a tsakaninmu ko wardugu? Marahut ya fada yana dubansa Wardugu ya ce" zan so haka, sai dai ka ga rashin jin nata ne ya yi kamari, tana shigo da kwaya ne tana siyarwa wannan ba boyayiyar shaida bace, abinda nake bincike kawai na samu hanyar da take shigo da ita ko wanda ke bata sai na mika su kotu koda kuwa *kai ne*, sai dai ban san ba yin hakan ko Allah zai kama ni da shi? Da sauri marahut ya ce" Quoi? (What?), wani irin kwaya? A Wardugu place din? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, wardugu ka kara mani haske a lamarin nan Wardugu da ya ji ya dan samu sasauci, domin a sama yake, jininsa a saman akaifa, tsoro yake kar a je rinjayar nata ya kai ta saka Marahut a wannan harka? Aman yanzu ko ba komai ya ji dan sanyi a ransa dan kuwa har gobe da sunnan mahaifinsa yake anfani, Wardugu ka fada mani mana, Marahut ya fada yana dubansa da yannayin serius Wardugu ya yi umarnin a kawo AISATA, Shigo da ita aka yi, dare daya tak du ta fara fita hayacinta abinka da wada ya saba da hutu, Tana gannin Marahut ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi kafin da sauri ta nufi wajensa ta saki kukan kirsa, Tana kukan ta ce" ka ga abinda Wardugu ya yi mini? Wannan wani irin tsana da cin mutunci ne? A gaban jama.a ya saka mini anker tamkar wada na yi sata, ai a tunanina ya dace komai ya fice tsakaninmu ko me na yi sai ya hukunta ni a gida ba wai a gaban duban mutanen da zasu yi min dariya ba, Hannunsa ya saka ya dagota daga jikinsa yana dubanta, kadara, Aisata kadara ce mai wutsiya, a dalilin Aisata ya rabu da farin cikinsa da girmansa a idannuwan iyalinsa, maciya ce Aisata, Aisata zinari ce, A nitse ya ce" me da me kuke aikatawa a Wardugu place? Aisata ta yi tsam kafin ta shiga cicira ido ta kali dan ta kali uban, cikin yannayin barikinta ta ce" me muke yi kuwa banda neman kudi? A wardugu place ba abinda muke yi, Wardugu dake rubutu a takarda ya dan yi tsam ya dago ya dube su ya maida kansa ya ci gaba da aiki, Bai jima ba ya daga wayar office din ya danna kira, Cikin girmamawa ya gaisar da jujun kafin yake fadin" mai girma na gama nawa binciken, yanzu ana kawo maka takardu ka duba, daga nan na mika maka su kawai , Amsa shi ya yi kafin yake kashewa, Marahut da ya gama fahimtar wayar da Wardugu ya yi shima yana dubansa, cikin yannayin nutsuwarsa dai ya ce" har yanzu baka daina jin haushina kan Aisata ba? Wardugu ya juyo da sauri, ido ya zazaro baki daya kafin yake mikewa ya tofar da yawu a nan cikin office din ya ce" kan wannan? Ya fada yana nuna aisata, Ya girgiza kai ya ce" ai koda me daraja ce bata kai na yi anfani da damata dan wulakanta ku ba, ka gane laifi ta yi, idanma baka yarda ba ai kai din oga ne kawai ka je wajen wa.inda zan mikawa takarda idan sun baka matarka ruwansu ni dai ai na tono barnar ko? Ka fi kowa sannin waye wardugu domin kaine mutun na farko da ka rikeni a duniya bayan likitar da ta fitar da ni daga cikin mahaifiyata! Yana gama fada ya ja kys din motarsa ya dauki gilashinsa ya fice a office din yana mai jin haushin yanda mutane ke magiya kan a bari a ci gaba da yada barna! Jikin Ayya ne ya yi sanyi bayan korar Agaishat da ta yi, a hankali ta mike ta nufi dakinta tana mai jin wani iri me ya yi zafi harda laifin wani zai shafi wani? Tana zuwa ta shiga da salama, Agaishat dake zaune kasa ta dora kanta a gefen gado tana jan carbi da hannunta ta dago da sauri tana kokarin mikewa tana duban Ayya, Karasawa Ayya ta yi ta riketa ta zaunar da ita gefen gado, A nitse ta ce" ki yi hakuri yar gidan Ayya, ba zan kuma yi maki irin haka ba , Agaishat ta sauke ajiyar zuciya tana dubanta, Ayya ta ce" bara na baki labarin mu..... na fada maki wacece *AYYA?*, na fada maki waye *MARAHUT a rayiwar Ayya?*, na fada maki wanene *WARDUGU* sannan wani irin girman daraja yake da shi a rayuwar Marahut da Ayya? Yarinta bara na baki labarin da ba kowa ya sani ba................ 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣2️⃣ labarin Wardugu da tushensa a gajarce . ........ .................. Sunana *Zanaba SHAU*, sunnan Mahaifin Wardugu *MARAHUT ELUM*, ni marainiya ce gaba da baya, na taso a hannun kakata ta wajen uwa da ta yi min saura, Marahut dan gata ne gaba da baya, ya kasance a lokacin anguwarmu daya domin gida uku kawai ke tsakaninmu, Tun wayona bai gama fahimtar Marahut na sona ba har na gane domin kiri kiri idan na yarda wani lokacin na yi dan shirin atampa na yafa mayafi na fito zai rufe ido ya kora ni yana masifa, A anguwa ana girmama kakata domin mace ce da ta san girmanta, ba abinda ya shafeta da abin hannunka, ga mutunci ga zumunci,...du juma.a zaki ga an kawowa kakata abinci daga gidajen anguwar nan ciki kuwa harda gidan su Marahut inda mahaifiyarsa shuwa arab ke turowa kakata da gurasa ta kasa, irin wace ake yi a kasa ta ainahin da miya mai dadi harma ki ga an zuba tawa miyar mai magi domin a lokacin an hana kaka shan magi. Sosai muke soyaya da Marahut, duk da wani lokacin nakan zauna na yi shiru ina tunanin Marahut na so na kamar yanda nake son sa kuwa? Hakan sai ya tayar min da hankali sosai domin Marahut dai jarumin namiji ne mai cike da abubuwan da mata ke marari har suna kai wawa, harma wani lokaci na kwatanta masa.... Tsareni ya yi da ido kawai, zuwa wani dan lokacin ya mike ya fice abinsa hakan ya haifar min da faduear gaban ko ya yi fushi ya bar ni ne? Kwana biyu tsakani na dawo daga makarantar dare islamiya da nake zuwa a kusa da mu na tarar da kakata zaune tana jan carbinta da rufarta bata kwonta ba, ba kamar sauran lokutan ba, Da sasarfa na karasa wajenta dan gannin abinda ke damunta sai dai ina zuwa ta rike hannayena tana kallona ido cikin ido ta ce" Zannaba, kina ta adu.ar neman Allah ya baki miji na garin nan kuwa? Na amsata ina dubanta da wani irin yannayi ta ci gaba" an zo neman auren ki daga gidan Elum, Zannaba kin ji zuciyarki ta aminta da Marahut? Wara irin kunya ce ta diro mani, domin fa Agaishat yata tubawa na da muguwar kunya, batuben mutun na da kunya harda ta mamaki, hakan ya saka na sada kaina kasa harma jikina ya fara rawa, Kakata ta ce" kul, na hane ki da ki yi haka da ni, ke kawai gare ni kema ni kawai na rage maki, Allah shi ne gatanmu, zan so ace na bar ki hannu mai kyau, dan haka maza bani hankalin ki mu gama magana, In takaice maki a wannan rana bamu kwonta ba du sai da muka dauki niyar istihara wace cikin kwana uku hankalin mu ya gama kwonciya har ma muka aminta da auren nan, Marahut ya yi min gata , agaishat ya kai kudin aurena ya yi min kayan da aka jima ana labarinsa, aka daura aurena irin na kowace yar gata inda kakata ta bada mamaki ashe tana ajiye da sarkokin aurensu ita da mahaifiyata, ta kai aka buge akai min tafkekiyar sarka da abubuwan hannu na zinari irin na kowace batuba yar gata, sannan ta fitar da kadarorin mahaifanna harma da nata gaba daya ta raba aka yi min kayan daki sauran ta damkawa mai anguwar anguwarmu amana, Wsshe garin auren mu Marahut ya dankara min wata makekiyar sarka ta zinari tatare da kwacakwablarta bisa al.adun tubawa wanda hausa ce cikin hausa, ba.a jima ba muka daga dan komawa bakin aikinsa inda aka maida shi domin baban likita ne kuma yana harkar kasuwanci da kiwo..... Mun kasance cikin farin ciki, mutunta juna, da kaunar juna, muna tafiar da rayuwar aurenmu bisa tsarin islama muna kiyaye du wani abinda zai firgita mu sai dadaykun da baza.a rasa ba na yau da kulun! A haka na samu cikin wardugu, Mu kai rainon abinmu har na tashi haihuwa inda Allah ya taimake ni na haihu a hannun mijina a asibitin da yake aiki da taimakawar nurse.. . Mun koma gida dan zanen sunna, nan Marahut ya gabatar da sunnan *WARDUGU* a matsayin sunnan da ya zaba, Kowa ya jinjina lamarin sai dai ikonsa ne, dansa ne, aman sunnan Wardugu linzami ne ga mutun mai zuciya, mai fada, mai balaki, kai ba.a zama lafia da mai sunna wardugu, Wardugu! HUM, ko canfawa ne mun yi kuma yana bin mu, kwarai zahiri ne Wardugu duniya ne guda, ba sai an koya masa ba da abinsa aka haife shi....... Ina wanka a gida wajen kakata, tana kula da lamarina sosai da sosai, wata rana muka wayi gari da kyautar Allah, inda mutuwa ta sake zagayowa ta tsame min wace ta min saura a tarihin iyayena, Ayya ta yi shiru ta share kwalar da ta zubo mata, Agaishat da ta yi lamo ta dora kanta a hannun Ayya, Ayya ta ci gaba" Agaishat na ji mutuwar baiwar Allahn nan, domin ni ita ce duniyata, ko me na kwaso ita nake fadawa a nitse ta warware min, ta rasu ta bar ni da jaririn da a lokacin bana iya daukansa da garaje dan girmansa masha Allah, ta bar ni da dan labubun yaron da yakan calara kuka wai shima nice mahaifiyarsa, na ga rana na godewa Allah, Agaishat ta kara jimke hannun Ayya itama tana jin yanda hawayen ya zubo mata, Ayya baiwar Allah, bata da kowa gaba da baya, ashe du yanda mutun ya kai ga malakar arziki bashi da cikeken farin ciki na yanayin rayuwar yau da kulun? Ayya ta ce" na dawo ga marahut, bani da kowa bani da komai sai Shi a nan cikin duniya, Bayan an yi bakwai muka juya garinmu inda na dauki girma na ajiyewa kaina na karfi da yaji na ci gaba da karatun likitana da nake yi a Ensp, Can tsakiyar dare nakan dadaba Marahut, idan ya farka sai nace" Marahut, kar ka wulakanta ni a duniya, kai ne duniyata, kai ne farin cikina, Yakan riko ni jikinsa ya ce" ban aure ki ba sai da na gane ke ce lumfashina, a duniya baki daya me ya kai lumfashin mutun tsada? Ba zan yi garajen gannin hawayenki ba sai na kadara! Magangannunsa da alkawarurukansa suka saka na samu nutsuwar zuciyata harma na warware na ci gaba da shagulgulana na yau da kulun tare da yarona, Tun Wardugu na da wata bakwai ya mike, yana tafiya da kafafuwansa digir digir tamkar dan gwari, Du inda na yarda na je da shi idan ya damki yaro ko matashi sai an kwace da kyar, Ya kasance ba.a gardama da shi da ya warware, yana fama da ciwon athsm wace in dai na yarda ransa ya baci toh fa a kadan mu yi kwana uku a asibiti domin athsmar nan zata tashi ne ya kasance daga ta kwonta sai ta kuma tashi domin ba zai kwontar da hankalin nasa ba, Wardugu zuciyar mahaifinsa ne, domin daga shi ko batan wata ban kuma yi ba, muna bibjyar komai nasa tamkar ranmu, kai har bama kawaici a nuna soyayarsa, A haka Allah ya hada mu da baba tsofo, wanda kawai salama ya yi yace yana bayar da magungunnan hausa ne, Nan muka zanta a bayan idon mahaifin Wardugu domin baya son lamarin hausan nan wai tsoro yake ya taba masa reins, Cikin ikon Allah ya ki karbar kudina, muka ajiye magana idan Wardugu ya samu lafia zan yi masa kyauta, Yakan zo lokaci zuwa lokaci ya kawo mana magannin da cikin ikon Allah muke bashi da nonon rakumi sabon tatsa da sasafe, tun ina boyewa har na bayannawa Marahut shima ya kama mani domin sauki kamar da wasa Wardugu na samu a hankali a hankali har ya daina lumfashi da bakinsa ya dawo yi da hancinsa, Agaishat na kasance mutun mai shegen son mutane, ko dan na sakawa kaina bani da kowan nan a duniya sai Allah sai mijina? Ya kasance son yaya da yawan kula zumunci da jama.a, A haka na hadu da babar aminiyata matar sarkin agadez, na hadu da kawata ta damagaran hajia Falmata, da sauran su, Wardugu rashin lafiarsa kawai ya warke aman halaya na nan, a haka aka tsahe mu aka maido mu garin nan inda kwata kwata baba tsoho ya bace min na neme shi na rasa har muka taso aman abin na tsaye a raina sannan ina yawan tambaya, Kwonci tashi wardugu ya tashi da niyar shi fa soja, soja, hakan ya sa mahaifinsa ya sama mana waje a Babar makarantar sojojin niger wace ke a kwalo, wace tun yaro na karami ake kai shi shikennan shi da iyayensa sai jifa jifa, Karatu yake, sannan kwazo yake da shi ko a filin training, Hakan ya sa babansu yake kaunarsa harma yake zumunci da mahaifinsa Wardugu na da shekara ashirin da biyu ya fito gagarumin comandan, jikaken saurayi, kaukauran namiji, zakin zamani, yaro da kudi kamar yanda ake kirarinsa....... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣3️⃣ To tunda Wardugu ya dawo sai kuwa yan mata suka ce bismillah, ba kalar wace bata zuwa , kin dai ga yanda yake uwa kurman nan? Toh haka zasu zo su karaci haukansu sai dai su yi su gama su tafi, Ban san ya aka yi, ta ina aka yi suke kawance da wannan mai sunna Alhinayettt wace ni hakanan nake gannin karya ne ba wani kawance may yiwuwa soyaya suke ba halin aurenta domin aurensa bai wani jima ba, Ana haka ya amincewa yarinya daya soyayarsa, yarinyar da ta yi kundubala da sauran yan matan, Soyaya suke ta hauka irin soyayar yayan zamani, ni ba zan shaidi yarona ba ba kuma zan ce yana aikata masha.a ba, aman a lokacin da yake kwana a gidan nan har kwana ta sha yi a wajensa dan kuwa sai da na rufe idannuwana na ci masa mutunci sannan na daina kamata a dakinsa, Waye shi da zai rantse min ba abinda ya shiga tsakaninsu? Namiji ne, ita kuwa mace, sun kadaice a wajen da ba kowa sai su sai Allah, ai hankalina ba zai dauka ba! Ire iren abubuwan da sukai ta faruwa kennan da yarinyar da ta gama kwana gidan mu, mamaki nake da tsoro, Wardugu ina ya zubar da kunya irin ta batube? Gaba daya wannan karatu da ya yi ya saka du ya zama wani kiritace wani tsayaye! Sam ya zubar da al.adu da dabi.un tubawa idan na yi magana sai yace ai ba wani adini bane, shi gaskiya ya girma a birni ba zai ci gaba da rayuwa irin na daji ba, ! ALLAH ya shirya, Ana haka ya tafi karo karatu inda suka hadu da mu.azam suka kula zumunci mai ma.ana, a can ya hadu da matar da yake aure yanzu wace a lokacin ba irin azabar da bata sha ba domin shi soyayarsa tana kan *AISATA* , Aisata? Agaishat ta tambayi Ayya, Ayya ta ce" kwarai Aisata dai wace ubansa ya aura, Agaishat ta ce" aa, Ayya na shiga rudani, Ayya ta ce" bara na warware maki,.... Haka kawai mun ci gaba da fahimtar juna alhamdulilah har wardugu ya dawo daga tafia, Nan ya zo da maganar a tura wajen yarinya a tambayo aurenta, Tashin farko ya dira cewar ba da yawuna ba, kuma in har ni na haife shi ba za.a yi haka da ni ba, domin yarinya bata da da.a , zan so matar da zai aura ta fari ta kasance mutuniyar kirki ko dan fadar adini ku zabawa yayanku iyaye na gari, Nan fa aka shiga tashin hankali, yarinya ta zo har gida ta tsire ni, nan ta yi ikirarin cewa" AYYA kike ko wa? Kin dai ganni, kin ga yanda nake, nice farar mace , kwakwa! Dole na shigo gidanki ko a sarakuwarki ko a kishiyar ki! Abin ya bani mamaki, zuciya ta kama ni na tunkareta kafin take ankara na damketa, ina faman ihun sai na nuna mata ruwa ba sa.an kwondo bane malalaciyar banza da wofi sai ga Marahut ya shigo da sauri Kwaceta ya yi daga hannuna kafin yake fadin" ke Zannaba, baki da hankali ne? Kike ikirarin yarinya bata da tarbiya ke kina iya rantsewa waye malamin waye dalibin tsakaninta da dan naki? Ki shiga tatayinki ki daina abu tamkar wata yarinya karama! Agaishat , a wannan rana, a gaban wannan yarinya Marahut ya wulakanta ni, ya yi min tas abinda bai taba shiga tsakaninmu ba, Ke dai kwana biyu tamkar kura ta lafa, domin Wardugu da ya ga na nace sai kawai ya basar ya yi biris ya shiga wata sabgar gaban nasa inda ya fara kula Walyn, Ba.a wani jima sosai ba, domin ba .a yi wata hudu tsakani ba Marahut ya zo da maganar zai yi aure, Agaishat ban wani nuna halinmu na matan tubawa ba, na ja ajina na yi masa fatan alkhairi, na shiga rokon Allah da ya rufa min asiri kar a je dan haihuwana ya tsaya ne wani abin zai tunkaro ni, Sannu sannu sai abubuwa ya fara bilo mani, halayen Marahut suka shiga canzawa, Ya fara cika dare sosai a waje kafin ya shigo, ya dawo ya fara kin cin abincina sai yace baya jin yinwa tamkar wani inji, A hankali ya kaurace min, Na sha zuwa na duka nace da shi" menene damuwar? Wani abin na yi ne? Dan Allah ka yi hakuri , har ka manta alkawarin fa ka yi min? Marahut kace nice lumfashin ka, ka yi hakuri ka dawo min kamar da, ni ban wani hanaka aure ba, aman kar ka tayar min da hankali, Marahut sai kawai ya yi min murmushi ya mike ya fice, Du abin nan Wardugu bai san ubansa zai kara aure ba sai wani lokaci ya ji a gari, a lokacin ya garzayo gida da sanyin safiya ya tambayi uban, ashe auren ma a ranar sauran kwana biyu ni banma sani ba, A wannan ranar na ga tashin hankali, na ga rikici, domin Wardugu idannuwansa sun rufe hakama na ubansa, ke sai da na fita a guje na kira direbobi da masu gadi da yaren gida du suka shigo suka yi kokarin shiga tsakannin uban da dan dan kuwa Wardugu ya rike wuka hannunsa yana ta balaki! Agaishat, wannan bai isa ba sai da aka shigo da amarya Aisata, aisata yar buzaye, aisata yarinya kyakyawa, A ranar wardugu ya yi dan karamin hauka, ya ja iska ya zo kusan babansa ya ce" aban Wardugu ka sake ta, ka rufa mani asiri ka saketa , kar ka yarda wani abin ya shiga tsakaninka da ita, Aba, wannan bata da tarbiya, bata da haramun! Abanna ya zaka kawo macen da ta gama talatarmin da kanta a irin yannayin da ta fado duniya ni danka a matsayin matarka? Haba Abana, me mukai maka da zafi haka? Marahut ya dube shi ya ce" ita ba mutun bace? Kun haihu da ita ne? Na yi niya ina sonta na aureta da kudinka ne? Ka bini a sannu Wardugu, ni na haifeka kar uwarka ta zigaka ka kauce hanya! A lokacin ni tuni na fara gannin jiri, ni Marahut? Na sha dukan kirji nace ni mijina dan goyo ne, ba zai wulakanta ni ba, sai gashi haka ta faru, ni ba aurensa ya dame ni ba, tau da gobe ai sai Allah Allah wacece ni da zan ce ba za.ai min kishiya ba? Damuwana irin auren da ya yi, ya yi shi dan ya nuna min iyakata? Dan ya wulakanta ni? Ko wani abin ke tsakaninsa da yaronsa mai zafi haka? A lokacin Wardugu ya fara wani irin numfashi, idannuwansa suka shiga canza launi zuwa ja, suka cicika da kwallah, ina gannin hakan na tisa shi gaba da kyar na samu muka shiga motarsa na ja muka nufi gidansa, Muna zuwa muka tarar da Wakyn ta zo nemansa, a nan ya sauke haushin kanta domin sai da ya bala mata hannu du ya kusan canza mata halita baiwar Allah da kyar aka kwaceta, Kin ji marabina da gidan Marahut domin akai ruwa aka yi iska Wardugu ya hau, ya gindaya rantse rantse, ya juye, nima fushi, mamaki, tsoron lamarin maza ya saka na yi watsi da shi na rungumi yarona wanda na san a duniyarnan ni ce duniyarsa ,..... Ayya ta karasa tana dan shafa kan Agaishat, Agaishat ta dago fuska shabe shabe da hawaye,, tana duban Ayya , ta sani bata da damar da zata iya tofa wani abin a wannan lamari domij ta yi imanin ba komai Ayya ta fada mata ba, tabas ta boye wani abin ko dan karancin shekarunta, Sai dai wannan lamari ya tuna mata mahaifiyarta, Anna baiwar Allah, yoh ita haka rayuwarta ta kare fa, kuma bata da wani mai dauketa ya matsata daga wajen da ake cuzguna mata, ita bata san bama marainiya ce ko yar dangi, bata san daga ina ta fito ba, ba abinda ta sani, A hankali ta mayar da kanta saman cinyar Ayya , daidai lokacin da Wardugu ya shigo dakin da salama, Daga inda take kwoncen nan take kare masa kallo, tabas wardugu ko bashi da ko sisi sai mace ta yi haukansa, ko bashi da hali zai mitsa zuciyar mata, dan farin batube mai zamani, Idannuwanta ta lumshe a hankali wani hawayen ya kuma zubowa daga gurbin su ta mike a hankali bayan ta share hawayen ta kai dubanta wajensa , kanshin turarensa ya cika mata hanci, A hankali ta ce" ina yini, Gaisuwar da tunda suka daukota daga timiya shi dai bai taba jin ra yi masa ita ba, tsumamun idannuwansa ya zuba mata ba tare da ya amsata ba, yana kallonta har ta fice a dakin dan basu waje su tatauna ta nufi wajen Mu.azam dan gannin ko ya ci abinci? Ayya ce ta lakato shi tana yi masa murmushi tana saisaita kanta ta ce" dan gidan Ayya, sannu da dawowa, Wardugu ya juyo da sauri yana dubanta, ya yi murmushi ya ce" Ayyana, ina yini? 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣4️⃣ Amsawa ta yi tana dubansa da madaukakiyar kulawa kafin take mikewa ta kama hannunsa, Shima biye yake da ita suka fito daga dakin Agaishat suka nufi dakinta, Walyn ce zaune a saloon mai suna Tawaye saloon, fitacen saloon ne na manya wanda sai ka isa kake saka kafarka, Akifunta ake gyara mata bayan an yanyanke su an wanke su sosai aka dauko na kanti zako zako din nan aka shiga dora mata, Kawarta dake gefenta tana karanta magazine, itama ana gyara atach din da za.a yanyara mata kitso ........ Wata mata da ta tsare Walyn da kallo tunda ta shigo ce ta yatsina fuska, a ranta ta yi murmushi tana ayyana ba laifi , matar tasa bata da laifi, Kadan ta dan muzguta ta dubi cousint dinta dan daudu wanda suka zo gyaran gashin tare da shi ta ce" ina son aikin General a rayuwana, ina son yanda yake cin uwar kananun yan iska! Kallota ya , ya wani yi far da idannuwansa, ya yatsina fuska tamkar mace ya ce" ke kawa, ya iya tata rashin mutunci ne fa, mutumen nan kin san da matar tsohonsa ce ya rufe? Uhum ke ni ko a lahira bama fatan mu hade da General Wardugu domin bashi da mutunci, ya iya aiki da doka, ke matarsa fa ta yarda ta kai dare a waje sai ta kwana a cel! Daman inda take so a tabo mata kennan dan haka ta maida hankalinta sosai ta kali dan daudun nan ta ce" kawaliya matar naci ta taba daraja ne? Walyn dake kalonsu tana kada kafarta, ta kai dubanta wajen mai saloon din, ta maida wajen kawarta da ta yi kasake itama tana jiran gannin me zata yi? sai sauran matan dake wajen da yan tsirakun ya daudun dake wajen suna suba nasu sha.anin..... Walyn ta saki murmushi mai ciwo, ta daga idannuwanta cike da isa da takama ta ce" Wardugu kennan, mijin mace daya, jarimina mai ban tsoro, Warduguna zazafa ne, kawata kin san Wardugu baya bin kadangarun bariki? Ke na yi imanin da Wardugu na bin mata zai je ya zabo zuga zuga ne, wa.inda idan ya zaga zai dire chek ba wai ya dane karamar yar bariki ya kasa iyanta harda kason shekara sanadiyar rabuwa da mace ba! Dan daudun nan ne ya sheke da dariya yana duban matar da suka zo tare, wace ta ji abin tamkar saukar guduma domin mijinta ne ya jewa wata yar bariki ya ki biya sannan ya yi mata duka hakan ya sa harda su kaso, wani tukukin bakin ciki ne ya taso mata, bata tsamaci jin haka ba , abin ya dake ta, Kallonta ta yi da yannayin bacin rai ta ce" ke Walyn kike ko wa? Kin san ko wacece ni? Walyn ta fizge hannunta daga hannun mai saka mata farcen ta ce" ke ce katuwar yar barki marar aji! Sai me kuma? Mikewa ta yi itama ta ce" ke din ba yar barikin bace? Ke naki a boye kike yi ko ji kike ba.a sani ba? Meye bambancinki da yar bariki? Ke kawai bakya yi dan kudi ne aman menene bakya yin? Ko dan kina rufe takunki ne baki san wa.inda kuke labewar da falasawa ba? Ki jika ki ajiye Wardugu General ya fi karfin zama da mace daya wace na sani ne bakima goge a kai shi wata duniyar ba! Zaki ga aikin gogagiyar yar bariki domin Wardugu katuwar kadara ne wanda malakarsa sai tsayaye ba isa ce zata kai ki ba mu je zuwa!...... Walyn ta yi murmushin rainin hankali kafin take bufe jakarta, Yan jika goma goma ta fitar dami guda ta bale yar takardar dake zagaye da su wace itama sai kyali take, ta dauki bakin gilas dinta ta jefa katuwar wayarta a jaka ta juyo sosai wajen matar da sauran mutanen saloon din ta daga kudin nan ta sake su a iska wanda hakan ya saka du suka shiga wawusoso harda mai saloon din da yarenta kiwa na nema har wasu suka shiga dambacewa , aman banda wace ake kira da kankana! Walyn ta bi kawayen da kankana ta zo da su da ido ta ga suma sai wawa suke harda yan daudun, Yatsina fuskarta ta yi ta ce" abokin mai kanwa ba ya rasa burbudi, Wardugu ya daure min a niger tunda ya sakar min yayan banki, na kwana lafia koda Wardugu ya shiga tsakiyar yan bariki ba zata motsa ba domin kyankyaminku yake! Ta kara taku har gabanta ta zaro idannuwanta ta ce" ki sauke girman kai ki duka ki kwashi kudi.....su kike kwadayi! Iska ta ja ta kaiwa Walyn duka warda itama ta damketa suka shiga dukan junnansu, Sai da suka lilisa junnan su sannan mutanen wajen suka shiga tsakanin su kowace na haki, Walyn ce ta warce jakarta ta yi gaba inda kawar tata ta biyota da gudu tana kiran ta tsayata, aman ina cikinta take ji yana wani irin hautsina mata, bata san me ke damunta haka ba yanzu, ya kasance tana yawan jin abubuwa a tatare da ita, Wardugu ya jima wajen Ayya, inda suka tatauna sosai sannan ta saka shi a gaba kan sai ya ci abinci, Agaishat na fitowa ta nemi Mu.azam, sai dai bata ganshi ba hakan ya saka ta fice ta nufi wajen runfar Ayya mai wani ni.imtacen sanyi tana neman Mu.azam, Nan kuwa ta same shi, ya kurawa waje daya ido, ya zurfafa sosai a tunani wanda yannayin fuskarsa ta nuna ba tunanin dadi yake yi ba, A hankali ta karasa ta kuma maimaita salamar da ta yi ta yi masa tun daga dan nesa da shi, A dan tsorace ya kalota kafin yake daidaita yannayin fuskar sa ya amsata yana mai kokarin gyara mata kujerar dake kusa da shi, A hankali ta ja ta zauna tana dubansa, yannayinta ya nuna itama ta shiga damuwar da yake ciki, A hankali ta ce" me ke damunka ya Mu.azam? Daman ita yake kallo, dan haka ya bi bakinta da kallo yanda ta fadi maganar a hankali sannan a cicire domin dai tana faman koyon yarensa ne, A nitse ta janye idannuwanta daga cikin nasa, domin kallo nr yake mata tamkar zai fada idannuwan nata take ji, A hankali ya ce" Agaishat, Ta dago tana dubansa, inda a take ta ji gabanta ya fadi da yannayinsa, Mu.azam ya ce" kin san soyaya? Agaishat ta zaro idannuwanta tana dubansa, tama rasa me zata ce da shi, Mu.azam ya ce" kin taba yin saurayi wanda kika ji kina so? Agaishat ta saki murmushi mai kama da na sakalci, domin ita abin har ga Allah dariya ma ya bata, A hankali ta maimaita kalmomin" *So, Soyaya, Saurayi?* Mu.azam ya dan kankance idannuwansa ya ce" yeah, Agaishat ta dube shi, duba na ido da ido kafin take fadin" *Ban san shi ba*! Da mamaki yake kallon ta, bata san shi ba tace fa? Aman daga ina Agaishat ta fito haka? Ko dai masu son nata ne basu yi mata ba? Yin wannan tunanin ya saka gabansa ya fadi, a ransa ya ayanna ya salam, kar dai a je nima ban yi mata ba,? Muryarsa sanyaye ya ce" du a maneman soyayar ki ba wanda kika taba jin kina so? Agaishat dake dubansa itama, bata dago ina ya nufa ba, domin dai ita ba.a taba kamanta za.a ce ana sonta ba, dan haka ta bashi hankalin ta sosai ta ce" ba wanda ya taba fada min ya ake so din ne, Dariya ya shiga yi kasa kasa yanai mata wani duba kafin yake fadin" ba fa zolayana nace ki yi ba Madame, Bata san kalmar madame ba, aman ta gane yana nufin wasa take yi masa, dan haka ta ce" ban taba yin saurayi ba, ko an zo zaben yan mata a gidan mu ba.a taba zabena ba, Ba yace dan na cika baki da muni, ni ba alkhairi bace dan baki ba alkhairi bane, hakan ya sa ba mai zabena bare a biya sadakina, har kanwata an zaba sai dai kafin auren ta rasu ita, Dubanta yake har ta gama yi masa bayani da kwatance da komai dan ya gane da kyau, ajiyar zuciya ya sauke a ransa ya ayanna na godewa Allah ai da basu zabe kin ba da sun saka ni a ukunna, A fili kuwa ya ce" wa ya fada maki baki ba alkhairi bane? Agaishat ta ce" da alkhairin ne, da mahaifina bai kyamace ni ba da alkhairin ne da nima ana yi min dinkuna irin na yan uwana, da alkhairin ne da jama.ar gari sun mutunta ni a matsayina da dan adam mai daraja a cikin halitun Allah, da alkhairin ne da na yi saurayi koda mahaukaci ne a *Gida*, Katseta ya yi da fadin" aman sai na ga kina da ilimin adini sosai, ya aka yi kika kasa imani da haka? *Agaishat , malamata, wa ya halici fari da baki,?* Agaishat dake dubansa ta sada kanta a hankali, kafin ta ce" Allah ne, Shin da ya halici baki ya kawo wata ayya a alkur.ani mai girma, a hadissai ko wani litafin na adinin fake nunin bakar fatar nan da ya halita ya haliceta ne dan wani laifi? Ko mai wani laifi? A hankali ta kuma fadin" aa, ban karanci haka ba, Mu.azam dake dubanta ya ce" Bilal, bawan Allah, wacece kalar fatarsa? Ya darajarsa take? Dago da idannuwanta ta yi ta ce" baba tsofo ya ce shi ne ya fara kiran sallah , ya ce mutun ne mai daraja, makusancin fiyayen halita, Mu.azam ya gyada mata kai kafin yake ciro wayarsa ya samo hoton ka.aba ya ce" zo ki ga ka.aba a hoto Agaishat, zo ki gani... A hankali ta matsa tana kallo, kalar bakin ya tafi da imaninta, abin ya yi mata kyau a ido, a hankali ta kai yatsarta ta dan shafa hoton, A hankali ya ce" ba wani bawan da ya fi daraja, ya fi kusanci fa ubangijinsa sai mai yi masa biyaya, mai tsoron shi, mai kiyaye dokokinsa, a cikin nan kin ji an ce *Farar fata ta fi bak'a?* Agaishat da take jin wani yamyamyam a jikinta na dadi ta girgiza kanta, Mu.azam ya ce" makafi ne ko kwakwaluwar su bata ja? Ya aka yi basu yiwa abin kaunata wawa ba? Da sauri ta kallo shi, Kansa ya dan sada ya ce" kina da tsararen kyau, fitinanan kyau, baki da tsayi Agaishat...baki da kiba har can, yannayin jikin ki ya tafi da yannayin tsayin ki, Bakin ki ba mai tabo bane bare shaida, gaba daya ya tafi iri daya ne baki mai haske mai nutsuwa, agaishat, fuskar ki yar doguwa ce mai dauke da dara daran idannuwan da a kowani yannayi kike su kadai sun ishi mutun, Agaishat Allah ya tsara ki da hanci mai tsayi mai yan kofofi wanda ya yi das da dan madaidaicin bakin ki, Rashin hayanniyar ki ya hadu ya kara kawata halitar ki, ke da ba dan kar na kauce hanya ba da na fada maki sauran tsaruwar ki, Dan dakatawa ya yi gannin yanda ta zuba masa ido, sai a lokacin ya tuna ya saki baki sai zuba yake mata, Dan kimtsa kansa ya yi a hankali ya ce" Agaishat arrrakam (Agaishat ina son ki), Wata irin faduwa gabanta ya yi, da wani irin firgici ta akle shi, tsoro, mamaki, surprise, murna suka hade suka saka jikinta ya dan fara rawa, So na? Ji ta yi wani nauyinsa ya diri mata,da sauri ta sada kanta kasa, kafin take mikewa da wani irin sauri ta jua inda Mu.azam ya mike yana kiran sunnanta daidai Wardugu ya yi kokarin kawar da kansa dan kar su ganshi bayan ya jima wajen, Ganninsa ta yi yana ta faman taba labulen ayya wanda ke gyare tsaf a wajen aman kamar wanda yake gyara shi, Kanta ta shiga sosawa kafin take dan rabar gefensa ta shige ta taka matatakalar da gudu gudu ta nufi dakin ta, Da ido ya bita, da wani irin kallo, a hankali ya lumshe idannuwansa ya juya ya fice a dakin ya nufi wajen mu.azam da ya koma ya zauna ya dan dafe kansa da hannunsa cike da tsoron kar a je ta ki karbar sa, Gaban wardugu ya ji na wani irin gudu wanda har ya ji wata yar zufa ta karyo masa, A dan hanzarce ya karasa wajen amininsa yana mai cike da zulumin yannayinsa, a nitse ya kai hannunsa ya ce" Mu.azam? Agaishat na shiga dakinta ta karasa da sauri wajen madubi, lufayar jikinta ta warware ta tsurawa kanta ido, du abinda ya fada take son gani sai dai ita bata wani gannin kyanta, , ..... A hankali ta kai zaune ta cuje abinda ta daure gashinta da shi wanda hakan ya baiwa gashin damar zubowa baki dayansa ya yi lumbuk a jikinta, hannayenta ta cusa ta fashe da wani kuka mai zafi, a hankali, muryarta na rawa ta ce" Anna, ina kike? Anna wai yana so na? Ashe nima mutun ce Anna? Anna wai ina da kyau, wai nima mai daraja ce, Anna nima na yi saurayi...........tana kukan kuma ta shiga dariya a hankali ta furta" Mu.azam, nawa😌😌😌😌😊😊😊😊😊😊😊 I.m sowi fans , jiki da jinni ne 🤦‍♀ 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣5️⃣ A hankali Wardugu ya kai hannunsa ya taba Mu.azam, murya a sanyaye ya ce" Mu.azam? Da sauri ya dago da kansa daga yannayin da ya afka, ya kali Wardugu da kyau kafin yake sakar masa murmushi, Wardugu ya ce" me me ke damun ka? Mu.azam dake dubansa ya dan sada kai, ya kuma dagowa yana dubansa ya ce" jinta nake a raina har jikina Wardugu, sai dai ban san ba ko zata aminta ta aure ni a dan kankanin lokaci kafin mai yiwuwa ta yiwu da ni? Wardugu ya ji gabansa ya fadi, Allah yana ganni idan da abinda ke tayar masa da hankali a yanzu bai fi rashin lafiar Mu.Azam ba, lamarin na girgiza shi in ya tuna, yakan tsinci kansa ba karfi bare laka a jikinsa idan ya tuna, ....... Duk da ya fahimci wa yake nufi aman sai ya kashe ido guda yana kallon Mu.azam ya ce" kai, soyaya ka afka daga zuwa garin mu? Fada mini wacece mai sa.ar samun abokina ? Mu.azam ya lumshe idannuwansa ya ce" Wardugu, na kan ji wani iri idan muna hira da kai a yanzu, domin du ka canza min kan da, a da idan muna hira tamkar yaki muke, ka warto ni na tsokaneka mu yi ta shirirta har sai an shiga tsakanin mu, aman a yanzu du abinda zan maka sai na ga ka wani yi shiru ka kyale ni ko kuwa ka wani lalaba ni, malan matarka ne ni? Ko dan bani da lafia? Ni irin yanda muke da ya fi birge ni, sai ka wani dawo ladabi? Wardugu dake kallonsa ya ji zuciyarsa ta mugun karye, hakan ya saka wata zufa ta karyo masa, a yanzu da suke zaune a haka ba mamakin shi wardugun shi ne gawar fari, aman kuma rashin lafiar Mu.azam da ta bayana kanta ne ake kiran kisan mumuke, domin dai ta hana kowa walwala tsakanin mutane ukun nan, Mu.azan din, docternsa, sai Wardugu da ya sani shima, Wardugu ya saka hannunsa ya share gumin da yake , ya miko hannunsa kusan na Mu.azam ya ce" wa kake so? Ko yar gidan waye, ko wa take takama da shi nan duniya sai ta aure ka, kuma dole ta so ka! Mu.azam ya kwace hannunsa yana dubansa da yannayin tausayi, ya san waye Wardugu farin sani, wannan yannayin da yake ciki yayi imanin da ace zai samu kuka da ya koka tun karfinsa ko zai samu sauki, Goshinsa ya dafe yana dubansa, ya ce" ka daina damuwa da lafiata Wardugu, Wardugu ya katse shi da fadin" idan muka gwada aikin nan fa? Mu.azam ya ce" bayan ka tirsasa ni shan lemun tsami cikin ruwa masu zafi, kana tirsasani cin tafarnuwa, kuma zaka bijiro da maganar aikin da na guduwa ? Wardugu aikin nan fa mai yiwuwa shigar da za.a yi da ni a fitar maku da gawata, Wardugu ya ce" kuma tana iya yiwuwa a fitar mana da kai ras ka sami lafia, Mu.azam ya ce" mafi akasari idan Allah ya yi an sami lafiar ma kwakwaluwa na tabuwa, ko a samu shafewar tunani, cikin kaso dari bai fi 2/100 suke mikewa garas ba Wardugu, na fi son idan ta Allahn ce zata kasance da ni nan kusa ya kasance ina kusa da mutanen da nake so suke so na, Wardugu ya kura masa ido, kallon cikin ido, ya ce" ba zan iya ba, zuciyata mai mugun rauni ce a kanka, ina jin rashin karfi a abinda ya shafe ka, baka yi min adalci ba idan har ka yi min haka, ! Ya mike ya dauki kys dinsa, ya dora hanayensa saman table din yana dubansa ya ce" baka isa ka min haka ba, ba zan taba barinka ka yi min haka ba! Zan nemi karin bayani ...... Juyawa ya yi ya fice inda yake jin kansa na mugun sara masa, Mu.azam ya girgiza kansa bayan ya bi shi da kallo, a hankali ya furta" ban so ka ji ba, sai dai rigumarka ta saka ka tankalo abinda zai hana maka nutsuwa!, ya hana maka jin dadi! Tukin garari ya yi wanda ikon Allah kawai ya kai shi gidansa lafia, Yana zuwa ya sauka daga motar ya rufe ya nufi bangarensa kansa duke yana mai jin yanda yake sara masa, Har zai bude ya shiga, sai ya fasa ya dubi bangaren Walyn, A hankali ya juya akalar tafiar tasa ya nufi bangarenta yana wata irin tafia wace da ka gani zaka fahimci da karfi ne ake yinta ba dan ana jin dadinta ba, Wardugu na shiga ya zarce falonta baba inda kamshin turaren da aka turara ya yi masa salama. A hankali ya shige yana hangenta kwonce saman doguwar kujerar falon nata tana danna waya ranta da yannayin bace, sannan da maganin zazabi mai tafasa a gefe da alama dai ita ta sha bata jin jikinta, Da sauri sauri ya karasa gareta yana mai cire rigar tasa ta sama ko zai ji dan sanyi sanyi ya karasa wajen Walyn da ta zabura ta mike tana dubansa da wani irin yannayi mai fasara abu uku, na farko ganninsa a bangarenta, na biyu yannayinsa ya firgitata, na uku mugun haushinsa da take ji domin yanzun ma a cikin grup dinsu na manyan mata ne ake tatauna maganar har wata na ikirarin ita walahi a duniya ba wanda ya yi mata irin wardugu halayensa na kasheta da dadi, idan ta kali hotonsa takan jita a wata duniya, tunani take wannan mutumen ya kasance hazarsa a gabanta kadai ya isheta, duda an kwabeta cewar da matarsa a gidan fa , kamar an zungureta ne an tirata domin a lokacin ne ma ta ce" Wardugu ai mijin mace hudu ne wanda Allah ya halita masa ba wani shege ba, duniya kuwa idan takamarka sauko wani a can ya kwana, Tana wannan tunanin wardugu ya karaso jikinta, batai tunani ba ta ji ya rungumeta da karfi wanda sai da ta ji kamar numfashinta zai tsaya dan ya kanainayeta ya hana ta motsi, A hankali ta rungume shin itama, ta shiga sauke ajiyar zuciya tana shakar turaran jikinsa wanda koda ya yi zufa bata hadewa da turaran ta bayar da wari wari, turaran ke cin karfinta bama zaka gane ba sai dai idan mafi kusanci da shi ta ji gishiri gishiri a jikinsa a irin wannan yannayi 🤣, Gajiya ta yi da tsayuwar domin daman ba wani karfin jikinta take ji ba, A hankali ya bita saman kujerar domin shi a wannan lokacin bashi da bukatar komai sai na ya jima a jikinta , ta rungume shi, yana so ne kawai ya ji shi a jikinta ba komai ba, Haushi Walyn ta ji, aa me wardugu ya dauketa ne? Jiya ya gama wulakantata, ya fanshi jikinta, ya tashi ya yi tafiyarsa, ta je saloon ta kwashi rashin mutunci dan shi, ta zo gida mata na wawarsa shi oga! Yanzu ya kuma dawo mata da bukatar sa? (Domin a tunanin ta , bukatuwa ce ta dawo da shi a irin wannan lokacin ), A hankali ta zame jikinta tana dubansa yanda ya yake ringeshe jikin kujerar idannuwansa du a lumshe, Baki ta dan yatsina, a fili ta ce" ka san yau a saloon wata karuwa ke ikirarin sai ka aureta? Daga yanda yake kwonce yake dubanta, a hankali ya ce" ki zo gare ni Walyn..... Ya mika mata hannunsa, Kafadarta ta make irin na yangar nan na mata ta ci gaba da fadin" ka saurare ni mana, ina maka hira ka wani basar, A hankali ya kai hannunsa wajen goshinsa kafin yake mata alama da ta ci gaba, domin ya lura kwata kwata matar tasa bata lura da yannayinsa ba, bata da niyar fara sauraronsa, zata tiso abinda ke damun nata wato *kishi da isa*, Zamanta ta gyara tana mai dubanda da kyau ta ce" ni kuwa na bata amsar cewa , Wardugu mijin mace daya ne, ba zai kula wace ta san mutuncin kanta bama bare ita karamar yar bariki, Wardugu nawa ne ni kadai! A hankali, ba tare da wani damuwa ba ya ce" *wa ya yi miki wannan albishir?*, Da sauri ta dubo shi, da yannayin mamaki ta ce" me kake nufi? Dagowa ya yi yana dubanta ya ce" *Auten zobe muka yi da ke?*, Walyn ta kara zabura da mamaki ta ce" kana nufin sai ka kula wata macen? Wardugu ya buda idannuwansa da kyau, ya ce" *To waye ni?* , an fada maki ni ba mutun bane? , Yanzu sai ka ci amanata Wardugu? Sai ka dubi wata macen da sunan so? Kallon kar ki raina min wayo ya yo mata sannan ya ce" tunda hirar kike so mu yi bari ki ji, da farko dai ni mutun ne dan Adam wanda nake tara ba goma ba wanda nake cike da laifuka , nake dauke da zuciya mugun nama, wanda na kwonta da sannin Allah ya halasta min auren hudu na jera, nake da sannin ina da wajen saka su, ina da abinda zan ciyar da su, na tufatar da su, sannan ....ya yi murmushi ya ci gaba da fadin" na sauke hakinsu saman lit (bed) ba tare da gajiyawa ba! Ke kin san wa kike aure shi ya sa kike kishi! To a haka da nake, akoy wa.inda ban yi masu ba, sam bana gabansu, bana cikin tsarin da zan samu koda gaisuwarsu ne! Walyn, ana aure dan soyaya, da tausayi, dan sha.awa, dan arziki, ba zan maki karya ba, ba zan yi maki rantsuwar ni na isa na kauce kaina daga kan *mace yar dagwas dagwas mai dorinar dukan maza ba* , ciki kuwa koda yar barikin ce da kike fadi mai yiwuwa na zama silar shiryuwarta! Gaba daya har Walyn ta fara fita a hayacinta , ta hayayako ta ce" me na gaza da shi Wardugu da kake kiran min sunnan wata a gabana?, *Kyau, fari, tsafta, girki, iya tarairayarka,* wane na gaza a cikin nan? Haushi ya kara kama shi, itace ke ikirarin iya tarairayarsa bayan yanzu ya shigo mata a wani yannayi maimakun ta dubi halin da yake ciki ta zauna a kusa da shi aa, sai ma ta tsankalo kabarun banza da wofi, kai da Walyn a wajen aikinsa take kai koda ficewa take ta hanyar da an kwashi yan kalo da ita da matan dake kai masa ziyara, wai kuma ta yi ikirarin ita ta san kanta ita mai kyau me memememe, *Isarta* ta hanata ta duka masa yanda ya dace, takamarta da halitarta sun hanata gane ainahin biyayar aure, sai idan baki ya bude ta shiga zubo masa abubuwa mararsa tsari, dan haka da yannayin haushin nan ya mike yana daukan rigarsa ya ce" *Kin san dadin miya ke sakawa a yi kari!* Wai wai wai wai , shin fans zaku kuwa iya zama da mai hali irin na wardugu🤦‍♀🤦‍♀🤦‍♀, Su waye wardugu ke ikirarin ko arzikin gaisuwa baya samu daga wajen su? Me ke damun wardugu? Me ke damun kwakwaluwar Wakyn? Ta hada kyau, fari, tsafta, kanshi, girki, bata isa ta daki kirjin mijinta na ita kadai bane?🤔 Mu.azam, zai kai labari kuwa? Agaishat Ayya, Anna, Ba, Marahut, ya labarin su ne?🤔🤔🤔 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣6️⃣ Rigarsa ya rataya a kafadarsa, ya juya da niyar barin mata bangarenta domin bai ga dalilin fa zai saka a caza masa kwakwaluwa a waje, ya zo wajenta dan samun nutsuwar zucuya itama ta caza masa, yana bauwa Walyn damarta ta mace, na ta yi korafi a kan abinda bai mata ba, ya sha duba korafinta ya nuna mata ya tuba a aikantance ta hanyar daina abinda ta kawo masa korafin a kai, sai dai abubuwa na damunsa na irin yanda ita ba abinda ya sha kanta da damuwa da damuwarsa, bata wani damu da yannayin da zata ganshi ba indai da abin fada zata rufe ido ta fada da gatsali, Murmushi ya yi yana girgiza kai bayan ya kare mata kallo du ta fice a hayacinta daga wannan yar maganar? To idan Allah ya kadarto min kara aure yaya zamu kwashe da Walyn? Rai bace tana kokarin fashewa ta kuka ta ce" Wardugu, idan ka yarda, idan ka saki, ka yi saken kula wata mace sai dai a kwashi gawarwakin mu baki daya! Wardugu kamar yanda Batuben namiji zai iya suka da wuka dan an kali matarsa toh zan iya suka da wuka dan an rabe ka! Tsayawa ya yi yana dubanta, iya gaskiyarta ta fada domin a tsaye take tana dubansa ido cikin ido, jikinsa ya ji ya dan yi sanyi, karasawa ya yi kusa da ita , ya dan sasauta murya aman a cunkushe ya ce" Walyn, bakya aiki da adini ne ke? Kin san da sunnar ma.aiki ce? Me ya sa zaki daukarwa kanki zafi haka? A haka Walyn ban ma nuna zan yin ba idan zan yi fa? Idannuwanta ta dago dan sakawa cikin nasa domin ya darata tsayi, ta ce" na tsinci kaina a zazafar kaunarka, haka na wayi gari na ganni zundum , na shanye wulakanci kala kala dominka, kai da kanka ka sha wulakanta ni mai girma, karaya uku ka min a gabai na, du na shanye! Kai a tunaninka ba zan shanye azabar kawar da du wata tsagerar da ta tunkaroka ba? Wardugu, mahaukaciya ce ni a kanka! Sakara ce da a yaren ka! , kamar yanda ka sumar da saurayin da ya yaba maka ni, ni kuwa ka yi min marin da na yi ta ihu sai da kyar jina ya dawo dan na yi kwaliyar da aka yaba ni, haka zan iya rike makigwaron du wata yar iskar da ta yabe ka! Kansa kawai yake dan girgizawa yana dubanta, Walyn, walyn Wardugu...ya saki murmushi ya juya, Haushi ya kara rike mata zuciya ta daga murya ta ce" ciki kuwa harda wannan tsohuwar kilakin da ta ki aure take binka gida ma.aikata, anguwa! *Alhinayett*, ciki harda ita, Dawowa ya yi ya tsura mata ido, kafin yake fadin" ki daina zagin Alhinayett domin mai son ki ce, tana yaki kan ki, tana yi min fada kan ki, Karuwancin kennan! Karuwancin kennan Wardugu! Ta shiga jikinka har ka ji in ba ka kasance da ita ba , ba zaka ji nutsuwa ba! Wardugu ya zauna saman kujerar dakin ya ce" Walyn, Alhinayett ba yar bariki bace, mutun ce mai daraja, mutunci ne tsakanina da ita, ke kin san da soyaya ne da tuni na auri abina na kilace, jimawarta ba aure kuwa Allah ne bai kawo lokaci ba, aman an kusa saka aurenta, ki daina magangannu irin haka Walyn , ke macece, ko a kan ki ba haihuwa zaki yi watarana, ba.a so mutun ya cika izgili, Kai ta kawar ta ce" wardugu, gaskiya ne baka so? Alhinayett ai kowa ya san kilakin ka ce! Wardugu ya mike a karo na uku kennan, ya karasa kusan Walyn yana mai binta da kallo, hannunta ya damko ya bude yana dubawa, ya riko fuskarta ya daga idannuwanta yana dubawa, ya gwale bakinta ya saka yatsunsa ya ciro harsanta yana dubawa, ya saki ya kama rigar dake jikinta ya dage sosai har biyu suka bayanna, nan ya tsura masu ido yanai masu kallon kurullah, Cikata ya yi , ya dan taka ya tako kafin yake nunota da yatsarsa manuniya, muryarsa ya saki baki daya ya ce" Ba karuwa bace! Aminiyata ce, du wanda ya zagar min ita zan bata ransa! Kika kuma kiranta da karuwa na rantse da girman mahalicina sai na aureta koda kuwa ta tsane ni , koda mutuwa zata yi dan kina na kawota na kwana da ita saman gadon ki! Ke da ba dan ina hangen kamar mai shigar ciki ba yau da na nuna maki tsagwaron rashin mutunci! Ya ina taro ki kina raina min hankali? Walyn ni in ban kara aure ba ni ba dan babana bane!, ni ba jinin tubawa bane! Walyn dole ki zauna da kishiya in baki kona mu ba ke ba yar babanki ba ce! Fuuuuuu ya juya ya fice yana jin kamar ya koma ya yi kwalo da ita, sai dai yana tsoron kar a je ciki ne da ita, ta ja ya yi mata lahani bayan adu.arsa kennan shima allah ya azurta shi da haihuwa, yar bakin ciki kawai take jan sa masifa salon ya biye mata idan cikin ne su barar su shiga uku! Haka ya koma bangarensa ya zube a falon sa ya yi ruf da ciki ya dora hannayen sa saman kansa yana yamutsawa yana tunanukan rayuwa,, walyn ba wayo , haka ya ayyana a ransa kafin ya kuma fadin....ta saka sai na kara zama da wata macen? Walyn shirme shirme🤦‍♀, *Timiya* Amai take kwararawa har kamar ta shide, inda *Ba* ke tsaye ya dan duka dan tsayinsa, da rawaninsa yana dubanta, Gefe guda kuwa su Anna ne da yayanta yauma Gaishat ta kawo mata ziyara da dan cikinta da ya tasa kafan wanda sarki ke mugun zumudi kansa tkar shi ne dansa ma fari, Suna kasan bishiyar gidan suna zaman su suna yar hirar su , domin yanzu da safiya ta yi Mariama ke fitowa ta gyara wajen ta shinfida tabarmar kabar da Anna ta siyo daga garin agadez ta dauki du abinda zasu bukata su koma can su yini abinsu , nan suke sallah su ci abinci, ta dauki na baba tsofo ta kai masa domin Gaishat na tsaye kan abinda zasu ci, sarki baya wasa da ta nuna tana da bukata ake kwasa a kai mata itama ta kwasa ta kaiwa mahaifiyarta, inda ta saka sarki ya yiwa *Ba* gargadin kar ya kuma kwashe masu abincin su, Bakinsa yake motsawa ya juya ya karewa Anna kallo da yarenta su uku sun zagayeta, ya juyo wajen amarya dake maida lumfashin kadangare bayan ta gama sheka amanta, Tabar sansaninsa ce yake gumtsa a bakinsa, Bakin ya bude ya totofar da yawu, domin du mai shan tabar sansani ya kasance yana tofe tofen yawu, ya juyo wajen amarya ya ce" sannu *Uwar mai uba biyu*, Kallon kasan ido ta yi masa kafin ta kada kai, Juya kansa ya yi wajen Anna ya ce" duniya, anai min kallon ina yiwa yarana aure suna tafia birni, ke gashi kin dauki yar santal ki badata yawon kilaki! Da sauri Anna ta kallo shi, gabanta ya fadi, Kura mata ido ya yi ya ce" karya na yi? Ke yanzu zaki daki kirjin yarinya na hannun kirki? To ni dai in tana aiko wani abin ake boyewa ana ci Allah ya isa! Dan ko dan ciyar da ita da na yi ya isa a yaga mini wani abin ba a rufe ni da baibai hannu ba! Gaba dayansu dubansa suke, Ya tako da fararan kafafuwansa da sukai fari fat na kasar garin ya dubi Gaishat ya ce" ke kuwa fa? Haka zaki saka mini ko? Kin samu na aura maki sarki , ya nada ki sarauniya aman ni kika saka kafa ki ka shure ni sai wannan tsohuwar matar kike baiwa abinki ko? Ai dukan ku Allah na kallon ku! Ko hakin ciyar da ku da na yi zai bi ku, Ya kara tofar da yawu yana duban Mariama dake bin sa da wani mugun kalli itama da sansanninta a bakinta kamar na sauran yan uwanta da Anna, ya ce" ke kuwa ke ce gagarara ko? Mai tarda ni wajen majalisa ki tirke ni gaban abokaina, ke mai karfi wace ta fi kowa iya rashin kunya, a gaban yan uba kika yi ikirarin zaki ga ubanda zai maki aure ko? Ba laifi, ba laifi Mariama, in sun zo sai mu basu gidan su saya su tafi mu kuwa mu koma zaman titi , Mariama ta yatsina bakinta ta kawar da kanta, Babar rigarsa ya kabe ya ce" kudinku yanzu na fara ci, ni da ku ba shari.a domin ni na haife ku! Dole na yi maku aure na mori kudin ku! , Ke kuwa, ya nuna Anna da take jan dan karamin carbinta tana shamaninta ya ce" kin ji kunya, anai maki kallon saliha sai gashi kun hada baki da tsohon can kun tura yarinya nema; ana zaton wuta a makera su Annar yara sun kunata a masaka. Yana gama fada ya fice a gidan yana ta tofe tofensa, Mariama ta dantsa yatsarta a bakinta tana yiwa yayarsu kallo mai kama da harara, domin ita ta yi masu kashedin kar ta kuma gannin wani ya biye masa, dan ta lura hakan na masa dadi Gaishat ta yi murmushi tana dubansu ta ce" baku lura ya fara yin sanyi ba? Mariama dake hararar Amaryar Ba ta ce" sanyi? A wannan tsohin najad..... Bige bakinta da Anna ta yi ya saka ta kasa karasawa tana turo baki, Da yannayin bacin rai ta ce" in kina irin magangannun nan hankalina tashi yake, mahaifin ki ne fa, ko me ta zama adu.a ce tsakanin ki da shi, ya zaki ringa halaya irin na wace bata da tarbiya? Bana so Mariama , Aman Anna, kina ganni abinda yake yi fa, ke tsoronsa kike , to ni bana tsoron sa, Kuma bakya tsoron Allah? Gaishat ta fada tana dubanta, hakin dake tsakanin ki da shi na matsayinsa na uba Allah ba zai bar maki ba, ki bi shi, ki yi masa biyaya, ki bar shi idan shi gobensa bata dame shi ba kai nasa, Shiru ta yi tana duban fatimata dake dan zane a kasa ta ce" wacen matar ciki ne da ita fa? Kuma kum san ba cikin Ba bane, Anna ta kwalalo ido tana dubansu, a dan harzuke ta ce" na ga mai isata yau da yaren nan, kun yi da shi ne? Bama wannan ba sa.anku ne? Du wace ta kuma gigin muguwar magana a kan mahaifin ku a gabana zamu bata da ita! Ba ruwana ban koya maku ba, baku ga ina yi ba, kuma idan na ji tsoronsa ai ba laifi ba, shugana ne, wanda aljannata ke karkashin kafafuwansa, a haka ma ya muka kare da shi bare na yi masa gatsali? Ku daina bana so! Ta karasa tana dan dafe kanta domin har ya sara mata maganar nan da ta yi, Da dadaya suke bata hakuri suna masu lura da yannayinta............. Daga inda yake ringeshe yake biya bagara a fili hannunsa a kan zuciyarsa, Sai da ya kai karshe ya samu ya dan daga ya jingina yana duban hanya dan ya san yanzu Mariama ta zo, Yana jin dadin lamarin mariama sai dai ita ba.a hira da ita, kimkim take masa har yanzu haushinsa take ji, bata san irin yanda shima hankalinsa ke kan Agaishat ba, adu.arsa a gareta ne, da fatan saduwar fuskokinsu kafin ya koma ga mahalicinsa, Jama.a Wardugu na neman karin aure🤣, du mai son karya kafa ta shigo layi🤦‍♀🤦‍♀🤦‍♀................... dan Allah aunty Alhinayett kar ki tura masa wannan page din wollah lalla batai kwari ba kar ya karya min kafar nima😟😟😟 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣7️⃣ Yana nan zaunen kuwa sai gata ta shigo da salamarta ciki ciki, Ajiye masa robar abincin ta yi bayan ta dan jefa masa wani kallo , Wajen ruwa ta je ta dibo masa ta zo ta tsuguna ya wanke hannunsa ta kuma cikowa ta ajiye , Dakin ta tatare kamar kulun shi kuwa yana cin abincin yana duban yannayinta, Mariama akoy shiru shiru sai dai yannayinta na yau kamar ranta a bace ne, A hankali ya ce" me ke damun Mariama? Tana gurza goron hannunta ta dan dago ta dube shi, ta ci gaba da gurzar abinta, Can ta ce" idan ta zo hankalinta a tashe, ranta a bace, idan ta fada maka ka taba yi mata maganin damuwarta ne sofo? Baba tsofo da ya gane Agaishat take nufi sai ya girgiza kansa a hankali , kafin ya ce" ban taba magance mata damuwarta ba Mariama, sai dai nakan saurare ta, na ji damuwarta, na yi mata nasiha a musulunce da girma, nakan ji ciwon damuwarta a raina na nuna mata ba dadi, aman kuma sai na nuna mata girman hakuri, Shiru ta yi tana jinsa, can ta ce" wai dan na kire shi da mumunan sunna Anna ta dake min baki bayan bata taba koda shakunana ba, kana da labarin irin manya manyan munana halayansa, aman sai ta wani tare mashi? Baba tsoho dai kallonta yake , har ta dasa aya tana hucin bacin rai, a nitse ya ce" su iyaye, sune masu madaukakiyar daraja in kika cire Allah da mazon sa a wajen dan adam, su iyaye Allah ya ce a bi su a yi masu biyaya banda hanyar sabonsa, Shi abinda yake ba sobon Allahn bane yake?, ta fada tana duban Baba tsofo, Baba ya gyada kansa yana dubanta ya ce" ya taba daukan y'a ya bayar ba.a daura aure ba? Mariama ta girgiza kai, Ya ci gaba da fadin" yana yin aurwn yayansa dan dukiya, adini bai jaramta hakan ba sai dai ta yannayin da yake yi ne, Yana yi ne tamkar yana siyar da yayan, Wa ke tafe da duniya da abinda ke cikinta Mariama? Ya kuma watso mata tambaya, Mariama ta ce" Allah, Shin baki da labarin ya fi gannin abinda kike aikatawa? Ya fi ki jin abinda ke wakana a tare da ke? Na sani , ta fada tana kawar da kanta, Baba tsofo ya ce" shi zai kare ku! Yana fadin hakan ya yi shiru tamkar ba shi ba, Da mamaki take dubansa, bata san lokacin da ta dawo facing dinsa ba ta riko hannunsa tana dubansa ta ce" shikenan? Hukuncinsa kennan? Baba ya yi mata murmushi ya ce " ke kika halice shi da zaki hukunta shi? A hankali ta sada kanta, muryarta ne ya yi rauni ta ce" ya cika cin zalinmu, bai san darajar matarsa ba wace take mahaifiya a wajen mu, mu yayansa yakan dauke mu ne ya yi kudin mu, yanzu ya tare da matar da wani ke ziyara a kan idannuwansa, shin yaya ake so dole dole sai na daraja wannan mutun? Baba tsofo yana dubanta ya sada kansa shima, ya dago ya ce" muna tursasa ki yi masa biyaya ne dan goben ki, kar ki ga duban laifukan da kike hange nasa, idan kika taka hakinsa a kanki na matsayinsa uba a gare ki, Allah ba zai bar ki ba, ki yi masa biyaya, sai ki ga Allah ya jibanci lamuran ki Mariama, A hankali ta cika hannun Baba tsofo ta juya ta hado goronsa ta kule sauran ta kula a harshen zannin ta, Miko masa ta yi wanda ta gurzan ta duka gabansa tana dubansa ta ce"ya aka yi mutun mai mutunci irinka ya rayu shi kadai? Ni tunda aka haife ni kai kadai nake gani sai almajiranka wa.inda da sun fara tasawa suke tafiarsu birni neman kudi, ya aka yi baka da mata da yara? Dubanta yake da mamakin ashe dai ta iya magana, sai dai tambaya ne da Mariama tamkar me, komai so take ta gane ya aka yi ? Ta ina aka bi aka yi? Wa ya yi? Su waye shaida? 😅, Iyayena yaki ya tafi da su, Na tashi ni daya sai Allahna, Na yi aure sau biyu a rayuwana, sai dai rashin haihuwa ya saka matan na guduna, Me ke birge ka a rayuwar wannan daji kai daya kwal da ranka? Tsareta ya yi da ido kafin ya ce" nan ne muhalin da Allah ya ara min, Kalonsa take da wani yannayi na tsoro, a hankali ta mike tana dan duban yannayin dakin baba tsofo, Fitowa ta yi ta hangi anguwar ba wani mutun mai gitawa bukar baba tsofo a tsakiyar rana take sannan nesa da jama.a, A hankali ta waiwaya bayanta ta tsurawa kofar bukar ido, a ranta ta ayanna " *Wannan mutun ne ko aljan?* (🥺🚶🏻‍♀️😳😳😳😳🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️) Rakiyar Aghali aeroport tamkar za.a raka shi tafiar da ba zai dawo ba, Idan ma ya yi salama da iyayensa kuma yin salama suke , Har aka fara harama kiraye kirayen suna wanda hakan ya saka shi komawa wajen mahaifiyarsa ya dan duka kansa ya ce" Allah ya ja zamanin sarauniyar garin Agadez, sai Allah ya dawo da ni. Dago da habarsa ta yi tana dubansa ta ce" Allah ya kai ka lafia yarimana, ka gaisar min da aminiyata domin ban lamunci ka sauka hotel ba bayan gata a gari, Murmushi ya yi mata yana daga mata kansa , kafin ya juya wajen matarsa ya sakarwa yarinyarsa kiss a goshi da kunci, itama matar ya yi mata kiss a goshinta a hankali ya ce" *Tarhanine* (masoyiya) Dago da kanta ta yi ta dube shi, da dara daran idannuwanta ta yi masa salama kafin take juyawa ta nufi dankareroyar rangrover din su Sauka lafia Yarima Aghali . Yai tunda ta farka a barci ta ahige bayi ta yo wankanta ta fito ta kimtsa jikinta domin ta farka da al.adarta wace ta zo mata tsakiyar dare, Bayan ta gama ta kuma rufa ta turara turaren wutar da ya zame mata jiki karfi da yaji Ayya ta koyar da ita saka turaran wuta a jikinta da kowani lokaci, barema idan ta fito a wanka sai ta turaru kafin ta bushe, Sai da ta gama turaruwa ta dawo ta ciro doguwar rigar atampa , jar atampa ce mai adon baki baki a jikinta, An yi mata dinkin mai turmi , saman ya dan rike daidai kirjinta ya yi mata das sai ya bude kasan , , A hankali ta zauna saman yar kujerar gaban madubin ta caje gashinta wanda Ayya tace yau za.a kitsa shi, domin ana kitsawa yana warwarewa ne Ayya kuwa tace sai an yi kitso mace ce dole ta yi kitso, A ranta ta ayanna , ina yake? Ya ya kwana? Har yanzu yana kan bakansa? (Domin rabonta da Mu.azam tun guduwar da ta yi jiya,) yanzu har karfe goma ya gita na safe, tana jin lokacin da Ayya ta shigo take fadin zasu je su dauko Aghali dan aminiyarta , sannan ta ji lokacin da mai aiki ta shigo tana fadin Wardugu ya zo Ayya bata nan, aman ina ita barci ya ci kargfinta domin idan tana al.ada takan yi wani barci mai nauyi ne, A hankali ta saki murmushi ta kuma furta "Mu.azam nawa , Ji ta yi an turo kofarta dan haka ta mike tana duban kofar, Shigowa ya yi da salama a bakinsa, da sauri ta kai dubanta saman bed dinta, Allah ya so ta abin shinfidar ya rufe pant dinta da ta ciro ta zabi wanda zai riketa da kyau ta saka, bata rigaya ta mayar da sauran ba, A hankali ta mayar da dubanta wajensa, kafin murya a sanyaye ta ce" i....i.ina kwana , Yauma bai amsata ba, sai kallo da yake binta da shi na mamakin yaushe ta iya saka kaya haka? Yana gannin yan aikin gidansa har kulun su shigarsu tamkar an tsamo su daga rafi, domin Walyn nata daukan yan aiki yan birni sai yan kauye, baya taba gannin sun waye su kulun tamkar mahaukata, shi ya sa koda wasa ya hana su taba wani abin a bangarensa, hakan ya sa ta samo masa namiji mai aikace aikacen bangarensa wanda ta yi ta rantsuwar ba dan daudu bane, shi kuwa dan daudu ne idan ya shigo gidan ne yake namiji! A hankali ta karasa ta dauki dan kwalin atampar ta daure gashin kanta da kyar , wanda yake lumbuk gaban goshinta, ta koma gaban madubin ta zauna abinta ta shiga daure gashin kanta, Wani irin mamaki ne zai kashe wardugu dake tsaye yana biye da ita da kallo, kai! Ya fada a ransa, ya shigo ne dan ya tambayeta kys din dakin Ayya dan ya san ita zata barwa, sai dai mamakinsa, ya hadu da macen da bata nuna tsoronsa, kakahin ta birge shi, shishigi a gare shi ba, ita bata nuna tana tsoronsa ba , ita bata nuna bata tsoronsa ba, ita dai ta gaishe shi, gaisuwar da ya tsana wai wani *Ina kwana*, sai kace wani sa.anta! Yana nan tsaye har ta gama daurin dan kwalin da ya boye baki daya gashin kanta, ta dauki turaren ruwa ta kuma fesawa a jikinta mai sanyin kanshi wanda Ayya ta sayi kwali guda irinsa sunnansa princesse , Kwali ta dadage ta saka sannan ta shafa dan man lebe kadan, , Mikewa ta yi ta juyo facing dinsa tana dubansa yana dubanta, a hankali ta shiga takawa tana nufo shi, wanda du takunta daya sai ya ji gabansa ya dadage ya fadi , da sauri ya kawar da dubansa a kanta daidai nan ya jiyo muryar Ayya, Tamkar an hankada shi haka ya fito daga dakinta wanda har ya waiwaya da sauri yana duban kofar, hankali ya furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, abinda Wardugu ya furta kennan kafin yake tura dakin Mu.azam dake kasa kadan da dakunnan su Ayya ya shige ya rufo ya nufi gaban madubi da sauri, Duban kansa ya tsaya yi, kaki ne a jikinsa, sosai yannayinsa na ban tsoro ya bayana a jikinsa, sai dai kaki din wandon ne kawai sai bakar rigar da ya saka, a fili ya furta" ko dai makauniya ce? 😳😳😳😳😳😳 Ba laifi yau kun yi comment, dan haka ga kari😍😍😍😍😍😍 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣8️⃣ Murmushi ya yi bayan ya tabatarwa kansa da yarinyar ba makauniya bace tana gani sosai, To aman ayar tambayar shi ne me ya sa bata tsoronsa? Ko ta tsaya ta shagalta a kallon sa kamar yanda du yawancin mata da mata ke yi? Bale ita da ga irin wajen da ta fito wato kauye zai kasance shi ya zama abin kallo a wajenta, sai dai abin mamaki tamkar ba.a yi halitarsa a gabanta ba, Kansa ya girgiza a fili ya furta" Ayya kwashe kwashe, idan kuma aljana kika kwaso mana ba sai ki huta ba🥴. Sai da ya gama abubuwansa sannan ya juya ya fice ya tafi falo domin yana jin hayaniyar samarin biyu da muryar Annarsa. Agaishat tsam ta yi bayan fitarsa ta sauke ajiyar zuciya, murmushi ya kubuce mata a fili ta furta" idan Mu.azam nawa zai aure ni, cikin abokan ango da zasu zo daukana a rakumi (🙁😕😟 ke malama a birni kike🙄), harda wannan mai kama da mutanen cikin alon nuno mutane (tv), Dariya ta yi tana dafe goshinta ta ce" kai aman katoto ne, kuma wai dan Ayya ne🤦‍♀, ko ta yaya ta goya shi? Kys din Ayya ta dauko ta juyo zata fita, ta ja ta tsaya ta dubi wajen da Wardugu ya tsaya ya zuba mata ido, nuna wajen ta yi da hannunta ta ce" kai katoto, ka daina irin kallon nan, baba sofo yace ba kyau irin kallon nan da kake! Yatsina fuskarta ta yi , ambaton sunnan baba sofo da ta yi ya sace mata lakar jiki, a hankali ta shiga takawa da zancen zucin ko ya yake? Ya Annarta? Ya yan uwanta? Ko da wasa bata tuna yannayin mahaifinta, sai ta tuna da baba tsofo sau dari bata kawo sunnan Ba a layin zuciyarta ba, tsananin tsoronsa da ya dasa mata ya saka har a zuciyarta idan ta yi kamar ta tuna shi sai ta gargadi kanta cewar ki kula Agaishat kiyayarsa gare ki madaukakiya ce. Agaishat na saukowa, kanshin turaranta ya fara karasowa, kafin a hankali ta idasa fitowa fallon, Da murmushi Ayya ke kallon ta, domin ta ji dadin irin yanda yar tata ta koyi saka kaya da wuri haka, Mu.azam da ya dago daga hirar da yake yiwa Wardugu ya zuba mata mayatatun idannuwansa , zuciyarsa na luguden kida yana dubanta da wani yannayi mai nuni da " kin azabtar da ni, Wardugu dake gefensa yana sauraron sa, jin ya yi shiru ya saka shi duba wajen nasa, nan ya bi abinda ya tsurawa ido, ya kai dubansa wajen Aghali da yana tsakar waya da mamansa yana shaida mata ya sauka lafia, aman ya tsaya mamakin wai yarinyar da Ayya ta dauko ce haka? Da sauri Wardugu ya mayar da dubansa wajen Mu.azam, shima zuba masa idon ya yi yanai masa kallo mai cike da ma.anoni, Salama ta yi , kafin ta zarce wajen Ayya , inda a takaice ta ce" ina kwana.......... (wannan na cikin abubuwan da Ayya ta koya mata, cewar ta ringa kiyaye sakin baki, kai ko gaisar da bako zatai ta takaita , in dai ta yi salama cikakiya halas!) Tana zuwa ta zauna inda Ayya ta nuna mata, Hannunta Ayya ta kama tana duba faratunnanta , domin ta umarce ta da sakawa yatsutsanta jan lale, Ta kuwa saka , ya kama yai mata das a hannun , Ayya ta saki hannun ta lakaci kuncinta, kafin ta yi kiran Hanne, kan ta kawowa yarinyarta abin kari, Kai Wardugu ya girgiza, ya mike yana daukan wayarsa ya kai dubansa wajen samarin dan ya ankarar da su , da haushi haushi ya ce" ni zan tafi, Da sauri Aghali ya mike yana fadin" zamu tafi dai oga, Wardugu ya ce" a mashin fa nake Aghali, Aghali ya dafe kansa, ya kai duban sa wajen Mu.azam ya ce" docter tashi mu je ka kai ni , Mu.azam ya dubo su, irin yanda Wardugu ya yi kicin kicin da fuska ya san ko sun bi shi walahi zai bace masu ne, dan haka ya ce" ni sai na karya, Idan kana so ka karye! Wardugu ya fada ya juya yana fadin" premiere dame (First lady, wato Ayyarsa), sai na dawo , Ayya ta amsa shi da" ka dawo lafia *War*, Haka ya fice a gidan cike da takaicin girman kan yarinyar, domin shi kawai ya ajiye haka a matsayin girman kai, wai su *Ashak* ko? Ba buzuwa ba dai, su waye ma su buzayen nan da suka raina mutane har suke yiwa mutane Ashak? Sosai ya kunsa a lamarin Agaishat ya bashi mamaki, wanda hakan ya saka ya dauki aniyar nazartarta a tsanake, shi zai koya mata ladabi da biyaya a haukace! (Toh fa), Kuka take na tashin hankali tun da ta shiga bayin da kamar minti biyar, da gudu ta fito ta mikowa mamanta abinda ta yi gwajin fitsarin nata dan gannin ko ciki ne da ita? Domin tunda Wardugu ya yi maganar komai nata ya tsaya ya daina aiki, Da yannayin farin ciki uwar ke dubanta, ta ce" kukan murna kike ko na me Walyn?? Da madaukakin tashin hankali ta ce" ba zan haihu yanzu ba, bana son cikin nan walahi sai an zubar da shi, bana so! Da mamaki uwar ta mike tana dubanta, kafin take nunota da yatsa ta ce" ke ke ke, da hankalin ki kuwa? Walyn ta dan tsagaita kukanta ta dubi uwar, kafin take kara barkewa da wani kukan ta ce" ba zan yarda na dauki ciki da Wardugu a wannan lokacin ba, a bai tabatar ina da ciki bama ya yi min rantsuwar sai ya yi mini kishiya ina da ya gane ina dauke da ciki? La haula wala kuwata ila bilah, maman Walyn ta fada, ke bashi da hankali? Yaushe ma aka yi auren da har ya fara yi maki maganar zai maki kishiya? Me kikai masa da zafi? Ki bakya barinsa zuwa wajen ki yanda ya dace?, fada mani me ki kai masa da zafi haka? Nan walyn ta warwarewa mahaifiyarta yanda suka yi da Wardugu, Haushi kamar uwar zata dake ta ta ce" yaushe zaki gane mahaukaci ki ke aure ki iya takun ki da iya zama da shi? Da sauri Walyn ta ce" Ma, Wardugu ba mahaukaci bane ! Uwar ta yatsina fuska tana dubanta ta ce" toh dan uban ki ba mahaukacin bane, aman wannan cikin ko aman jini kike sai kin haife shi kin sama mana magaji, ke ko me zaki yi sai kin kawo shi duniya, bara ma ki ga na fada masa, ai shi kina tsoron sa tamkar ran ki! banza sakarya marar tunani!..... Rigima ta kirki suka kwasa kafin da kyar ta samu ta zaunar da ita ta ce" Walyn , kina bani kunya a rayuwa, wani lokacin har kokonto nake ko dai an canza min ke a asibiti ne? Ina yi bakin kokarina dan gannin kin yi fice a gidan ki aman a kulun sai da hadu da abin takaici abin mamakin da zai saka ni jin kunya, Matar Batube, ta kasance tamkar abinda ya malaka kwalin kwal a duniya, wanda tamkar numfashinsa ne, yana ririta ta, yana kulawa da lamarin ta kafin na kowa, na sani ci sha sutura kilacewa, kayan burga ba wanda baki da, matsalar daya ne baki isa ki saka mijin ki ko ki hana shi ba! Menene dalilin haka? Na kasa ganewa, na kasa ganewa walyn, Walyn dake zaune du ta hade jikinta, a ranta kuwa ayannawa take ko da jaraba sai ta zubar da wani tsinanan ciki, a haka ma tana cas cas dinta yanai mata maganar kishiya, ina da ta haife? Bama zai yiwu ba, idan ta haifi guda ai ta kama hanya, kofa ta budu, sauran zasu zo ko fa balaki ne, kennan shikenan kishiya ta tabata a gare ta ? Duda tana tsoron lamarin wardugu, ya yi aure haka ba tare da ya cika al.ada ba ba damunsa zai yi ba, tsohuwar uwarsa kuwa ba tirsasa shi zatai ba! Mrning alll 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 3️⃣9️⃣ *baki ba zai iya misalta maku irin yanda zuciya ke cike da farin cikin karanta ku Bak'a fans, Allah ya bar kauna baki daya* Ya Allah, kar ka kai labarin mutuwarmu zuwa kunnen da baki ba zai fadi alkhairi kan gawarmu ba 👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻😭 Haka Walyn ta wuni wajen mahaifiyarta , inda uwar ke kwatanta mata yanda zata yi ta ci ribar zama da wardugu, ita kuwa tana tsara yanda zata rabu da ciki! Tana komawa gidanta ta zauna falo, ko kayan bata iya cirewa ba tsabar tana cikin tashin hankali, fatar jikinta kuwa du ta yi ja abinka da jan mutun, Tv ta kunna ta kamo tashar labaru, An yi sa.a kuwa ana watso labarun su Aisata kan an yi bincike har an fara cafko masu shigo da kwayar, inda alkali zai yanke masu hukunci, , nan aka hasko sunnanta baro baro hade da sunnan mahaifin wardugu, aka fadi cewar ta bada hadin kai wajen kamo wasu masu harkar dan haka zata samu sasauci kan hukuncin da aka yanke mata, Tsaki ta ja ta kashe tv din ta mike nan ta shiga baci domin ji take tamkar idannuwanta na dauke da yaji ne dan tsabar nauyin da su kai mata. Wardugu na tsaka da aikinsa aka shigo aka shaida masa Marahut na son ganninsa, a shigo da shi ko kuwa? Wardugu ya dafe goshinsa, a ransa ya ayanna me ke damun Elhaj Marahut ne da zai mayar min da office wajen zuwa haka? Umarnin a shigo da shi ya bayar , ya ci gaba da aiyukansa yana hada takardun wasu yan gudun hijira ne da aka kamo , ya duduba da kyau ya ga du yawanci yan libia italia da dai sauran su, yana son mika su hannun likitoci a duba lafiarsu kafin su yi masu takardun tafia su juya garuruwan su! Shigowa Marahut ya yi ya zo ya zauna saman kujerar zaman mutun daya yana duban Wardugu, Kai shima yana alfahari da namijin yaron nasa, suna mugun kama aman ko a zamanin da yana saurayo bai kai Wardugu tsayi da yannayin karfi da cikowa irin nasa haka ba, Murmushi ya yi masa ya miko masa hannu ya ce" Asalamu alaika Wardugu Dago da kansa ya yi , a nitse ya miko masa hannun shima ya amsa da" amine wa.alaika salam *Elhaj Marahut*. Murmushi ya kuma yi ya rike hannun na wardugu, sam baya son sakin hannun, rabonsa da rike hannun yaron har ya manta, Da ido Wardugu ya yi masa nuni da ya cika shi mana? Sakin hannun ya yi , a nitse ya ce" Wardugu sunana kake kamawa haka ko? Wardugu ya dube shi, ya yi masa murmushi ya mayar da dubansa kan takardarsa, Ka saka baki wajen alkalin nan ya sasauta mata hukuncin da ya dauka a kanta, kaso har na shekara biyar ya yi tsauri Wardugu, Wardugu ya dago yana dubansa , ya ce" ka san ba hurumina bane, sannan bana saka hanuna a irin haka, kaima ai kana da hanyar hanata yin kason ma domin ka fi ni fada a ji a wajen su, Wardugu sunana zai bace Wardugu, sannan hakinta a kaina yake! Marahut ya fada yana dubansa da yannayin iya gaskiyarsa kennan Wardugu ya ce" ni nawa sunnan sai na kai na dulmiya ko? Ah koda yake daman sunana a bace yake a bakin al.umar da suka aikata laifi, sai ya yi ta baci jar a bakin wa.inda basu taka dokar bama? Marahut ya dafe goshinsa, ransa ya fara baci ya ce" har sai yaushe zaka daina mugun fushin nan a kaina? Ni fa na haife ka! Baka tsoron goben ka? Kai idan naka suka ki yi maka biyaya fa? Wardugu ba laifina bane abinda ya faru a baya , Wardugu ya dube shi ido cikin ido ya ce" wannan tsohuwar magana ce Marahut, kana iya tafia ba zan saka bakina a maganar iyalinka ba! Wardugu! Ya fada da dan karfi yana mikewa, Wardugu ma ya mike ya ce" Marahut! Marahut ya tsura masa ido, a hankali ya ce" dan na kula wata, na aureta , ba laifina bane, laifin uwarka ne! Sannan dalilin halayan da na gane nata na rabu fa ita yanzu, Wardugu ya hadiye abinda ya tsaya masa a wuya, ya karya kansa ya ce" sai dai yanzu Wardugu bashi da budurwa bare ka kwace, Marahut ya daga hannunsa ya zabga masa mari wanda ya yi mugun kara kara, ji kake tas, ya maya masa a gefen kuncinsa wanda hakan ya sa hularsa dagawa, Kan Wardugu a kasa a hankali ya dago jajayen idannuwansa ya sauke a fuskar mahaifinsa, Mahaifinsa, ubansa, wanda ya haife shi, a yau ya so a ce wani ne ya kai hannunsa jikinsa, kai kai kai, balaki, Ido cikin ido suke duban juna, Marahut ya ce" ko me ka zama, ko me kake takama da shi dai haihuwarka aka yi, na yi tunanin rashin mutuncin naka zai saka ka daga hannu ka rama! Ka rama marin mana Wardugu! Wardugu ya sakar masa murmushi mai ciwo , a hankali ya ce" ko shege mai mutunci ba zai rama ba bare kai da ka haifi dan halal ka bashi tarbiya?, kar ka daga murya yarana su ji, domin ban san in zan iya rike kowa, wai ina gudun ba nan gaban idona ba, ka san soja shegen yawo ne da shi, gashi da ramuwar gaya, Ka je kawai Marahut. Jikin Marahut ne ya yi sanyi, ji yake dama da hali da ya rungume shi ya shafa wajen da ya mare shi ya bashi hakuri, A hankali zuciyarsa ke sauka har ya ji dumbin kaunar dan ta kuma mamaye khalbinsa bashi da wani , baya tunanin zai samu daga shi, fatansa su sauko daga dokin zuciyar da suka hau bisa gangancinsa, sai dai ya rasa yaya zai yi, shi ba zai duka gabansu ya basu hakuri dan ya kara aure ba, su ya dace su yi hankali su zubar da makaman yakin su, yanzuma ba wai ya zo ne dan Wardugu ya yi magana harkar Aisata ba, shima yana iya sakawa a saketa aman ya barta ta je ta yi kasonta kawai domin ta taka doka, ciki harda ta musulunci , da aurensa a kanta take bin wasu mazan. Ya zo me dan ya kara ganninsa su sami hira ta kusanci na da da uba, sai dai ga yanda ta kare, A hankali ya juya dan barin Office din, Ja ya yi ya tsaya, a hankali ya dawo ya dube shi, hularsa da ta dage ya janyo ya gyara masa a kansa, ya gyara masa gaban rigarsa da kyau ya ce" Allah ya yi maka albarka, na yafe maka dukan abinda ka yi min wanda na sani da wanda ban sani ba, Allah ya kare gabanka da bayanka! Yana gama fadar haka ya juya ya fice a office din, Ran Wardugu a cakule ya hade takardun ya fito gaba dayansa a haukace ya mikawa Lieutenan Jalo takardun bai masa magana ba yana kallon mashin dinsa ya fice ya bar shi a wajen aikin ya kama tafia a kafarsa cikin sauri, ya yi niya a kafa zai je gidansa ba zai hau mota ko mashin ba, ya ki din , kai bama zai kuma hawa ba! Zai je a kafarsa , du wanda ya fasa kawo masa wargi ya ki Allah! (🥴 wani da laifi , wani da shan duka? Tap🤔), Bayan kwana biyu, fitina ta dan lafa gefen Wardugu, Juma.a ce yau, ranar da ake bada damar shiga gannin yan gidan kaso harma a dan jima a wajen su, A wannan ranar ne mutane ke cika prison dan gannin nasu, Wannan damar Walyn ta rike ta yi shiga irin ta larabawa ta yane kanta da dan kwalin bakar abayar da ta saka ta yane har habarta sannan ta saka bakin gilas, A kafa ta samu ta fito bakin titi nan ta ja ta tsayar da mai taxi ta yi shatar ita daya. Basu zame ko.ina ba sai justice ta ciri takardar gannin dan prison ya dauketa ya sadata da gidan kason, A hankali ta cire gilas din idonta, sannan ta dan ja mayafin dan bude habarta dan kar ta jawa kanta matsala da masu tsaron gidan kason Takarda ta nuna, ta je saman kuje ta zauna inda aka shiga aka kirawo mata wanda ta zo nema, A hankali take takowa har ta karaso wajen warda aka nuna mata a matsayin uta ke nemanta, Kallonta take, irin kallon san sannin wacece? Hakan ya sa Walyn ta bude rufarta dan ta shaida ta, Murmushi Aisata ta yi tana dubanta, aman a kasan zuciyarta mugun kishin Walyn take, kai da tana da dama da ita ce ajalin yarinyar da ta auri gwarzonta! Walyn ta kare mata kallo sama da kasa, cike da yanka da jan aji ta ce" *wanene shi*? Bata amsa ba , sai da girarta irin na rikakun yan duniya da suka san kansu ta yi mata tambayar *Wane?* Walyn ta fara shaka ta dubeta da kyau ta ce" *waye malamin da ya miki aiki kan Wardugu da mahaifinsa?* waye shi?, idan kika fada mani komai, zan saka a fitar da ke daga wajen nan. Murmushin rainin hankali ta yi tana dubanta, cikin kissa ta ce" kina da damar sakawa a fitar da ni din ne kika shigo cikin gidan kaso dan samu adress din malamina? Kina son samun kanki ne a wajen Gwarzona? ......... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣0️⃣ *Walahi ni ba kowa bace, ni ba komai bace, Allah ne gatana👏🏻😕👏🏻* Walyn ta zaro ido, rai bace ta ce" zan datse harshen ki idan kika kuma kiran mijina da gwarzon ki! Aisata ta ce" da kuwa na ji dadin yin makota da ke, da zan gani idan kema da ya kilace zai saka ki a kaso dan kin zalinci wani! Walyn ta tsareta da ido, a hankali ta ce" zan biya ki, ki fada min kar lokacin da aka bamu ya kare , Aisata ta ce" na sani kina da damar iya biyana aiki, dan ni mai nema ce, ina nema kamar me, kudi baya isata, da yana isata da na tsaya da sirikin ki kawai! Walyn ta ja tsaki ta ce" lokaci! Aisata ta ce" kar ki damu, yau ai akoy lokaci isashe , Walyn ta kuma tsareta da ido, ta ce" me zai rage ki dan kin fada mani? Kin san dai kin haramta wa wardugu tunda kika kwonta da ubansa! Aisata ta lumshe idannuwanta, a hankali ta lashe lebenta na kasa, rage murya ta yi kamar zataiwa Walyn rada ta ce" *Ke ba fa kowa ke da haram ba*, Walyn ta daki table din ta ce" zaki fada mani ko ba zaki fada mani ba? Har sai da hankali ya kawo kansu inda wani soja ya karaso yana tambayar lafia? Nan Aisata ta kalamance shi da"Oga ba komai, Juyawa ya yi ya koma, Aisata ta dubeta da kyau ta ce" kina tunanin na taka farar kafata na je wajen Boka dan tsibu dan ya malaka min saurayi? Kina tunanin aikin boka ya malaka min mazaje biyu ? Walyn ta ce" kin gane, ni fa ba yarinya karama bace, kuma na san bariki ki ka yi ! Dan haka kar ki bi min ta wannan hanyar ba gyara mu zata yi ba. Aisata ta ja rigarta kadan, hakan ya baiwa saman mamarta damar fitowa sosai, ta ce" *kin ga malamaina* Walyn dake kallonta ta yi dariya tana girgiza kai ta ce" ba dai Warsuguna ba, Wannan abin bai isa ya ja ra.ayin namiji mai sunna namiji ba! Aisata ta ce" haka ya fada maki? Ko irin zaman da kike yi da shi? Walyn ta ce" ba sai ya fada mani ba, haka ne, Wardugu kamili ne, girman kansa ba zai bar shi bama ya lura da wani abin jikin yar bariki! Aisata ta bushe da dariya har tana rike ciki, nunata ta yi da yatsa ta kuma kecewa da dariya, sai da ta yi mai isarta ta ce" lale kin rako mata, ina mai baki albishir din in dai kallon da kike masa kennan ki farka tun kafin ki kuma jaza mana wata yar balakin da ta fi mu ta karbe mana Gwarzon mu! Walyn bata ce mata komai ba, sai duban kin raina min wayo da take mata, Aisata ta tsagaita tana duban Walyn ta ce" Walyn Wardugu, ba kowace mace ce ta san kofar boka ba, koda kina jidana da na yi bariki dan na fita da d'a na kuma dawo kan uba , ina mai tabatar maki ba boka ne ya tsaya min ba. Ya zan zo cikin wannan wajen mai fitar da wari ki saka ni gaba kina yi min rainin wayo? Walyn ta fada, Aisata ta juya idannuwanta ta ce" kar ki yi garaje, zuwa gidan yari rubutu ne wanda Allah ke kadara shi, diyawa a wajen nan basu taka basu karya ba.... Walyn bara ki ji wani abu....: du namiji na duniya yana da abinda idan ya ganshi a gabansa yakan ji ya rasa dabararsa, Wani namijin mace mai kissa, mai kisisina, mace mai kyan dan maciji ke tafia da imaninsa, wani namijin mace mai adini mai rufe jikinta, mai mutunta kanta ke tafia da imaninsa, wani namijin yana son mace mai halaya irin na yan bariki ce zabinsa, wanin mace mai kyau ko muguwa ce zasu taka rawar, wanin yana son mace mai shiru shiru, wanin yana son mace mai kamar maza irin mai kafkaf da ita, wani baya jure gannin mace a cikin yannayi na abin tausayi...zaki ga ya fada tarkon kaunarta, wani farar mace ce zabinsa, wani kuwa *bak'a*, ke wani duka biyun yana so....tambayar a nan shi ne *Sai ka karanci mutun kake gane waye shi harma ka tabo wajen da ba zai jure ba, da kansa zai nuna shi sai kai*, Walyn kallonta kawai take, Aisata ta ci gaba" mijin ki dan ra.ayi ne, gwarzona ya bani wahalar da wani namijin bai bani ba , kyauna, zubina, yannayin rayuwana na saka shi fadin"Aisata ke matar kilacewa ce, ki yi zamanki a gida zan zo na dauke ki na mayar da ke matata. kafin na samu kansa na jigata.da kuka da komai ya furtan kalmar so, domin na kai karar tsohon saurayina wajensa inda na biya mutumin ya yi min dukan tsiya, ke dai na takaita maki sai da na zama tamkar kaska, du inda wardugu yake ina nan, da naci da taimakon aminiyarsa ya furtan kalmar so... Sai dai abin haushi du irin yanda muke soyaya da shi idan na nuna koda shan minti ne a dan zaga sai ya fatatake ni, A ranar da na tube zindir a gabansa sosai na kusa cin masa wani tsinanan abokinsa ya shigo dakin domin ke shaidan ba abinda baya hasawa , kwana dakin wardugu na kusan cinma burina nan na fahinci irin zaman da ake tsakanin matar Marahut da shi, Ayya ta kasance mace mai tsafta, ta iya girki, tana yiwa mijinta biyaya ....sai dai na sha na fito tsakiyar dare falon su na kunnuwana su tsinkayo min rigimar ba zata bashi ba, ta gaji da ayyuka ya bari sai da safe! Wani wal wal wal ta yi da idannuwanta ta ce" *Walyn ba.a matsa lamarin nan, idan aka tashi a yi kawai!*, A lokacin da na gama gane Ayya ba zata aminta na auri farin cikina ba, na dauki damarar itama sai na cusa mata bakin ciki , kuma ko da kwaya sai na kwonta da d'anta! Walyn ta ce" shi Marahut din asiri ki kai masa ko? Aisata ta ce" na fada maki ban san wannan ba! Walyn ta rafka tagumi ta ce" fada mani yanda kika tarwatsa su , mai yiwuwa na yarda da labarin wai Wardugu ba asiri ki kai masa ba. Aisata ta buda bakinta zata fada mata kennan aka zo aka ce ya isa haka sun jima suna hira domin dai Aisata harkar kwaya ya kaita kaso, ido a kanta yake dan kar a kawo mata har gidan kaso... Haka Walyn na ji na gani ta fito ta kama hanyar gidanta ba tare da ta samu komai ba! Alhinayet ce zaune tare da saurayinta, malamin university ne, saurayi ne domin bai taba aure ba, bazabarme ne baki dogo , hira suke cikin nishadi nan yake shaida mata yana son turowa, Alhinayet ta fada masa zata fadawa abanta tukunnan , abinda ya ce in sha Allah. Haka suka gama hirar su ya mike ya yi mata salama ya shige motarsa ya tafi, Mikewa ta yi ta je cikin gidansu , Shiryawa ta yi ta saka dogon hijab dinta blue, ta dauki bakar leda ta je wajen mamansu , wato matar mahaifin su ta shaida mata zata je ta kaiwa Agaishat hijaban Adu.a ta yi mata kafin take fita ta shiga motarta ta tayar ta nufi gidan Ayya............. Aghali ya zo garin Niamey ne dan duba gininsu da ake yi a unguwar cité laraba, Ya gama abinda ya kawo shi aman ya ki tafia bisa bukatarsa na Wardugu ya siyar masa da mota , sun tsayar zai shigo ranar lahadi wato gobe baya aiki sai su fita su je ya gani...... Soyaya suke a nitse, a hankali yake koya mata mecece soyayar ma wace a kulun sai sun gama bitar zai jefo mata tambayar" Agaishana, shin kina jin du abubuwan da na zana maki a kaina? Dariya take yi a fili sai tace" ni yaya Mu.azam gudun fankan dakin Hane mai aiki kawai ke saka zuciyata gudu, ka ci gaba da koya mani na san zata yi gudun wata rana idan na ganka Yakan tsareta da ido ne kawai , bai san me zai da ita ba, soyaya ai shigar farat daya take yi, shi da yake so ya kai kudirinsa wajen Ayya kan a aura masa ita da wuri? Kai ba zai wani jira har ta kamu da sonsa ba, zata so shi a zaman da zasu yi, shi kam yana kwadayin zama da ita a rayuwa.... Docter Mariam ce tsaye tare da shugabansu ta asibiti, kanta duke kuka ne take har jikinta na bari ta ce" nima marainiya ce docter, a lokacin da na zo wajen nan shi ya tarbe ni, ya ciyar da ni da aljihunsa, kafin na tsaya da kafafuwana shi ne komaina, tun a lokacin nake mugun son sa, ba zan yafewa kaina idan ban je na dawo da shi ba, ki taimaka mani ki sama mani takardar nan na roke ki, Cike da tausayi take dubanta, su musulmai haka suke ko kuwa wasu da wasu ne? Tana jinjina girman son da Mariama ke yiwa docter mu.azam, in sha Allah zata sama mata takardar su biyu wace zata bata damar zuwa ta zo da shi su shiga aiki, koda bai tashi ba , ba zata tsangwami kanta ba, A hankali ta dafa kanta ta ce" kar ki damu Docter, ki je zan neme ki, zan nema maki takardar Da murnarta ta yi godiya ta fito ta shiga office dinta, hotonsu ta kaiwa duba kafin a fili ta ce" wai baka son farar mace ko? Dole ka so ni docter, ni ina son ka😭😭😭 Wayo hanuna😕😕😕😕😕😕 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣1️⃣ Ayya ki duba lamarina na roke ki, Mu.azan ya fada kansa a kasa, kunya ta hana shi dago da kansa ya dubi Ayya domin ya fadi abu mafi nauyi a bakinsa Da mamaki take kallonsa, so? Aure? Yana son Auren Agaishat? Aman yaushe suka yi wata soyaya da fahimta har za.a kai ga aure? A nitse ta ce" Mu.azam, aman me ya sa kake sauri haka? Mu.azam dake kallin kasa ya ce" Ayya , ina so ne a yi mu juya tare da ita. Aman ai ka san sha.anin aure na bukatar nutsuwa ko? Sannan yarinyar nan amana na daukota daga garin su, eh lale mahaifiyarta ta bani damar ko aure ya tashi na yi mata aman da ransu da lafiarsu ba zan yanke hukunci irin na aure ba tare da yawun iyayen yarinyar ba ko? .... Ayya ta fada jikinta sanyaye tana dubansa Mu.azam ya gyada kansa, hankalinsa ya dan fara tashi ya ce" Ayya, ki tura ni wajen dagin nata, na je na nemi a bani aurenta, bana son jan abin ne Ayya ta kuma kale shi da mamaki, bai taba naci kan abu irin wannan ba, jikinta ta ji ya kara yin sanyi, aman Agaishat dinta dukanta ma nawa take da har za.a yi gagawa a lamarinta haka? Sai dai kuma bata tunanin Mu.azam zai wulakanta mata yarinya, duda haka tana son bin hanyar da kakarta ta bi da ita, zasu kai kulansu wajen Allah, a hankali ta ce" yarona, na ji, kuma zan fi kowa farin cikin sannin tana hannu mai kyau, kar ka damu zan san abin yi nan kusa in sha Allah, in dai Agaishat matarka ce zaka aureta kisa ba da jimawa ba. Cike da murna ya yi mata godiya ya mike ya nufi dakinsa dan yin wanka, Tsaye take a tsakiyar gidan tana kallon manyan tantabarun gidan dake kiwo nan balbalin gidan , tana yi tana duba kofa domin ranar juma.a da alhinayet ta zo tace zata dawo ranar lahadi su je gidan kitso Ayya sai fadan kitso take, Kallonta yake daga inda yake tsaye, inda ya shiga takowa a hankali har ya karaso inda take tsaye, ma.ana suka jera, A hankali ta dago da kanta daga kallon tantabarar ta kai dubanta wajensa , nan da nan ta matsa gaba sannan ta sada kanta kasa cikin yanayi na bawa wanda ke kusa girma. Aghali ya ce" a garinku ke yar gidan waye? Agaishat ta dube shi, ta kuma sada kanta, sarkinta ne, ita talakarsa ce, sarkinta ma talakansa ne, dan haka cikin yannayi na girmamawa ta ce" sunnan mahaifina *Ba*, Ba , ai sunnan du uba ne a garin buzaye! Aghali ya fada yana kara tsareta da ido, Agaishat ta ce" ka yi hakuri, Aghali ya ce" baki min laifi ba, Soyaya kike da shi? Kina tunanin zai mutunta ki zai so ki da zuciya daya? Kallonta ta dago wannan karon ta sauke kan nasa,, Bata kai ga bashi amsa ba Wardugu ya shigo da wata galeliyar mota fara kar, kusa da shi Alhinayet ce da ya dauko zai ajiye su wajen kitso wai🤦‍♀, Birki ya ja irin na ka taka baka shiryan nan ba, da bakin gilas dinsa ya dan kale su kafin yake taka motar ya karasa wajen da ya dace a ajiye motar. Yana tsayawa ya kai dubansa wajensu, gani ya yi aghali na magana, yar gidan Ayya kuwa na kallon kasa, kansa ya girgiza kafin ya maida dubansa wajen Alhinayett ya ce" Alhi, Aba ya saka na yi bincike a kansa, yace bai yarda da adinninsa ba , hakan ne kuwa ba musulmi bane yace shi musulmi ne dan ya saje da jama.ar garin nan, Alhinayett ta ce" General ya kuke so na yi ne? Ina zan shiga na samo wanda ya yi 100/100? Wannan na uku kennan yana zuwa da niyar aure abin na watsewa tun kafin a je ko.ina, Wardugu bana son auren Lieutenan na fada maka bana son auren soja. Wardugu ya yi musrmushi yana dubanta ya ce" kuma ki ce ke aminiyata ce, a gabana kina fadin bakya son auren mai sana.ata, me zamu yi maki ne? Me muke yi? Alhinayet ta girgiza kanta ta ce" Wardugu, bana iya zama da namiji mai mugun karfi, ba zan iya rigimar sojoji ba, ba zan iya firirita irin ta matan sojoji ba, ka san ko ni wacece ban iya fada ba, ban iya ihu ba Wardugu ina son namiji mai sanyin hali ne, Wardugu ya ce" ba daga nan take ba, sai ki ga kin auri wanda ba sojan ba kuma ya kasance irin wanda bakya so din, kin gane Alhi ke dai ki yi adu.a , aman na san kina son lieutenant sosai, ke ra.ayinki na ba zaki auri soja ba dan bakya son mai fada, wannan ai shirme ne, ni na fi son ki auri wanda yake na san shi , du ranar da ya taka min ke na nuna masa bashi da wayo! Murmushi ta yi ta kai hannunta suka cafke ta ce" Wardugu, aa fa, ba zaka dakar min miji ba wollah.... Ido ya zaro ya ce" kai, har kin fi son shi da ni? Bakinta ta yatsina tana hararsa da wasa ta ce" oyah bude na gaishe da Ayya mu tafi kar yama ta yi sosai , Idannuwansa ya kai wajen su, nan ya ga Aghali baya wajen aman ita tana tsaye, Cikin hijaban da Alhinayet ta kawo mata ne ta saka milk mai haske, hijabin har kasa yake mai hannaye sannan tamkar zubin riga aka yi masa ya dinku ya yi kyau sosai, ta saka takalminta mai dan tsini kadan da igiyoyinsa ta daure abinta das da ita, Ajiyar zuciya ya sauke ya kai dubansa wajen Alhinayett da ya ga ta tsare shi da ido, sarai ta ga me yake kallo duda ya saka bakin gilas ya tamke kar a gane me yake ciki, Kuma kallon wajen ta yi ta ga Agaishat ta juya wajen kofar falon ayya tana murmushi, Wajen ta mayar da dubanta sai ta ga Mu.azam ne ya fito cikin shigarsa ta shada ya yi shar da shi , daga inda yake tsayen sai turo mata irin abin nan na soyaya yake sai yace Muah, Ita kuwa sai ta rufe ido tana dariya, Tsaki wardugu ya ja ya ce" ji wani shirme kuma? Alhinayett da lumshe idannuwanta, ta ce" na me? Ba wani shirme walahi sai soyaya, Dubanta ya yi kafin ya yi murmushi ya girgiza kansa, motar ya bude ya fita inda itama ta fito, Tafiya ya fara da sauri sauri kamar yanda yake yi kulun, dakatawa ya yi ya dubota ya ce" kuma na saka ya tura magabatansa wajen Aba , Ido ta zaro ta ce" Wardugu, Wardugu, Ina tuni ya yi tafiarsa, Murmushi ta yi itama a fili ta ce" Wardugu zai min auren dole da soja......... Yana zuwa suka gaisa da Mu.azam ya tsare shi da ido ya ce" haka ka koma kan mace? Ka saka yarinya gaba kana abu irin na yara? Mu.azam ya daga girarsa ya ce" kai raba ni amini, soyaya ce, Kai ya dafe yana mai jin matsanancin faduwar gaba, juyawa ya yi ya shige ya barshi nan kar ya hadasa masa hawan jini, Ayya bata falo dan haka ya haye sama dakinta dan ya san Aghali wanka ya shiga ..... Yana zuwa ya gaisheta kamar yanda ya saba sannan ya zauna daf da ita yana dan mamatsa mata kafarta, Ayya ta ce" Mu.azam ya zo min da maganar yana son auren Agaishat, Wardugu dake rike da kafar Ayya yana matsawa sai tsayawa ya yi tsam da matsawar yana duban kasa, Baka ji bane? Ayya ta fada, A hankali ya dago dubansa ya sauke kanta, idannuwansa ya lumshe dan ji yake har kansa ya fara sara masa sanadiyar faduwar gaban da yake ji, me ke damuna? Ya tambayi kansa, me ya sa da an kirayi sunnan yarinyar nan ko na ganta sai na ji faduwar gaba? Kansa kawai ya gyadawa Ayya, Bakinta ta yatsina ta janye kafarta da haushi haushi ta ce" Wardugu bafa na son rainin hankali, ya zan fada maka magana ka wani gyada min kai sai kace inai maka wasiya? Wardugu ya hadiye yawun bakinsa da kyar ya ce" Ayya, wai ya aka yi bakya yiwa sunana kara irin na d'An farin nan? Sai kawai in ji kin kama sunana kai tsaye wai Wardugu, Ido ta zaro tana dubansa yanda ya yi maganar walahi sai ta ji wata kunyarsa ta kamata, ai kuwa ta juya ta dauki filo ta juyo dan buga masa sai gani ta yi ya fice da gudu a dakin, Murmushi ta yi ta ce" ja.iri, ja.iri, ja.iri, ! Zan yi magana da yarinyata , in dai tana son sa, zan baiwa Aghali sako ya je da kansa wajen Mahaifanta idan sun amince ya kai kudin aurenta a daura kawai, Allah ya sa Alhairi ne...... To fa🥴🥴🥴🥴 😎😎😎😎😎😎😎😎😎😎 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣2️⃣ Alhamdulilah Alla kulli halin... A wannan rana bayan Wardugu ya ajiye su agaishat saloon dan yin kitso suka zarce park dinsa tare da samarin, inda Aghali ya zabi daleliyar mota irin ta ratsa rairai mai shegen tsada, Bayan sun gama magana da yaron Wardugu, Mu.azam ya tsaya gurin wata mota mai ruwan ash , karama mai kyan gaske, kallonta yake yana murmushi, Wardugu ya gama da Aghali yace" ku mu je .... Mu.azam ya ce" wardugu, wannan motar nake so, Aghali ya ce" me zaka yi da motar nan kai kuwa? Ta mata ne fa, Mu.azan zai bashi amsa ya ji lumlumlum lema a hancinsa, Da sauri ya juya yana mai ciri hankicin a aljihunsa ya goge jinnin da ya zubo masa ta hanci, a hankali ya karasa motar Wardugu ya bude baya ya shiga ya jinginar da kansa jikin kujera, Ajiyar zuciya yake saukewa yana kara goge jinnin inda wata number ta fara shigowa saman screen dinsa, number saudiya ce, A kasan zuciyarsa ya ji nutsuwa da number dan haka ya daga ya yi shiru ba tare da ya yi magana ba, Ajiyar zuciya ta sauke kafin take share dan guntun hawayenta, so take ta yi magana tana tsoron kar ya ji muryarta ya kashe , ta godewa Allah da da ransa, ta godewa Allah da ya daga wayarta duda bai san ko wacece ba, A hankali ta ce" ina son ka Mu.azam Sai da ya ji wata kasala, a hankali ya dubi screen din, ya mayar kunnensa, ji ya yi wata nutsuwa na kara ratsa shi, a nitse ya ce" docterna, me kika je yi saudiya a tsakiyar shekara? Idannuwanta ta lumshe ta ce" na zo rokar Allah ya baka lafia, ya nuna min jininka a duniya, Murmushi ya yi ya girgiza kai, ya ce" kin ga jini ke zuba a hancina, bayan ina son na yi aure, har na saka a tambaya min auren yar, ina son yarinyar a raina ina son na aureta koda shi kadai zan yi a duniya, Wani irin faduwar gaba ta ji, jikinta ya dauki rawa, a hankali hawaye ya shiga zarya a idannuwanta, a hankali ta ce" zaka aureta, kar ka damu, zaka rayu Mu.azam, Shima idannuwansa nasa ya lumshe yana mai jinta gaba daya jikinsa, yana son yarinyar nan fa tamkar ransa, sai dai ba zai yarda haka ta faru da ita ba, ba zai yarda yana ji yana gani ya tsareta haka ba, ya sani ne idan ya nuna mata eh yana so zata sakawa ranta da zata jima da shi bayan yana ji a jikinsa an kusa zare sauran numfashin da ya ragewa gangar jikinsa, A hankali ya datse kiran inda ya shiga shafa kansa yana mai jin jikinsa ya dauki zafi,, a hankali ya furta Agaishat ki aminta da ni na dan lokaci, ina son ki kema (🙄) Wardugu da kansa ya fitarwa da Aghali motar nan dan baya so a komawa su yi mota daya, yana gama fitar masa da komai ya bashi hannu ya ce" aboki, ka gama da Muhsin ni sauri nake, Amanda aghali ya yi inda ya raka Wardugu da kallo yana ayyana a ransa ko lafia? Wardugu na tafiya yana sake sake a zuciyarsa, yakan tsinci kansa wani sakarai idan ya ganshi gaban wanda yake so a ransa yana cikin wani halin da ba zai iya fitar da shi ba, Motar ya bude ya shiga, a hankali ya juya fuskarsa gefensa ya ga ya lumshe ido tamkar mai barci, Motar ya tayar ya juya a hankali ya nufi saloon din da ya ajiye su Alhinayett Yana zuwa ya yi mata message cewar ta turo masa Agaishat, yana kofa, Ba tare da ta tambayi komai ba ta dubi Agaishat da aka gama yi mata tsararan kitso a kanta mai dan girma girma aka saka wani dan roba a karshen kitson dan kar ya warware , ta mugun yin kyau tace da ita ta je mota wardugu na kiranta, Duda gabanta ya fadi, aman sai ta dake ta mike tana tunannin lafia? Domin yace idan sun gama su yi tafiarsu, wani abu ya faru ne? Bata da amsar da ta fi ta fice a nitse tana mai jin faduwar gaba, Wardugu dake kallonta tunda ta fito, du takunta daya na kayar masa da gaban da bai san na meye ba, ya dai ajiye hakan a matsayin zai shige gaban abinda bai taba shiga ba, zai shiga rayuwarsu ba tare da izininsu ba, zai yi iya yinsa dan faranta ran amininsa, Kare mata kallo yake, a kasan zuciyarsa ya ayanna"""""meye na naci a kan bakar mace? Menene sirin Mu.azam?, Tana kara kusanto motar yana kara dubanta dan so yake sai ya karanto sirin a tare da ita, , Da yake ta gaban motar take nufo motar, kuma Wardugu ne ke tuka motar hakan ya saka idannuwanta sauka cikin nasa, manyan idannuwanta masu ruwan madara da bakin dake tsakiya mai girma wanda ke watso da hasken ruwa ruwa yana sheki , kallon nan mai shige da mai jin bacu shine kallon Agaishat wanda hakan ya samo asali da tun tana karama mahaifinta bata isa ta daga ido ta kale shi ba, sai ta saba da yin kalli a lumshe tamkar zata rufe idon aman kuma ta fi wanda ke kallo tar tar ganni domin wata kibiya ce ke jefo gannin nata har wajen inda ta yi niyar kallo, A hankali ta lumshe idannuwanta wa.inda ta yi niyar cire nata idannuwan a idannuwan Wardugu, domin kuwa tsai kallo na cikin ido sukaiwa juna wanda basu san da haka ba sai fa ta cire nata ya farka ya yi gagawar mayar da dubansa wajen Mu.azam dake jingine da kofar motar, Murya a dake ya ce" malan dan bani waje zan tatauna da yarinyar can, Sai a lokacin Mu.azam ya ga Agaishat ce ke karasowa wajen motarsu , a wannan lokacin har ta karaso sosai jikin motar tana jira a bude mata kanta a kasa, Mu.azam ya kali Wardugu , murya a raunane ya ce" war, kar ka yi min haka , me ta yi? Dan allah kar ka yi mata fada ko ka rikitata, na tuba , Wardugu ya tsare shi da ido yana mai jin wani tsoro a ransa da faduwar gaba, mutun ne shi tamkar kowa, dole abinda zai kayarwa kowa gaba ya kayar masa, sai dai ba zai taba nunawa ba, ba zai taba bari wani ya san halin jin tsoronsa ko faduwar gabansa ba, Da ido ya nunawa Mu.azam ya fice fa, Mu.azam ya turo baki ya bude motar ya fitar da kafa daya ya juyo fa haushi haushi ya ce" idan ka batawa abin kaunana rai , sai na tarar da wannan matar taka na nuna mata waye bos Mu.azam! Wardugu dai bai ce da shi komai ba har ya fita a motar ya tsaya yana kallonta kafin ya bude mata gidan bayan ta shiga motar jikinta a sanyaye ta gyara hijabinta ta kai dubanta Wajen Wardugu, Yana son magana da ita wanda zai fuskanceta, ya sani shi ya dace ya koma baya ko dan saboda gaban ana iya kallon su ta gaba du wanda zai fice, aman wani abu ya tsaya masa ya hana shi fita ya koma bayan motar, Dakewa ya yi , ya ce" dawo gaba. Agaishat dake duban gaban motar ta kai dubanta wajensa, a ranta fadi take" shi koda yaushe fuskarsa ba wani fara.a zai wani tantankewa yake yiwa mutane, to ni me na yi masa ? A hankali ya dago da kansa ya juyo fuskarsa dan bai ji ta motsa dan bin umarninsa ba, Kamar na dazu yanzun ma idannuwansu ne suka sarke da juna, a tare gabansu ya shiga luguden duka , Wannan karin Wardugu kasa cire idannuwansa ya yi a nata , tsai ya tsaya cikin kogin idannuwanta yana mai jinsa baki daya a cikin idon, Da sauri Agaishat ta janye kwayoyin idannuwan nata a nasa ta shiga kokarin bude motar hannayenta na rawa baki daya tana neman nutsuwarta na neman gagararta, Bude motar ta yi ta fita, shakar sansanyar iskar duniyar ta yi kafin ta juya da dukan kuzarinta ta bude gidan gaban ta shiga, Shi kam binta kawai yake da kallon da bai ya kureta da shi har haka ba, sam bai san yanai mata kallon da ya fice ka.ida a adinnance ba, A hankali ta ja ta rufe kofar, aman wannan karon ta gagara dubansa cikin ido kamar yanda shi ya tsareta da idannuwansa wa.inda ta rasa gane me yake kallo, Zuciyarta ke ingizata da ta dube shi, domin bayan ta dawo gaban ma ya yi shiru ne bai ce da ita komai ba, hakan ya saka a hankali ta kuma buda dara daran idannuwanta cikin nasa, Lumshe ido ya yi ya kuma budewa kan fuskarta, haka kawai ya ji baya iya yi mata magana tun karfi ko eani gatsai gatsai, ji yayi yana kokarin sanyaya muryarsa fiye da yanda yake yiwa kowa magana a duniya, girmanta, tausayinta ne ya ji a lokaci guda, yana jin kunyarta wace bai san ko ta meye ba, ya ajiye hakan kan dan tana abar kaunar amininsa, tabas zai ci gaba da jin haka a tare da ita balema idan ta aminta da zuciya daya zata kular masa da amininsa, Sangartar da muryarsa ya ci, marainiya ta zama a makogwaron sa, da kyar ya iya sarafata wajen fadin" *Kina son sa? Zaki rayu da shi?* Ajiyar zuciya ta sauke mai cike da ma.anoni, kanta ta sada a hankali ta ce" *shi ne zabina* Furucinta da faduwar gabansa ba zai tantance wane ya fi wani karfi wajen saka jinnin jikinsa gudu a karfin da ya zarce yanda yake, kirjinsa ke duka da sauri sauri inda ya ji hankalinsa ya tashi, ya rasa menene haka? Me ke faruwa da shi, Dakewa ya yi ya cire hular kansa yana dan alamun fifita da ita, bai daina kallon Agaishat ba, ya ce" zaki iya rayuwa da shi da zuciya daya? Ki so shi domin Allah? Zaki sadaukar da komai na rayuwarki wa shi? Dagowa ta yi ta tsurawa fuskar Wardugu ido, a hankali ta ce" *ka damu da amininka ko ka damu da amanarka?* Bai bata amsa ba, domin bai fahimceta ba, dan haka ta gyara zamanta ta ce" a gida, muna da Anna daya, du yaran gidan yan uwa ne, daga bakin ranar da Anna ta baiwa Ayya ni na zama yar Ayya, hakan na nufin ni kanwarka ce, baba tsofo yace idan iyaye ko yayu kai dangi baki daya zasu yiwa yarinya aure hankalinsu a tashe yake, su ne bincike kan waye mijin? Halaya da sauransu, su ne tabatarwa idan yarinyar na son sa ne domin Allah, kai dai a firgice suke, Dan Allah, *zaka zama yayana?* mai saurare na? Mai share kukana kamar yanda yayuna ke yi? Tunda ta fara labarin lebenta yake kallo tamkar mai koyon yaren da take magana da shi, a hankali ya ringa jinta a jikinsa har ta zagaye ilahirin jikinsa, wani irin nanauyan abu ya ringa ji wanda zaka ji shi ne idan kana son abu, ko dan uwanka ko wani na jikinka sosai , farat daya Wardugu ya ji ya yi kanwa daya kwalin kwal, jal, kwara , wace yake mararin samu, ya jima yana son samun kanwa daga mahaifiyarsa dan ya shagwabata , ya ririta ta, ya sangarta ta, ta fi yar shugaban kasa gata, a yau a yanzu ya aminta da bakuwarsu, ya ji ta zama jikinsu, zai iya cewa ya samu kanwa, zai kare mata duka cuta, zai iya yin fito na fito da koma waye kanta! Agaishat Agaishat kanwa ce a ransa wace yaje jinta tamkar jini daya suka fito, Ji ya yi zai iya sakewa ya yi hira da ita irin ta dan uwantaka, lokaci daya ta shiga kokonta idan ya aura mata mu.azam ya kyauta mata kuwa? Nan da nan zuciyarsa ta kwabe shi ta hanyar tunasar da shi ai komai na Allah ne , . A hankali ya dan jirga jikinsa bangarenta yana dubanta , ya dan saki fuskarsa ba laifi, dan karamin yatsarsa ya miko mata ya ce" zaki zama kanwata? Murmushi mai hade da dariya da farin ciki ta dan yi masa ta ki bashi hannun sai alamu da ta nuna zata hade hannayen nasu ita da shi , Shima murmushi ya sakar mata yana mai nuna alamun dimple dinta har biyu sun shige sosai, A hankali ta ce" yayana, Duda suna ne wanda kowa ke fada, karamin suna, sai da ya ji dadin abin, ya amsa mata da ido, Agaishatt ta ce" *ina son sa!*.................................... I.m back😕😕😕 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣3️⃣ 😕😊😊😊😊😊😊😊 A hankali murmushin fuskar nasa ya bace, shima ya yi kalar serius ya ce" kina son sa? Zaki aure shi? Agaishat ta dan kawar da kanta daga dubansa, ta ce" *eh zan aure shi,* Ajiyar zuciya ya sauke ya wauga bangaren Mu.azam, ya ga yana zaune kasan wata bishiya yana dadana wayar hannunsa, dubansa ya dawo wajen Agaishat, ya dan jima kafin ya ce" *Zan aura maki shi*, Agaishat bata ji wani yannayi na daban game da abinda wardugu ya fada kan aure da za.a yi mata, duda abu ne da take cike da murnar itama zata yi, aure da mutun kamar Mu.azam, itama zata yi rayuwar aure, aman zumudin da farin cikin ba wani can can ba , bata san dalili ba ko fargaba ne ya hanata jin madaukakin farin ciki kan lamarin? Murmushi ta sakar masa ta kai dubanta wajen Acn motar da ya gama kashe mata gabobin jiki dan mugun sanyin sa, Wardugu a hankali ya kai hannun sa wajen ky din motar zai kashe sai kuma ya bari, duban Agaishat ya yi ya ce" mu ga kitson yan matan Ayya? Ai kuwa ya washe baki tana zabga murmushi cike da farin cikin irin yanda ya sauko daga hararanta ya mayar da ita mutun gashi har ya damu da kitsonta take dubansa tana kokarin jan hijabin baya ta bude masa kitson tana fadin" Alhinayett ne tace kar a yi min kananuwa dan kar na wahala sosai, ka san me, kuncewa yake yi fa, Ayya ne taki yarda na daina kitson nan, kuncewa yake yi shi kadai.....ta karashe tana dan turo bakinta irin na shagwababun yaren nan, Murmushin da a yau ya kai sau hudu da ya yi du a gabanta ya kuma sakar mata yana duban kitson har ta rufe , bai san ta ina ba bai san lokacin ba sai ji ya yi ya ce" aa, ki yi ta yin kitson ki, yana yi maki kyau, Tsai ta yi tana dubansa, a ranta fadi take...da gaske ne ko kuwa? Me ke damunsa yake magangannu irin haka yau ne? Bata bashi amsa ba sai lumshe idannuwanta da ta yi ta bude motar tana fadin" Allah ya tsare ka, Da ido ya bita bayan ta bude motar inda yana kallo Mu.azam ya karaso wajenta da sauri yana alamun tambayoyi inda ya hangi ta sakarwa Mu.azam din murmushi bata ce komai ba, daga nan ta juya ta tafi cikin saloon din. Karasowa motar ya yi ya bude gidan gaba ya shiga ya tsare Wardugu da kallo, Wardugu ya tayar da motar ya juya akalarta zuwa gidan Ayya Tafiyar kurame ne suka yi har suka karasa gidan Ayya, suna tsayawa Wardugu ya daga karamar wayarsa ya danna number ya kara a kunne Ana dauka ya ce" ka cira min tiket biyu zuwa agadez yau. Yana gama fada ya katse kiran ya fita a motar shima ya bi bayan Mu.azam Yana shiga dakin Ayya ya zarce direct, yana zuwa ya tarar da ita tana ninke abin shinfidar da ta cire Kama mata ya yi suka ninke sannan ya gyara mata wanda ta shinfidar da kyau ya nemi waje ya zauna ya tsura mata ido, Bakinta ta tabe ta karasa inda yake zaune ta ce" menene? Murmushi ya yi mata yana dubanta ya ce" sai da wani abu d'a zai kali mahaifiyarsa kyakyawa Ayya? Kanta ta girgiza , ta ce" da ace uwar bata san halayen dan nata ba, me ke tafe da kai malan? Wardugu ya yi murmushi kafin yake yannayin magana mai mahinmanci, ya ce" na tambayeta idan tana son sa, amsarta ita ce" *Ina son sa, zan iya zaman aure da shi* , zan je na nema masa aurenta domin shima yana son ta, A hankali ta zauna tana mai yi masa wani irin duba, ta ce" baku da hankali ne? A me kuka dauki kalmar aure? Sai kace wani abin wasa? To ko yar zan baku ai sai da alwalin da zan gindayawa dokoki kan yata bale ni bamu wani yi magana da ita ba, aikin banza gagawar me kuke haka ne? To naki din! Kallonta kawai yake har ta dasa aya tana kawar da kai da yannayin haushi a fuskarta, Murmushi ya yi , a hankali ya ce" Ayya, aure ai tayashi ake ko? Sunnar mazon Allahn salalahu alaihi wa salam din kike cewa baki bada ba? Haba Ayyana, Yatsarta ta nuno masa ta ce" Wardugu ka kiyayeni, ni ban ce ba zan bada kwata kwata ba, aman yannayin yanda kuke maganar ne ya fara bani tsoro, meye na gagawa bayan kun san aikin shedan ce? Sannan yarinyar nan dai amana na dauko daga gidansu, idan wani abin ya sameta ba zan yafewa kaina ba! A hankali ya dawo kusa da Ayya ya zauna, hannunta ya kamo ya rike yana dubanta ya ce" abinda ke sakawa ana jan aure bincike, da halin rayuwa na yau da kulun, Mu.azam namu ne, mun san waye shi, sannan Allah ya hore mana abinda zamu kawo mu nemi auren ko nawa ne, Ayya, bana son mu zurfafa bincike ne, ina so ki yi min lamuni ki duba , ba zan saka kaina a maganar idan na san shirme ne, ba zan tarki tarbenta a haka da garage ba idan na san cutarwa ne wa amanarki, ina iya yiwa aminina alwali, kuma tare da shi zamu tafi namiji alwalin kansa ne, ki taya mu raya sunna da yar ki, kina da damar bibiyar rayuwarta da shi ...idan an yi maki abinda ba shi ba ki raba Ayya kam du jikinta ya yi sanyi, tana dunansa gabanta na faduwa tana ayana lale da kwakearan dalilin da ya saka Wardugu shiga wannan maganar auren, A hankali ta ce" menene? Me ke faruwa ne? Wardugu ya kara sada kansa yana jin yanda zuciyarsa ke bugawa ya ce" alkhairi ne, ki taya mu. Can daman Ayya ba mai musa maganar wardugu bace, hakan ya sa ya yi gagawar shawo kanta kan zasu je garin su Agaishat neman aurenta wa iyayenta......, Bai bar dakin Ayya ba sai da ya tabatar da ya samu kanta ta bada amanarta da dukan yawunta, ta yi fatan alkhairi Haka ya fito ya tisa keyar Mu.azan dake cike da mamakin lamarin sukaiwa Ayya salama suka nufi aeroport dan tafia garin agadasawa su nufi timiya gari mai gawo 🙁 ........sowi kadan ne..... 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣4️⃣ Basu dauki tsahon lokaci a jirgi ba Allah ya sauke su lafia, Direct hotel suka nufa infa Wardugu ya yi kira kan q shirya masa mota da yan tsiraku sojoji zasu je kauyen Timiya, Sai bayan ya yi wanka ya mike saman bed ya danna wayarsa ya danawa hajia Walyn kira yana mai lumshe ido, Daga bangarenta ta daga tana duban agogon dake dakinta, hakimce take ta hada uban maltina tana son kwankwada tana tsoro, ance mata yana zubar da jaririn ciki wai, dan haka ta gyara zama da niyar sha sai ga kiran Wardugu, Dagawa ta yi gabanta na faduwa kar a je ya zo yana nemanta ne, Walyn........ya fada yana mai jan sunnan, Idannuwanta ta lumshe ta kwontar da kanta saman hannun kujerar tana sauraron yanda ya wani ja sunnan har tsakiyar kanta, Bakya neman mijinki wuni guda? Ki ji na ci abinci? Me ke damuna? Da wa na hadu? Karshema inda nake? Ko kin yarda da kanki har haka ne? Walyn ta yi murmushi ta ce" na yarda da kaina ne, Murmushin ya yi shima ya ce" baki da matsala, Kana ina? Ta jefo tambayar Wardugu ya daga kai yana karewa dakin kallo ya ce" ina hotel , a Garin Agadez. Me? Hotel? Agadez? Yaushe ka je? Me ka je yi? Kuma a hotel? Kai da wata yar iskar?, Idannuwanda ya lumshe, a hankali ya dora hannunsa na hagu saman kansa, shafawa yake yana lalabar kansa, shiru ya yi mata wanda hakan ya saka take ta kiran sunnansa da karfi tana fadin ka fada min da wata tsinaniyar kake hotel? Har ka bar gari da gari ka je garin agadez? Me ka je nema? Farin, kyan, ko gashin? Wanene bani da? Ka ban amsa Wardugu, A hankali ya katse kiran da wayar baki daya ya furzar da wata zazafar iska ta kai dubansa wajen Mu.azam da ya yi tsai cike da takaicin matar abokin nasa yana dubansa, mamakin irin rashin hankalin Walyn yake, du yanda wardugu ya kai ga zafin rai yana raga mata, yana matukar kawar da kai a shirmenta, tunda ya zo niger bai ga inda Walyn ta taka kafarta gidan mahaifiyar mijinta dan ta gaisheta, bayan kulun sai ta fice yawo kwararo kwararo,, ga abubuwa na rashin da.a da take shukawa suna zuwa kunnuwansa , sai ta tafkawa talaka rashin mutunci ta yi ikirarin me ka isa ka yi bayan ikon a hanuna yake a matsayina na matar General Wardugu, Karfi da yaji ta saka wasu talakawan na shayin tunkarar iko koda da gaskiyarsu , suna tsoron gawo ya juye da mujiya! Sam halayar Walyn suna bukatar gyara, Bai iya cewa Wardugu komai ba, domin du tsakaninsu basa irin maganar nan, sam Wardugu baya bada fuskar a yi maganar iyalinsa da kowa, idan abu ya ishe shi yakan ja dogon numfashi ya ce" Mata kennan, kwakwaluwarsu irin ta yara ce, Wardugun ma dubansa yake har ya karasa wajen bed yana dana waya ya ce" Wardugu, yanzu kayan buzaye ne zamu nada , kawai kai tamkar diarhee kake idan ka tashi abu yi kake? Bamu wani shirya ba, bamu zo da datijo ba zamu je a bamu aure? Ni dai kar ka ja iyayen yarinyar su hana min Agaishat ba zan jure hakan ba , zan haukace maka ne! Tsuru ya yi masa daga kwoncen yana jin wani iri da maganarsa, wani irin tashi ya yi zaune yana dubansa ya ce" kai zo zauna mu yi magana! Mu.azam na dubansa ya karaso ya zauna yana kara kare masa kallo, Wardugu ya ce" dan tausayi zaka aureta ko dan so domin Allah? Mu.azam ya yatsina fuska ya ce" ina sonta mana, meye a tare da ita na tausayi? Nine ma ai abin a tausayawa, Wardugu ya ce" kana ji, bana son ka yi auren nan da wata manufa, Mu.azam, ba zan jure gannin hawayenta ba koda kai ka jawo shi ranka zai bace, ka kara tunani ! Yana gama fada ya muke ya nufi bayi dan ji yake kamar ya yi ta ihu, sam baya jin dadin duniyar, Yana kasan shower idannuwansa rintse, zuba take da karfin gaske ga ruwan sanyi karara da su, Idannuwansa da sukai ja ya bude ya barsu haka ruwan na shigar masa ido , hanunsa na dama ya jimke ya daki bangon yana wani irin nishi mai nuna tsananin tashin hankalin da yake ciki, A kadan Wardugu ya kai minti arba.in a bayin nan sai da ya saisaita kansa ya kashe gudun showern ya dubi hannunsa da ya daki bango a kala sau uku wajen ya dan tashi abinka da farar fata, Towels ya dauka ya daure jikinsa ya fito ya nufi bed ya kwonta rigingine yana adu.a a cikin ransa Da ido Mu.azan dake saman salaya ya bishi, kansa ya dukar ya ci gaba da jan carbinsa yana tunani barkatai a kasan zuciyarsa.......... Bayan ta gama ibadarta , zuwa ta yi ta hada complet dinta biyu ta saka a jakar computerta, ta duba kudin dake jakarta , ta kuma duba wayarta da passport dinta ta koma bakin dan madaidaicin bed din da take kwana tun zuwanta ta dauki carbinta fari kar ya fito tana mai kuma kiran docter Elisabeth Dagawa ta yi suka gaisa, nan docter Khadija ta yi shiru, Docter Elizabeth ta ce" kina ji, sati biyun nan shi dai kawai na iya sama maki domin kin ga aikinki ya kasance aiki mai daraja, bangaren zuciya bama so koda wasa masu kula da lamarin mu rasa daya koda na minti daya ne, na yi iya yina a haka aka tsaya, dan haka ki hanzarta zuwa niger din ki gama komai kafin likaci ya cika, ni dai fatana ki yi ki dawo da shi mu shiga aikinsa , Kanta kawai take gyadawa , bata san ya zasu kwashe da masoyin nata ba, ta so ta samu lokaci isashe sai dai hakan bai samu ba , zata je da wannan din ma Allah ya sa ya amince. *Timiya* Tunda suka iso suka sauka wsjen baba tsoho suka fada masa abinda ke tafe da su, Baba kam tsufa ya kara rufe shi, bawan Allah daga ringeshe yake binsu da kallonsa domin idannuwansa ramram suke ganni, murya irin na datijai ya ce" na ji dadi na yi farin ciki, aman me zai shaida min da gaskiyar maganarku? Ina mahaifiyar taku? Ina agaishat? Ina alwalin mai neman auren? menene shaidar da zata saka na aminta da ku? Wardugu dake dubansa ya karaso a hankali kusa da shi, kai shi yanzu yana jin nauyin tsohon wanda a da nauyin bai kai haka ba, Yana karasawa ya kama hannun Baba tsoho cikin yaren buzanci ya ce" bamu zo da su ba, sai waya da na dauke su suna magana, mai neman auren Agaishat abokina ne , aminina, shine wannan , ya nuna Mu.azam, ya ci gaba da fadin" Allah ne shaidar mu, shi ne alwalin kansa, idan kuwa ni zaka baiwa amanar yarka zan dauka baba domin ina jinta tamkar kanwata ta jini, Baba tsoho yana dubansa da wani yannayi, a lamarin Agaishat du idan ya yi istihara yakan hango wani duhu kafin ya ga haske, , dubansa yake ta kaiwa kan samarin biyu, Mu.azam da bai sani ba , da kuma Wardugu da ya zubawa ido, ya rasa me ya sa bai ji wani zumudi ba, Bashida ikon hanawa ko sakawa a lamarin agaishat duda shine silar zuwanta da mutanen nan, bai isa ya yanke hukunci ba, sannan idan ba zaka fadi alkhairi ba ka yi shiru, Shiru ya yi ya yi masu jagora inda suka talabe shi sosai suka shiga motar aka nufi gidan Ba Zaune suka same shi kofar gida , ya tisa sansaninsa a gaba yana zaune kan tabarmar kaba yana ta gyara sansanin yana kukulewa da zaren daure abu yana kashi kashi , shi nan sana.a ce ya fara, Da ido ya bisu har suka firfito infa ya hade rai yana hararar baba tsoho Daidai wannan lokacin suka karaso inda sukai masa salama, Wani kallon ya bisu da shi, yana tatare sansaninsa, Wani uabn tsaki ya ja ya ce" ai ko ba.a birne gawarta ba sai na siyar da tabata , ka ga bakin ciki, du ranakun nan baku zo fada min ta mutu ba sai ranar da zan fara sana.a? Ni na san *Bak'a* bata son ci gabana, wato dan ubanta mutuwarma ba zata yi ba sai ranar da zan fara sana.a Baki dayansu dubansa suke, wardugu da tunda gari ya waye jikinsa a mace yake bai iya ce masa komai ba sai sakin baba tsoho da ya yi wajen Mu.azam ya karasa saman tabarmar ya zauna , Hannunsa ya mika wajen sergent, Da sauri ya karaso ya dire wata bakar jaka ya koma wajen da suke tsaitsaye, Bude jakar Wardugu ya yi ya shiga fitar da daurin daurin kudi cefa yan jika goma goma yana direwa gaban Ba, Du daurin nan million guda na cefa ne, sai da ya dire ashirin wanda zuwa lokacin Ba sai zufa yake jikinsa na rawa yana fitar da harshe tamkar kare shi ya ga kudi, Wardugu ya ce" bata mutu ba, da ranta da lafiarta, aurenta zaka bamu, ga gudin auren nan idan kuwa sun yi kadan a karo! Domin *Darajarta* ta fi karfin a yi cinikinta! Ta fi karfin a aureta dan kudi, *Agaishat* na da daraja a idannuna! Gaba daya dubansa suke, magana ne yake daga zuciyarsa, fuskarsa ta nuna wani yannayi mai wuyar fasara, ba zai iya jure wulakancin Ba a wannan halin ba, sannan ba zai iya biye masa su yi ba dadi ba ko dan albarkacin haihuwar Agaishat da ya yi, Wani irin rawa jikinsa yake, auren bak'a da sadakin da ba.a taba bashi ba na sauran yayansa? Wani irin zama ya gyara yana fadin" ai kawai a matso a daura domin kuwa ya shirya, ba ruwansa da tambayar da wa za.a daura, ina take? Tana so? Ina zata zauna? Waima da ranta? Jiki na rawa Ba ya umarci baba tsofo ya yi alwalin Agaishat inda nan da nan sarki ya karaso da jama.ar anguwa ana ta yaba sadaki (kar abin ya baku mamaki ko ya girgiza ku, na gani da idanuwa sadakin buzuwa million arba.in na kudin nigeria bama niger ba, ana amsan karamin sadaki kamar jika hamsin aman yawanci auren garinmu kama daga agadez da kauyukan bugaje ana kashe kudi na mamaki wanda ba.a dauki hakan a matsayin laifi ko wani almubazaranci ba,), A wannan rana , gaban duban shaidu, Mu.azam ya zama alwalin kansa inda Baba tsoho ya zama na agaishat, aka daura auren Mu.azam da Agaishat bisa sadaki mai tsoka lakadan, Sai bayan an gama daura aure Ba ya tatare kudin nan jiki na rawa ya zube a cikin rawaninsa ya daure, bai wani tsaya ya bi ta kansu ba ya yiwa gidan tsinke sai washe baki yake yana ihun kiran sunnan Anna inda ya yi fatali da sansanin, Da amarya ya fara cin karo sai murkashi take ymtana rauda kai domin cikin nata mai matukar bata wahala ne, tana ta fama da kanta du ta lalace, Tsayuwa ya yi ya tofa mata yawu a fuska ya ce" ke kadarara, jeki na sake ki! Daidai lokacin da Anna ta fito tana dubansa sai kiranta yake yana kashe murya irin za.a tuna da din nan, Yana karasowa ya ce" ashe *Agaishat alkhairi ce?* Da mamaki take dubansa tana jiran karin bayani, Agaishat kuma? Ita tana tunanin rabonsa da ya kama sunnanna da daraja haka tun rada mata shi da ya yi, me ke faruwa? Ina yarta ? Innalilahi wa ina ilaihi raj.une, sam bata daukan fara.ar Ba a alkhairi, hakan ya sa ta fito da sauri ta yi waje ko zata ga Agaishat din Baba tsoho ta tarar yana yiwa Wardugu magana kansa a sade yana sauraronsa inda jikinsa ke fitar da hucin zafi gaba daya bashinda laka tamkar wanda ruwa ya daka zazabi ya rufe shi, zuciyarda kuwa ba dadi, dandannon bakinsa daci firit, sam baya jin dadin yannayin ranar nan. Tana zuwa ta tsuguna infa suke, Muryarta na rawa cikin yaren buzanci ta ce" me ya same ta? Idannuwansa ya dago ya sauke kan fuskar Anna, duda turkudi ya rine mata fata ba wani kula take samu ba, aman idan kana neman ainahin kyau, tsararan kyau ka ja ka tsaya wajen Anna, Agaishat kama take da ita sai dai hasken fata da ya bambanta, yaren tubanci ya juye da shi inda ya shaida mata komai cikin nutsuwa da sada kai da girmamawa, Kunyarsa ce ta kamata, har ta hanata yi masa wata tambaya, Kanta ta sada bayan ta hangi Mu.azam dake tsaye ya rungume hannayensa yana kallonsu ta kawar da dubanta ta mayar wajen Wardugu, Muryarta a nitse ta ce" *kar ka damu da bani hakuri d'ana, na saba da gannin auren yayana a wulakancema bale ita nata kun mutunta, ai dama halal malak na baiwa Ayya Agaishat, koda a can kuka daura mata aure bani da ja, fatana zaku ci gaba da riketa da amana, sannan ba sai ka kawota ba, ka barta a can kawai bara na kawo maka sako ka bata, ka fada mata Ayya uwa ce a wajenta, ta yi mata biyaya!* Asalamu alaikum, Rayuwa ce da aka yi nake bi maku, duda na rufe abu dayawa, na kuma gyara wani dan labarina ya yi ma.ana, aman kar ku manta rayuwar nan an yita, kuma a gidan bak'a akoy Alhinayett dake yayata uba daya, team Mu.azam da Wardugu,,.....ku biyoni sanu zamu ji meye sirin, sanu zamu yi murmushi😍😍😍😍😅😅😅😅😅 Hhhh yau kam na cika da yawa😕😕😕😕 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣5️⃣ Yana kallonta ta shige bata jima sosai ba ta fito da yayun Agaishat, inda Mariama ta hade rai tamkar ta zunduma ihu dan bacin rai, Sai dai suna zuwa wajen Wardugu ta ji ba zata iya yi masa wulakanci ko kashedi ba, dan haka ta sada kanta ta ce " Amana kanwata, Kalonsu kawai yake har suka koma inda Anna ta bashi wani zani a kule wanda bai san ko menene ba, Kamar bashi da laka haka ya mike jiki a sake inda su Mu.azam suka kama baba tsoho suka saka shi a motar suka dauki hanya, Mu.azam na lure da yannayin Wardugu, inda gabansa ya yi ta faduwa kan lamarin, tambayoyi me cike da zuciyarsa *Me ke damun Wardugu? Me ke adabarsa haka? Bashi da lafia ne? Me ya fauke murmushinsa?* Sai dai bashida mai bashi amsoshin tambayoyinsa domin rabinsa da jin muryar wardugu tunda suka baro kofar Baba tsofo inda baba ya baiwa Wardugu wani kuli a baiwa Agaishat shima harda carbi fari ya shaida masa cewa ya fada mata bata da gata sai na Allah. Rike yake kamkam da sakon Baba da Anna, carbin kuwa sai ja yake yana duban hanya har suka karaso garin Agadez, Fir Wardugu yace qi sai dai su tashi a jirgin sojoji , inda nan da nan aka taso daga garin niamey aka zo Agadez aka dauke su su biyu tal aka juya da su duka a cikin awowi hudu har jirgin ya sauke su inda dare ya fara tsalawa, Tunda ya fito a jirgin ya daga kansa sama, garin niamey da yannayin zafi hakan ya sa ya fara jin har kamar ya cire rigar nan ya yar, Dubansa ya kai wajen Mu.azam ya kirkiro murmushi ya ce" zan karasa gida, zamu hadu gobe in sha Allah, Mu.azam ya amsa shi da kai yana kallonsa har ya bace masa da gani, Wardugunsa ne ya juye haka lokaci daya? Hannayensa ya dora saman kansa ya furta" innalilahi wa ina ilaihi raj.une, me na aikata haka? Na kutsa wajen da ba nawa bane ko me? Da sauri ya kawar da zacen nan ya nufi wajen da ya tabata ba za.a rasa motar wardugu ba dan yawan tafiye tafiyensa yakan zo da mota ya bari a aeroport, Yelemun kuwa ya samu ya shiga ya tayar ya nufi gidan Ayya ransa cike da tunani, Wardugu bai zame ko.ina ba sai kofar gudan su Alhinayett A lokacin karfe goma na dare ya kusa, anguwar ana dan kai kawo domin ba laifi suma anguwar yan gayu ce, manyan yan mata da samari sai kai kawo suke suna bada kala. Wayarsa ya danna mata kira, tana dagawa ya ce" ina kofa, Da sauri ta mike ta daga labulen tagarta, hango mutun ta yi duke a kofar gidansu, Da sauri ta fito da zumbulelen hijabinta infa kanwarta dake kusa da ita ta nace ita sai ta bita, Dubanta ta yi da kyau ta ce" *Tghmass*, wajen yaya Wardugu ne fa? Thgmass ta turo baki ta koma saman bed tana kunkunnin je ki, ba zan biki ba ya yi min muhunta wannan katoton da bai san yara ba! Murmushi ta yi ta fice da sauri ta fito ta karasa da sauri tana fadin" Wardugu lafia? Me ke damunka? Me ya faru? Baka taba zuwa gidan nan a wannan lokacin ba, menene? Wani ne ba lafia? Wardugu ya dago kansa daga duken ya kamo hannunta na dama murya a dake ya ce" Alhinayett, zuciyata ke min ciwo, ina jina tamkar zan mutu, ina jin dari sosai, na kasa tabuka komai, ina jin tamkar na rasa wani baban abu a rayuwana, ina jin iskar duniya ta yiwa kofofin hancina kadan, ji nake tamkar jikina na gasuwa da wani irin azabeben zafi da sanyi, ina jin jikina ya yi min nauyi, Alhinayett me ke damuna? Menene wannan? Ban taba jin wannan abin ba, mutuwa zan yi! Da sauri ta dafe kirjinta gabanta na bugawa, A hankali ta duka inda yake ta ce" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Wardugu baka da lafia ne? Jikinka zafi, ka je asibiti ne? Daga ina kake yanzu? Ayya ke ce min ka je Garin su Agaishat nemawa Mu.azam aurenta, ko ka yi gamo ne? Bara na kira Abanmu, Kokarin tashi take ya riko hannunta ta dawo gwarab kusa da shi tana share hawayen amininta yayanta a wani hali, a firgice ta kuma fadin" ka bari na tado abanmu ya baka magani ya yi maka turare ko ka yi gamo da wani mugun ne Wardugu Wardugu ya ce" bana tunanin hayaki, tashin hankali, likita, kudina, ko mulkina zasu warkar da ni, tabas zuciyata sakara ce banza ce da take da gagawar yanke hukunci, ke kin fi kowani makusancina saurarata , na zo ne dan nima yau ki saurareni kamar yanda nake sauraronki, Alhinayett, a yau da inada mace nutsatsiya da na kwontar da kaina saman cinyarta ta taya ni saisaita bugun numfashina, Alhinayett halayen Walyn na tayar min da hankali, ina sane, ina hankalce, kawar da kai ne nake dan ta kula da kanta ta gyara, Alhinayett nima mutun ne, kuma inada rauni fa, ina da zuciya, ita a kulun hirarta da ni tuhume tuhume da zargi ne, a jiya jifana ta yi da maganar wai ina tare da watatsinaniyar? Ni ba mashayi ba, ni ba mazinaci ba, aman ta ki godewa Allah sai fata take yiwa kanta? Yau da zinar nake ta isa ta hana ko ta yi wani abin? *Wani lokacin nakan dauki niyar zuwa na yin na ga sai me?* (hatara mata, walahi yawancin lokuta mu ke jawowa kanmu masifa da bakinmu da banzan tunanin mu), sai dai har yanzu ban aikatan ba, Alhinayett sauraronsa take cike da yannayin tashin hankali, ko me ya firgita mata Wardugu ba karami bane, meye shi da yace ba zai iya masa ba? Ya fi karfinsa? Meye wannan? Gashi ya hanata kiran Aba, Sai da ya gama ya ce" ki daina kuka, yau nima na yi jajen abinda ke raina ne. Alhinayett ta ce" me ka fada bayan komai a dunkuke ka fada Wardugu? Me ke damunka a ranka? Tsai ya yi yana tambayar kansa takamaiman damuwarsa har haka? Kan matar wani ko me? Da sauri ya mike ya mikar da ita ya jata har kofar gidansu ya tura ya turata ya ce" asuba alkhairi Alhi........, A wannan rana Wardugu ya ga dare tamkar rana, ya kwana bautawa allah inda ya roke shi yafiya da nutsuwar zuciya, kuma alhamdulilah ya samu nutsuwar harma ya kwonta da safe bayan ya gama salar asuba ya samu baci Gidan Ayya, Kallon Mu.azam take kafin ta ce" aa, toh shi wardugun ya aka yi baku zo tare ba? Mu.azam yaushe abokinka zai yi hankali? Ina wayar da na ce ku dauko min komai? Sai a lokacin ya tina ya mike da sauri ya je dakinsa ya dauko wayar wajen Ayya da ta basu lale lale su dawo mata da dauka, Yana zuwa ya kunna mata ya mika mata inda ta tsurawa komai ido tana kallo har karshe domin daya daga cikin yaran wardugu ya dauko komai, Baya ta maido kadan tana duban yannayin wardugu, Kanta ta dago da niyar yin magana ta hango Agaishat ta farka tana saukowa a hankali, kanta na duban kasa, hankalinta a yannayin tashe, kayan bacinta ne jikinta dogon wando sakake da riga budadiya, kitson kanta cikin hula baka, a hankali ta sauko ta dago idannuwanta ta sauke kan Ayya, Kuka ta fashe da shi ta karasa da gudu jikin Ayya tana ta shesheka Hankali tashe Ayya ke bubuga bayanta ta ce" me ke damun ki? Lafia? Y'ata menene? Agaishat ta kankame jikin Ayya ta ce" Ayya, mugun mafarki na yi, wai wuta na cin gidanmu, Aya gobara a gidanmu, an yi an yi da Anna ta fito ta kiya tana jira sai Ba ya bata umarni domin bata fita sai da umarninsa , shi kuwa ya tsaya yana ta dariya ya ki bata umarnin! Ayya tana shafa kanta ta ce" mafarki ne fa Agaishana, mafarki ne, ki kwontar da hankalinki, kin ga jiya su Wardugu sun je din , an gama komai kuma harma Mu.azam yace da sakonki da Annarki ta bayar a kawo maki, Gabanta ne ya yanke ya fadi, an gama komai? Kennan yanzu ita ta zama matar aure? Ta zama matar wani? Ta zama sa yi hani bari? A hankali ta dago da dubanta ta kai wajen Mu.azam, Ido ta tsura masa kamar yanda ya tsura mata, Murmushi ya sakar mata yana dubanta kafin yake karasowa dan kusa da su kadan ya ce" Anna lafiarta kalau, hakama su Mariama, du sun fito mun gaisa, baba tsofo yace a gaishe ki, du suna nan kalau, Maimakun ta bashi amsa sai ta mayar da kanta jikin Ayya ta lafe tamkar mage, sannan ta lumshe idannuwanta gamgam Da ido Ayya ta yi masa magana tana murmushi tana shafa kan Agaishat inda ya mike jiki ba karfi ya nufi tsakar gida. Karfe shida na yama jirgi ya ajiye su, inda fito bakin titi ta tsaya tana kallon yanda motoci ke ficewa, Tsarin garin ya yi mata ba dati ga kyau. Taxi ta tsayar, don ta san ba wanda ya kai dan taxi sannin gari, ta san garin akoy tsaro, sannan ta san da wuya a samu wanda bai sani ba, Tana tsayar da shi ta ce" *Gidan Elhaj Wardugu Marahut nake so ka kai ni* Juyowa ya yi yana dubanta ya ce" gidan su ko gidansa? Tsai ta yi ta tuna yace mata idan ya zo wajen Ayya yake sauka, fan haka ta ce " *gidan sa* domin tana son fara magana da shi kafin ta je ga Mu.azam! To fa fans, shin bata san walyn ba? Ya kuke hangen wannan cakwakiyar? Ga kari😕 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣6️⃣ Tafia mai nisa suka yi kafin ya dangana da tankamemen kofar gidan wardugu, Kamar kowani gidan baban iko , kofar gidansa sojoji ne ke gadi wa.inda suka canji wasu, Can gefe katuwar motarsu ce ta iko, sunna dan hira tsakanninsu lokaci zuwa lokaci kuma suna kule da aikinsu yanda ya kamata, Tana sauka ta biya mai taxi ya juya inda ta nufi wajen sojojin . Kamar yanda suke kallonta haka itama ke kallon su, har ta karasa dan kusa da su Daya daga cikinsu ne ya yi mata tambayar wa take nema a nan? Amsa ta bashi gamshashiya ta kuma nuna masa carte dinta shaidar ko ita wacece din, Waya ya dauka ya yi kiran layin ogan, Ya jima yana ringin kafin ya daga, Yana dagawa ya kora masa bayani, Wardugu dake bacin gajiya ya bada umarnin a sayota a gwada mata part din Walyn su hadu a can. Mikewa ya yi ya shiga wanka, bai wani jima ba ya fito da alwalarsa ya tayar da sallah ya yi ramuea domin wani nanauyan baci ne mai wahala sosai ya yi, Yana gamawa ya bi ta dayar kofar ya fice dan nufan bangaren Walyn wace ya gama tunanin kar a je tana can tana zuba hauka! Maradin Walyn baya kunya, Yana tura kofarta ya tarar da bakuwar tsaye rike da jaka tana kallon kasa, jikinta da bakar abaya doguwa ta yane kanta da mayafin Abayar, Walyn kuwa na zaune saman kujera ta dora kafa daya kan daya tana kadawa ta turo daurin dan kwalinta gaba tana kaskaskas da cingan Salama ya yi mata yana duban Walyn, kafin yake fadin bismillah zauna mana ga kujera, A hankali ta karasa wajen da ya nuna mata ta zauna tana mai duban Walyn, Gaisawa suka yi cikin mutunta junna, kafin ya yi shiru yana sauraronta Gyaran murya ta yi ta ce" Wardugu sunana Nana khadija Canel Noor, muna tare da Mu.azam ne a can wajen aikinsa inda yake aiki can muka hadu, akoy shakuwa tsakanina da shi mai girman gaske , na biyo..... Bata kai ga karasa maganar ba walyn ta bushe da dariya tana dubanta, Hannunta ta nuno mata ta ce" halan saurayinki ne? Da mamaki take duban Walyn, ashe tana jin french? Da ta zo ba yanda bata yi ba Walyn ta fahimci maganarta aman ta juye yaren tubanci ta yi ta dura mata zagi da hannayenta kuwa ta nuna bata san yarenta ba, sannan ta daure fuska ta tsare gida ta jefa cingan a bakinta tana taunawa tana kada kafa tana chating. Walyn bata yi kasa da gwuiwa ba ta ce" wace irin shakuwa ce tsakanin mace da namiji? Ke jiya fa aka daura masa aure, jiya suka je suka dauro aurensa, Walyn! Wardugu ya fada da kakausar murya wace ta saka ta yi shiru tana binsa da kallo sai kikifta ido take uwa ta yi karya, Kansa ya juya ya ce" ki je dakinki, Baki ta turo gaba ta mike ta yi wata girgiza ta juya ta nufi dakinta tana rauda jiki ita matar general, Tunda ta fadi maganar nan, jikin Khadija ya mutu, ta sada kanta kasa, hankalinta ya gama tashi, innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, shine abinda take ta fada a ranta, kuka take so ta yi aman ya ki zuwa, Wardugu da ya dago ya yi mata kallo daya ya kawar da kansa ya ce" desoler (Sorry), Wani abin ta hadiye da kyar kafin ta ce" ko ka san da bashi da lafia? Wardugu ya rintse idannuwansa, ya gyada mata kai, Ta tatara dukan kuzarinta ta ce" Wardugu, ana iya yi masa aiki, tabas aikin na da mugun hatsari aman idan Allah ya nufa sai ka ga an dace, ana tashi sosai, wa.inda nasu ya yi mugun tsanani ma sun tashi , ka taimakeni ka saka baki ya biyoni mu je a yi masa aikin nan, bana tunanin idan ya mace a haka zan iya wata rayuwa, Wardugu ka taimake ni, Menene tsakaninki da shi mai girma haka? Excuse moi (excuse me), kina magana ne tamkar rayuwarsa na tafe da taki, na san ki, ya min maganarki a matsayin kawa, kawance ne ko da wata maganar? Wardugu ya fada , bai yi niyar yi mata wani kwakwaf ba, aman yannayinta ya tsorata shi, kar dai Mu.azan nada wata ya zo ya auri Agaishat? Khadija ta sada kanta kasa ta ce" ni ke binsa yana guje min, ya fada mij zai yi aure, kennan dai auren ya yi? Meye laifina dan Allah ya dora min soyayarsa? Bani da ja da aurensa, bani da damuwa da matarsa, ni dai burina a yi masa aikin nan, idan da rabo ya samu tsayin rai, Mikewa Wardugu ya yi, ya dubu wajen Tv din Walyn, kys din motarta ya dauka ya yiwa Khadija alama da su je, Mikewa ta yi itama gabanta na faduwa, bayansa ta bi tana tunanin ya zasu kwashe da Mu.azam? Ya zata tsinci kanta idan ta gane shi da wata? Adu.a kawai take a kasan zuciyarta, sannan miskilancin Wardugu ya sakata shiga tatayinta sosai, Gudu yake na balaki, jalabiyar nan ta jikinsa baka wace ta mahaukacin haska fatar jikinsa itace a jikin nasa bai canza ba, sai gajeran wandondake kasa, daga su ko yannayin gashinsa bai caje ba, fuskarsa fayau da ita ta bada wani ni.imtacen kyau du kuwa da irin yanda ya hade ta. Da garajen dai ya danna cikin gidan Ayya inda ya fito da tarin balaki ya nufi wajen mai gadi domin ya bar kofar a bude, (za.a dai sauke masa fushi ne) Nemansa yake bai ganshi ba, hakan ya sa ya dawo wajen motar inda take tsaye tana duban ikon Allah, Tun shigowarsu Mu.azam yake kallonsu, domin yana kasan inuwar tsakar gidan Ayya yana ta tunanin rashin gannin Wardugu da yanda Agaishat ta kaurace masa kwata kwata bai ga fara.arta ba, danma tun dazu Alhinayett ta zo wajenta. Baii ga fuskar Khadija ba domin ta dayan bangaren ta fito kuma ta ba inda yake baya sai lokacin da Wardugu ya karaso ya yi mata nuni da bayanta ba tare da yace da ita ci kanki ba Juyawa ta yi, inda likaci daya Mu.azam ya mike tsaye yana zaro ido, Da sauri ta nufi wajensa inda shima ya tako suka hade tsakiya suna yiwa juna wani kallo mai wuyar fasara, Hannunsa ya kai fuskarta ya shiga share mata hawayen da suka fara zaryo mata a fuskarta suna masu yiwa juna murmushi..... Alhinayett ce ta fara fitowa, inda hankalinta ke kan Agaishat dake biye da ita suna hira harda dariya domin Agaishat ce ke fadin" ashe itama zata ga ranar da za.a ce ta yi saurayi wai harda aure? Ashe yan birni ba haka suke ba? A kauye bata taba tunanin ko mahaukacin kauye zai kulata ba, Dif ta yi da maganar inda idannuwanta suka sauka kan Mu.azam da wata kyakyawar mata fara kar , jikinsu tamkar zai hade, sannan sai shafa fuskarta yake kamar mai rarashinta,, Sanye Agaishat take da atampa an yi mata dinkin riga da sket, dinkin zamani ne ya mugun karbar jikinta ga dauri da Ayya da kanta ta caka mata mai shegen kyau, Fuskarta ba wata kwaliya sai dan jan baki mai ruwan atampar sai annurin amarci domin amarya ko ta daji ce tana fita daban, Sosai take fitar da kamshi mai nutsar da zuciya, annuri na fita a fuskarta, idan ta yi murmushi kuwa kaima zaka tsinci kanka da yi ne dan irin murmushinsu ke saka murmushi, Idannuwanta dara dara da su sun sha kwali, dogon hancinta ya sauka kusa da dan madaidaicin bakinta mai lebe masu santsi da kyali domin kida yaushe tana amfani da rob san gyaran bushewar lebe da saka su laushi da kyali, A hankali ya dora hannayensa duka biyu saman motar ya dora kansa ya tsura mata ido, Wani abin ya fargar da shi inda ya yi saurin watsakewa ya juya da sauri ya nufi wajen garden, Sai a lokacin Mu.azam ya ankara da su Agaishat, shi din ma gabansa ne ya fadi, inda har ya ji kafarsa na dan rawa, aman ya dake ya kama hannun Khadija suka suka nufi wajen su Agaishat........ 👏🏻 🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ 4️⃣7️⃣ Yana karasawa ya dan fara kame kame yana dan susar kai, da kyar ya iya sakin murmushi yana duban Agaishat ya ce" wife, ga Khadija, khadija ga matata. Kanta ta juyo daga duban su Agaishat ta sauke kwayar idannuwanta cikin nasa, wanda ya ki bari su hada idon ya kawar da nasa wajen Agasihat wace itama su kawai take kallo inda ta ji wani irin faduwar gaba, Khadija ta yi iya yinta ta karasa kusa da Agaishat da Alhinayett ta mika masu hannu tana sakin murmushin yake ta ce" asalamu alaikum, Hannu Alhinayett ta fara bata tana mai amsa salamarta suka gaisa, hakama Agaishat wace Khadija ta ji hannunta wani irin laushi (toh ba dole ba, tunda ta zo Ayya ke tsaye kan du wata gaba ta jikinta , jiki kuwa na samun gyara nan da nan yake hadewa ya yi cas), ta yi mamakin irin kaushin hannunta duda ta tarar da ita a gidan su Wardugu, Daga nan dugunzuma suka yi cikin falon Ayya inda Agaishat ta haye dan kanta ke sara mata, ita ta kasa gane wacece kuma tare da mijin da aka aura mata jiya? Sai a lokacin ta mike zaune daga saman bed dinta ta nufi wajen window ta daga labule dan gannin ina ya je? Ina ya tafi ne? Ta ganshi harma sun yi ido hudu inda ta yi masa murmushi shi kuwa ya hade fuska, daga nan bata san ina ya nufa ba, aman motarsa na nan wajen hakan na nufin yana gidan. Tunda ya je ya ja ya tsaya waje guda yana duban yanda lambun yake da irin sanyayan sanyin dake tashi a ciki ya afka tunani, tambaya daya ya yiwa kansa wace ta saka kansa sarawa, idannuwansa ya lumshe ya dubi hannunsa a ransa ya shiga yiwa kansa fada kamar haka" ba kanka farau ba, da yawa sun rasa sun ci gaba da rayuwa, dole ya girgizaka domin kaima mutun ne mai rai da lafia mai zuciya mai motsi, aman kuna yarda da wannan jarabawa zai kara daukaka darajarka a wajen ubangijinka, kai ba kowa bane face dan adam da Allah subahanahu wata ala kan jarabta a rayuwar yau da kulun, dan ka shiga hali na jarabawar rayuwa ka aminta shine cika namiji, Murmushi mai ciwo ya yi a fili ya ce" Wardugu, ? Kana bata time dinka bayan wannan baya cikin tsarin rayuwarka! ........ Zai ci gaba da yiwa kansa magana yar wayar da baima yi tunanin ya dauko ba ta dauki tsuwa a hankali tana kidan nan na sojoji tamkar ana harba bindiga, Shiru ya yi da maganar ya tamke fuska bai dauki wayar ba , bai kuma ci gaba da magangannun da yake ba, Ya kai sau biyar ana kiran wayar dan haka ya saka hannunsa ya cirota ya duba sunnan, WALYN, Dagawa ya yi ya kara a kunnensa yana sauraro, Asalamu alaikum General, docter Sagir Sulaiman ne, an kawo matarka emergency minti sha biyar da suka shige ne, yanzu da muka dan daidaita lamarin ne ta bamu wayar dan mu yi kiranka, A dake ya ce" wani asibiti? Likitan ya ce" dan clinique dan gawo ne domin a inda ta samu hatsarin nan ne mafi kusanci da ita. Katse kiran ya yi bai bashi amsa ba ya saka hannunsa cikin gashin kansa ya yamutsa , Juyawa ya yi da tafiyarsa mai kama da yana sauri aman a gadarance ya nufi cikin gidansu wajen Ayya, Tunda ya nufo wajen ta tsura masa ido, kallonsa take tana murmushin da bata san na meye ba, Dan yatsanta ta nuna inda yake zuwa ta ce" ban taba gannin mutun mai rihima irin dan Ayya ba, ya san kan rigima, ko dan Allah ya bashi dama ne? Wannan mutumen idan kokowa ta hadaka da shi ba zan so ganninka a karshe ba, Dan bakinta ta murguda ta ce" ke Agaishat kin manta karfi daga zuciya ne? Juyawa ta yi wajen madubi tana kallon kanta, a fili ta ce" nima mai karfi ce! Yana shiga falon ya tarar da su Mu.azam da Ayya da Khadija dake zaune zuru Ayya fuskarta a dan hade ba kamar kowani lokaci ba, Tana ganninsa ta bala masa harara ta kauda kanta, Murmushi ya yi a fili ya zauna yana duban Alhinayett dake son karantar yanayinsa, ya maida dubansa wajen Mu.azam, Murmushi ya sakar masa sannan da ido ya yi masa maganar da shi kawai ya gane, Mikewa ya yi ya bi bayan Ayya da ta mike ta yi sama dan ya san tana son ganinsa ne aman ba zata fada ba a gaban mutane Yana shiga ta mike da zafi zafi tamkar zata wanke shi da mari ta ja tunga gabansa ta ce" kai! , kai! Ka fita a idona na rufe! Kai Wardugu na fika danyen kai, yanzu dan raini ka zo na baka damar zuwa daurowa yarinya aure ka dawo dan bahagumen tunani ba zaka zo ka fada min ya aka yi ba? Sannan yau ya shigo min da zankadediyar budurwa ya fada min aminiyarsa ce? Ohk tare kuke amintar kai da shi da yan matan ko? Ba zai yiwu ba, ba zan bashi y'ata a wannan halin ya je min da ita wata uwa duniyar ba, ba zan lamunci ya dauki y'ar amana ya tafi nesa da ita ba, wannan yarinyar tamkar marainiya take nesa da iyayenta, nice uwarta nice ubanta, kuma ina son abina, Wardugu ba zan lamunci shashancin nan ba! A hankali ya ja hannunta har bakin gado ya zaunar da ita, idannuwansa sun kade sun masa ja, ya kamo hannun nata ya ce" *Ayya, a cikin gidan duniya, lungu lungu, ba inda kafata ba zata shigaba dan gannin halin da take ciki, ba zan lamunci ko kuda ya yi mata ilah ba!* Da mamaki take dubansa, yannayin yanda ya yi maganar har wata jijiya a gaban goshinsa take motsawa irin magana ne yake da zuciyarsa da gangar jikinsa, Mikewa ya yi ya yi taku biyu zuwa uku ya dawo yana mai yamutsa gashin kansa ya zauna ya ce" Mu.azam bashi da lafia, wannan aminiyarsa ce mafi kusanci da shi, ta zo min da maganar tana so a yi masa aiki wanda idan Allah ya taimake mu aka dace zai tashi, Ayya na roke ki, ki saki ranki, ki yiwa dukan lamarinnan kyakyawan gani, ki bashi matarsa su tafi, Galala take dubansa har ya karasa maganar ya mike ya nufi fita, Kuma juyowa ya yi ya ce" Walyn ce ta ba lafia, zan je clinik Damuwarta ta nuna da yi masa adu.a, taso ma binsa aman ya nuna ta yi zamanta dan yayi imanin in dai Walyn na cikin hayacinta sai ta batawa mahaifiyarsa duda tana boyewa shi ai ba makaho bane, Yana fitowa ya tsurawa kofar Agaishat ido, wani abin na tunzura shi ya je wani na hana shi, A hankali ya taka ya je kofar dakin ya tsaya, Hannunsa ya dora saman abin budewar ya lumshe ido, Da sauri ya saki ya juya sai dai me Alhinayett ce tsaye, bai san lokacin da ta hayo ba, bai san ko tun fitowarsa take wajen ba, idannuwansa sun rufe, Hade fuska ya yi tam irin karma ta ga fuska ta kawo masa raini, Rabata ya yi ya fice ya sauka kasa inda ta bi shi da wani irin kallo, Hannayenta biyu ta dora saman kanta, ta shiga girgiza kai da yaren buzanci ta ce" na shiga uku Nauyin baki ya saka aminina tafka barna, Wardugu me ka aikata haka? Tura kofar Agaishat ta yi ta shiga da salama, Agaishat dake kwonce saman bed ta mirgino tana amsawa da murmushi shinfide a fuskarta tana duban Alhinayett, A nitse Alhinayett ta karasa kusa da Agaishat inda ta mike zaune tana duban yannayinta, Hannayenta Alhinayett ta kamo tana dubanta cikin yaren buzanci ta ce" Tarhanine (masoyiya), ina son mu yi magana da ke. Agaishat ta bata hankalinta sosai , Alhinayett ta ce" ban taba aure ba, aman a islamiya an fada mana irin girma da darajar aure da kuma girman ikon miji a kan mata, Sunna ce ta ma.aiki, daga lokacin da aka daura aurenki maganar mijinku ta fi iko kanki fiye da ta iyayenki, kin ga kuwa banban nauyi ne da bawa zai kasa rintsawa idan ya tuna, A yanzu ba maganar kina sonsa ko bakya sonsa, ba maganar ke wata ce ko wani ya tsaya maki, in dai mace na tsoron haduwarta da ubangiji to ya zama dole ta gane itace karama mijinta ne baba, ta yi masa biyaya. Agaishat, ki yiwa Mu.azam biyaya, kin samu tarbiya domin zaman da nayi da ke na dan lokaci jifa jifa ban ga rawar kai , tsayaya a tare da ke ba, zan so mijin aurenki ya yabe ki, ki ci gaba da girmama Ayya domin uwace a gare ki, ki nuna mata hankalinki ya kwonta da auren ko natama zai kwonta, kar ki tsananta bincike Agaishat, ke dai ki yi ta rokon Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi, Tunda ta fara Agaishat kallonta take, ita sai yanzuma tsoro ya shigeta, aure, aure, bautar Allah, sunnar ma.aiki, da tana tunanin ta yi nisa da iyayenta a hankali hankalinta ya kwonta da su Ayay harma ta samu gurbi mai girma ta basu a zuciyarta, aman yanzu gashi an mata aure? Kuma bama a kasar zasu zauna da mijin ba domin Mu.azam na shirye shiryen su daga da Agaishat ne? Hannayen Alhinayett ta damke tana dubanta ta ce" *ina jin tsoro, bana son barin su*, A hankali ta dora kanta saman cinyar Alhinayett inda ita kuwa take dan bubuga bayanta alamar rarashi Yana zuwa kai tsaye office din likitan ya je, wanda ya tataba za.a mika takardun matarsa can ne dan hatsari ne Gaisawa suka yi inda likitan ya nuna masa wajen zama, Labarin lokaci da yannayin da aka kawota ya bashi, inda ya ce" tanada shigar yaron ciki ne kuma ta karya da cokacola mai karfi bata ci komai bayan hakan ba, Shi ya hadasa mata ciwon ciki mai tsanani ko nace mara hakan ya saka gudan jinin ya shiga barazanar zubewa, tana cikin wannan halin ta samu hatsarin domin ciwon ya girmami nutsuwarta, A hankali ya dago da idannuwansa ya sauke kan doctern, idannuwansa ya lumshe yana jin wani irin dadi na ratsa shi, ciki, a daidai lokacin da ya rasa wani abin ya samu wani, Murya a kausashe ya ce" *Cikina, ba abinda ya samu cikina?* To fa😔😔😔, na zama raguwa, tun safe nake tsakurar rubutun nan😔😔😔😔😔😢😢😢😢😢😢😢 🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* 4️⃣8️⃣ Da sauri docter ya bai Wardugu amsa gamsashiya tare da nuna masa echo din cikin, cewar bai yi kwari ba ya so zubewa aman Allah ya tsayar da shi, dan haka a kiyaye du wani abinda zai zo mata da garaje har ya zauna ya yi kwari, Kansa kawai yake gyadawa kafin ya mike ya nufi number dakin da aka fada masa take Yana zuwa ya kwonkwasa , bai tsaya an bashi izinin shiga ba ya tura ya shiga, Walyn ce zaune tana rusawa mahaifiyarta kuka inda uwar ke fadan da bai fahinci na meye ba, Gannin mai shigowar ya saka gaba dayansu sukai kit suka daina maganar inda Wardugu ya nuna tamkar bai ga abinda suke ba, A hankali ya karasa wajen kujerar dake dan nesa da su inda mahaifiyar Walyn ta saki hannunta ta mike daga kujerar dake kusa da walyn din tana mai son ta bar dakin A nitse ya gaisar da ita inda ta amsa kafin take barin dakin tana jin wani irin haushin Walyn, ta sha jus din nan ne dan cikin ya zube, da ba.a yi gagawar kawota asibiti ba da tabas sai mai afkuwa ta afku, bata san wa zata fadawa dan ya tsoratar da Walyn ba domin ba wanda take tsoro! Bayan fitar mahaifiyarta a hankali ta kwonta saman bed din tana kallon sama, Wardugu dake yi mata kallon kasa kasa ha jima a haka kafin yake tasowa ya dawo kujerar dake kusa da ita ya ja ya zauna, Rigar jikinta ta atampa wace akai mata dinkin zamani ya dora hannunsa wajen mararta ya samu ya dage rigar a hankali, Lalausan hannunsa ya dora saman mararta, a hankali ya shafa ya jara shafawa, ba zai gane komai ba shi dai yanda cikinta yake ne bai wani canza ba, tana da dan teba kadan, ko dan an ce cikin bai girma bane? Kalonsa ya maida wajen fuskarta a hankali tamkar bai so magana ba ya ce" ina son cikina Walyn, kema kina so? Wani katutun abu ya tsaya mata a makogwaro, ina ita fa ba zata iya wannan lamarin ba, ka haifi dan uban ya dawo sonsa fiye da kai, ba zata iya barin wannan cikin ba duda kuwa azabar da ta sha, Gannin tana ta yamutsa fuska ne ya saka shi kara kusanta kansa da ita ya ce"wani waje na maki ciwo ne? Da haushi haushi ta dube shi ta ce" tun cikin bai zama gudan jini ba, ba.a kai ga halitarsa ba, har ka fara manta abinda ya dace ka fara damuwa da shi? Har ka fara manta nice damuwarka ta farko domin nice zahiri? A hankali ya janye hannunsa daga wuyanta yana dubanta da wani irin yannayi, tafia ya yi ya dawo basu wani hadu ba, tun maganar da ta yaba masa a agadez basu wani hadu ba, shima ya shareta ya shiga harkokin gabansa, yanzu sun hadun zata wani saka shi gaba da hayaniya kamar yaronta, du irin murnar karuwar da ya samu da dokin da ya afka sai ya ji lokaci guda ya dishe, dubanta ya yi irin na tsai din nan, Hannunsa ya saka a aljihun doguwar jalabiyarsa ya ciro cart dinsa ta bank, Ajiye mata ya yi nan ya juya ba tare da yace da ita ufan ba, Tana kallonsa har ya fita a dakin, Ba.a jima ba mahaifiyarta ta shigo dakin tana dubanta , Wani uban tsaki ta ja ta ce" kin masa haukan ne? Walyn ta dafe kanta ta dauki cart din ta mikawa uwar ta ce" Ma, ga abinda kike nema! Plz kama ki barni na ja numfashi mai dadi! Yannayin maganar walyn, da irin furucinta bai taba zuciyar mahaifiyarta ba, hasalima dokin karbar tikitin bankin Wardugu ya sakata sakin murmushi ta karba ta fita da hanzari bayan ta shaidawa yar zata turo a tayata komawa gida ta karbi code number dinsa. Bayan ya karaso gida dakinsa ya shige, Yana shiga ya cire rigar da ya kusan wuni da ita ya kaita wajen injin wankinsa ya ajiye ba tare da ya wanke ba dan hankalinsa ba nan yake ba Dawowa ya yi ya shige bayi ya yi wanka ya dauro alwallah, Sallah ya yi a nitse, bayan ya salamce ya mika hannu ya dauko wayarsa android ya kuna, Yana kunnawa data na hawa domin baya kasheta kwata kwata, Ba.a jima ba messages suka shiga shigowa na mutane daban daban, tun daga abokan aiki, manyan mutanen da yake hulda da su, da yawa kan harkar mota ne da yake siyarwa, wasun kan kamen da ya yi ne watani da suka shude, wasun baima bude ba dan bakin number ne, Yana bin messages din yana karantawa sai dai baya bada amsa, Nan ya fita ya shiga Facebook, roger banasaran da suke harkar motoci da shi ya masa sababin zubi, zubi na sababin motaci na manyan mutane, Yana dubawa ya ga number yarinyarnan dai sai kara turo masa gayata take , a whatsupp ma sai message take turo masa tana karawa, Fita ya yo ya koma whatsupp ya shiga message dinta, Duka kalamaine na rarashi, da magiyar ya kulata, da yannayin kaskantar da kai, wai ita BASMA yar gidan minister, Hotunanta da take ta turo masa ya bude, A hankali ya tsurawa hotunan ido yana kallo, Kansa ya girgiza ya fita ba tare da ya bata amsa ba, Mesage ta turo kamar haka" du bakin da zai furta kalmar so ba makiyi bane, sannan adini bai haramta mace ta nuna tana son namiji ba, kuma ni ban roki wayar gari da kaunarka ba, kar ka ja zuciyata a kasa dan Allah ya baka dama, Mesage din yake bi yana karawa, bai iya bata wata doguwar amsa ba sai mikewa ya yi da wayar a hannunsa ya haye saman bed dinsa ya kwonta ya jawo pilow ya dora kansa, a ransa ya ayyana" haka fa suke idan suna so, da dama ta same su sai su fara gwada halaya na rashin tarbiya da hadama, Yana kokarin neman baci wayarsa ta shiga ruri, Kansa ya shafa yana jan tsaki, Kin kula wayar ya yi sai da ya ga mai kiran ya fishi naci ya dauko wayar ya daga yana fadin" ai aikin nan sai kai daman! Mu.azam ya yi murmushi, ya ce" me tace da kai Wardugu, Wardugu ya yatsina fuska ya ce" wace fa? Mu.azam dake zaune yana hangen shige da ficen Agaishat kicin tana girki ya ce" wardugu mana, bakuwata man Wardugu ya bude idannuwansa ya ce" meye tsakaninka da ita bayan amintaka? Mu.azam ya yi tsam gabansa na dan faduwa, a hankali yake goge zufar da yake ya ce" amintaka ce mafi kusanci, Budurwarka ce? Wardugu ya kaste shi, Mu.azam ya sauke ajiyar zuciya, ya kasa magana hakan ya tabatarwa da Wardugu zarginsa Ransa ne ya ji ya mugun baci, hannunsa ya jimke ya kaiwa garu duka ya kausasa murya ya ce" dan me ka shigi yarinyar mutane bayan ka san amana ce? Mu.azam ya mike zumbur dan yannayin muryar Wardugu ya shaida masa ransa ya baci, A nitse ya ce" ka kwontar da hankalinka Wardugu, bamu yi soyaya da ita ba, itace ke so na, bamu tana soyaya da ita ba, ban zowa Agaishat dan na cuceta ba, kuma ba zan taba gigin cutar nata ba, Wardugu dake tsaye shima ya dafe gaban goshinsa, baya jin zai baiwa Mu.azam amsa a wannan maganar, Mu.azam ya ce" Wardugu, dan *ina sonta* na aureta, Wardugu ya matse karfen jikin bed dinsa yana rintse ido, kansa yake ji na mugun sara masa, hakama juwa na dibansa, Mu.azam ya kara sasauta murya ya ce" ina son mu tafi , na san ka san komai game da abinda yarinyar nan ta zo da shi, Wardugu koda ban auri Khadija ba tana da darajar da ba zan misalta maka ba a raina, tamkar yar uwata na fauketa kamar yanda na dauke ka, zan bita a min aikin nan, idan Allah ya yi na rayu zan tashi na rayu da *Matata*, idan ban rayu ba na san zaka kula da *Iyalina*, gobe ake bani passport din Agaishat, Khadija bata zo ba sai da ta shirya domin komawata da shigana block duka ta irga min kwana tara ya yi saura, Wardugu ka...... Wardugu ya katse shi da wani irin yannayi ya ce" *Zaka rayu in sha Allah*! Ku ci gaba da shirin tafia, in sha Allah ina nan za.a shiga aikinka, zaka rayu Mu.azam...... 😔 *☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________ *Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘 🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* 4️⃣9️⃣ Bai jira amsar Mu.azam ba, Wardugu ya silale yana dafe kansa, a fili ya furta" *ban shirya ba, ba zan iya dauka ba, bani da karfin kokowa da hakan, sannan haramun ne a gareni, ya Allah baka dorawa rai abinda ba zata iya dauka ba, Allah ka cire min wannan gingirmin mikin , domin ni dai ban saba ba*!!!!! Timiya Duniya sabuwa ce ta budewa Ba, wannan karon da sabon salo domin kuwa tafe yake da isa da takama da nuna kansa a matsayin uban *BAk'a*, Anna dubansa kawai take idan yana abubuwansa, bata taba buda bakinta tace da shi uffan ba, a cikin kudin ya basu million guda wada Mariama ta karbe , ya canza masu katifa ya kawo masu buhun dawa guda ya yar masu sannan ya shiga fakar takun Anna yana so ta koma turaka Kamar yau, zaune suke su hudu domin Gaishata ta zo masu , labari suke duka yawan zancen a je a dawo ne a tile kan maganar Agaishat, Anna ta sauke ajiyar zuciya tana dubansu ta ce" mahakurci mawadaci, du wanda ya ce zai yi hakuri Allah ba zai bashi kunya ba, sannu sannu kuma bata hana zuwa, sai dai a jima ba.a je ba, Gaishata ta yi murmushin itama da tsohon cikinta haihuwa ko yau ko gobe ta ce" ni abinda ke bani mamaki Ba, wai shine har yake yi mana kallon mutunci? Mariama ta tabe bakinta ta ce" na dan lokaci ne, idan kudin hannunsa ya kare zai dawo kamar da, Anna ta ce" ki daina mumunan zato Mariama Mariama ta yi mata wani malalacin murmushi dan kar ta yi fada, Suna tsaka da zancen sai gashi ya shigo yana jan arzizimin wando bakinnan kuwa jajajir sansani su ta bata shi, Bai yiwa yaren magana ba sai Anna ya kalla ya yi kiranta ya shige dakin Da kallo suke binta dan gannin zuwa zata yi kuwa? Gani sukai ta mike ta nufi dakin ba tare da ta yiwa kowa cikinsu magana ba Tana shiga ya damko hannunta yana washe baki ya ce" Ke bakya marmarina? Kin jima baki neme ni ba, kin ga baki fice haihuwa ba, ki zo mu kara samun wata Bak'ar, ina son samun yarinya a gidannan, Sakai kawai ta yi tana dubansa, kanta ta girgiza ta janye hannunta ta juya da niyar barin masa dakin Ba da yannayin fushi ya ce" in kika yarda kika fita a dakin nan , sai na nuna maki na fi yan yamai *Niamey* iya rashin kunya! Wani irin birki ta ja ta juyo da madaukakin tashin hankali da kuma tsoron da ya bayana karara a fuskarta, Bakinta ta buda zatai magana sai dai ina jini ne ta shiga bin hancinta, juwa ta kwasheta ta zube nan tana fida wani irin numfashi Karar faduwarta ya saka Mariama mikewa domin da marfin kwano a hannunta marfin ne ya kai kasa ya bada kara wanda sam Mariama bata yarda da shi ba dan haka da hanzari ta fada dakin tana mai kiran sunnan Anna, Tana shiga daidai Ba ya kai kasa zai kamata jikinsa sai rawa yake, Da mugun gudu da taratsi ta ce" kar ka tabata, kar ka taba mini uwata! Bai sanma tana yi ba, shima fama yake ya ga ta mike, yau dai haukansa ya kaishi taka dokar da aka dodora masa na ya kiyaye kama mata sunnan garin haihuwarta, ya kiyaye du abinda zai alakantata da garin makarin duhun kan Anna shine Ba ya kusantata da asalinta, ya kama sunnan garin haihuwar Anna garin neman jarabarsa, Ihun da Mariama ke yi masa ne ya saka yan uwanta shigowa suma a guje sunna nufar inda Ba da mariama ke turayar juna kan sai sun taba Anna Gaishata ce ta dora hannayenta saman kanta da karfi ta ce" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Ba Mariama ku dagata ku dagata na ce! Tsai Ba ya yi , jikinsa na rawa ya nufo Gaishata tamkar zai maketa ya raba ta gefenta ya fice a gidan yana dumumuwa shi kadai , Da kyar suka iya cicibata domin Gaishata ba wani kokari zata iya yi ba sai su biyun ne suka iya kamata suka dora saman tabarmar kaban dakin Hurhutu suke mata suna shafa mata ruwa aman ko motsi, sai numfashinta dake fita a hankali iamar a cicire ta samkame ita ba gawa ba ita ba rayaya ba, Gaishata ce ta ciciba ta mike tana jin yanda mararta ke wani irin juya mata ta nufi kofa tana takawa da kyar tana saurin da zata iya ta nufi fada Tunda ta karaso dogaran sarki ke mata sannu inda aka sakar mata hanya ta shige fadar suna mamakin ganninta domin sarki ya hanata zuwa fada kar a kake masa ita, Kanta tsaye ta nufe shi inda ya mike da sauri daga kujerar mulkinsa dogarai suka shiga baza manyan rigunansu suna kare su, yan zama fada suka fara darewa da sauri sauri Tana isa jikinsa ta zube wanda sukai taga taga dalilin kibar da ta kara ga kuma tsohon ciki, A hankali ya samu ya daidaitata a jikinsa ya dora hannunsa inda ta dora nata wato saman cikinta da take ji baki daya yana wani irin yamutsa mata bayanta na sarawa, Me ke damunki Gaishana, Ya fada yana mai nuna tsantsar damuwarsa da tashin hankali, yanaiwa Gaisha soyaya mai karfin gaske, Da kyar ta iya sauke ajiyar zuciya muryarta na rawa ta ce" Anna ce, Anna ce ta fadi, kuma tana numfashi aman ta ki farkawa, Rigarsa ta jimke jin ciwon na tsananta ta ce" idan wani abin ya sami mahaifiyata zan shida duhu sarkina👏🏻 Zaunar da ita ya yi saman kujerar ya cire babar rigarsa ta turkudi ya rufa mata ya yi gyaran murya, Dogari ne ya amsa masa, Sarki ya ce" ka je wajen jakadiya ingozoma ka fada mata Gimbiya na Daka. Da gudu ya juya inda sarki ya daga karewar da akai masa ya fita da niyar zuwa gidan su Ba, yau kam za.a yita ta kare, ba zai yarda haka ana tayarwa matarsa hankali ba, ! Gashinnan tashin hankali ya sakata nakudar dole, *Niamey* Tunda Ayya ta fara magana tana duban Agaishat da dukan kulawa kan Agaishat ke kasa tana zubar da hawaye, Abaya ce baka mai shegen kyau , bata da wata kwaliya sai zif din da ya hadeta a jikinta, gyaran fatar kwana biyun da Ayya ta yi ta dilketa ya saka fatarta ta kara wani haske da santsi wanda ko a ido ka dubeta zaka ga ta gyaru iya gyaruwa, Dan kwalin Abayar ne ke dan zamewa tana rikeshi har ya kai karfinta ya kare ta sake shi ta duke sosai tana kuka inda gaba daya jikinta ke jijiga Idannuwansa ya rintse da karfin gaske, sannan ya jimki kujerar da yake kai, Kansa ya juyar gefe yana jin saukar kukan nata tamkar ana narkar masa da dalma a kahon zuciya, Mu.azam dake gefensa shima cike da tausayin matar tasa ya mintsini hannun Wardugu yanai masa nuni da ya yi wani abin mana? Wardugu ya juyo inda take suke Ayya na rarashinta itama na sharar hawayen ya hade fuska sosai ya ce" ke! Yannayon yanda ya ambaci ke din sole ka tsorata, yannayi ne ya garwaye da halin da yake ciki, Da sauri ta juyo tana kara shigewa jikin Ayya, Mikewa ya yi ya ce" mu je! Da sauri ta waigo wajen Ayya, wace rake cikin damuwar rabuwa da yar tata, wace kamar da wasa shakuwa mai girma ta kara shiga tsakaninsu, Tun jiya ya dace su tafi aman cikin ikon Allah Agaishat ta rikice ta yi ta kuka har zazabi ya rufeta wai ita ba zata bisu ba, Ayya ta yi gargadin ta yi fadan, ta dawo lalaba tana mai shaida mata tamkar suna tare ne, ga waya, ta bi mijinta zai dawo da ita da wuri Kamar da gaske ta yarda a jiya da dare, a yanzu da suka shirya har Wardugu ya zo rakiyarsu ta kuma birkicewa, Ayya ta ce" Wardugu kar ka yi mata da zafi mana, rabuwa da iyaye ba dadi ka lalabata na roke ka, Wardugu ya juyo yana duban Ayya, idannuwansa sun kade sun yi jajir, a ransa kam birgeshima suke , su sun samu kukan, sun huta, Lebensa ya dantse kawai ya girgiza kai ya dawo da wani irin taku ya dauki dan kwalinta dake kasa ya rufa mata , da idannuwansa ya yi mata nunin ta fice ko jikinta ya gaya mata, Da sauri ta yi gaba tana waiwayen Ayya, wace ta koma saman kujerar tama fasa rakasu dan ba zata juri yanda Agaishat ke kukan ba zata je wata kasa ba, ba zata je ba ta fasa auren! Ko a cikin mota Mu.azam na gaba ne, Agaishat da Mariama na baya, direba na jansu, ta madubi yake duban yanda ta yi lakwas da ita, yana matukar son ya rarasheta aman yana jin nauyin Mariama, baya so ran Mariamarma ya bace dan haka ya adanna rarashin idan sun sauka zai mata, duda har yanzu Mariama bata ce komai game da auren nasa ba, bata nuna damuwarta ki farin cikinta ba, haka shima kwata kwata baya nuna zumudinsa ko wata shakuwa tsakaninsa da amaryar tasa, Mita wajen biyarce ke tafe har aeroport, suna karasawa inda ake ajiye motoci du suka firfito banda taron sojojin dake tare da su, Wardugu ya bude gefen da yake ya fara fitar da kafarsa ta dama kafin ya fitar da ta hagu, Yau a kakin sojoji yake, ya nanade hannayen rigar har saman damtsen hannunsa hakan ya baiwa rigar damar tamke shi, jijiyoyin hannunsa sun yi rado rado , Da karfinsa ya taka ya shiga inda iya su suka bi bayansa Bakin gilas ne rufe da idannuwansa , duda haka zaka gane fuskarsa a tamke take ba alamar fara.a Polisan dake aiki a wajen du idan ya zo ficewa sai sun sara masa, shi kuwa sai dai ya shige yau arzikin daga hannunma basa samu A haka har suka karaso, yauma Allah ya so su da sun rasa jurgin domin lokaci ya tafi har an fara shiga Tsaye ya yi a inda iyakar yan rakiya kennan, ya juyo wajen Mu.azam dake biye da shi, Hannunsa ya kamo suka damke juna, Murmushi Mu.azam ya sakar masa yana mai nuna masa ba komai ya kwontar da hankalinsa, Bai bashi amsa ba sai kafadarsa da ya daka da hannunsa ya nuna masa sai ya zo, Gaba Mu.azam ya yi shima yana mai jin zuciyarsa na tsintsinkewa ya nufi wajen da zai shiga jirgi dan an kirayi sunnan Khadija har ta yi gaba . Du takunsa dan nufar wajen da take tsaye wanda wajen ya kasance hanyarsa ta fita, daidai da bugun zuciyarsa ne, bai so tsayawa ba, sai dai ya ji ya tsaya facing dinta A hankali ya dora hannunsa dake dan bari kan habarta ya dago da ita inda ya tsare idannuwansa da kallo, A hankali ya saka hannunsa na hagu ya share mata hawayen dake mata zarya, Wayar hannunsa ya saka cikin hannunta ya dan ja gefe ya kama hannunta ya jata a hankali har inda Mu.azam yake ya saka hannun nata cikin na Mu.azam ya dan yi tsai sannan ya juya da wani mugun saurin da sai da ya gansa a waje shi kansa Da sauri Mu.azam ya kama hannunta suka shiga taka matatakalar jirgi, wanda ya kasance hawanta ya farki, shigarta ta fari suka shiga Kusa da Khadija ya zaunar da ita shi kuwa ya je kujerar bayansu , du yana haka ne kar Khadija ta kulace ahi, wanda shirunta ke damun nutsuwarsa 😅😅siga baya kiran kansa siga, sai dai wani ya fada,😅😅 *☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________ *Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘 🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫 Na *SAJIDA* 5️⃣0️⃣ Allah ya sauke su lafia, du kuwa da irin yanda Agaishat ta jigata domin har amai ta yi a lokacin fa jirgi zai tashi da irin yar jijigar nan da yake kafin ya mike da tafia, sannan a lokacin saukarsa wannan kasan da abubuwan ciki ke yi suka saka shima ta yi tamakar ta sume, Mu.azam na kule da ita , tausayinta yake ji, khadija ce ke kiran yan matan nan na jirgi da ta ga zata shiga wani yannayi , su ke zuwa su bata kulawa har jirgin ya sauka, Agaishat dai na mamakin irin halin shariyar da Mu.azam ke nuna mata idan suna tare da Khadija, tun bata gane komai ba har ta gane sai dai bata nuna ko a fuska ba, Ko wajen sauka shi ne gabansu su kuwa suna biye da shi a baya inda Agaishat ta zama ta karshe Kanta ne ta ji yana juya mata lokacin da ta ganta cikin tankamemen aeroport din *Paris* A hankali ta sada kanta dan ta lura du idan ta daga kan ta ga irin tsaruwar garin ne hankalinta ke tashi, Fitowa suka yi inda manyan motocin taxi ke laye, da yawa an yi kiransu je, daidaiku ne suka zo wajen dan radin kansu Wajen motar suka nufa , nan Mu.azam ya juyo gannin Khadija bata biyo su ba, Budewa Agaishat ya yi ta shiga ta zauna inda Direban ya saka akwatinta bayan motar, Wajen Khadija ya nufa yana son sai ya karanci fuskarya aman ta ki bashi dama, Yana zuwa hannayenta ya kama yana dubanta ya ce" ba zaki biyo mu ba? Murmushi ta sakar masa ta girgiza kai ta ce" ku je da matarka, nima zan dauki wata taxi din, zan leko ka, ka kular min da kanka nan da kwana hudu zaka dawo asibiti ka kwana biyu bisa kulawar docters kafin a shiga aiki da kai, Murmushi ya sakar mata ya lakace hancinta ya saki hannayenta ya juya ya nufi motar inda sai a lokacin Agaishat ta kawar da fuskarta gefen madubin motar Satar kallonta ya yi, sai a lokacin ya ji wani nauyinta, rabonsa da ya yi wani maganar nutsuwa da ita tun da Khadija ta sauka a gidan Ayya, Kwarai Ayya ta yi masa mutunci ta nuna komai ba komai ba ta hanyar kawar da kanta ta kuma karbi bakuwarsa duda tsanar akidar kawance tsakanin mace da namiji da ta yi kuwa, sannan koda suka tashi tafia ta yi masa gargadi nasiha kamar yanda iyayensa zasu yi masa, sai dai kuma ta nanata ya rike amanar baiwar Allah, Gabansa ne ya ji ya fadi, amanar Agaishat ya karbo fa, amana ya karba, anya kuwa haka amana ta ce? A hankali ya mika hannunsa na hagu ya dora saman cinyarta , wanda ke nuni da yana son kara kusancinsa da ita, Agaishat ta juyo ta dora tsararun irannuwanta saman hannunsa, daga nan bata kai dubanta sama ba ko dan kar idannuwansu su shaku da juna, sai ta kawar da kanta ta mayar bakin titi tana kallon hanya da mamakin irin tsarin garin da irin shigar mutanen garin Bai dauke hannunsa ba, bai kuma yi mata magana ba har suka karaso kofar wani gida Daga kofa raga ne na karfe baki, haka ya ja jakar tana biye da shi tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki har ya saka cod din kofar gidan nasa suka shiga, Fulawowi ne a gidan, ba wani tankamemen gida bane , dan madaidaici ne tsarare, Matatakalar suka hau suka shiga ainahin falon gidan, Plat ne, ba bene, dakuna kwaya biyu ne sai katon bayi da kicin mai girma da tsari da wajen buga game, kujeru farare kar ne a falon sai dan table fari, tv tankamemiya jikin bango sai wajen da ake kuna wuta dan dakin ya dau zafi , sai ac biyu a iya falon Kofar ya mayar ya rufe ya saki akwatin nata nan, A hankali ya juyo yana takowa inda take tsaye kanta na kallon kasa, Yana isowa ya kama hannayenta yana yi kata kallon kurullah, Jin ya jima bai yi magana ba ta dago a hankali ta sauke tsumamun idannuwanta cikin nasa, Fuskarsa ya shagwabe ya jata zuwa saman kujera mai zaman mutun biyu ya zaunar da ita, Kusa da ita sosai ya zauna yana so sai ta kara yi masa kallon da ta yi masa aman du yanda ya so ta kiya, Muryarsa ya kimtsa ya ce" kin daina so na😭, me ya sa kika daina so na? A hankali ta juyo da dubanta wajensa, kurawa fuskarsa ido ta yi, a ranta ta ayyana, ai bamu kai ga gane menene so din ba aka daura auren mu, a fili kuwa sai ta kifta idannuwanta da suka fara cika da kwallah, Murmushi ya yi ya ce" ki yi hakuri Agaishana, kar ki yi fushi da ni, na san kina da tarin tambayoyi aman ki yi hakuri ki bar su a wajenki har sai lokacin yin su ya yi , ki sani ina son ki ba zan daina son ki ba, ina gannin girmanki ina daraja ki a rayuwana, ban aure ki dan cutarwa ba, Wani sanyi ta fara ji a ranta , nan da nan ta ji ta fara manta shaku da rudannin da ta shiga dalilin nesanta kansa da ya yi da ita kwanakin nan, (kar ku ga laifinta, baki daya a duhu take), Dan murmushi ta sakar masa aman batai magana ba, Mikar da ita ya yi ya ja hannunta suka nufi daki............🙄 *Timiya* Wasa wasa sai da Anna ta wuni ta kai tsakiyar dare wajen karfe biyun dare ta wani irin kwala karan da ya firgita yayanta dake zagaye da ita ta aniya amsa kira tamkar ana kiranta , fadi take" *Na.am, Na.am, Na.am?*, Kuftaya ta shiga yi da dukan mai kokarin riketa, idannuwanta rufe suke ruf tana ihun amsa kiran da basu san mai kiranta ba, Digarin da Sarki ya bari ya kula da lafiar Gaishata dake ta faman nakuda tare da Jakadiya har zuwa lokacin bata haihu ba gashi da ta dora masa kuka sai da aka sakata cikin kurakura aka kawota gidan Annar, haka suka wuni har gashi rabin kwana zar suna fama ne ya shigo da sauri jin hayaniya, Fitikar kwan da ya kunna ce ya kara masu haske a dakin da ta wajensu , subahanallah shine abinda yake ambata gannin irin yanda suka kasa tareta ga kuma Gaishata sai murkashi take tana kuka gashi kusa da ita suke jakadiya sai tarewa take kar a fado mata, Gannin ana iya fado mata a samu matsala ya saka shi saurin shiga dakin ya je suka hadu su uku suka kai Anna kasa inda Jakadiya ta shiga fadin ya taho ya taho, Da sauri Dogari ya mike ya kama Anna da ta fara dan yi lakwas ya cicibeta su kai waje domin ya gane Gimbiyar sarkinsa zata haihu ne, Nishin Gaishata da nishin Anna du tare ne, cikin ikon Allah Gashata ta haihu lafia ta sako yaronta har Jakadiya ta yanke cibi ta dauke uwar da ta fado ta nade a zanin Gaishata bayan ta dora mata yaron saman cikinta ta aniya kimtsata tana ta murna, A galabaice Gaishata dake lumshe ido tana budewa na ni.imar nakuda 🤣 ta kallo jakadiya, murya a disashe ta ce" Annata? Jakadiya ta ce" Allah ya ja da zamaninki kar ki damu in sha Allah da sauki, ai dogarin nan dan gidan cheik Ne, baban almajiri ne gayacan sunai mata adu.a, Sosai suka dukufa suna yiwa Anna du adu.o.in da suka iya inda shi kuwa dogari ya dauro Alwallah ya zo shima da ruwa a kwanon kwano ya zauna ya shiga karanto mata manyan adu.o.in karya sihiri, na rukuya kai harma da na tsari duka yana tofeta da shi kuma yana tofawa a cikin ruwan, Mikawa Mariama ya yi ta shafa mata gaba daya jikinta suka ci gaba da adu.o.in , Wasa wasa sai da garin Allah ya waye domin kuwa sai da aka kirayi salar asuba Anna ta ja wata irin ajiyar zuciya ta yi wata irin mika kafin take zabura ta ce" *Ayya, Ayyana, wani abu zai rufe min ido, wani abu Ayya* (kar ku manta tubawa ke kiran Mama da Ayya, wace Ayya xce haka? Shin Anna ta dawo hayacinta?)))) Kadan ne