*All thanks to Allah SWT for the chance, privilege and ability to start this book, my special greetings goes to my lovely Mum Hajiya Hajarah and my sweet aunties (Small mums) my siblings/Cousins aren't excluded also... I love them all, Hajiya Adama (Mrs Garban kauye) gaisuwa da fatan anyi sallah lafiya, Chamo da tawagarta su ma duk na gaishesu kyauta😹 and My Sophiee I know you won't see this but get this.. jiddo Love's you dear, Lovely fans and Friends ina maku fatan alkhairi da fatan gamawa da iyaye lafiya* _kafin dai in fara post din book din nan i want to let everyone know this.... Although most of my fans sun san i am a final year student, to cut it short... 2 month to our final exams aka tafi strike, so if God should touch Fg's mind by letting dem do d needful i have no choice then to take a break and face my final exams... Balle ma nasan xamu gama in sha Allah before then, coz i have written and keep enough.... thanks for understanding_😉 💖 *Jeedderhh*💖 _By Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 1..... Slowly yake driving din idonsa a kan titi yana sauraron abokinsa, amininsa, kuma d'an uwansa dake xaune kujera me xaman banxa cikin motar, can dai ya ja tsaki ya girgixa kai, speaking calmly yace "Ni fa da ma ka canxa labarin nan naka Ahmad, in anyway ban ga amfaninsa ba..." Dariya abokin nasa Ahmad yyi yace "Toh ai ni yana da amfani gareni sosai tunda ina sonta and i want to marry her, look Captain don Allah ka cire son xuciya ka gaya min meye aibun Maryam let me know" Wanda ya kira da captain ya shafa lallausan gashin kansa yace "Kasan mene?" Kallonsa kawai Ahmad yake yana jiran jin abinda xai ce, Captain yace "Ina son ka sanar dani me yasa ku Hausawa baku da xancen da ya wuce na soyayya, ga dai abubuwan ilimi iri iri masu ma'ana da mutum xai karu da su duniya... Amma ku dai soyayya kadai ku ka sa a gaba, did u know that it's just of recent ina wani karatu nayi discovering cewar Airplane water is riddled with bacteria, not even that, jiya jiyan nan na gano cewar...." Ahmad dake masa wani kallo ya dakatar da shi ta hanyar cewa "Wannan kai da masu tunani irin naka ya shafa, what u are saying now will add no value to people like me gaskiya" Captain ya maida hankalinsa gaba daya kan tukin da yake, Ahmad yace "Duk sanda na kawo maka maganar Maryam you always have a way to get rid of the discussion ko me yasa?" Captain yace "Ohk you asked me of her flaws if i am not mistaken, right?" Ahmad yace "Yes so" Captain yace "To xaka ji ynxu.... first of all she is local, secondly she gat no qualities da xai sa ka makale mata dude, just imagine an undergraduate fa?? And worst of all she isn't even beautiful enough, ga dai big babes a garin da ka baro Abuja, sannan..... her hygiene is nothing to write home about, i mean nothing.... Shine ma babban damuwata ma ni" Da mamaki Ahmad ke kallonsa, da farko kasa ce masa komai yyi, can kuma yace "Wani rashin tsaftar kaga tayi??" Captain ya saci kallonsa yace "Oho, wataran xaka gani" Ahmad ya girgixa kai yace "You are talking off hook, Maryam tana da qualities din da ni nake so, I think that's all? Kuma dama kai idan baka son abu to fa baxa ka ta6a son abun ba, ka dingi discouraging mutum a kai kenan" Captain ya gyada masa kai yace "Ehh haka ne, plss close the chapter" Ahmad xai yi magana ya hango inda ake tuyar awara a gefen titi, da sauri yace "Captain plss ka d'an tsaya, I want to get this, na mance yaushe rabon inci awara, tun kafin in tafi Uk fa..." Captain ya d'an kalli wajen da ake tuyar awaran ya kara ma motarsa gudu yace "Allah ya kiyaye, domin na je dauko ka a railway station doesn't mean xa ka mayar da mu gantalallu a hayi.... Meye kuma awara?" Ahmad yace "Toh ka ajiye ni, ai bance sai ka xo ka daukeni a tasha ba dama, you offered to do so" Captain yyi kasa da murya yana rage gudunsa yace "Yanxu Ahmad kasan ta ynda suka yi processing abun nan da xaka ci? Hayi ne fa nan, ka bari kaje gida kasa ayi maka mana, ni Allah bana son locality din nan naka" Calmly Ahmad yace "Su 'yan hayin ba mutane bane Abuturrab?" Captain yace "Aa ba haka nake nufi ba, I mean... hygiene din, they don't value it, ka gane ai" Ahmad yace "Kai komai sai kace hygiene, to sannu sarkin 'yan tsafta, a haka kuma nake son in siya, ba ruwanka kuma" Captain bai kuma ce masa komai ba ganin wani waje da ake suyan yyi parking kafin ya karasa wajen yace "To sai ka sauka kaje ka siya, amma gaskiya you ain't worth being a Dr wllh, very careless Dr that looks down on Hygiene" Ahmad na hararansa yace "Ae ba dankali nace maka xan ci ba malam, Awara nace kuma nan dankali ake siyarwa" Captain ya kalli wajen masu tuyan yace "Toh ai ban san yanda Awaran yake ba, ba shi bane wnn din?" Ahmad yace "Ba shi bane" Captain ya ja motarsa yana tukin a nutse, can underneath his breath ya ja tsaki, Ahmad is just too local for his liking, Ahmad yace "I think ga wani wajen can" ta gefen wajen da ya nuna masa Captain ya gangara yyi parking yana kallon yarinyar dake tuyan awaran yana yamutsa fuska shi wnn ko yunwa xai kashesa xai iya cin abinda take yi kuwa, Ahmad ya bude motar ya sauka ya tafi gun ta, ita kadai ce xaune sai yara da almajirai dake tsaye suna jiran a siyar masu awara, Ahmad yace "Me awara nawa nawa ne awaran naki?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Daya Ashirin" Ahmad ya buda ido ya rike waist dinsa yace "Ikon Allah, kamar dai muna fada da me awara irin wnn amsawan" Still bata kallesa ba ta ci gaba da sallaman yaran da ke gabanta, ta mota Captain ke kallonsu, shi dai Ahmad na tsaye bai sake ce mata komai ba ganin mood dinta, sai da ta sallami yaran gabanta ta daga kai ta kallesa tace "Na nawa xa'a sa maka?" Ya daga kafada yace "Na dari biyar kawai" Tace "Baxai kai ba, sai dai in xaka jira a soya wani" Yace "Toh ba damuwa xan jira a mota" Daga haka ya juya ya nufi motar ya bude ya shiga yana kallon Captain da ya kauda kai da sauri yana kallon daya side din. Leda biyu tayi masa sannan ta hadasu gaba daya a wani ledan daban, yajin ma ta xuba masa a wani ledan snn ta mike ta nufi motar ta mika masa ta glass dake bude, amsa yyi yana kallonta da murmushi fuskarsa yace "Kamar dai an 6ata ma me awara rai" Ita dai bata ce masa komai ba, dubu biyu ya ciro a aljihunsa ya mika mata yace "Toh gashi" ta daga kai tana kallon kudin tace "Na dari biyar kace" Yace "Ehh sai ki rike sauran canjin ai ko" Ta sauke idonta kasa tace "Aa ka dai bani dari biyar din dai kawai" Ya bude ido yace "Dama ana maida hannun kyauta baya" ta girgixa masa kai tace "Ban san wa xance ya bani ba a gida" Cikin sanyin murya ta karasa maganan, yayi murmushi yace "Sai ki boye kayan ki" Daga haka ya saki kudin nan kasa yace "To sai anjima me awara, Allah ya kawo kasuwa" captain da ya ki kallonsu ya tada motar suka bar wajen. Sai da suka kusa fita titin hayi Ahmad yace "I imagine may be condition ne ya sa yarinyar tuyan awara a rana ko, the country is getting tougher and tougher for the less privileged everyday....." Captain dai bai ce masa komai ba, Ahmad yyi kasa da murya yace "On a serious note ina jin tausayin poor masses a kasar nan, yanxu banda situation me xai sa iyayenta su barta bakin titi tana wnn sana'a? Allah dai ya rufa ma kowa asiri" Still Captain bai ce masa komai ba har suka shigo Unguwan Sarki, yana kallon Ahmad yace "Mu je can gida ne kawai?" Ahmad ya gyara xama yace "Aa kai ni in ga Ummata tukun, da yamma xan shigo in sha Allah" Captain bai ce komai ba yyi driving har xuwa gidan kanwar Mum dinsa Hajiya Ramlah warce ita ce mahaifiyar Ahmad... A kofar gida yyi parking Ahmad na kallonsa yace "Baxa ka shigo ba?" Captain yace "Aa ni fa ko jiya na xo gidan nan" Ahmad yace "Sai dai idan Ummi ce ta aiko ka ba dai xuwan kanka ba" Captain ya shafa kansa yana xare manyan idanuwansa ya kasa cewa komai, Ahmad ya ta6e baki ya bude motar ya sauka, da sauri Captain na nuna masa ledan awaransa yace "Heyy ga kullinka ka mance min a mota" Juyowa Ahmad yyi ya jefa masa wani kallo ya dau ledan awaran ya nufi cikin gidansu, Captain ya bi sa da kallo yana murmushi, can ya kashe motar ya sauka ya bi bayansa walking slowly... Siyama ta sake yayanta da ta rungume ganin Captain da ya shigo parlon, tana murmushi tace "Yaya sannu da xuwa" Yace "How are you Siyama" tace "I'm fine" Yace "Ina su Maimuna?" Tace "Sun tafi islamiyya" Yace "Ke fa" Tace "Ka manta nace maka bani da lafiya jiya?" Yace "Ohhh ohk na tuna, Allah ya kara lafiya, Umma fa" Tace "She's in her room" Tuni Ahmad ya nufi dakin Mahaifiyarsa, Captain ya bi bayansa. Sai bayan Magrib Captain ya bar gidan tare da Ahmad xuwa nasu gidan a Malali, Babban gida ne duplex me wadatattcen tsakar gida.... Captain yyi parking a daya daga parking lot biyu dake katon compound din, suka sauka motar tare da Ahmad suka shiga ciki Ahmad na cewa "Amma Abba baya gari ko?" Captain yace "Ehh baya nan" Zaune take a d'an karamin tsukakken tsakar gidan nasu da kwanon tuwonta a gaba sae dai ba ci take ba duk da kasancewar hannunta cikin kwanon, wata matashiya ce xaune cikin daya daga kananun dakuna uku dake D'an tsakar gidan hannunta rike da mafici tayi daurin kirji, xaune a tsakar gidan kan tabarma wani middle aged man ne da baxai wuce 58 ba, daga cikin dakin matar ke cewa "Munafuka algunguma kawai, sae ana magana tayi mukui ta ki cewa komai, a haka xaki kare cikin nukurci da bakin hali, banda haka uwar me ya ci min naira hamsin a kudina, ko da yake dama ae kin saba halin bera, sae dai na yau yayi min ciwooo tunda ko biyar ubanki bai kawo min yace gashi kiyi cefane ba, to a kan me??" Ita dai bata iya ta ce komai ba har lkcn hannunta na cikin kwanon tuwon ta kasa ci, mikewa matar tayi tana gyara daurin kirjin jikinta ta fito a fusace ta janye kwanon tuwon jin almajiri na bara tace "D'an malam shigo ka amsa" Malam Isuhu dake xaune saman tabarma yace "Ita kuma ta ci me Hansatu??" Wani kallo ta jefa masa tace "Sae ta ci wanda ka nemo aka girka yau" tana fadin haka ta juye ma almajiri ta ajiye kwanon tayi shigewarta daki, shi dai bai kuma cewa komai ba, a hankali ta mike ta dau kwanon ta kai wajen wanke wanke ta shiga hada kayan wanke wanken tsakar gidan, sae da ta gama gaba daya ta mike mahaifinta dake tsakar gidan har sannan ya fiddo hamsin a aljihunsa yace "Gashi ki je ko dankali soyayye ki siyo ki ci Jiddah" karasawa tayi ta amshi kudin da ladabi tace "Nagode Baba" bata rufe baki ba Hansatu ta fito da gudu ta warce kudin tana kallonsa da kyau tace "Saura dari hudu da hamsin kudin cefane na na yau" tana fadin haka ta kulle kudin bakin xaninta ta shige akurkin dakinta, Jiddah ta juya a hankali ta shiga dakinsu ba tare da ta yarda hawayen dake makale idonta ya xubo ba. Washegari da safe wata dattijuwa da baxata haura 55 ba ta shigo wani babban daki ta kulle kofar tana kallon wanda ke kwance yyi rub da ciki saman gado, karasawa ciki tayi ta buga gadon, juyowa yyi da sauri ya mike xaune ganinta yace "Aunty ina kwana?" Tace "Jiya da daddare ina kaje har bayan isha baka shigo ba" yace "Aunty ina gidansu Ahmad fa, kuma tare ma muka dawo nan da shi na xata kin yi bacci shi yasa bamu shigo ba" Tace "Ohk, jiya Ahmad din ya dawo" Yace "Ehh" Tace "Ai na xata tadi kaje" D'an murmushi yyi yace "Tadi kuma Aunty... Ai tana Abuja" Tace "Atoh na sani ko ka kyallara ido ka ga wata ka watsa min kasa a ido??" Bai kuma ce mata komai ba sai murmushi da yayi, ta juya ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita ta kulle kofar, mikewa tsaye yyi yana kallon agogo dake nuna karfe tara ya shiga bathroom. Kasancewar ranan asabar ce sai kusan karfe sha daya Abuturrab ya fito daga dakinsa sanye cikin kananun kayan da suka matukar amsar sa, lkci daya kamshin turarensa ya gauraye parlon gaba daya, kanninsa mata ne xaune Main parlor din gidan, duk kallo daya suka yi masa suka dauke kai, bangaren Mahaifiyarsa ya nufa, Ramlah ta bi sa da kallo tace "Ummi ta fita fa" Ya juyo ya wuce side din Stepmum dinsa... A parlonta ya sameta tana yi ma autarta Aisha tsifa, yace "Xan je gidansu Ahmad Aunty" Tace "Breakfast din fa?" Yace "Ni nayi breakfast da asuba fa" tace "Oh ka dawo breakfast din asuban kenan" Yace "Ehh" tace "Kawata xata tafi Lagos ranan Monday daga kano shine nace kilan ma you will be piloting the plane...." Yace "In dai flight din safe ne" Tace "Na safen ne ma ina ji" Yace "Allah ya kai mu" Daga haka ya juya yace "Sai na dawo" yana fita parlon, Hajiya Amina da suke kira da Aunty ta kalli autarta tace "Me yasa baki gaida sa ba?" Aisha ta buda hannu tace "Wllh Aunty ranan ce mana yyi mu daina gaishesa a gidan nan idan yana nan, and he was serious about it" Aunty tace "Me ku ka yi masa?" Aisha tace "Babu komai, ranan Thursday da ya dawo duk muna parlor da su Aunty Safiyya muka gaishesa bai ce komai ba, muka sake gaishesa, har ya tafi ya dawo on a serious note yace mana kar mu sake gaishesa baya so, and since then no one is greeting him again and he is very comfortable with that" Aunty ta ta6e baki tace "Toh ai shkkn" A daki Abuturrab ya tadda Ahmad bayan ya isa gidansu, Abuturrab ya nufi window din dakin ya dage curtains din ya bude windon yace "Allow natural ventilation mana" Ahmad yyi dariya yace "Gaskiya ne bature, to kashe Ac din ko?" Abuturrab ya xauna yace "Aa bar shi, how are you?" Ahmad yace "Fine, ya su Ummi" Abuturrab yace "Cool" Ahmad yace "Are you flying on Thursday?" Abuturrab ya d'an yi shiru trying to recall his piloting schedules, kafin yace "Yea, Kano to Lagos, Then Lagos to Abuja, on Friday kuma Abuja to port harcourt" Ahmad yace "Ohk dama Maryam will be going back to schl Thursday I tot kana nan mu kai ta tare" Abuturrab ya ta6e baki yace "Ahmadu Bello?" Ahmad yace "Ehh" Abuturrab yace "Ka kai ta tasha ka sa ta a mota mana, kawai yarinya karama tayi ta juyaka" Hararansa Ahmad yyi, Abuturrab ya fiddo wayarsa dake ring yana duba me kiransa. Bude kofar dakin aka yi Maimuna ta shigo da tray dauke da warmer din danwake da tamarind drink a jug, ajiyewa tayi ta gaida Abuturrab da murmushi fuskarta yace "Ya kike Moon?" Tace "Alhmdllh, Yaya xan je Abuja fa" Yace "To sae ki xo in makala ki a jirgi ko?" Dariya tayi sosai tace "To ai shi sa na gaya maka" yyi murmushi bai ce mata komai ba, ta mike ta fita, bude warmer din Ahmad yyi, Abuturrab dake ta kallon danwaken warmer din yace "Ya ma abin nan da ka siya jiya a hayin Rigasa? Kamar shi nake gani a nan" Ahmad ya wara ido ido yyi dariya yace "Ohh wannan danwake ne, wancan kuma awara, kamar kuwa kasan yau ma xan je in siya, kaji dadin awaran nan kuwa? Gaskiya sun iya sosai, har Umma sai da ta ci, ni uku kawai naci su suka cinye sauran" Abuturrab ya dinga kallonsa da mamaki, can yace "Har komawa xaka yi kenan ka sake siya" Ahmad yace "Yes, I had intention dama" Abuturrab ya gyada kai bai sake ce masa komai ba. Har yamma Abuturrab na tare da cousin din nasa kuma abokinsa.... Su yi fada su shirya, duk bayan sati uku Ahmad ke shigowa kd yyi weekend daga Abuja don a can yake aiki as a medical Doctor, throughout weekend din kuma tare suke spending dinsa da Abuturrab idan shi ma yana garin, karfe biyar saura Ahmad ya mike yace "Captain mu je ka rakani mana pls" Captain ya kallesa yace "In raka ka ina?" Ahmad yace "Hayin Rigasa" Abuturrab yace "Aa sae dai Hayin banki, kaga malam mu fita tare kawai kayi hanyarka inyi nawa, don gida xan wuce yanxu in sha Allah" Ahmad yace "Ae ko baka isa ba, wllh sae ka rakani" Abuturrab ya dau wayarsa xae dau makullin motarsa Ahmad ya dauke yace "Sae ka tafi da kafa ai" kallonsa Abuturrab yyi, lkci daya ya wani hade rai, Ahmad ya fita dakin yana murmushi. Driving Ahmad yake yi, ya kalli Abuturrab dake xaune gefensa yace "Wai Aneesah fa?" Abuturrab ya gyara xama yace "She's good, baka ji muna waya daxu ba" Ahmad ya girgixa kai yace "Kai ynxu da gaske mace da idanuwanta suke a bude da sunan wayewa kake so Captain...." Abuturrab yace "Look at you, kai baka san wayayyun sun fi tsafta ba, ni fa I don't care.... As far as xata yi tsafta 100%, wllh ko haduwa da mace kazama ban son yi a rayuwata, sae inji gaba daya hankali na ya tashi, u know how sensitive I am...." Dariya Ahmad yyi yace "Ita Aneesar tana da irin tsaftar da kake so kenan" Abuturrab yace "Kai ma kasan da ba don haka ba da tuni ae na rabu da ita, kawai sae kaga mace ta ci kwalliya iya kwalliya ta fito amma just check inside, ni in dai mace na da tsafta ko kyanta bai fi 80% ba i will manage her..." Girgixa kai Ahmad yyi yana kallon titin gabansa, Abuturrab yace "Ba ga wajen danwaken can mun wuce ba" Ahmad bai san lkcn da yyi dariya ba yace "Aa D'an gyero ne ba danwake ba" Abuturrab dai bai ce masa komai ba da ya lura u turn yake son yi, dai dai gun awaran Ahmad yyi parking, wata yarinya ce da baxata wuce shekara sha daya ba xaune a wajen tana juya awaran cikin kasko, Ahmad na kallonta yace "Ina me awaran?" Yarinyar tace "Ta je dauko canji a gida shine tace in tsare mata, ae sunanta Aunty Jiddah, a gidansu Bibalo take..." Ahmad ya koma jikin motarsa yace "Gidan ba nisa?" Yarinya ta nuna masa wani rubabben layi dake gefensu tace "Can karshen layi ne, gidansu daya da Bibalo" Shi dai Abuturrab na xaune kujera me xaman banxa yana kallonsu, Yarinyar tace "Lah ga ta can xuwa" Duk suka kalli direction din da ta nuna, Tafe take fuskarta daure hannunta rike da yar karamin bokiti dake a rufe, wanda ke dauke da dafaffen awara, sanye take da hijab ruwan kasa da iyakarsa gwiwa duk man awaran da take tuya yayi staining Hijab din, Abuturrab ya d'an yi tsaki ya hade girar sama da ta kasa yana kallon titin gabansa, tana isowa yarinyar ta tashi tace "Aunty Jiddah gashi xa a siya a awara, da motarsu ma suka xo" Ahmad ya wara ido yace "Aunty Jiddah a bamu kalan na jiya" Ta daga kai ta kallesa tace "Na nawa?" Yyi murmushi yace "Yanda kika sa jiya" Bata ce komai ba ta durkusa ta sa masa awaran sannan ta mika masa ledan, dubu daya ya ciro ya mika mata, tana kallon kudin tace "Yanxu na kai kudi gida na amso canji, ka d'an yi hakuri sai in koma in dauko..." Ya juya ya kalli Abuturrab yace "Ko a siya maka kai ma Captain?" Kallon Abuturrab din tayi ita ma suka hada ido, yyi saurin dauke idonsa yaki cewa komai, Ahmad ya kalleta yace "Toh kinsan abinda xai faru me awara? ki ajiye canjin...." Da sauri tace "Aa ka jira in tafi in dawo ynxu" yace "To tsaya ki saurareni mana, ajiyewa xa ki yi gobe idan Allah ya kai mu na xo sai a bani awara na canjin" tace "Toh" murmushi yyi ya nufi mota rike da ledan awaran, sae da ya shiga motar ta ga ledan yajinsa bata sa masa ba ta mike da sauri tace "Kayi mantuwa" motar ta nufa tana mika ma Abuturrab ledan yajin, da mamaki yake kallonta kamar dai mugun abu take mika masa, yace "Kai!! kinga na siya abu a wajen ki ne?" wani kallon cikin ido tayi masa snn ta xaga ta mika ma Ahmad ta koma gun xamanta tana juya awaran kan wuta, Ahmad ya tada motar suka bar wajen yana hararan Abuturrab da ko a jikinsa. Jiddah na xaune a d'an dakalin kofar gidansu bayan isha, dawowarta kenan daga bakin titi ta gama tuyan dankali da take yi, ta ta takure waje daya cikin hijab din jikinta, wani matashi ne da baxae wuce shekara ashirin da tara ba xaune d'an nesa da ita, yace "Kin yi shiru Jiddah" Ta d'an kallesa tace "Nace babu wata matsala" yace "Kin tabbatar?" Ta gyada masa kai, yace "To ki ci gaba da hakuri kin ji.... In sha Allah idan....." Kamar daga sama suka ji muryar Hansai, ta rike kugu tana kallonsa da kyau tace "Ta ci gaba da hakurin gyatuminka?" Ya kalleta ya duka har kasa yace "Ina yini Baaba" Ta wani sha kunu tace "Da ban yini ba xaka gan ni algungumi?? Ta ci gaba da hakuri a saboda ana cutarta ko? Sannan ban rabaka da kofar gidan nan ba? Dama tun da naga yara sun shigo da kayan tallanta ita bata shigo ba nasan da walakin goro a miya, shine nace bari dai in leko in ga ikon Allah" shi dai bai ce komai ba ya sunkuyar da kansa, tuni Jiddah ta mike ta makale da bango gabanta na faduwa, Hansai ta cire takalmin kafarta ta jefa mata a mugun fusace tace "Wuce ciki munafuka kawai, dama ban rabaki da wnn yaron mara tarbiya ba, ni xa ki ja ma abun kunya a unguwar nan?" Da sauri Jiddah ta shige ciki Hansai ta kai mata dundu da karfi, sannan ta maida dubanta kansa tana huci tace "Wllh na sake ganin ka tare da yarinyata gidan gayun garin nan yyi mana kadan da ni da kai, idan kuma karya ne mu xuba da kai" Tana kai wa nan ta shige ciki ya mike a hankali ya bi ta da ido.... 💖 Jiddatul~khair 💖✍🏻 *Ina me mika sakon ta'axiya xuwa ga Chamo bisa rashin mahaifinta da tayi, Allah ubangiji ya ji k'an sa ya gafarta masa, ya sa aljanna makoma, ya bada hakurin rashi, mu kuma Allah ubangiji ya kyautata namu Ameeeen*👏🏻 💖💖 *Jiddatul~khair*💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 2..... Abuturrab na kwance saman gadon dakinsa yana rike da wayarsa, kunnensa sakale da earpiece, video call yake da wani matashin da baxai wuce sa ba, matashin na xaune cikin wani ubansun parlor yana cin apple, Abuturrab ya girgixa kai yana kallonsa yace "Look... I don't want to say anything about that.... idan Mummy na kusa ka bata mu gaisa" Matashin na taunar apple yace "It's already late, tayi bacci..." Abuturrab yace "It's late tunda baka son fita, so when are u coming to kd?" El-Basheer yace "Xa mu shigo kano tare da Mai martaba next week in sha Allah, probably ni xan karaso, amma sai kana nan" Abuturrab yace "In dai Friday ne ina nan in sha Allah" El-Basheer ya daga kafada yace "Ohk then" Abuturrab yace "Let me pick a call, sai da safe" El-Basheer ya gyara xamansa yana murmushi yace "The lady u don't want to talk about?" Katse call din Abuturrab yyi ya dau daya wayarsa dake ring ya daga ya kai kunne hade da cewa "How u babe?" Abuturrab ne xaune parlonsa a gidansa dake Abuja shigowarsa gidan kenan ko awa daya bai yi ba, kasancewar weather babu kyau yasa suka yi landing flight da suka yi piloting daga Lagos a Abuja a maimakon kano.... Grapes ne gabansa yana ci a hankali yana kallon wani action movie da ake yi a tv, bude kofar parlon aka yi, lkci daya ya daga kai, he was expecting no one other than Ahmad da ya sanar ma yana Abuja... Tsayinta matsakaici ne.... ita ba siririya ba ita ba mai jiki ba, ta karasa shigowa parlon ta kulle kofan tana kallonsa ta cire Nikab din fuskarta, fara ce sosai, kallonta shi ma yake, she looks so orderly from head to toe, tuni kamshinta ya baxa parlon, shi dai kallonta kawai yake ta nufesa da damuwa ta xauna gefensa tace "Why ain't you picking my call Captain?" Ya gyara xamansa yace "It wasn't long da muka sauka ai, na sa wayar a caji a can daki, how are you doing?" A hankali tace "I'm fine, ya gajiya?" Yace "Alhmdllh, where are u coming from?" Ta buda manyan idanuwanta tace "Home... kace min xaka sauka Abuja shi sa na samu na fito" ya shafa beard dinsa yace "Ahmad na hanya, bana son ya xo ya sameki nan, u know how he thinks" Ta langwabar da kai tace "Ohk, amma nace maka ina son muyi magana, ina ta bin ka yau kusan sati biyu kenan sai kace min you will be piloting today, u will be piloting tomorrow...." Da damuwa ta kare maganar, Ya kalli agogo yace "To ina jin ki yanxu, I'm sorry i forgot about that" Shiru tayi, ya kafeta da idanuwansa, sai kuma yyi murmushi ya kamo hannunta yace "Ina jin ki Aneesah" Tayi kasa da murya tace "Aliyu a gidanmu an takurani in fito da miji, kwanaki kuma na gaya maka baka ce komai ba, idan har da gaske kake kana sona what is hindering you pls?" Ya dauke idonsa daga kallonta, bayan few seconds yace "To a jira ki gama karatun mana ko? Ina ce saura kadan" Ta girgixa kai tace "Aa last week Abbana ya kara min magana, and he is very serious about it this time, don't u love me ne Aliyu?" Abuturrab ya xaro ido yace "Not at all Aneesah, kema kinsan ina sonki.... kar ki damu xa mu yi magana, yanxu ki tashi ki tafi kafin Ahmad ya xo..." Ta gyada masa kai sannan ta mike, mikewa yyi shi ma ya wuce daki ya dauko kudi ya mika mata kafin yace komai tace "Aa ni da motana na fito don't worry" Bai ce komai ba ya rakata har balcony snn ya amshi jakarta ya sa mata kudin yace "I know da mota kika xo, Chocolate din da ban kai maki ba last week sai ki siya, ba kudi ne me wani yawa ba" Murmushinta me kyau tayi, tayi kasa da muryarta tace "Thank you my Captain" ya kashe mata ido yace "C'mon babe.... Nikab din kuma na meye yau kika sa?" Tace "I just felt like" ya daga kafada yace "Alright sai mun yi waya" ta gyada masa kai ta nufi gate ya juya ya koma parlor, her neatness melt his heart always nd make him fall for her deeply. Wata dattijuwa ce xaune dakinta tare da yan mata biyu, aka bude kofar dakin duk suka daga kai, Dattijuwar na murmushi tace "Aa Abuturrab sannu da xuwa" ya karasa ciki yana murmushi shi ma, ya xauna sannan ya gaisheta da ladabi, tace "Ka dawo weekend kenan" yace "Ehh daxu muka sauka, ya karfin jikin Umma?" Tace "Alhmdllh na ji sauki yanxu" yace "Allah ya kara lfya" tace "Ameen" ledan hannunsa ya ajiye yace "Ahmad yace in taho maki da wannan" Tace "Kun hadu a Abujan kenan" Yace "Ehh kwana na biyu a can, weather babu kyau sai yau na samu muka bar Abujan xuwa kano, daga kano na biyo private jet" Umma tace "Toh Allah ubangiji ya tsare mana ku dai, Allah ya rabaka da sharrin kayan bature, haka kai kuma Allah yayi hanyar cin abincin ka" Amira tayi 'yar dariya tace "Kabu kabun jirgi Ya Abuturrab yake fa" Ta gefen ido ya kalleta bai ce komai ba, amma ya hade rai sosai, Umma tace "Ni dai Allah ya tsare min shi" a hankali yana kallon kanwar mahaifiyar tasa yace "Ameen Umma" Tace "Mun yi waya da Ahmad daxu nace masa wani awara da yake kawo min nake son ci wllh, gaba daya bani da appetite, yace kuma a hayi ake yi ko" Abuturrab ya d'an buda ido, sae kuma da sauri yace "Allah sarki, baxa a iya maki a gida ba Umma? Ae kamar yafi tsafta ayi a gida kawai" Tace "Aa da wahala, beside babu ma waken suyan a kasa, Hurairan da xata yi ma ta tafi garinsu daxu, kanninka kuma babu abinda suka iya gasu nan dai xaune, gwara kawai a siya a wajen ya fi, naga me kyau ne sosai ran da ya siyo ae" Abuturrab dai bai sake cewa komai ba, tace "Kuma yace ka san wajen, tare ma ku ke xuwa" Da sauri Abuturrab ya kalleta, lkci daya ya kirkiri murmushi yace "Anya xan gane kuwa Umma, a wani layi ne can cikin hayi fah, the place is very complicated" tace "Aa Aliyu na fa sanka sarai, ko baka sob xuwa ne, idan ma da gaske ne baka gane wajen ba ai kiran Ahmad din xaka yi ya sake maka kwatance" Bai ce komai ba amma lkci daya mood dinsa ya canxa har hakan ya kasa boyuwa a fuskarsa, sai dai bai bari ta lura ba, ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna karfe biyar da few minutes, Umma tace "Ko kana da inda xaka je ne?" Ya d'an shafa kansa a hankali yace "Aa, bari in je in dawo" tace "To Allah yyi maka albarka" da kyar ya amsa da "Ameeen" snn ya mike ya fita, sosai ya hade rai bayan ya shiga motarsa, why will Ahmad tell her ya san wajen, ynxu kawai sai ya fara driving xuwa hayi wai yaje siyan awara why??? wani tsaki yyi ya tada motarsa ya bar compound din. Driving kawai Abuturrab ke yi har ya shigo hayi, he was very observant kar ya wuce inda ake suyan awaran, haka nan yake jin ransa na baci, wani ma ya gansa ya xata shi xai ci, U turn yyi ya samu waje yyi parking yana kallon yarinyar da ta mike xata shiga karamin layin nasu bayan ta sauke kaskon awaran kasa, almajirai uku ne tsaye gun da wasu yan mata biyu, Abuturrab ya dake yace "Kee" bata juyo ba don tafiyarta kawai take kuma da alama ma bata ji ba, Daya daga yan matan wajen tace "Bata ji ba, yanxu xata dawo, xata amso canji ne" Bai ce komai ba ya jinginar da kansa jikin kujeran motar, bayan kusan minti biyar sai ga ta tana dawowa, kallonta yake har ta iso bakin titi, ta kalli motar sannan ta durkusa gun sana'arta, Yarinyar daxu tace "Ke jiddah jiranki ake xa a siyi awara" Sai snn ta daga kai suka hada ido da Abuturrab, ya hade giran sama da ta kasa yace "Nawa kike siyar da kayan siyarwar taki?" Tace "Wanda ya rage a nan bashi da yawa, amma ynxu xa a kawo daga gida...." Bai ce komai ba ya dauke kai, ta sallami mutanen dake tsaye a wajen, bata son komawa gida dauko danyen awaran Gwaggo Hansai ta sake koranta tace bata gama ba, kuma ta bar mata dukiyarta a titi almajirai su sace, Abuturrab ya jinginar da kansa da kujeran motar yana kallon agogon wrist dinsa, wata yar tsohuwa ce ta xo wucewa da kullin icce a kanta, hannunta daya rike da yar leda, ta rike ha6a tana kallon jiddah tace "Har yanxu kaddararren awaran nan bai kare ba har na je inda xa ni na dawo? Ke dai kin yaye islamiyya ko, Amma Hansai dai daga d'an iska sai ita, ko da yake ba ruwana, ba dangin iya balle na Baba ace na fiye sa ido, amma banda haka kullum ke kenan bakin titi kina tuyan awara babu arabi ba boko ubanki kuma ba bakin magana ya xama mijin ta ce, to ba dai ruwana da abinda bai shafeni ba...." daga haka tayi wucewarta, Jiddah ta bi ta da ido hade da daure fuska, Abuturrab ya bi tsohuwar da ido har ta isa wani d'an kuturun gate ta bude ta shiga, ya sake kallon Jiddah dake gyara wutan murhun kusa da ita, Bibalo ce ta iso wajen rike da bokitin awara ta ajiye nan kasa tana fari da ido, fuskarta kamar warce ta shafa boju tace "Hansai dai tace na dubu da dari uku da tamanin ne kafin anjima da daddare kice na dubu da dari uku da hamsin kika gani tunda dama kin saba...." Ko kallonta Jiddah bata yi ba tayi wucewarta tana taunar cingam... Jiddah na fara xuba awaran a mai Abuturrab ya sauke glass din motarsa gaba daya yace "Ke malama jiranki nake fa, kina bata min lkci, kinsan minti nawa nayi a nan yanxu" Sai a sannan ta kallesa tace "Toh ai sai an soya ko baka ganin danye ne? Idan kuma danyen kake so ai magana xaka yi" Dauke kanta tayi ta ci gaba da abinda take, ya rungume hannu daga xaunen da yake cikin mota yana kallonta da mamaki yana sake apprehending abinda ta fada masa, sai bayan minti goma ta kallesa bayan ta kwashe awaran da ya soyu tace "To na nawa kake so?" Ya mata wani kallo yace "Me kika ce min daxu? Sake fada in ji" Ta rufe awaran da ta kwashe a takaice tace "Toh baxan siyar ba, ka tafi gaba can akwai wata me awaran a gaba" muryar Hansai taji a bayanta tana cewa "Bai soyu bane Jiddah, ko ba awaran me motar xai siya ba? Baxa kiyi da jini ba kin xauna kamar wata rubabbiya ni Hansai" da sauri Hansai ta karaso tana kallon Abuturrab tace "Alhaji yi hakuri a kwashe maka yanxu, ta nawa kake so?" Abuturrab na tada motarsa yace "Ae tace ba na siyarwa bane, in tafi akwai a gaba" Da sauri Hansai ta bude roban awaran taga soyayyen awara da ta kwashe a jibge, ga wasu ta xuba a mai, wani lafiyayyen mari ta wanke ta da shi tace "Ubanki ne xai siya wannan da kika kunshe min a gwagwa? Yo ina ma yaga arxikin siyewa tukun, muguwa, axxaluma yar bakin ciki, to Allah ya isa cutata da kike...." Wani marin ta sake wanka mata a mugun fusace ta hankadata, Abuturrab ya xaro ido yana kallon ikon Allah, Hansai ta juya garesa da sauri tana dukawa tace "Don Allah kayi hakuri Alhaji, kayi hakuri Alhaji.... wllh akwai na nawa kake so?" Kasa ce mata komai yyi, ya kalli Jiddah da ta mike tsaye tana shessheka ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta, Yace "Toh har ya kai ki mareta haka??" Hansai ta kara hankade Jiddah da karfi tace "Toh idan ban mareta ba me xan mata, wannn da kake gani makira ce me mugun hali, kuma babu abinda na rageta da shi wllh tllh" cikin tsawa tace "Baxa ki bace min daga nan ba sai na watsa maki man kaskon nan a jiki gaba daya?" Matsawa tayi daga wajen tana kuka sosai, Hansai ta kara turata tace "Muguwa bar min awarata xan karasa suyan, ki je wannan tulin wankin na tsakar gida ban son in xo in ga ko hankici a kasa, duk in samesu kan igiya da lema" Tafiya kawai Jiddah take bata ce komai ba tana kuka, Abuturrab dai dauke kansa yyi, Hansai ta marairaice murya tace "Kayi hakuri Alhaji nasan ta 6ata maka rai sosai, na nawa kake son awaran?" Yace "Dubu daya" da sauri ta shiga saka masa har ta gama sannan ta mike ta kai masa ya bata kudin ta risina ta amsa tana murmushi hade da godiya, bai ko kalleta ba ya ja motarsa ya bar wajen. Washegari Saturday Abuturrab da yamma ya shirya ya fito daga dakinsa, Umminsa ce xaune parlor da Stepmum dinsa, duk 'yan matan gidan sun tafi makaranta, Ummi ce ke magana Aunty na ta kallonta absentmindedly lkci lkci tana duba wayar hannunta, Ummi tace "Ai mu ma ba sonmu Allah ya fi yi a kansu ba, toh meye a ciki don ta shigo nan ta xauna?" Aunty tace "Haka dai kike ga babu komai a ciki, amma kina da labarin kudin cixo na makalewa jikin kaya kuwa?" Ummi tace "Gashi ai naji a bakin ki yau" Aunty na kallon Abuturrab tace "Kai ka ji fa Aliyu.... Musa me gyaran fulawa ne ya xo da matarsa da yara uku wai sun xo gaishemu daga kauye ina laifin parlan can na boys quarter da har sai sun xo nan don Allah, baka gansu ba wllh abun ba acewa komai, ni yanda kake da kyankyami ma nasan da kyar idan baka yi throw up ba, sai fa da nasa turaren wuta a parlorn ynxu...." Abuturrab ya d'an yi shiru, can kasan xuciyarsa yace for peace to reign.... Sai kuma ya dago kai a bayyana yace "To ai can din ya kamata suje dama ba nan ba Aunty" Wani kallo Ummi ta jefa masa, yayi murmushi yace "That's the fact mum, ita Aunty tsoron bedbugs take...." Aunty tace "Toh ita cewa tayi wai ba a kyauta ba, haka kawai a bada mana kudin cixo a parlor a cuce mu?" Ummi tace "Toh Allah ya baku sa'a, idan walakanta d'an Adam abun yi ne, ku ci gaba" Abuturrab ya shafa kansa ya nufi kofa, Aunty tace "Ina xa ka Captain?" Yace "Xanje wajen wani abokina he just arrived from New york...." Har ya fita parlon Ummi bata ce masa komai ba, yyi murmushi bayan ya shiga motarsa, ko ina ruwansa da 'yan kauye da suka xo da Aunty xata yi involving dinsa at d first place, girgixa kai yyi ya tada motar ya bar gidan, tafiyar kusan minti talatin yyi tunani iri iri na yawo a ransa, ba kasafai yake kwana da abu a ransa ba, infact it's very rare hakan ya same sa, amma jiya ya kwana da yarinya me awara a ransa, dalili kuwa he lead to her been maltreated, she was slapped severally because of him, he felt guilty shi ne ma yasa ya kasa samun nutsuwa a ransa, yana isa dai dai gun da take awaran ya tarar bbu kowa, alamar ba ayi awaran yau ba, yyi ta bin dirty unkept layin da kallo wanda ko mota ba lallai ya iya bi ba sbda gutters dake kwance ta ko ina, ji yyi kamar yyi amai, hankalinsa ya tashi sosai Bibalo ce ta xo wucewa fuskarta yau ma dai kamar warce tayi dambe da powder ga bakinta ya sha jan janbaki, lkci daya ya ganeta, ya sauka motarsa da sauri yana yamutse fuska yana kallonta yace "Yau babu abinda ku ke siyarwa ne?" Tayi fari da ido tana kallonsa tace "Ehh wllh, mijin kanwar babaarmu ne ya rasu yau da safe, tana can gidan mutuwar tace yau baxa ayi awaran ba" Yace "Ohk, ita warce take soyawan tana ina??" Ta wani yatsine fuska tace "Ohh wai Jiddah, tana can gida xata daura sanwan tuwon dawa, nima yanxu gidan mutuwar xa ni Baabarmu tace inje" yace "Ohkk, sai anjima" Tana murmushi tace "Toh sunana Bibalo kai fa?" Wayarsa ya ciro ya kara kunne snn ya koma cikin motarsa ya kulle, ta bi sa da ido sai bayan da yaga ta wuce snn ya bude motar ya tsirtar da yawu yana yamutsa fuska, ita kanta tsami take yi ga uwa uba warin gutter din anguwar, yaji gaba daya cikinsa ya fara hautsinewa, ya fi minti biyar xaune motar bayan ya cika Ac, har yaji ya dawo dai dai, wani yaro ya hango yana tafiya ya sauke glass ya kirasa, yaron ya xo, yana kallonsa yace "Wani gida ne ake awara a layin nan?" Yaron yace "Gidansu Bibalo ne" Ya sauko motar ya kulle sannan yace "Toh kai ni gidan" Nose mask ya sa a hanci bayan glass dake idonsa yana biye da yaron har suka isa kofar wani kuturun gida wanda shi dai ko dabbobi yake kiwo baxai sa su gidan nan ba don kilan Allah sai yayi ma dabbobin sakayya a kan ajiyesu da yyi a nan, gaba daya tsigar jikinsa tashi yake ga cikinsa da ya fara hautsinewa again, he have never been uncomfortable all his life kamar wannan moment din, yana kallon yaron da kyar yace "Shiga ka kira min me awaran" Ba musu yaron ya shiga, can sai gashi ya fito yace tana xuwa, ba a dau lkci ba sai gata ta fito, Hijab ne ta saka iya cinya sai xanin jikinta, gefen farin fuskarta duk bakin gawayi don wuta take rurawa, kallonsa kawai take alamar bata ganesa ba, ya sauke nose mask dinsa, ya cire glasses din idonsa, lkci daya gabanta ya fadi sosai bayan ta ganesa, hakan kuma bai hanata hade rai tana kallonsa ba duk da a tsorace take, shi ma dai cike da karfin hali yace "A xaton ki an mareki jiya sbda ni?" Kauda kai tayi, ya hade rai yace "Ki juyo ki kalleni ina maki magana" Ba tare da ta juyo ba tace "Ni dai ka rufa min asiri bance an mareni sbda kai ba, me ya sake kawo ka nan, in dai awara ne yau babu bamu yi ba" kallon yanda take maganan yake wanda komai ta fada sai dimples dinta ya lotsa, ta kallesa jin bai ce komai ba tace "Nace maka babu awara yau" Yace "Ohk dama sai kuna awara kenan kike wanka ki xauna bakin titi?" Ta wani xare ido tace "Ni nace maka banyi wanka ba??" Tana fadin haka ta kalli Hijab din jikinta wanda shima duk bakin gawayi ne hade da xaninta, slippers din kafarta ma duk ya tsufa, haka kawai ta ji kunya ya rufeta, ta 6ata rai tace "Ni sai kace nace ma banyi wanka ba, bayan girki nake yanxu" Bai tankata ba ya mayar da nose mask dinsa da glasses dinsa ya juya ya bar wajen ta bi sa da ido kamar me shirin kuka har ya kusa bakin titi snn ta juya a hankali ta koma cikin gidan nasu. 💖💖 *Jiddatul~ Khair*💖💖 _By Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 3..... Karfe taran dare Jiddah ta fito tsakar gida ta xauna kan tabarman dake bakin kofar dakinsu, muryar Hansai ne ya kaurade d'an tsakar gidan tana ma mai gidanta isuhu masifan ita ta gaji da ciyar da shi, shi dai yana xaune baya cewa komai hakan yasa tayi ta daga murya wanda da kyar ba a jin ta a kofar gida, a hankali Jiddah ta mike ta sa takalminta ta fita gidan, wani karamin gida can karshen layinsu ta tafi, tana waige waige ta shiga zauren gidan sannan ta karasa ciki, Wata yar dattijuwa ce tsakar gidan xaune tana ma yara uku dake kwance kan tabarma fifita, Datijuwar tace "An gama tuyar kenan..." Jiddah ta kwance ha6ar xaninta ta ciro dubu biyu tace "Aa yau ai bamu yi ba Baabarmu taje gidan gaisuwa, Iyah ki ajiye min wannan Usman ne ya bani daxu mun hadu bakin titi naje auno waken suya, ki dau dari biyar, sai ki ajiye min dari biyar sai ki sa dubu dayan a asusun da nayi ma Abbana" Iyah tace "Kai Allah dai yyi ma yaron nan albarka, kwana biyu ma bai shigo ya gaisheni ba, ni da a shirye yake ai da ya fito kawai ko Allah xai yanke maki wnn shegen wahalan, kai ko da akwati daya yayi maki indai xai rabaki da Hansai yafi maki wllh, ba yace min a can cikin gari yake da iyayensa ba, nan kuma wajen kanwar babarsa yake xuwa?" Jiddah ta gyada mata kai ta mike ta nufi kofa tace "Sai da safe Iyah kar baabarmu ta nemeni" Tana fadin haka ta fita da sauri kafin a lura bbu ita a can gida, Iyah ta girgixa kai tace "Allah sarki, tsakaninsa da Allah yake sonta wllh, tsorona daya makirar bakar matar can kada ta shiga ta fita ta raba su, tunda ga bibalo babu mashinshini har yanxu sai yawon unguwa unguwa take a hayi, kuma duk sa'annin juna ne, to dai bbu ruwana tunda babu dangin iya balle na baba" Ahmad ya gama sa cover shoe dinsa yana kallon Abuturrab dake kwance kan 3 seater hannunsa rike da remote yace "Ya naga kamar duk ka damu in tafi ne Captain?" Abuturrab ya kike xaune yace "Ohh toh ka yi xamanka mana ina ruwana, dama don kace kana night duty ne yasa nake ta reminding dinka, naga it's almost 6, an kusa kiran magrib" Ahmad ya ta6e baki ya mike yace "Yaushe xa ku wuce kanon ne?" Abuturrab yace "Am off for someday kawai i just decided to be in Abuja for a while, may be on friday xan bi train in sha Allah" Ahmad yace "Ohh that's great nima friday nake son xuwa kadunan, rabona da kaduna ai an kwana biyu" Daga haka ya nufi kofa ya fita, yana fita gidan ko minti goma ba ayi ba Aneesah ta shigo, Abuturrab na kallonta yace "Sorry i kept u waiting kinsan Ahmad...." Ta karaso parlon tace "Yeah i understand..." Xaunawa tayi ta ajiye jakarta, ya dawo kusa da ita yace "Kwana uku xan yi a Abuja...." Ta wara ido tace "Har uku?" yace "Yea, ko baxa ki tayani xama ba?" Ta juya ido tace "Aa kaga Dad dinmu yana gari, sai dai in dinga xuwa Ina tafiya..." Ya jingina da kujera yace "No need inyi kwana uku kenan, gobe inyi tafiyata kaduna dama sbda ke na sauka Abuja" Ta marairaice masa tace "Haba dear, to kar ka damu i will try and be with u" Mikewa tayi tace "Me xan girka maka nasan har yanxu baka ci abinci ba" Yace "Just a cup of tea now, mun sha fruits tare da Ahmad" bude kofar aka yi duk suka juya lkci daya, Ahmad ne ya shigo parlon, kallo daya yyi masu ya nufi gun da ya mance wayarsa ya dauka, yana kallon Abuturrab yace "Shi yasa ka damu in tafi kenan" Aneesah dai daure fuska tayi, kamar baxata ce komai ba sai da ya nufi kofa tace "Ina yini?" Banxa yyi mata ya fita ya kulle kofar, Abuturrab ya shafa kansa, a hankali tace "But am afraid Captain..." Yace "You are afraid of what?" Komawa tayi ta xauna da damuwa tace "I think this is the 5th time da Ahmad ke ganina a gidanka, ina tsoron kada ya sa iyayenku su ki amincewa da aurenmu" Abuturrab yace "Ni xan xauna da ke ko wani, don kina xuwa gidana does that mean anything?" Ta girgixa kai bata dai ce komai ba, ya mike ya isa kusa da ita ya kamo hannunta yace "Cheer up dear, beside Ahmad will never do that, i know who he is" kallonsa tayi da manyan idanuwanta ya sakar mata lallausan murmushi ya kai hannu dogon hancinta yace "Basu san samun me tsafta irin ki yanxu sai mutum ya dage ba?" Murmushi kawai tayi yyi pecking cheeks dinta yace "Babu wanda xai raba mu in sha Allah" hanyar kitchen ta nufa ya bi ta da kallo. Suna fitowa train station suka nufi motar dake tsaye yana jiransu, Ahmad ya bude back seat yana kallon saurayin dake xaune driver seat yace "Sorry for keeping u waiting salem, mun hadu da wani abokinmu ne muka tsaya gaisawa" Salem na murmushi yace "Ina yini ya Ahmad" Ahmad yace "Lafiya lau, ya su Aunty" Salem yace "Lafiya kalau" Abuturrab ya xaga ya shiga front seat bayan ya gama wayar da yake yana kallon stepbrother din nasa yace "How are you" Salem yace "Fine, how was the journey?" Abuturrab yace "Cool" Driving din motar salem yyi suka fara tafiya, tunda suka hau saman titin hayi idon Abuturrab ke gefen hanya, Ta madubi ya kalli Ahmad dake danna wayarsa, da kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Yau baxa ka siyi awara ba kenan" Sai a sannan Ahmad ya dago kai ya kalli inda suke, ganin sun kusa wajen da yake siyan awaran yace "I had no intention but let me get it for Umma and my siblings" Abuturrab ya ta6e baki bai ce komai ba, Ahmad na kallon Salem yace "Kana wuce layin nan ka tsaya a layin gaba" Salem yyi parking dai dai inda Ahmad yace, Ido hudu Jiddah tayi da Abuturrab da sauri ta sunkuyar da kanta tana gyara hijab din jikinta, Ahmad ya bude motar ya sauka yana kallonta smiling broadly ya rungume hannunsa yace "Sannu me awara" Bata yarda ta kallesa ba tace "Ina yini" yace "Lafiya lau ya kasuwa?" Tace "Na nawa xa a sa maka?" Yace "Ki sa na dari biyar ko?" Satan kallon Abuturrab tayi suka sake hada ido ya dauke nasa idon yana kallon gefen hanya, ta gama sa awaran ta mike ta mika ma Ahmad, ya amsa yana kallonta, sae kuma ya juya ya kalli Abuturrab yace "Bani 1k wajenka I'm not with cash" Abuturrab bai ce komai ba, ita dai tana tsaye, can ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu daya ya mika ma Ahmad, Ahmad ya amso ya mika mata ta amsa ta koma ta durkusa xata dauko canji yace "Aa ki bari idan na xo sake siya, shkkn ba sai na sake bada kudi ba koh?" shiru tayi, lkci daya ta mike tace "Toh ai akwai canjinka dari biyar a wajena da ka siya ranan nan, ka tuna?" tana fadin haka ta mika masa dubu dayan, yace "Aa ni na manta..." Daga haka ya shiga mota yace ma Salem su tafi, da ido ta bi motar sannan ta koma ta xauna gun kaskon awaranta. Hansai ta rike ha6a tace "Yau naga ikon Allah, baxa ki fito ana jiranki ba Jiddah???" Sai kuma tana murmushi ta kalli Iliya dake xaune kan tabarma tace "Da yake bata yi la'asar ba kilan sllh ta fara, bari in shiga ciki dai" daga haka ta mike daga kan kujeran tsugunno da take ta shiga dakin, can taga Jiddah xaune kusa da ghana must go din kayansu tana kuka a hankali, Bude baki Hansai tayi tana kallonta, can ta karasa a mugun fusace ta fincikota ta bugata da bango murya can kasa tace "Don ubanki kina ji na kika kyaleni bawan Allah ya xo tun daxu yana jiranki? Saukansa fa kenan daga legas yace kuma anjima da daddare xa su bi tirelan kaya su koma" Cikin rawan murya hawaye na sauka idonta tace "Wllh Baabarmu bana sonsa, shaye shaye fa yake...." Bata rufe baki ba Hansai ta buge mata bakin da karfi ta rankwasheta ta hankadata bakin kofa tace "Fita kar in sumar da ke, yar bakin ciki kawai muguwa" Goge hawayenta tayi ta fita da sauri tana hadiye kukan dake son subce mata, Can nesa da tabarman ta xauna ta hade rai taki cewa komai, Iliya na murmushi da jajayen idonsa yace "Hauwa kuluwa kwandon kilishi..." Sosai ta kara hade rai, yace "To d'an kalleni mana farin cikin xuciyataa" wani harara ta xabga masa, yayi wani murmushin da lebensa da ya dafe saboda shaye shaye ga idanuwansa kamar garwashi, yace "Mun sauke wani kayan ne yau, amma mun yi lodi xa mu koma xuwa nan da bayan magariba" Ita dai ko kallonsa bata sake yi ba, ya ciro rafan 'yan ashirin ashirin guda biyu sababbi ya ajiye kusa da ita yace "Hansai tace Babanki ya bukaci in turo magabatana, to in sha Allahu ranan laraba xamu yo lodi daga lagos, ina dawowa kuma xan turo tsohona da yayansa, a nan take ma xa a bada sadaki a saka mana rana, don ni a shirye nake" Wasu hawaye suka kawo idon jiddah, ya mike yace "Kice ma Hansai na tafi sai Allah yayi mana dawowa" daga haka ya fita ta bi sa da kallo da dafaffen farin shaddan jikinsa, yana fita Hansai dake la6e tana sauraron duk abinda yace ta fito, dauke kudin tayi tace "Allah yayi masa albarka, ai iliya ba dai xuciya ba, ga masara can ya kawo mana rabin buhu, da wake xai yi kwano biyar wllh, Allah yayi masa albarka" tana gama fadin haka ta dau gyale ta fita gidan..... Jiddah ta hade kai tana kuka sosai, mikewa tayi ita ma ta fita gidan, ta shiga gidan iyah, Iyah ta dinga salati tana kallonta ganin yanda take kuka, duk lallashin duniyan nan tayi mata amma taki sauraronta balle tayi shiru, Iyah tace "Atoh bari in je in ci gaba da tankade gari na kawai" daga haka ta mike ta koma gun da take tankadenta ta xauna ta ci gaba, Da kyar Jiddah ta dago kanta bayan wani lkci tana share sauran hawayen idonta cikin rawar murya ta shiga gaya ma Iyah abinda ya faru, Iyah ta ajiye matankadin hannunta tace "To ubanki ya xama sususu shashasha kenan, banda haka meye mutum xai maida kansa kamar gunki, ko min wani irin asiri tayi masa ai bai ci ya xama kamar gunki haka ba, mutum kawai bai da amfani Allah na tuba, Hansai dai wllh baxata gama da duniya lafiya ba, me yasa bata ba ma Bibalo iliyasun ba, waye bai san iliya ba a garin nan, kawai don axxaluma ce ita ta dage sai ta hadaki da d'an gwangwan d'an shaye shaye? Ranan babu inda labari bai kai ba kan cewar Iliya ya mari mahaifinsa, ba ga uwarsa can a kana radd ba tana 6ara, kanninsa mata kuwa duk karuwanci suke kowa yasani ba wani boyayyen abu bane, ohh na shiga uku ni iyantama, kaiii Hansai da kyar taga annabin rahama, da tasan abun arxiki ne iliya wllh baxa ta so ki da shi ba sai dai Bibalo amma da yake tasan waye shi sai cusa maki shi take alallai adole...." Jiddah dai kuka kawai take, Iyah tace "To dai ba ruwana nawa ido tunda 'ya yana sun hanani shiga maganan da bai shafeni ba, barin ma na gidan Hansai matar da bata gaji mutunci ba" tana fadin haka ta tafi ta ci gaba da abinda take, a hankali Jiddah ta mike tana share idonta ta fita gidan kada Hansai ta koma taga bata nan. Abuturrab na xaune parlon Umma tare da Ahmad suna cin abinci a tare, Umma dake xaune tana kallo tace "Toh ba dole ku yi shiru ba dama" murmushi kawai Abuturrab yyi, Ahmad yace "Ni xan kawo maki ita ai ta gaisheki Umma...." Umma ta katse sa tace "Ka kawo min wa?" Bai kuma cewa komai, Abuturrab yace "Warce xai aura wai Umma" Umma tace "Akwai wata da xai aura bayan Ramlah ban sani ba?" A tare suka kalleta, Ahmad dai ya ci gaba da cin abincin gabansa bai ce komai ba, Umma tace "Ban da dai ku yaran yanxu abinda ku ke hange daban gida bai koshi ba ai ba a kai waje ba, is there anything wrong with Ramlah da baxaka iya aure ba?" Still Ahmad bai ce komai ba, Umma tace "Ni baxan yi abinda xai cutar da kai ba, meye da Ramlan da baka sonta ka gaya min" Jin bashi da abun ce mata ta mike ta fita daga parlon, Abuturrab dai sai kallon Ahmad yake, bayan few seconds Ahmad ya dago ya kallesa, d'an murmushi kawai yyi ya ci gaba da cin abincinsa, calmly Abuturrab yace "I dont want to believe kayi ma Umma shiru ne saboda Ramlah kanwata ce" Ahmad ya d'an kallesa sai dai he was mute, Abuturrab ya girgixa kai yace "Don't be quiet because of me, coz if i were in ur shoes i wont keep quiet, baka son Ramlah ga warce kake so to meye na yin shiru? Abinda ake tunanin shi xai karfafa xumunci shi ke 6ata shi, meet Umma.... Pour out ur mind to her, tell her who u intend marrying" Murmushi kawai Ahmad yyi ya maida dubansa kan TV, mikewa Abuturrab yyi yace "Xan amsan ma Ummi drugs a pharmacy so i will be on my way now" Ahmad yace "Alright, anjima da daddare xan shigo in sha Allah" Abuturrab yace "Ok then" daga haka ya fita parlon, amma sai da ya fara shiga main parlor yyi ma kanwar Mahaifiyarsa sallama sannan ya fita gidan. Abuturrab na bedroom dinsa bayan magrib Ahmad ya shigo, Ramlah ce biye a bayansa hannunta rike da cup din shayi da xata kai ma yayanta kamar yanda ya sa ta, Ahmad ya xauna gefen gado, Abuturrab na kallon Ramlah bayan ta ajiye shayin yace "Aunty ta dawo?" Ta girgixa kai tace "Aa bata dawo ba" Yace "Ohk" Ta kalli Ahmad dake danna wayarsa tace "Ya Ahmad su Umma fa?" Ya kalleta yace "She is fine, ya school?" tace "Lafiya lau, ya su Siyama" Yace "Alhmdlh" tace "Kai ma in hado maka shayin?" Yace "Aa sai kace nine Abuturrab" Dariya tayi, Abuturrab dai bai ce masu komai ba, ta nufi kofa, bayan ta fita Abuturrab yace "Mun yi waya da El-Basheer daxu yana gaisheka" Ahmad yace "Oh Yarima, kwana biyu bamu yi magana da shi ba ma" Abuturrab yace "Xai shigo Kadunan amma may be kana Abuja lkcn" Ahmad yace "Allah sarki, Allah ya kawosa lfya" Abuturrab yace "Did u talk to Umma?" Ahmad yace "About what?" Abuturrab yace "Ohh har ka manta" Ahmad yyi murmushi yace "No i dont need to, tunda ga abinda Umma take so, in sha Allah hakan xa ayi" Abuturrab ya mike a fusace yace "What nonsense, why will u say so bayan kai ba son hakan kake ba" Ahmad yace "Tunda Umma tana so nima dole in so" Abuturrab yyi masa kallo yace "Why just speak like an illiterate now?" Ahmad yace "Wait Captain, is there anything wrong with Umma's choice?" Abuturrab yace "Yes tunda ba son choice din kake ba" Dariya Ahmad yyi yace "Mun ta6a magana da kai nace bana son Ramlah? Asali ma duk cikin cousins dina babu wanda muke shiri da irin Ramlah, Ramlah was kinda brought up in our home since she was 2, tunda takwaran Umma ce kuma rainonta ce ita shi yasa take son ta hadamu, fine if Ramlah is okay with that ni bani da damuwa" Tsaki Abuturrab yyi ya koma ya xauna, Can yace "Ita kuma Maryam din dama yaudaranta kake kenan?" Ahmad yace "Idan wani xai min wnn kallon banda kai Abuturrab, it's just that my Umma's choice is my choice" Abuturrab ya jawo wayarsa dake ring ganin Aneesah ke kiransa ya katse ya shiga kiranta, Ahmad ya mike yace "Bari in gaida Ummi" daga haka ya fita dakin.... 07087865788✍🏻 💖💖Jiddatul~Khair💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 4...... Jiddah ce xaune kusa da Abbanta dake kwance tsakar gida saman tabarma da wani pillow da ya yakune, hawan jininsa ne ya tashi tun daren jiya, magunguna ne ajiye daga gefensa wanda da kudin da take tarawa wajen Iyah ta samu ta siyo masa magungunan, ko bi ta kan inda ta samo maganin Hansai dake ta yankan dafaffen awaranta bata yi ba, Sosai Abban nata ke jin jiki shi yasa duk hankalinta ya tashi, Hansai dai sai ta6e baki take, lkci lkci kuma tayi tsaki har ta gama abinda take yi ta mike tace "Yau ai sai ki xuba ruwa kasa ki sha tunda baxaki siyar min da awara ba kin wani makale kusa dashi wai bai da lafiya, to a duniyar nan yanxu wake da lafiya? Kowa ba lallaba kansa kawai yake yi ba, idan ka xauna ka fake da ciwo ai sai yunwa ta kar ka, ko da yake shi kwanciyar tasa ma da rashinta duk daya ai, Atoh duk daya mana tunda mace ce ke rike da gidan" Daga haka ta daura roban fentin dafaffen awaranta a kai da jarkan man gyada tace "Idan kinga dama in Bibalo ta dawo kice ta sameni bakin titi, tun safe ni ko ganin gilmawarta ban yi ba ko ina taje oho" kofa ta nufa da xaninta da yyi dukundukun xata fita, Jiddah ta goge hawayen dake makale idonta tana kallon Abbanta a hankali tace "Sannu Abba...." Bai iya yace mata komai ba, Hansai ta saka kai xata fita suka kusa cin karo da Iyah, Hansai ta koma baya tana washe baki tace "Sannu da xuwa Iyah" Iyah tace "Yauwa Hansatu, ya me jiki naji ance Isuhu bai ji dadi ba" Hansatu tace "Wllh da sauki kuwa, ga magungunan da na siya masa can ma, to ko kwayan hatsi bamu da shi a gidan shine nace Jiddah ta xauna tare da shi in fita in siyar da awaran nan, ba wata me yawa bace ta dubu uku ce kawai don dai a samu na cin abincin yau da gobe, kinga ai ba a xauna dukka ana jinya ba" Iyah tace "Gaskiya ne, Allah dai ya rufa asiri, yi maxa yamman ma tayi, Allah ya bada sa'a" Hansai tace "Ameen" Daga haka ta fita gidan, Iyah ta karasa ta dau kujeran tsugunno ta xauna tace "Sannu Isuhu" Da kyar ya gyada mata kai, Iyah ta rike ha6a tace "Farin mutum bafillatani duk ya kode kamar bai ta6a haske a rayuwarsa ba, Allah dai ya baka lafiya ya rabaka da cutan nan" Nan ma dai ya gyada mata kai, Iyah ta kalli Jiddah tace "Ya sha magungunan kuwa?" Jiddah ta gyada mata kai, Iyah tace "Toh Allah ya yaye masa" A hankali Jiddah tace "Ameen" Iyah ta bi d'an kuturun tsakar gidan wanda hansai ta mayar kamar na mahaukata da tarkacenta da kallo snn ta ta6e baki ta maida dubanta kansa tace "Amma kana ji na Isuhu" shi dai kallonta kawai yake yana numfashi da kyar, tace "Don muhammadurrasulillahi S.A.W.... ba a dai san gawan fari ba amma ka dubi Allah ka gaya ma wnn yarinya Jiddah inda dangin uwarta suke taje ta nemo su a fadin duniyar nan" Ya sauke numfashi da kyar muryarsa baya fita sosai yace "Iyah Mahaifiyar Hauwa 'yar Nijar ce...." Iyah tace "Kullum xancen ka kenan Mahaifiyarta yar Nijar ce, to a Nijar din bata da dangi ne Isuhu?" Ya sauke wani numfashin yace "Ni dai kowa yasan ni maraya ne ina almajiranci Uban gidana Alhaji Auwal ya daukeni ya rike kamar d'an sa sbda duk safiya xan wanke masa mota in share masa tsakar gida har ma in je masa aike, ni ban san garinsu Amina mahaifiyar Jiddah ba a Nijar din, ni dai tace min su 'yan Nijar ne, rana daya uwarta ta daukota suka dawo Nigeria wanda babu tantama kurciya aka mata, ko da suka dawo Nigeria basu walakanta ba don wata Hajiya ta amshe su hannu bibbiyu kakar Jiddah na masu aiki...." Iyah tace "To kai duk a ina kasan wannan labarin da ka kunshe ma cikin ka isuhu?" Yace "Mahaifiyar Jiddah ta bani labarin" Iyah tace "Toh ina ji" a hankali yace "A haka har Allah yayi haduwata da Mahaifiyar jiddah ranan naje kasuwa mai dakin uban gidana ta aikeni, ita kuma Jiddah Mahaifiyar ta aiketa, ban wani sha wahalan samun Mahaifiyar Jiddah ba sbda uban gidana ne ya tsaya min kan komai, a gidan da muka xauna wanda uban gidana ya kama mana haya a lkcn, muka hadu da Hansatu tana xuwa gun kanwar Mahaifiyarta, suka shaku sosai da Amina Mahaifiyar Jiddah duk da ko a lokacin Hansatu xata yi Shekara kusan talatin da wani abu amma bata ta6a aure ba, a lkcn kuma aurenmu ko shekara bai yi ba da Aminatu, ni dai nasan watarana na dawo daga kasuwa Amina ta sani gaba ai sai na auri Hansatu sun xauna tare yau Hansatu ta 6ata labarinta da irin tsananin da ake mata a gida duk don bata samu mijin aure ba kuma taji tausayinta sosai, wllh wllh Auren Hansatu kaddara ce daga Allah amma Amina ce sila, ta takurani, hatta iyayen gidana basu amince da auren ba a sannan, amma sbda son da nake ma Aminatu bana kuma son bacin ranta na lallabasu sai dai sun nuna min babu ruwansu a batun auren kuma babu biyar dinsu a auren, yawanci xannuwan da nayi ma Hansatu na lefe ma xannuwan Aminatu ce ta bani, kinji dalilin auren Hansatu, ni baxan ce sun yi xaman tashin hankali ba gaskiya don ko hakan ya faru Amina bata ta6a nuna min ba don har yau ban ga mace me hakurin Amina a duniya ba duk da xaman mu bai yi nisa ba don ta haifi Jiddah da shekara daya ta rasu, a lkcn Hansatu na da cikin Bibalo kin ji yanda rikon Jiddah ya koma gun Hansatu tun ba a yayeta ba, Uban gidana ya so Jiddah ta dawo wajensu bayan rasuwar Mahaifiyarta amma Hansatu ta saka mana kuka xa a rabata da jiddah, ita a bar mata ita xata raineta kamar yanda xata raini Habiba su taso tare, hatta Mahaifiyar Amina ta so amsan Jiddah bayan rasuwar 'yar ta, Amma Hansatu ta bi ta da dadin baki taki bata, ashe ita ma ba mai tsawon rai bace, don bayan rasuwan Amina da shekara uku ita ma ta rasu...." Jiddah dai kallon Abban nata kawai take don bai ta6a bata labarin nan ba sai yau, ta dai sha jin mutane na cewa Hansatu ba baabarta bace amma bata yrda sbda ita ta taso ta gani, Iyah sai girgixa kai take tana cewa "Allah me girma, ashe dai Hansatu baxata wanye lafiya da duniya ba... wuhuhu, Allahu akbar, To su iyayen gidan naka suna ina suka bar ka ka walakanta ka gantale haka, ai ko ba komai nasan sun ci moriyarka dai ba adadi" lkci daya Hawaye ya kawo idonsa yace "Hansatu ce dae ta rabamu, Alhaji Auwal ya bani kudi miliyan 2 in kai masa banki ban samu xuwa bankin a ranan ba sbda ruwan da aka yi kamar da bakin kwarya ina tsoron bin hanya da kudi haka, sae na dawo gida da kudin, Hansatu ta xare dubu dari biyu a ciki, kudi ko sama ko kasa, sbda Alhaji Auwal din yace bai yrda ba bayan na sanar masa 6atan kudin da naga bani da mafita, shine matar nan taje har gida ta ci masu mutunci ba na wasa ba, basu yi mata komai ba amma shine har yau, kudi kuma yace ya yafe min ya dai amshi sauran kudinsa, to kinji abinda ya faru... Wnn gidan ma da muke ciki ai shi ya siya min wllh, yau shekara bakwai kenan da ya bar kaduna suna Abuja da iyalansa" Iyah tayi tagumi tace "Yau naga tsinanniyar mata, dama ance ita ta talauta ka da ba haka kake ba, ilai ga magana ta fito...." Yace "Duk ta bi ta siyar min da filayena biyu da gonata daya, da wnn gidan kadai na tsira...." jiddah ta goge hawayen dake makale idonta duk jikinta yyi sanyi, Iyah tace "In sha Allahu xa mu ga karshenta kuwa, abinda Allah baya bacci, ynxu damuwata inda wnn yarinya jiddah xata samo danginta, to gidan da kakarta tayi aikatau a ina yake?" Yace "Wnn ai sun fi shekara sha biyar da barin kaduna, idan ko ba barin kaduna suka yi ba to sun sauya wani gidan ne don xuwana biyu duk akan haka amma aka sanar min sun tashi" Iyah tace "Abu ya lalace kuwa, banda haka ai baxata rasa basu labarin kanta da garinsu ba, kaga da ko su sai suyi ma jiddah hanyar xuwa dangin uwarta ita ma ta dawo mutum, amma ina mutum a nan ba dangi" girgixa kai kawai yyi, Iyah tace "Toh Allah ya rufa asiri, xaka ci tuwon masara da miyar kubewa in tafi in yi maka yanxu?" Jiddah tace "Xai ci iyah, tun safe bai ci komai ba sae kunu da ya sha" Mikewa Iyah tayi tace "Toh bari in je in hura gawayi yanxu ina da komai a gida, yanxun nan xan gama, to ae mayyar ba wani damuwa da rayuwarsa tayi ba, ehh Hansatu ba" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta ta ido har ta fita, murya can kasa yace "Kiyi ta hakuri kin ji Jiddah, wataran sai labari, nasan ban ta6a cutan wani tsawon rayuwata ba, ina fatan Allah ya dubi hakan, albarkacin hakan kada ya bari ki walakanta, Allah ya yanke maki wnn wahala da kike sha cikin gaggawa yayi maki abinda yafi alkhairi a rayuwarki, ina maki addu'an Allah ya baki hakuri da juriya da kauda kai irin na Mahaifiyarki Amina, kar ki kaga ana maki abubuwa ina shiru Jiddah, har gobe bani da kamar ki a duniya jiddah tun bayan rasuwar mahaifiyarki, Ban yi shiru a kan batun aurenki da wannan takadirin yaron da take ba, don har yanxu ban furta komai ba hakan ba yana nufin na aminta da auren bane, idan anyi duniya domin manzon Allah xaki auri mijin da xai kula dake yayi maki abubuwan da mu muka kasa maki, xaki auri wanda xai rike ki bisa gaskiya, wanda xai yanke maki wannan wahala da kike ciki in sha Allah" Hawaye ya shiga sakko mata ta kasa ce ma Abban nata komai, amma taji hankalinta ya kwanta sosai, da kyar ya ci gaba "In sha Allahu wannan takadirin ba mijin ki bane Jiddah..." ta gyada masa kai tana gyara masa kwanciyar kansa, ya lumshe ido yace "Tashi ki je kiyi wanke wanken da ta sa ki kar ta dawo kin ji" Ta goge idonta cikin sanyin murya tace "To Abbana Allah ya baka lafiya" Yace "Ameen Jiddah" Mikewa tayi ta tafi gun uban kwanukan da Hansai ta tula bakin kwararo k'uda sai fareti suke a kai, sbda yawan kwanukan sai kusan la'asar ta gama ta mike ta dau buta ta xuba ruwa jin ana kiran sllh ta ajiye inda Abbanta ke alwala ta koma kusa da shi ta durkusa tace "Abba ka daure ka tashi kayi alwala" Jin yyi shiru ta kai hannu jikinsa tace "Abba la'asar yyi...." hannunsa taga ya xamo kasa daga jikinsa, ta kamo hannun tace "Abba...." Shiru bai amsa ba, komin bacci ko rashin lafiya shi din ba me nauyin bacci bane, hakan yasa ta sake kiransa nan ma shiru, jijjigasa tayi taga dayan hannun ma ya xame, bata san lkcn da ta kwala wani ihu da karfi ba kan kace me mutane suka shigo gidan da sauri jikinta na rawa tace "Ku taimakeni Abbana yaki tashi" Wani makocinsu wanda har da shi ya shigo ya kai hannu jikinsa lkci daya ya saki salati yace "Isuhu ai rai yyi halinsa" Daga wnn Jiddah bata sake jin komai ba ta dai bude ido ta ganta kwance saman tabarma dare yyi ga mutane cike tsakar gidan. Bayan kwana uku, Jiddah na xaune tsakar gida da idonta da yyi bulu bulu ga wani rama da tayi don har sannan bata iya cin komai, Hansai sai faman yankan awara take tana cewa "Ke kadai aka ma mutuwa idan ba munafurci ba, Ita Bibalo ba ubanta ne ya rasu ba halan, munafuka kawai me neman suna, kin taso kin fita da kayan awara bakin titi ko sai na taso na nakada maki shegen duka, idan bamu yi awara ba yau ubanki xa mu kwakulo a kabari mu ci?" Hawaye kawai Jiddah take ta mike ta dau kaskon awara da coal pot da wasu kananun kayan ta fita xuwa bakin titi, Hansai tace "Ni wllh idan ba binsa kabarin kika yi ba bansan kina yi ba, bayan mutuwan da yyi ya bar ni da wahalan yi maki kayan aure duk da dai katifa da robobin kitchen kadai Allah xai hore min inyi maki, to ince me wnn wahalan da ya bar ni da shi, ina ta sintirin xuwa gidan Saude xaman makoki miji ya rasu ashe nima nawa na kan hanya xai tafi ya bar ni da wahala, to banda dai dama ya gaji da duniyar daga tashin hawan jini sai mutuwa Allah na tuba, shi dai yaji da munafurcinsa kawai dama ya gaji da duniyar ne, to ba dai ya mutun ba dai ai shkkn, yanxu ga aurenki dake ta karatowa ya gudu ya bar ni da wahala" A haka jiddah ta dawo ta sameta tana ta kumfar baki ta dau robon awaran ta fita, har sannan jiddah taki dawowa dai dai, gani take kamar mafarki take xata farka taga Abbanta bai rasu ba, har yau da aka yi uku abincin kirki ta kasa ci, don ma Iyah na tsareta sai ta sha kunu, banda tsine ma Hansai babu abinda yan anguwan ke yi ganin Jiddah bakin titi tana tuyan awara, daga mutuwar miji da kwana uku har ta ci gaba da awaranta wnn wani irin xuciya gareta, yawanci duk Jiddah ake tausayi don shkkn ta xama marainiya gaba da baya yanxu.... Abuturrab na kallon Ramlah dake yankan ma Umma Fruits yace "Umma ta ci abinci kuwa?" Ramlah tace "Aa bata wani ci ba, Amma Aunty Zainab taje gida xata yi mata tuwo yanxu" Ummi dake xaune kan farin kujera a ward din tace "Ga farfesun hanta ma da nayi mata bata ci ba" Abuturrab ya kalli Umma dake kwance da drip a hannunta yace "Umma ko a siyo maki awara?" Ta d'an yi shiru kafin a hankali tace "Toh Allah ya sa in iya ci, bana jin dadin komai a bakina" Ummi tace "Toh wannan ai dole ne Ramlah... Kawai daurewa xaki yi kici ko kadan sai kiji jikin ya maki kwari" Abuturrab yace "Toh bari in je in siyo maki yanxu" Daga haka ya fita, Slowly yake driving din har ya karasa hayi, dai dai u turn din wajen ya juya ya nemi waje yyi parking yana kallonta ta glass din motar, kanta a kasa tana juya awaran cikin man kaskon a hankali, ya sauke glass din motar yace "Ki bani awaran dari biyar" Dago kai tayi tana kallonsa, kallon idanuwanta da suka kumbura yyi, bata ce komai ba ta saka masa awaran yanda yace snn ta mike ta isa gun motar tana mika masa ledan, bai amsa ba yace "Kukan me kika yi haka??" Ta sauke idonta kasa, lkci daya xuciyarta yayi mata rauni wasu sabbin hawayen suka cika idonta, da mamaki yake kallonta, bata san lkcn da ta fashe da kuka sosai ba tace "Abbana ne ya rasu" Daga nan kuma kamar warce aka tunxura ta jingina da motar ta dinga rera masa kuka, a hankali underneath his breathe yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Kuka kawai take so painfully, ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ya bude motar ya sakko ya xagayo yace "Yaushe ya rasu?" Cikin kuka sosai tace "Yau aka yi uku" Da mamaki yace "Shine kika fito suyan wannan abun" Cikin rauni tace "Baabarmu ce tace sai na fito" Dauke kansa yyi, can yace "Awaran na nawa ne gaba daya?" Ta juya ta kalli roban awaran cikin shessheka tace, wai na dubu biyar tace min" Ya girgixa kai bai ce komai ba, can ya juya ya bude motarsa, kudin da ya ciro xa ayi masa delivering eye glasses da yyi ordering online ya dauko a motar, kamar wanda ya tuna wani abu ya fasa fito da kudin a haka sai da ya saka a wani ledan turare snn ya juyo yana kallonta, har sannan kuka take sosai, ya mika mata ledan kudin yace "Gashi ki kai mata kice ance kada ki sake fitowa sai an kwana biyu" Kallon ledan ta dinga yi da yyi mata dishi dishi sbda hawayen idonta ya kamo hannunta ya mika mata ledan ya amshi ledan awaran ya saka a mota yace "Allah ya gafarta masa" daga haka ya xaga ya shiga motarsa ya tada ya bar wajen, share hawayen idonta tayi ta leka ledan taga dari biyar sababbi dal a rafe, sosai gabanta ya fadi, ta kasa kwakkwaran motsi, wani almajiri ne yace "Awaran ki na konewa" Da sauri ta juya ta sauke awaran, ta xauna xuciyarta na bugawa da karfi, muryar Hansai taji a bayanta, Hansai ta ajiye bokitin wani awaran tana cewa "Ta dari biyar ce wnn, gaba daya ya kama dubu biyar da dari biyar...." ganin awara ya kone a mai tayi tsit tana xare ido, lkci daya ta saki salati da karfi tace "Na shiga uku awaran kika kona min Jiddah???" A mugun tsorace Jiddah ta mika mata ledan kudin tace "Baabarmu wllh wani ne ya xo ya kawo min wnn wai in kai maki kar mu sake fitowa sai bayan kwana biyu...." Hansai ta karbi ledan tana duba ciki da sauri, xaro ido tayi tana kallon tulin kudin cikin ledan, lkci daya ta dinga bin anguwan da kallo, murya can kasa tace "Daga ina yake?" Jiddah ta buda hannu har sannan jikinta na rawa tace "Wllh ban sani ba" Hansai tace "Dauko jarkar man da roban awaran mu wuce gida ai ya kare ma" A haka Jiddah ta kwashi kayan awaran ta bi bayan Hansai dake tafiya da sauri da sauri, A bakin kofar dakin Hansai Jiddah ta makale tana kallonta tana ta faman kirgan kudi duk ta hada xufa, har ta gama kirgen tana xaro ido tace "Dubu dari a wannan marran ni Hansatu, Allah yyi ma bawan Allahn nan albarka, yanda ya taimaki marayu Allah ya taimakesa haka shi ma, kaiii a duniyar nan ma dai xaman wasu toshe hanyar alkhairi kawai yake, banda haka daga rasuwan Isuhu kamar daga sama Allah ya jefo bawan Allah ya bamu dubu dari cif cif, yaushe rabon inga dubu ashirin da idona ni Hansatu" Jiddah dai ta sunkuyar da kanta xuciyarta na mata xafi bata ce komai ba, Hansai tace "Maxa ki sa ruwa kiyi wanka kema ko kya ji dadin jikin ki, kinga dai mutuwar nan alkhairi ne garemu sai kiga Allah yyi ta bude mana hanyoyi iri iri, aa ni dai wllh gwara da ya bamu hanya mu san me muke ciki a duniyar, to da ya baki kudin sai yace maki me?" Cikin sanyin murya tace "Yace kar in sake fitowa sae bayan kwana biyu" Hansai ta fashe da kuka tace "To dama banda talauci me xai sa mijina ya mutu in fara awara a ranan da aka yi sadakan uku, ai sai dai talaucin dama" Ta kara rushewa da kuka tana matsar kwalla da bakin xaninta, juyawa jiddah tayi a hankali ta bar bakin kofar tana dada jin mutuwar mahaifinta kamar a mafarki wanda hakan yasa hawaye kawowa idonta. *Still on free pages kar labari ya dauko maku dadi ku ga an datse don free pages din ba yawa ehee, u can proceed with payment sbda kawai a ci gaba ba sai an tsaya ba after free pages din, that is idan kunyi payment kenan fahh....*👌🏻 Tunda dai littafin me sunana ne wannan kunsan baxan gantalar da littafin ba, don haka kar kuyi fargaban komai ku ma baxan gantalar da xuciyoyin ku ba a gaskiya😹😹 Ping 07087865788 for payment details. 💖💖 Jiddatul Khair💖💖 _By Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 5..... Alhaji Usman ne xaune parlonsa tare da Hajiya Hauwa, ya ajiye wayar hannunsa yace "Toh ke ya kika ga Madam?" Ummi tace "Aa in dai tana so babu wani matsala daga gareni sai yanda kace" Ya jinjina kai yace "Toh shi Ahmad din ne yace yana sonta?" Ummi tayi murmushi tace "Toh wannan kuma gaskiya i can't say Alhaji" Abba yace "Toh sai na fara magana da shi Ahmad din da Ramlah, don ke da kanwar nan taki na lura kanku kadai ku ka sani" Yana murmushi ya kare maganar, tayi 'yar dariya tace "Aa ai baxa ayi masu dole ba dama" Yace "Toh Allah yayi xabi mafi alkhairi dai" Ta amsa da Ameen. Bayan sati daya aka saka ranan bikin Ahmad da Ramlah wanda xa ayi bayan wata uku. Abuturrab na gidansa na Abuja tare da Ahmad da shigowarsa gidan kenan, banda kamshi bbu abinda ke tashi a gidan, ko ina so very neat and tidy kai kace da mace a gidan, Ahmad ya fito daga kitchen rike da cup din coffee yana juyawa da spoon yace "Matar gidan bata iso ba har yanxu kenan" Wani kallo Abuturrab ya jefa masa, Ahmad yyi wani dariya yace "Ka gama yaudaran yar mutane daga karshe ka samu yar sweet sixteen ka aura abun ka" Abuturrab yace "Sai ince na auri me? Ashe xaka sha mamaki kenan idan kaga na auri Aneesah" Ahmad yace "Gaskiya don ban ta6a sawa a rai cewar xaka auri Aneesan nan ba, ku dai gama holewan ku tayi auren ta kayi naka" Abuturrab bai kuma ce masa komai ba ya maida hankalinsa kan TV dake aiki, Ahmad ya nemi kujera ya xauna yace "To in har da gaske sonta kake da aure kayi magana mana a saka mana rana daya gaba daya" Abuturrab that is already getting pissed up yace "You dont have to tell me what to do with my life dude..." Dariya Ahmad yyi yace "Of course, especially in a case like this" Tsaki Abuturrab yayi ya mike ya dau wayarsa ya wuce daki ya bar masa parlon... Ahmad na gama shan coffee din ya mike ya bisa xuwa dakin, xaune ya samesa da wayarsa yana magana alamar video call yake, Abuturrab ya kallesa sannan yace "Toh gashi nan ya shigo sai ku gaisa" Ahmad yace "Waye?" Abuturrab ya mika masa wayar, amsa yayi yana kallon screen din, suna hada ido ya buda baki yace "Mutanen Egypt ne dama" Bai rufe baki ba tace "Waye wannan???" Dariya yayi yana kallon uban glass da ta saka a ido fuskarta duk ya cika screen din wayar yace "To glass din kuma da kika maka haka wa ya ara maki?" Ji yayi tana cewa "Farida xo ki mayar min da fuskar Aliyu don Allah, kamar ya shiga wani kiran fuskar wani nake gani" Wata yar budurwa ce ta leko wayar ta xaro ido tace "Lahh Hajja ai Yaya Ahmad ne" Warce ta kira da Hajja tace "Kaji wani xance to ni ina ruwana da shi xa a sako min fuskarsa, ki mayar min da fuskar Aliyu nace, idan kuma baxai yiwu ba ki kashe kawai, waye kuma wani Ahmad, ni na san shi" Ahmad dake ta dariya yace "Nima ae ba saninki nayi ba kawai miko min wayar aka yi" Hajja ta sake wayar ya fadi tace "Ni dai na shiga uku, A gaskiya wannan ai walakanci ne da cin fuska, ya xan dinga magana da Aliyu fuskar wani kato ya fito, wayar taki ce ta lalace ko wa'adin da aka debar mana na magana da Aliyun ne ya kare aka sako min fuskar wani can" Farida ta ma rasa abun cewa sai dariya take, Ahmad ya katse wayar ya jefa gefen Abuturrab shi ma yana dariya, Abuturrab yyi murmushi yace "Yanxu fa take tambayar ka shine ka shigo na baka fa...." Iyah ce tsaye kan jiddah dake ta kuka kamar an aikota, A fusace tace "Toh meye amfanin wnn shegen kukan da kike ne wai, nace ki hado tsummokaranki in sa ki mota tunda da kudin ki a hannuna ki tafi legas wajen Salame kawai" Jiddah na kuka tace "Toh Iyah idan iliyan ya hadu da ni a legas din fa? Shi ma fa a can yake aiki ai" Iyah tace "Legas din bai fi Najeriya girma ba aka ce maki, ta ina xai ganki a gari me girma haka" Shiru Jiddah tayi tana kallonta wasu hawayen na sauka fuskarta, Iyah tace "Ni dai ba ruwana ina kokarin ganin na rufa maki asiri kar a aura maki takadiri kina min gardama, hakkin makotaka fa nake son in fita, banda haka me na hada dake Jiddah?? Sannan ni ce mutum ta karshe da Allah ya ba iko nayi hirar karshe da mahaifinki kafin ya mutu, to sai in xuba ido ki tagayyara ya kullace ni duk inda yake?" Jiddah ta sauke idonta dake xuban hawaye xuciyarta yyi rauni, Iyah tace "Atoh babu ruwana wllh, ba dai gobe xata tafi kasuwar tasha siyo kayan sana'arta ba, sai ki shirya tana fita in kai ki tasha kawai, ko da tirela ne sai ki bi xuwa legas din, amma idan ba haka ba shkkn rayuwarki ta lalace idan aka aura maki Iliyasu" Iyah na kai wa nan ta tafi gun tuwonta dake kan murhu tana cewa "Na fita hakkin ki duk da ba dangin iya ba na baba, amma hakkin makotaka fa??" Jiddah dai gaba daya jikinta yyi sanyi, she is too young to even think straight for her age, hakan yasa taji gwara kawai ta gudun don gashi har an xo an sa mata rana wata daya dai dai da Iliyasu a yau. Aunty na kallon Nafisa, cike da fada tace "Tashi ki fita ki ban waje" Ba musu Nafisar ta mike ta fita kamar xata yi kuka, Aunty ta dubi Abuturrab dake dakin yana kallonta tace "Wllh baka gansa ba Captain, ni dai ban ta6a ganin haka ba, banda yarinta da dolanci me xata yi da shi don Allah??" Abuturrab na cin Apple din hannunsa yace "Meye da shi wai Aunty?" Cike da takaici Aunty tace "Don dai sai da yamma ka dawo jiya da ka gane ma idonka...." Yace "Aa ni a garin nan ma nayi sllhn juma'ah, private jet muka biyo daga kano, sha biyu da rabi ina kaduna..." tace "To a ina ka tsaya sai bayan la'asar ka dawo gida?" Yace "Muna tare da wasu abokanmu" Aunty tace "Shi yasa, ai da ka gansa wllh... Muna xaune fa jiya da safe kamar abun arxiki tace mana wai Salis yace xai xo bayan an sakko juma'ah mu gaisa, na xata abun arxiki ne har da sa masu aiki su tayata yi masa snacks iri iri wai ashe gantalalle xata kawo mana..." Abuturrab dake ta kallonta yace "Toh meye da shi baki fada min ba har yanxu" Tace "Toh kaga Captain tun daga bakin titi da kafa ya tako har nan, ashe ko motar ma bashi da, sai kaga wani yakunannen yadin da ya sa bbu gugan arxiki, kana ganinsa dai kaga 'ya yan ya ku bayi, ni ko a raina nace ko ina wannan yarinyar ta samo mutumin nan haka, ni wllh a bakin stairs na tsaya amsa gaisuwarsa ban yarda na karaso parlon ba" Abuturrab yyi murmushi ya kai Apple dinsa baki yace "Wani sana'a yake yi?" Wani kallo ta jefa masa tace "Sana'a, wa ke ta wani sana'arsa banda abun ka, ko ka mance da wannan saying din that goes thus... The way u dress will be the way u will be addressed??" Abuturrab ya gyada kai kawai bai ce komai ba, tace "Wllh na sake ganinta tare da shi Allah sai na ji mata ciwo kowa ma ya huta, ita kuma Ummi da taya bera 6ari sai wani nan nan take da shi, tarba dai yanda kasan mutumin arxiki haka tayi ma yaron, ni ko kunya kamar in nutse wllh, Salem kuma inda ya burgeni ko kallonsa bai yi ba da ya shigo parlon kawai yyi wucewarsa daki..." Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya kyauta...." Tace "Ameen sai ka kirata and talk sense into her head... Ba ni xata kwaso ma abun kunya ba" Mikewa yayi, tayi saurin cewa "Captain ban kai ka kaje kaga filin da na siya ba ae" Yace "Xuwa gobe in sha Allah" tace "Lahadin xaka koma aikin?" Yace "Idan Allah ya yarda" Tace "Wancan satin kasa nayi maka tamarind drink baka dawo ba..." Ya shafa kansa yace "Wlh daya daga pilot din da xai yi piloting jirgi daga lagos xuwa port Harcourt bai ji dadi ba shine ni nayi, wnn satin ma ban yi niyyar dawowa ba coz i was so stressed out during the week" Tace "Gashi ko ka xo kadunan ba wani hutawa kake ba tunda ba xama kake gida ba" yyi murmushi kawai, tace "Sai kaji an sa ranan Ahmad da Ramlatu" Yace "So Abba told me" Tace "Atoh bai fi mata ba, yar uwarta ta tsaya kula ya ku bayin garin nan, Ahmad ai d'an gayu ne d'an boko ga hankali da nutsuwa duk da dai ni ba wani shiri muke da shi ba, though auren xumunci ne ma ai amma gwara hakan, Nafisa ma tace min ai tasan tsohuwar Budurwarsa Maryam islamiyyar su daya kafin ta canxa islamiyyan" Abuturrab ya nufi kofa yace "To Allah ya kyauta" Tace "Bayan an gama da na Ramlah sae a dawo naka da Aneesah ko?" Murmushi yyi yace "Allah ya kai mu lokaci" Daga haka yyi mata sallama ya fita yana duba agogon wrist dinsa, kira ne ya shigo wayarsa, ya duba ganin Aneesah ya daga ya kai kunne yace "Don't tell me har kin sauka?" Tace "God!!! Nima Don't tell me baka fito ba Captain" Ya wara manyan idanuwansa yace "Ban dade da shigowa gida ba... But in few mins time xan karaso I'm sorry" Bai jira me xata ce ba ya katse wayar ya fita ya hau motarsa.... Tafiyar minti ashirin ya kai sa train station, murmushi yyi ganin yanda ta hade rai tana tsaye daga nisa, abaya ne baki jikinta da yyi matukar amsan farin fatarta, ja da bakin lallen dake hannunta ya kara contributing wajen haduwarta a lkcn, she looks so sweet, mutane dai daya ne ke wucewa wajen basu kalleta sun sake kallonta ba, ya karasa inda take smiling, cikin soft voice dinsa yace "Sorry Baby, kinsan dole in je in gaida su Ummi da Aunty beside dole ma sai na koma gidan na dauko mota tunda ban dade da sauka ba nima...." Cike da shagwaba tace "Kasan mutane nawa suka tambayeni numbata tsayuwar da nayi nan yanxu" Yace "Sai kika basu kenan" Ta juya masa fararen idonta ta ki cewa komai, murmushi yyi ya amshi trolley din hannunta ya fara tafiya xuwa gun motarsa tana biye da shi tana kallonsa don komai yyi burgeta yake. A hankali yake driving din Aneesah dake gefensa tace "I learnt about Ahmad's engagement with Ramlah" idonsa na kan titi yace "So i heard also" Tayi kasa da murya tace "To mu kuma namu fa?" Still bai kalleta ba yace "Xa ayi" Tace "Yaushe??" yace "Am trying to put things in order first, i don't get why u are in a rush Aneesah, ba dai ni nace xan aure ki ba, meye kike damun kanki haka? Do i look like a liar or do my words sounds deceptive?" Ta kai hannunta kan nasa cikin sanyin murya tace "I just can't imagine loosing u My Captain, i just can't...." Yace "Keep ur mind at rest Neesah, i am all urs and urs alone" Yana fadin haka ya sakar mata murmushinsa dake kara narkar da xuciyarta, dai dai nan kuma ya kai layinsu Jiddah, yau bata awara a bakin titin don babu alamar ma ta fito, sai dai mutane ne cike fal a d'an layin nasu, a hankali yake driving din yana kallon cikin layin, Aneesah dake kallon direction din ita ma tace "What's happening there, ko anyi rasuwa ne?" kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Ko in sauke journalist taje ta gano mana???" Dariya tayi tace "Oops a wnn local area din xanyi journalism dina Captain? Haba this is so disgusting..." Tana magana tana yamutse fuska, shi dai bai ce komai ba yana ci gaba da driving dinsa, can gidan Kanwar babanta ya ajiyeta a unguwar sarki, bayan ya yi mata few shopping na kayan ciye ciye, ta sauka motar bayan yyi parking tana kallonsa, shi ma ya sauko ya fiddo mata da trolley dinta ya kai bakin gate din ya ajiye, ta dau ledan shopping din da yyi mata tana kallonsa bayan ya dawo cikin sanyin muryarta tace "Thank you My Captain, plss ka daure ka xo anjima da daddare mu yi hira..." Ya kashe mata ido yace "Ohk babe...." Daga haka ya shiga motarsa yyi reverse ta bi sa da kallo har ya fita layin tana sake jin wutan sonsa na ruruwa a xuciyarta. Abuturrab na komawa gida yyi parking nan kofar gidansu ya shiga ciki yyi alwala snn ya fito ya shiga masallaci don ana ta kiran magrib, bayan an idar ya fito masallacin ya shiga motarsa ya xauna yana danna wayarsa, ajiye wayan yyi yana kallon flowers dake xagaye kofar gidan nasu trying to imagine the meaning of the crowd they saw earlier a layin yarinyar nan me awara, did someone die again, tunanin hakan ya sa ya tada motarsa ya bar layin, yana isa yyi parking bakin titi ya dau nose mask dinsa a motar ya saka snn ya bude motar ya sauka, ashe da daddare sana'a ake yi sosai bakin titin layin, just like sauran layukan anguwan gaba daya, daga me soya wancan sai me soya wannan, masu siyar da gyada, rake, abubuwan ci na gargajiya dai yawa... A hankali yake tafiya cikin layin yana yatsine fuska, he is even afraid kada allergy ya je ya kamasa cos he is so sensitive to anything Filth,... har dai ya kai dai dai kofar gidan da yaron nan ya ta6a kai sa a matsayin gidansu yarinyar, tsaye yyi yana bin duk wajen da kallo, ginin block ne sai dai ko plaster babu, sannan gidan karami ne sosai, duk gidajen layin haka suke, banda gida daya da ya d'an darasu girma shi ma da kadan wato gidan Iyah, wata yarinya ce ke tafe ko takalmi bbu a kafarta, ya bi ta da kallo yace "Baby...." Juyowa tayi tana kallonsa yace "Xo in aike ki cikin gidan nan" Yarinyar da baxata wuce shekara shidda ba ta dawo tace "Gidansu Bibalo?" Yace "Ehh, shiga kice ana kiran me awara a ciki" Da gudu yarinyar ta shiga, babu kowa tsakar gidan don Hansai ko minti biyar ba ayi da fitarta ba, ta shiga makota, Bibalo kuma tun la'asar rabonta da gidan, yarinyar ta kutsa kai cikin dakin su Bibalo tana kallon Jiddah dake kwance ta takure waje daya kan yakunannen katifarsu da Bibalo, tace "Wai ana sallama a waje" Da sauri Jiddah ta mike xaune da idanuwanta da suka yi jajir, duk da tasan Hansai ta fita gidan don sai da ta bar mata sallahun bakar magana ma kafin ta fita amma hakan bai hana xuciyarta dinga bugawa ba jin abinda yarinyar tace, A tunaninta saurayinta ne Usman ya xo, kilan ya ji abinda ke faruwa ne, da kyar dai ta lallaba ta mike ta cire Hijab din jikinta ta dau wankakke dake a linke ta saka, sanyi take ji sosai don xaxxabi ne jikinta, ta fito dakin ta sa takalminta tana tafiya kamar iska xai kadeta ta fito kofar gidan, babu haske sosai wajen hakan yasa ta dinga kallon mutumin dake tsaye da fararen kaya ya juya baya, gani tayi ba Usman bane don wnn yafi Usman tsayi, ta bi layin da kallo tana kara tsoron kada Hansai ta dawo ta tarda ita a waje bayan an yi mata iyaka da wajen daga daxu da yamma, da kyar tace "Wa kake nema?" Sai a snn ya juyo ya sauke mask din fuskarsa yana kallonta, ta xaro ido tsoronta ya tsananta, haka xaxxabinta ma taji yana neman fin na da, don sanyi sosai ya dinga shigarta, kallonta ya shiga yi daga sama har kasa, rasa abin cewa tayi daga karshe ta jingina da bangon gidan, still looking at her yace "Baki da lafiya ne?" Ta gyada masa kai, lkci daya hawaye ya kawo idonta, bin layin ya sake yi da kallo, can yace "Baki sha magani ba?" Hawayen dake makale idonta ya silalo kasa ta girgixa masa kai tace "Babu maganin" yace "Ke da waye a cikin gidan?" Tace "Ni kadai ce, Baabarmu ta fita yanxu" Shiru yyi kamar me naxari sai kuma ya kalli inda motarsa yake yace "Akwai asibiti a nan anguwar?" Ta gyada masa kai tana nuna masa tace "A layin can gaba" Yace "Mu je" Da mamaki take kallonsa tace "Ina?" Ya wani hade rai yace "Mu tafi can din nace" ta marairaice cikin rawar murya tace "Baabarmu tace idan na sake fitowa ko nan bakin kofa sai ta kasheni wllh" Shiru yyi na few seconds kafin yace "Saboda me?" Tana share hawayen da ya ki tsaya mata tace "An sa min rana" Daga sama har kasa ya sake kallonta snn yace "Da wa?" Ta fashe da kuka tace "Da iliya" tana fadin haka kamar an tunxurata ta dinga rera kuka, yace "Ohk, amma bai san baki da lafiya bane bai kawo maki magani ba" Bata basa amsa ba sai kukan da take yi sosai, yace "Mu je" ganin ta ki motsawa ya daure fuska sosai yace "Ke kinsan daga inda nake?" Ta shiga goge idonta bata ce komai ba, yace "Mu tafi nace" A hankali ta fara goge idonta, ganin ya fara tafiya ta bi bayansa gabanta na faduwa tana waige waige har suka kusa bakin titi ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta don duk maxaunin bakin titin nan babu wanda bai santa ba, ya bude mata back seat, xuciyarta ya dinga bugawa da karfi ta tsaya tana kallonsa, ya sauke nose mask dinsa yace "Kina 6ata min lkci" A hankali tace "Baabarmu xata....." Wani kallo yyi mata yace "Nace ki shiga malama" shiga motar tayi a tsorace, ya rufe sannan ya xaga ya shiga maxaunin driver ya tada motar, sai da ya hau saman titi yace "Ina asibitin yake?" Layi uku dake gaba da nasu ta nuna masa ya shiga layin suna isa yaga irin asibitin yyi parking yana kare ma wajen kallo, kafin yace "Nan din ne asibitin?" Kai kawai ta gyada masa, ya ja tsaki ya tada motarsa yayi reverse ya bar wajen, ta dinga kallonsa gabanta na faduwa, wani asibiti a cikin gari ya kai ta, yana parking haraban asibitin ba tare da ya juya gareta ba yace "Sauka" kalle kallen motar ta dinga yi alamar bata ma san ta ina xata bude ba, ya sauka ya xagayo ya bude motar, sauka tayi ya rufe motarsa, ganin yanda ta tsaya ya dake yace "Mu je" he sounds so pissed off, Ba musu ta bi bayansa har cikin asibitin, nan take ya yankar mata kati, ba a dau lkci ba nurse din ta sanar masa xa su iya shiga gun likita, yana daga xaune ya nuna mata office din likitan yace ta shiga ta gaya masa duk abinda ke damunta, Jiddah ta mike gabanta na faduwa tana kallonsa a hankali tace "Ai tsoro nake ji" ya hade rai a d'an tsawace yace "Tsoron likitan sbda xai cinye ki?" Sunkuyar da kanta tayi, yace "Juya ki shiga" a hankali ta juya ta nufi office din likitan da ya nuna mata, kamar me tsoron kofar ta murda ta shiga, sai a sannan ya mike ya bi bayanta xuwa cikin office din, tana xaune ta takure waje daya likitan na cewa ta kwantar da hankalinta ta nutsu, ganin ya shigo sai taji hankalinta ya kwanta, ya ja kujera ya xauna suka gaisa da likitan, likitan na kallonta yace "Me ke damun ki?" Cikin sanyin murya tace "Kai na ke min ciwo, ina jin xaxxabi, kuma ina ganin jiri...." Mikewa yayi ya dawo kusa da ita yana duba idonta da wani d'an abu kamar fitila a hannunsa, Abuturrab dai na xaune yana dubansu har likitan ya gama gwaje gwajensa snn ya koma ya xauna yana kallon Abuturrab yace "Xa ayi mata test, though symptoms din na malaria ne, but it's good ayi test din sannan kuma .... Is she ur sister?" Abuturrab ya d'an kalleta sannan a hankali yace "Yea" Likitan yace "Me ke damunta haka, yar yarinya da ita na ga Bp dinta ya hau" sake kallonta Abuturrab yyi, likitan na kallonta yace "Kina da damuwa ne 'yan mata, idan ma baxa ki gaya ma d'an uwanki ba ni ki gaya min" Sunkuyar da kanta tayi lkci daya hawaye ya kawo idonta, Abuturrab yace "Dont worry Dr i will talk to her about that, ynxu dai idan ba damuwa kawai a hada mata drugs if there is need for injection ayi mata ba sai an yi mata test din ba cos i guess it will take up to 40mins kafin result din ya fito mu kuma a kan hanya muke" Likitan yace "Toh shkkn babu damuwa" daga haka ya fara rubuce rubuce yana gamawa ya mika ma Abuturrab ya amsa snn ya mike yyi masa godiya, ganin har sannan bata mike ba yace "Mu je" Mikewa tayi yana gaba tana biye da shi har suka fita office din, wajen bada allura Abuturrab ya ga abinda bai ta6a gani ba, don kememe taki yarda ta dinga rusa masu kuka a asibitin tana rokansu, hakan yasa ya koma office din likitan yasa ya rubuta magunguna kawai gaba daya ya biya bill din sannan suka fita asibitin, har sannan shesshekan kuka take, ya bude front seat ya hade rai yana kallonta a hankali ta shiga ya kulle sannan ya xaga ya shiga maxaunin driver, sai da suka fita asibitin yace "Kin ci abinci?" Girgixa masa kai tayi tace "Baabarmu ta ba almajiri nawa" Ya dinga nanata sunan da ta kira a ransa, wai Baabarta, girgixa kai yyi cikin ransa still yace ba dai baabarki ba, gidan wani cin abinci ya tsaya ya siya mata abinci sai malt guda biyu da bottle water, yana shigowa motar ya ajiye mata, kallon ledan ta dinga yi, can ta bude ta ciro malts din ta ajiye gefe tace "Ban iya sha ba" Yace "Sai me?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "Tambayarki nake" a hankali tace "Ban iya shan lemo ba ni" Bai kuma ce mata komai ba, sai da suka shigo titin hayi yace "Taron me naga aka yi a layinku daxu da yamma?" Shiru tayi sai kuma ta kallesa a hankali tace "Baabarmu ce take dukana" Da mamaki yace "Saboda me?" Ta share hawayen da ya kawo idonta tace "Dama Iyah ce tace xata sa ni a motar tirela in gudu legas don kar a min aure da Iliya, shine sai na gaya ma wata kawata da muke xuwa makarantar dare tare da ita da, don gobe Iyah tace xata kai ni tasha, sai kawata taje ta gaya ma baabarta shine baabarta ta xo ta gaya ma Baabarmu, shine Baabarmu ta dinga dukana wai xata kasheni, duk aka taru a layin...." Tana kai wa nan ta fashe da kuka, Shi dai sauraronta kawai yake yi, bayan few seconds yace "Wacece Ita warce tace xata sa ki mota ki tafi lagos?" Cikin rawar murya tace "Wata tsohuwa ce a layinmu ana ce mata Iyah...." Ya kalleta yace "Har yanxu xa ki tafi lagos din kenan don kar a maki auren?" Ta girgixa masa kai hawaye na sauka idonta tace "Aa baxan je ba amma xan kashe kai na" Bai ta6a expecting jin hakan daga bakinta ba, yyi parking yana kallonta da mamaki yace "Xa ki kashe kanki?" Ta gyada masa kai, yace "Da me xaki kashe kan naki?" Cikin rawar murya tace "Piya piya xan siya in sha" Bai san lkcn da ya bude baki ba yana kallonta ganin she is so damn serious, da wani expression yake kallonta ganin she is truly depressed and frustrated, tana goge hawayen dake xuba idonta tace "Dama ae Abbana ma ya tafi ya bar ni, ba sai in bi sa ba" ya kwantar da murya yace "Amma kina xuwa islamiyya kuwa?" Ta girgixa masa kai a hankali tace "Na daina tun da dadewa, tun sanda muka fara sana'a" Yace "Toh saboda xa a maki aure kike son kashe kanki?" Ta gyada masa kai, sai kuma ta hade kanta da gwiwa ta fashe da matsanancin kuka tace "Shaye shaye fa iliya ke yi, kuma har kwaya yana sha shine Babarmu take son in auresa...." Kallonta kawai yake, can yace "To wa kika ta6a ganin ya kashe kansa sbda xa ayi masa aure da wanda baya so?" Tana shessheka tace "Akwai wata ma ai ta kashe kanta a nan hayi" yace "Shine ke ma xaki kashe kanki?" Ta gyada masa kai, yace "Toh duk sanda kika shirya ki min magana ni da kaina xan kawo maki piya piyan, kin ji ni?" Ta dago tana kallonsa tace "Toh ai ni na shirya" yace "Yaushe?" Da kyar tace "Yau da daddare nake son in sha" yace "Aa kinga ni sai yau na sani, ki bari ko xuwa jibi xan kawo maki" tana shessheka sae kuma ta sakar masa kuka tace "Yayi min nisa" Yace "Ya sunanki?" Tana kallonsa da hawaye idanuwanta tace "Jiddah" Ya d'an yi shiru, bayan few seconds yace "Jiddah.... shekaranki nawa??" Cikin sanyin murya tace "Babaarmu tace sha bakwai" yace "Toh ki jira sai na kawo maki da kaina, kar ki kuskura ki siya da kanki, kin ji me nace maki?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ki yi min alkawari xa ki jirani" Tace "Nayi" yace "Kina komawa gida ynxu ki ci abinci ki sha maganin ki ai nurse din ta nuna maki ynda xa ki sha" Ta gyada masa kai, tada motar yyi ya ci gaba da driving dinsa gaba daya yana kara naxarin xancenta. 07087865788✍🏻 💖💖 *Jiddatul Khair*💖💖 _By Khaleesat Haiydar_✍🏻 6..... Suna kusa layinsu cikin sanyin murya tace "Toh me xan ce ma Baabarmu idan ta dawo, wllh har dukana xata yi" Bai ce komai ba yyi parking d'an nesa da layin snn ya d'an kalleta yace "Amma ba Baabar da ta haife ki ba ko..." Ta girgixa masa kai a hankali tace "Abbana yace ita ta rasu tun ina yar karama" ganin hawaye idonta ya dauke kai bayan few seconds yace "Allah ya gafarta mata" Ta sunkuyar da kanta ta amsa da Ameen, yace "Sai kice mata saurayin da xaki aura ne ya xo kika fito" Ta marairaice tace "Ai yana legas bai dawo ba" Yace "Kwanaki da na baki kudi ki bata don kar ki sake fitowa bakin titi, kin sake fitowa?" Ta girgixa kai tace "Aa bamu sake yin awaran ba sai shekaranjiya ta fara" bai ce komai ba ya tada motarsa ganin ya fara tafiya ta kallesa da sauri tace "Ina kuma xaka kai ni?" Bai bata amsa ba ganin wani shago da ake cire kudi ta Pos ya tsaya sannan ya sauka motar, without taking much time ya dawo ya shiga motar.... Dai dai layin nasu ya sake parking ya ciro kudi a aljihu yace "Gashi ki kai mata yanxu ma" Kallon kudin ta dinga yi, sannan ta kallesa tace "Ince wa?" Yace "Kice wani ya bata" Amsan kudin tayi gabanta na faduwa, yace "Me nace kiyi idan kin koma gida yanxu?" tace "Kace in bata wai in ji wani" Yace "Kafin wannan" Ta d'an yi shiru sannan tace "Kace in ci abinci in sha magani" Ya d'an daure fuska yace "To sauka" yana fadin haka ya bude mata motar ba tare da ya yarda ya ta6a ta ba, ta sauka, yace "Kulle min mota" Ba musu tayi yanda yace sannan yayi wucewarsa without looking at her, sai a sannan bugun xuciyarta ya tsananta, ta fara tafiya a hankali xuwa cikin layinsu, ta fi minti biyu bakin xaurensu ta kasa shiga, daga karshe ta kutsa kai ciki, tuni hawaye ya fara sauka idonta tana jiran jin saukan duka, sai dai me... Har sannan Hansai bata dawo ba balle Bibalo, gidan babu kowa, dakinsu ta shiga duk da akwai wutan nepa amma kamar ko da yaushe wutan is very low, xaunawa tayi ta ajiye ledan hannunta sannan ta boye kudin cikin ghana must go dinta, a hankali ta bude take away din abincin ta ga shinkafa da katon kaza, ta xaro ido, ita yaushe rabon da ta ci shinkafa balle wata kaza, shinkafa sai suyi kusan sati uku ma basu ci ba daga tuwon masara sai taliya 'yar Hausa ko garin rogo, Kaza kuma dama ranan sllh ne kadai Hansai ke bata kai da kafafuwan ko kuma wuya, yau kuma ga kaza kato a gabanta har da shinkafa, kasa cin abincin tayi tana ta kallonsa, tunawa da tayi Hansai na iya dawowa yanxu ko Bibalo yasa ta xaro ido, a hankali ta fara cin abincin, sbda a tsorace take ta kasa nutsuwa ta ci abincin, ta dai ci wanda xata iya ci, jin almajiri na bara ta mike da sauri ta fita da abincin da ta kunshe a ledansa ta mika ma almajirin ta dawo ciki, ta fi minti daya tana kallon magungunan, kafin ta fito da su tana kallo, ganinsu kadai taji xuciyarta ya fara tashi ta mayar da su da sauri ta cusa a ghana must go, duk ciwon da xata yi bata shan ko d'an paracetamol da Abbanta ke siyo mata lkcn da yake da rai, Hansai kuma ko kasheta ciwo xai yi bata ta6a cewa ta sha magani, muryar Bibalo ta ji tana kiran Uwarta tun daga bakin Zaure hakan yasa ta boye goran ruwan da ta sha ta rage, snn ta kwanta ta rufe idonta. Washegari da asuba jiddah ta kasa tashi kamar yanda ta saba, duk karfe biyar dama take tashi ta fita ta debo ruwa a borehole ta cika jarkunan tsakar gidan da ma bokiti, ganin gari ya fara haske Hansai ta leko dakin tace "Yau naga walakanci, Jiddah kece kwance har yanxu baki fito ba, uban wa xai debo ruwan yau? Bibalo me ciwon kirji ko ni xan fita debo ruwan?" Bibalo dake kwance tana bacci ta gyara kwanciyarta hade da rufe har fuskarta da xanin gadonsu, Jiddah ta dago da kyar muryata na rawa tace "Baabarmu kaina ke min ciwo sosai, idan na tashi juwa nake gani" Hansai tace "To a rayuwar nan yanxu waye baya fama da ciwon kai, ko digon ruwan alwala fa babu a gidan nan, ni kike son in fita in debo ko Bibalo da ba cikakkiyar lafiya gareta ba" Jiddah dai bata ce komai ba, Hansai tace "Ai ko daurewa xa ki yi ki mike ki debo ko bokiti uku ne, gida idan babu ruwa ai ba magana" Daga haka ta juya ta fita tana cewa "Idan ma xaki rufa ka kanki asiri ga bishiyar gwanda da mangwara can ki tsinko ganyayyekin su ki hura icce ki dafa ki sha kiyi wanka don sile na baxanyi amfani da shi wajen siyo maki magani ba" Da kyar jiddah ta mike tana dafa bango ta fita, ta dau bokiti, d'an makotansu ne ya taimaka ya kawo mata ruwan har kai uku gidan, ta dawo da kyar ko tafiyan bata iyawa ta shige daki ta kwanta ko ina na jikinta na mata ciwo... Har karfe goma na safe tana kwance, Hansai ta shigo dakin cike da masifa sosai tace "Ke ni fa babu ruwana ki tashi kiyi ta kanki ki tsinko abinda nace ki dafa uban waye xaki daura ma wahala bayan na ciyar da ke da nake yi" Jiddah ta mike ko ina na jikinta na rawa sbda sanyi, tace "Xan yi" tana magana ta jawo ghana must go dinta ta fiddo kudin jiya ta mika ma Hansai tace "Jiya wani ya kawo wai a baki" Hansai ta xaro ido tana kallon kudin ta karba tace "wani kuma? A ina kika gansa?" Tace "Aikawa yayi in xo, ina xuwa yace in baki" Hansai ta xauna gefen gado ta fashe da kuka tace "Amma gaskiya isuhu ya tare mana abubuwa da yawa a duniyar nan sanda yake raye, to da ya baki sai yace me??" Jiddah ta koma ta kwanta tana fidda numfashi da kyar tace "Cewa yyi in baki kawai" Shiru Hansai tayi tana kirga kudin har ta gama taga dubu talatin cif, ta kalli Jiddah da sauri tace "Ko dai mutumin da ya ta6a baki kwanaki ki kawo min kada mu fito sana'a?" Jiddah ta gyada mata kai, Hansai tace "Toh don girman Allah duk ranan da ya sake dawowa kice masa ya shigo in masa godiya" Jiddah bata iya ta bata amsa ba, Hansai ta mike murna fal cikinta tana murmushi ta nufi kofa tana cewa "In dai haka ne duk wani nawa amma banda Bibalo ya mutu a duniyar nan mana, daga mutuwa sai billowan alkhairi ta ko ina? Ashe dama akwai sauran mutanen kirki a duniya ban sani ba" Jiddah ta bi ta da kallo hawaye me xafi na sauka idonta. Ummi na kallon Abuturrab tace "Ina kuma xaka da yamman nan kana ganin hadari?" Yace "Aa ni ba nisa xan yi ba, nan governor road xan je" tace "Ahmad din har ya tafi ne?" Yace "Aa tare xa mu fita da shi amma xai dawo" Tace "Toh Allah ya tsare, ka siyo min tsire while coming back" Yace "Alright, in sha Allah" Daga haka ya fita dakin nata ya dawo main parlor, Ahmad na xaune yana jiran sa, Ganinsa ya mike ya nufi kofa, bin bayansa Abuturrab yyi wayarsa ya fara ring, dubawa yyi yaga Aunty ke kiransa, ya daga ya kai kunne, wara ido yyi yace "Aunty yanxu ai xan dawo..." Murmushi yyi yana kallon wayar don har ta katse, juyawa yyi ya koma bangare Stepmum din tasa, Ahmad ya ta6e baki, a parlonta ya sameta, yace "Ba nisa fa xanyi Aunty" ta hade rai tace "Shine ni baxa ka min sallama ba amma ai naga ka shiga gun uwarka?" Yace "Toh kiyi hakuri" Yana fadin haka ya jefa ma stepsis dinsa dake xaune parlon wani kallo sanin ita xata gaya mata, Aunty tace "Toh me Ummin tace maka da ta kira ka?" Yace "Nothing kawai tace in taho mata da tsire while coming back" Tace "Toh nima ka taho min da tsiren" yyi murmushi yace "Toh" Daga haka yace "Sai na dawo" ya fita dakin. Yana driving ya d'an kalli Ahmad dake danna wayarsa yace "A ina xaka sauka?" Ahmad ya kallesa yace "Kai ina xa ka???" Abuturrab yace "Bakin ruwa, nan by pass" Da mamaki Ahmad yace "Me zaka je yi a bakin ruwa Captain?" Ya gyara xama yace "Xan amshi sako gun wani frnd dina ne, he is coming from Abuja kuma kano xai wuce, so yace min ya shigo kd yanxu mu hadu by pass in amshi sakon" Ahmad yace "Ohk, drop me home" Abuturrab ya nufi gidansu yyi parking bakin gate, Ahmad ya sauka yace "Sunday din xaka tafi kano?" Abuturrab yace "In sha Allah" Ahmad yace "Alright... Sai da safe" Daga haka ya shiga ciki, Abuturrab yayi reverse ya bar layin. Abuturrab ya fi minti goma tsaye a kan hanya bayan ya iso bakin ruwa, jinginar da kansa yyi jikin kujeran da yake xaune yana tunanin wanda ya sani wanda bai yi aure ba that he can do anything possible to see him married to this girl that is ready and wanting to kill her self, driver din Abbansa ko wata uku ba ayi da yyi aure ba, who again? Wani senior cleaner ne a Airport din kano ya fado masa, Guy din na da hankali... a Diploma holder, ga shi da mutunta mutane, Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya ganin ya kusa samun solution, and he will try all possible means sai Mu'axxam ya auri yarinyar nan, wani ajiyar xuciyar ya sake saukewa na relieve, driving ya ci gaba da yi, yana isa u-turn ya dau hanyar Hayi, kamar ko da yaushe parking yyi a bakin layin yana kallon cikin layin, nose mask dinsa ya saka da glasses din ido sannan ya sauka motar ya fara tafiya, calmly yake tafiyar har ya isa kofar gidan, wani yaro ya tura ya kira masa jiddah cikin gidan, Hansai na xaune tsakar gida tana cin shinkafa da wake da mai da yaji da salak wanda rabon da su ci shinkafar tun rasuwan Mai gidan nata, tana kallon yaron tace "Lawali daga ina haka?" Yace "Wani ke kiran jiddah a waje" Hansai tace "Jiddah kuma?" Jiddah dake kwance xaxxabi ya ci karfinta ta bude jajayen idanuwanta da sauri gabanta yyi wani mugun faduwa ta mike xaune, Hansai ta kakkabe guntun shinkafar hannunta a samiran cinyarta tace "Waye shi? Kuma daga ina?" Yaron yace "Wani dogo ne ya sa gilashi da takunkumi a hanci, ya sa fararen kaya" Hansai ta mike da sauri tana leka dakinsu Jiddah tace "Ke tashi, kaddai me kawo min kudin nan ne?" Jiddah ta mike tsaye da kyar jikinta na rawa tace "Ban sani ba" Hansai tace "To ai kuwa daurewa xa kiyi ki tashi ki saka hijabi ki fita ki ga waye, kika sani ko shi din ne wani kudin ya kawo yau ma" Kasa ci gaba da tsayuwa tayi duk ynda ta so yin hakan, Hansai tace "Yau naga tsiya, baxa ki daure ki tashi ba kamar ba mace ba Jiddah??" Jiddah ta dafa gadon ta kara daurewa ta tashi, Hansai ta warware Hijab dinta dake ajiye a linke kan jaka ta mika mata tace "Sa ki fita maxa maxa ki ga waye" da kanta ta sa mata hijab din, jiddah ta fita dakin, Hansai ta xauna gefen gado tana addu'an Allah ya sa shi din ne, kuma wani kudin xai bada yau ma, jiddah na fita kofar gidan ya juyo yana kallonta, durkusawa tayi nan kasa ta kasa ci gaba da tsayuwa, ya dinga mata wani kallo yace "Jikin bai maki sauki ba?" hawaye ya shiga sauka idonta, kana ganinta kasan tana jin jiki, yace "Kin sha magungunan nan kuwa?" Kin cewa komai tayi, Ya hade rai da d'an tsawa yace "Tambayar ki nake" Ta fashe da kuka a hankali ta kara jingina da bango tace "Ni amai xanyi idan na sha" Da mamaki ya dinga kallonta, Hansai dai na ta tsaye tsakar gida tana jiran ganin shigowar jiddah, jin shiru shiru ta nufo xauren cikin sanda tana leko waje, hada ido suka yi da Abuturrab, ta sunkuyar da kanta da sauri tana d'an kame kame tace "Sannu da xuwa Alhaji.... Ae da ta fito maka da tabarma ko" kallonta kawai Abuturrab ke yi daga sama har kasa, can yace "ina wuni" Hansai ta rutsuna tace "Lafiya lau Alhaji, sannu da xuwa, ko xaka shigo daga ciki...." Yana kallon jiddah yace "Ya mai jikin?" Hansai ta marairaice tace "Wllh da sauki kenan xa a ce, kuma fa ta sha magunguna amma shiru har yanxu" yace "Toh bari mu je asibiti" Hansai tace "Kai Alhaji da dai a je chemist kar hidiman yyi yawa, ga chemist can bayan mu" yace "Aa xa a je asibitin kawai" Hansai tace "Toh shkkn Alhaji, daure ki tashi Jiddan Mama, sannu... Ga dai ana shan maganin kamar ba a sha" tana fadin haka ta dagota, Abuturrab na kallon Hansai yace "Motata na bakin titi" Hansai ta kwance dankwalin kanta ta rufe jikinta da shi tace "Toh bari mu je can din" tana rike da jiddah suka isa bakin titin ya bude back seat ta saka jiddah ciki, mutanen layin sae kallonsu suke, Abuturrab na kallonta yace "Ina 'yar uwarta mu tafi tare" Hansai tace "Au wai Bibalo, ai kuwa bata anguwar nan yanxu haka, ko in shiga mu je ni?" Ya kalleta daga sama har kasa sannan yace "Yanxu xa mu dawo in sha Allah, ba sai kin je ba" tace "Atoh dama ae bai ma kamata in bi ku ba, toh Allah ya kiyaye Alhaji, a dawo lafiya" xagawa yyi ya shiga driver seat ya tada motar ya bar wajen Hansai sai washe baki take tana daga masa hannu, sai kuma ta hade rai tana kallon 'yan layin da suka xuba mata ido da kallo tace "To wai lafiya wannan shegen kallo haka??" Tsaki ta ja ta juya ta fara wucewa tana cewa "Jama'ah baxa su ji da talaucin da yyi masu katutu ba sai shegen sa ido da neman abun fade, to d'an uwanmu ne daga Habuja sai kowa yyi ta kansa haka kuma" Abuturrab na hawan saman titi ya kalli Jiddah ta madubi yace "Wato baki sha maganin jiya ba??" Shiru tayi bata ce komai ba, ya hade rai yace "Ki bude baki kiyi min magana ina tambayarki" kai kawai ta gyada masa, yace "Me yasa baki sha ba?" Kamar xata yi kuka tace "Nace maka amai xan yi idan na sha" Yace "To xa mu je su maki alluran yanxu ai" Ta mike xaune da kyar tace "Aa ni bana son allura" Wani kallo ya wurga mata, tayi shiru bata sake cewa komai ba.... Sai kusan karfe taran dare Abuturrab ya dawo da ita bakin layin nasu, yau ma da ledan take away din abincin da ya siya mata, ya sauko motar ya xaga ya bude mata side din da take xaune, da kyar ta sauko motar da wasu ledan magungunan daban da aka kara bata a asibitin da ledan abinci, ya rufe motarsa, har ya xaga xai shiga maxaunin driver ya sa hannu aljihu ya ciro dubu goma ya dawo ya bata yace "Sai ki ba Baabar taku" daga haka ya shiga motar yayi wucewarsa, da kyar ta dinga jan kafa har ta isa gida, Hansai na xaune da Bibalo dake cin abinci, ganin ta shigo Hansai ta mike a xabure tace "Me ya baki?" Jiddah ta mika mata duk ledojin hannunta da kudin sannan ta xauna nan bakin kofa ta jingina da bango kanta na juya mata, Hansai ta kirga kudin ganin dubu goma ne tace "Toh ya baxai bani dubu goma ba bayan kudi ya kare a shegun magungunanki, munafuka kawai, ciwo kalilan duk ta bi ta langwabe ma mutane kamar kyanwa, kuma da ganin asibitin me tsada xai kai ki, to Allah ya isa wllh...." Kallonta kawai Jiddah ke yi, Hansai ta ja tsaki ta shiga fiddo magungunan a fusace tana kyabe baki, can ta watsa mata su tace "Abun takaicin ma asaran kudinsa kawai yyi, ke din ce xaki sha ma mutane magani" watsa mata ledan magungunan tayi gaba daya sannan ta bude dayan ledan ganin shinkafa da dunkulelen kaza ta murmusa tace "Allah sarki bawan Allah" Tuni Bibalo ta tura kwanon gabanta ta dawo kusa da uwarta, Hansai tace "Toh bai saka da lemo ba sai ruwan gora?" Jiddah dai bata ce komai ba, Hansai da Bibalo suka shiga cin abincin kamar mayunwata, sai da suka kusa cinyewa ta kallo jiddah tace "Au, to ai ba mu sam mata ba" kwanon abincin da Bibalo ke ci ta jawo, tana kallon guntun shinkafar da Bibala ta rage ta debi na take away din loma biyu ta yarfa a kai, sannan ta dau tsoka me K'ashi, sai da ta ta66atar ta kwaye tsokan sannan ta saka k'ashin a kwanon ta tura ma Jiddah tace "Gashi kema" Jiddah dai bata ce komai ba, suka cinye nama da abincin tass sannan Hansai ta maka uban gyatsa ta mike ta shige daki tana cewa "Bibalo ke da yar yabi sai ku bibbi gobe ku kai cingam da sweet din sa ranan da aka yi, har yau ba a ba jama'a ba" Bibalo ta mike ta bi bayan uwarta tana cewa "Yo ai cingam din kwali daya ya rage..." Jiddah ta jingina da bango hawaye ya kawo idonta a hankali tace "Kuma bai kawo min piya piyan ba" Washegari lahadi Abuturrab ya fito gida misalin karfe sha daya na safe, Waya ne kare kunnensa yana driving a hankali don bai fita layinsu ba, girgixa kai yyi yace "No kai dai ka samu adaidaita ni na riga da na fito da mota, sai ka fadi inda xan sameka" Murmushi yayi bayan few seconds yace "Okay then, tunda kasan hospital din ba sai ka tafi ba" Yana fadin haka ya katse wayar hannunsa. Dai dai inda suka yi xai dau Ahmad yyi parking yana jiransa, bayan kusan minti goma Ahmad ya iso wajen da adaidaita ya shiga motar yana kallon Abuturrab yace "Amma ba yau xaka bar kaduna ba Captain" Abuturrab yace "probably.... Akwai abinda xan yi yau din" Ahmad yace "Ni train xan bi in sha Allah yau xan koma Abuja..." Abuturrab bai ce komai ba har suka isa wani hospital domin duba wani frnd dinsu da aka yi admitting, fruits iri iri suka siya masa a hanyarsu ta xuwa wajen, suna shiga ward din da yake suka tarar da abokansu hudu su ma sun xo dubiya, bayan an gaisa, wani frnd dinsu Umar na kallon Abuturrab cike da tsokana yace "Captain ko dai a hayin rigasa kake gini ne? Or probably neman aure...." Da mamaki Abuturrab ke kallonsa har ma da sauran abokansu, Ahmad yayi dariya yace "Haka yace maka Umar?" Umar ya gyara xamansa yace "To for the past 4 days kullum sai na ga motarsa a hayi" Abuturrab ya xaro ido yace "Ni kuwa?" Umar yace "Kai mana, yawanci kana ta daya side din nake ganinka, kai akwai ranan da ma na kiraka ina jin ka bar wayar a mota and u didn't even follow my miss call" Abuturrab yace "Subhanallah on a serious note ban lura ba...." Umar yace "To airport xa a bude mana a hayi ne kullum muke ganin Captain a can" Murmushin yake kawai Abuturrab yyi yana kallon Nasir dake kwance da drip a hannunsa yace "Barrister guda a gadon hospital, so how are u feeling now?" Nasir ya jefa masa wani kallo yace "Kai ma baka wuce a kwantar da kai gadon asibitin ba ai" Dariya kawai Abuturrab yyi, sun fi minti ashirin a dakin suna labarin duniya, daga karshe Ahmad ya sanar masu xa su koma bayan sun ma Nasir addu'an samun lfya, a tare suka fito da Umar daga ward din don shi ma wucewa xai yi, Abuturrab ya d'an kalli Ahmad dake bayansa suna magana da wani abokinsu da ya fito rakasu, ya kalli Umar da har ya kusa fita reception din hospital, ya kara pace dinsa har ya isa gunsa yace "Kai me kake xuwa yi hayi har kake ganina?" Umar yyi murmushi yace "A can fa Mahaifiyata take, so kusan kullum nakan je can din" Abuturrab yace "Ohhh Allah sarki..." Umar yace "To kai wajen wa kake xuwa?" Abuturrab ya d'an shafa kansa ya saci kallon Ahmad dake tahowa yace "Aboki nayi nima a can din" daga haka ya fiddo wayarsa ya d'an yi gaba kamar xai yi answering call don bai son Umar ya ci gaba da maganan gaban Ahmad. Abuturrab yana kallon Ahmad bayan sun hau saman titi yace "Gida xan sauke ka?" Ahmad yace "Yeah..." Driving kawai Abuturrab ke yi, Ahmad dake kallonsa yace "Wajen wa kake xuwa a hayi Captain?" Abuturrab ya kallesa da sauri cos the question came unexpected, ya dake yace "Ka yarda da Umar kenan, he was just pulling my leg idan ba dai a train station ba ya gan ni wa gareni a hayi da xanje? Wa na sani a hayi? Kawai dai idan mun hadu dole sai ya tsokane ni ne..." Ahmad na gyara xama yace "To na sani ko budurwa kayi a can baka sanar min ba kake boye min, ai idan tayi tsami ma ji" Wani kallo Abuturrab ya jefa masa yace "In rasa inda xanyi budurwa sai anguwar nan???" Ahmad na kallonsa da mamaki yace "Meye da su 'yan anguwan, ba mutane bane su din? Or sai da aka halicceka specially sannan aka halicce su aka ce maka? What's wrong with u Abuturrab? Why do u sometimes behave like...." Abuturrab yace "Illiterate right?" Ahmad yace "Of course" Abuturrab yace "Fine, but do not forget everyone is entitled to his or her opinion, ra'ayinka daban ra'ayina daban, kai xaka iya budurwa a can infact har ma ka aureta ku xauna a can din, it's ur opinion, ni kuma last thing da baxanyi ba kenan a rayuwata, and this is my opinion, so stay entitled to urs, and i stay entitle to mine also" Ahmad yace "Baxa ka iya aure a can ba sbda kafi su a wajen Allah ko??" Abuturrab yyi masa wani shegen kallo yace "Wai Ahmad ance maka ni kai ne?? Ni fa ina da class ina da taste, as in i am far beyond that ka daina yi min irin wannan maganan bana so wllh" Ahmad yyi d'an murmushi bai kuma ce masa komai ba, Abuturrab yyi tsaki yace "Haka kawai sai kace kowa sai ya bi ra'ayinka, kai mace ko min kazantarta da locality dinta xaka iya aurenta ku xauna lafiya, ni kuwa it's a big No for me, bana walakanta 'yan adam kai shaida ne, sannan kasan ko kai baka kaini tausayin d'an Adam ba, idan naga mutum na cikin damuwa ko wani yanayi more especially mace ina bakin kokarin ganin nayi duk abinda xan iya yi ko a ina ne kuwa, even with my last card i can help, amma sai ka dinga hadani da su kana wasu maganganu marasu ma'ana" Ahmad bai kuma ce masa komai ba har suka iso gidansu, Abuturrab yyi parking, Ahmad ya juya yana kallonsa still bai ce komai ba ya bude motar ya sauka ya rufe masa motarsa, tsaki Abuturrab yyi, yyi reverse ya bar layin kallon agogonsa dake nuna masa sha biyu da rabi yyi ya nufi gida kawai.... 07087865788....✍🏻 Almost done with free pages 💖💖 *Jiddatul Khair*💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 7..... Fitowa Hansai tayi tsakar gida jin ana sallama, ganin aminyarta Zulai ta ce "Aa ashe Zulai ce, shigo daga ciki mana" Zulai tace "Ina ta addu'ar Allah ya sa in sameki wllh" Hansai tayi dariya tace "Ai ko kin ci sa'a, don yanxu haka shiri nake xan fita kasuwar tasha in saro kayan sana'ata" Zulai ta rike ha6a tace "Kin fara wani sana'ar ne banda awara?" Hansai tayi shewa tace "Ai ni na kwan biyu ma banyi awarar ba, amma kilan idan na fita yau dai in siyo har da waken suyan, yanxu su maggi, kubewa, kuka, daddawa... Kai duk dai mahadin miya da kika sani nake siyarwa, ko kwana hudu ban yi da farawa ba, sannan ina sa ran fara dillalanci kwanan nan" Zulai dake ta kallonta tace "Ikon Allahhh..." Hansai ta shiga d'an dakinta tana murmushi, Zulai na biye da ita a baya, bayan sun xauna Zulai tace "To ina yaran?" Hansai tace "Bibalo yanxun nan ta shiga makota, Ita kuma warcan gantalalliyar na can kwance wai ba lafiya" Zulai tace "To Hansai wani labari dai nake ji a gari, shine nace bari dai in sa6o gyale in taho..." Hansai ta gyara xama tana kallonta tace "Me ke faruwa? Wani labarin kika ji?" Zulai tayi kasa da murya tace "Yawo ake da ke wai bayan an kawo gaisuwan wannan yarinya jiddah har an saka rana kina turata gun wani me katuwar mota kullum sai ya xo kofar gidan nan, meye gaskiyan lamarin nan?" Hansai ta saki salati tana tafe hannu tayi mici mici da ido tace "Amma dai Allah ya tsine ma duk wani me sa ido a duniya, da yaushe da yaushe na turata gun me mota? Yau naga lalacewa, Jiya ne fa bata da lafiya shine ya siyo mata magunguna, kai ni Hansatu jama'a basu da gadonka amma suna da gadon maganarka..." Zulai tace "To waye shi me motar ma dai tukun" Hansai na huci ta lafto wani uban ashar tace "Duk wanda ya fasa sa min ido bai haifu cikin uwarsa ba a garin nan, tunda isuhu ya rasuwa wani shege ne ya ta6a kawo min kwayar masara balle shinkafa ko man kulli yace gashi ki ci kanki Hansai?? kawai sai don bawan Allah ya ga muna cikin matsatsi da yanayin rayuwa yana xuwa yana taimaka mana domin Allah sai a sa mana ido a hau mana bakin ciki da hassada a anguwa? Ni wllh ji nake kamar in siyar da gidan nan in bar gantalallen anguwar nan ko xan samu ci gaba" Zulai tace "Ke ni duk ba wannan ba tsoho ne mutumin nan ko yaro?" Hansai ta ja tsaki tana gyara xama tana huci tace "D'an yaro ne fa Zulai, ina jin ma saurayi ne bai ta6a aure ba, baki gansa ba bawan Allah wllh...." Zulai tace "Gun jiddar yake xuwa?" Hansai ta kalleta da sauri tace "Waye kuma jiddah? ita a wa xai xo wajenta? kema dai da wani xance wllh, xuwa fa yake idan yaga tana tuyar awara bakin titi ya mika mata kudade masu yawa ta kawo mana, ai ya san halin da muke ciki, d'an gayu ne fa sai kin gansa me kuma xai yi da wata jiddah kamar warce uwarsa tace masa je ka ka gani?? Haba Zulai, wllh da kyar ma idan ba daga Habuja yake xuwa ba don d'an gaye ne" Zulai ta d'an leka waje a hankali tace "Bacci jiddar take?" Hansai tace "Oho...." Daga haka ta mike ta fita, bude labulen dakinsu jiddah tayi ganinta a kwance tace "Wannan shegen kwanciyar baxai fissheki ba idan xa ki tashi ki kwashi bokitai ki fita gashi can an kawo famfo bakin titi ki jido mana ruwa ko na alwala ina jin babu a gidan nan, tun safe kin wani makale daki a kwance kamar ruwa" daga haka ta fice daga dakin ta koma nata, jiddah ta mike xaune daga kan darduman da take a kwance bayan tayi sllhn azahar, duk da jikin nata ya mata sauki, amma idan ta tashi jiri take gani ga yunwa dake dawainiya da ita, tun safe kunu kadai ta sha kosan da aka siyo ma bata ga idonsa ba balle a bata ta ci, sai da Jiddah ta bar gidan da bokitai sannan Zulai ta rike kunnenta daya tace "Anya ba son jiddah mutumin nan yake ba kuwa Hansai, banda haka hidimar uban me xai maku, ku da ku ke gida, ga almajirai can a titi, ga gidajen marayu a gari" Hansai tayi kasake, sae kuma tace "Sonta kuma? Ta ina xai so ta Zulai, babban mutum ne fa, kudi yake bata ta kawo min mu kula da kanmu tun bayan mutuwar Isuhu fa...." Zulai tayi wani murmushi irin na boss tace "Lallai Hansai, ashe har ynxu da sauran ki, to wllh da kyar idan ba sonta yake ba me yasa bai mika ma Bibalo ta kawo kudin ba sai Jiddar" Hansai tayi tsaki tace "To Bibalo sana'a take min a bakin titi da xai ganta ya bata? Ai sai dai Jiddar dake bakin titi kullum" Zulai tace "To wllh ki farka daga wnn baccin da kike, kada ki kuskura ki bada kofar da xai shigo da wani batu bayan ihsanin da yake maku, idan kuwa kika yrda to kina ruwa, ga dai Bibalo ai ita ya kamata a so tunda da gatan ta, amma har kika yarda ya shigo maki da wani batu kan Jiddah to kashin ki ya bushe kina ji kina gani Jiddah xata xama matar babban mutum...." Shiru Hansai tayi tana kallonta ko kiftawa babu da alamar xancen Zulai ya gigitata, Zulai tace "Atoh, kada ki kuskura wllh, ihsanin ma idan son samu ne kada ki sake amsa don a bisa dukkan alamu ya ga Jiddah ne ya kyasa, to jiddah kuma a wa Allah na tuba, yarinyar da ko dangin kirki bata da, kai ina ma ta gansu, ke fa kadai ce gatan ta a duniya, ba dangin uwa balle na uba, yau da xaki koreta sai dai ta bi duniya bata da wajen xuwa...." Hansai tace "Toh wai hauka nake yi ne Zulai, bayan an amshi gaisuwa gun Iliya so kike d'an iskan ya 6a66aka ma gidan nan wuta mu shiga uku? ai jiddah yanxu bata da maraba da matar aure, Iliya ya kawo komai sadaki kawai ya rage da daurin aure, shi ma ni ce na ja lkcn ai an sa ranan kusa kusa na daga" Zulai tace "Atoh, tun wuri sanar masa ya dawo ayi ayi auren kawai, kinga wannan mutumi kam dole ya komo ma Bibalo...." Hansai ta sharce wani xufa tace "Ni dadina da ke akwai hangen nesa wllh Zulai, kinga bbu wanda ya xo ya wayar min da kai banda ke ina nan ina ta haukana, bari in sa a kira min Iliyan dama sbda kudin katifar da xan siya mata ya sa nake ta jan auren naki yrda a sa sati biyu kamar yanda ya bukata, amma tunda haka ne kuma ga wnn bawan Allah ya bamu kudade masu tsoka kema har na cire maki dubu biyu a ciki, sai ki rakani kawai gobe ko tsohuwar katifa ce in siya mata da 'yar robobin aikin gida" Zulai tace "Shkkn kuwa" kasa karasawa cikin compound din Jiddah tayi da bokitin ruwa a kanta jin abinda su Hansai ke cewa, ta fi minti uku tsaye duk tana sauraronsu Zulai tace "Idan kin kirasa kice yace a sa bikin sati biyu kawai kin shirya a wuce wajen" Hansai tace "In sha Allahu haka xan yi" A hankali Jiddah ta karaso ciki ta juye ruwan kanta duk suka yi tsit, ta juya ta fita tsakar gidan lkci daya hawaye ya kawo idonta, ita dai bata ji xancensu na farko ba amma daga inda suke cewa xa su ce Iliya ya dawo ayi auren ta tsinci maganar su. Bayan ta fito ta so shiga gidan Iyah amma sbda irin warning din da Hansai tayi mata yasa bata shiga ba, inda xata shiga tayi kukanta me isarta take nema, a haka ta dinga jan kafa har ta isa inda pampon yake ta jingina da bangon wani gida tana share hawayen dake makale idonta, ko yaushe xai kawo mata piya piyan da yace xai kawo mata, ji tayi baxata iya jiransa ba kuma, gwara kawai ta siya da kanta duk da kudin da ya rage mata yanxu bai wuce dari biyu ba tunda Hansai ta rabata da Usman dinta ta karfi da yaji, don kuwa wanke kafa tayi ta tafi har gidansu can cikin gari ta sanar ma iyayensa su ja ma d'an su kunne ya fita harkar 'yar ta jiddah don an sa mata rana, tun daga sannan kuma rabonta da Usman. Washegari da sassafe Hansai ta fita xuwa gidan Zulai don daga can xasu wuce kasuwan dillalai yi ma Jiddah siyayyar aure, wata tsohuwar katifa ce da ko riga babu suka siya a farashi me sauki da pillow kwaya daya, sai robobin kitchen su ma duk tsofaffi, hatta wuka basu siya sabo ba sai tsoho, suka dai kwaso tarkacen da xa a iya kai ta gidan miji da shi, suna shirin barin kasuwan Zulai tace "To baki siya xanin gado ba" Hansai tace "Ina da wani a karkashin akwati xai yi shekara goma da ajiyesa sai in bata kawai, buta kuma ta tafi da na ubanta yana can ba amfani muke da shi ba" A barrow suka kima kayan suka dau hanyar gida. Tunda Jiddah taga siyayyar da suka yi wanda ke nuna cewar an kusa aurenta da Iliya hankalinta yyi mugun tashi, Hansai kuwa tuni tayi kiran Iliya da ya sanar mata sun ma kusa shigowa kaduna, bayan ta katse kiran tana kallon Zulai da wata kawarsu Dije da ta rakasu siyayya tace "Atoh ai shkkn, yace sun wuce Abuja, kun ga wannan karan kenan da matarsa xai koma legas din" Zulai tace "Ahh shkkn, Allah dai yasa ayi bikin da mu" Dije tace "Ameen, ai Hansai 'yar halaq ce, babu wanda yayi tunanin xata yi ma jiddah wannan abun arxikin, kowa gani yake tunda Malam Isuhu ya kwanta dama shkkn watsi xata yi da jiddah, sai gashi ta ba mara da kunya, kuma in sha Allahu baxa ki ta6e ba, kin cika yar halaq wllh" Hansai tayi murmushi tace "Toh Allah na tuba ko uban na da rai wllh ba samun hakan xata yi daga garesa ba, sai in idanuwansa xai kwakule ya siyar yyi mata kayan daki, uban me garesa banda wannan rubabben gidan, bashi da komai sai wahala wllh" Zulai ta kwashe da dariya tace "Allah dai ya ji kansa, gashi nan kin rufa masa asiri kin rufa ma 'yar sa asiri, kin mata abun arxiki" Washegari Hansai ta azalzali Iliya da kira nan ya sanar mata nan da kwana biyu xa su je can gidan kawun nata da ake xancen auren a wajensa tare da magabatansa sai a saka sati biyun da tace, amma fa ba shi da kudin sadaki a yanxu sai dai a biyosa bashi, Hansai tayi shiru tana sauraronsa, can tayi kasa da murya tace "Iliya da kudin sadakin fa nake son yi mata dinki tunda ba lefe xaka yi mata ba kace baka da halin yi...." Ya katse ta cikin fada yace "Gashi nan da duk kudin hannuna na siyo maki masara kwano 8 da gawayi, ko in siyar in kai kudin sadakin?" Da sauri tace "Aa to ai tunda kace idan ka samu xaka bada babu wani damuwa xan ma kawun nawa bayani, Allah yayi maka albarka, ai kowa yasan kai me xuciyar yi ne Iliya, to a ina xaka ajiye Jiddar?" Yace "Ehh akwai shago daya gaban gidan kakana sai ta xauna nan kafin in sama mata haya" Tace "Atoh shkkn, ni na xata legas din xaku wuce tare ince shkkn xaka rabani da Jiddah gaba daya" Yace "Aa nan xan bar ta, mu ma gareji muke kwana a legas din" Hansai ta xaro ido tace "Atoh Allah ya rufa asiri, tunda ga gida ka samar mata a nan din shkkn, Allah ya kai mu wannan rana dai" Yace "Ameen" daga haka ta katse wayar tace "Toh ba shkkn ba" Abuturrab na kwance cikin resting cabin din jirgin da yayi piloting tare da Co-pilots dinsa daga lagos xuwa kano, ko minti talatin basu yi da alighting ba, idonsa a lumshe suke duk da ya rufe fuskarsa da hulan uniform dinsu na pilot dake jikinsa, tapping dinsa aka yi a kafa, ya xame hulan a hankali, Co-pilot dinsa ne tsaye kansa, pilot din yyi wani sigh yace "Done with the Secure Cockpit checklist.... Can we??" Abuturrab ya mike xaune yace "Alright..." Pilot din yace "Ain't you changing??" Abuturrab ya kalli uniform din jikinsa yace "Not at all" Jakunkunansu suka dauka suka sauka jirgin, sai da suka gaisa da incoming crew da suka hadu da sannan suka shiga cikin airport din. Driving Abuturrab ke yi cikin motarsa da yake bari a airport, hotel din da yake sauka yawanci idan yana kano ya nufa, duk da Abbansa na da gida nan kano wanda ke a kulle babu kowa ciki baya sauka gidan don baya son xama shi kadai shi yasa ma idan kwana ya kamasa a Abuja, it's either su kwana gidansa tare da Ahmad ko Aneesah ta xo tayasa xama, ya so tafiya kaduna yau amma bai samu flight me xuwa kaduna ba or even private jet, yana shiga hotel din ya karbi daki kamar yanda ya saba, wanka yyi ya sauya xuwa kananun kaya, yayi sllh sannan ya bude pepper soup din hanta da ya sa a kawo masa with cup of coffee, ya fara ci a hankali, ajiye spoon din hannunsa yyi tunawa da yayi bai samu Mu'axxam yayi masa magana ba a kan yarinyar nan ta Hayin rigasa, ya dafe kansa don shaff ya mance, tun a jirgi da ya tuna yake Allah Allah suyi alighting ya samesa da maganan, he can even go to d extent of taking all the marriage responsibilities in har Mu'axxam din yace bashi da hali, tsaki ya d'an yi don gobe da sassafe yake son driving xuwa kaduna baxai shiga airport din ba, a hankali ya ci gaba da shan pepper soup dinsa har ya ji ya ishesa sannan ya tashi ya shiga bandaki ya wanke bakinsa ya fito yayi kwanciyarsa. Washegari Saturday karfe goma saura Abuturrab ya shigo compound dinsu... Parking yyi kusa da motarsa da yake amfani da a kaduna, ya sauka sannan ya shiga ciki, part din Aunty ya fara nufa ya sameta parlonta tana breakfast, ganinsa tace "Daga ina haka kamar an jefoka captain?" ya xauna kasan lallausan carpet din parlon yana murmushi yace "Daga kano nake" tace "Ikon Allah welcome son..." Yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Lafiya lau ya hanya?" Yace "Alhmdlh" mikewa tayi tace "Let me get u breakfast" Bata jira cewarsa ba ta fita, sae gata ta dawo tare da mai aiki rike da tray din breakfast din, Mai aikin ta gaishesa sannan ta ajiye, ganin kallon da yake ma tray din Aunty tayi dariya tace "Taimaka min kawai tayi ta dauko flask din ba wai ita ta hada maka ba..." Bai ce komai ba ya dau cup dake a kife ya juya yana kallon ciki keenly kamar yana neman abu, Aunty tace "To yanxu da ba Aneesah bace budurwar ka ya xaka yi da wannan kyankyanin captain, yan matan yanxu da son jiki duk ya sa sun xama kazamai" Ba tare da ya kalli Aunty ba yace "Allah ya ga xuciyana shi sa bai hadani da mara tsaftar ba" Dariya kawai Aunty tayi tace "Jiya ma Aneesar ta kirani mun gaisa ashe ta koma Abuja" Yace "Ehh ta koma..." Tace "Idan ka gama sai ka ajiyeni U-rimi don Allah, driver baya nan kuma bana son driving" Yace "Alright" Yana gama breakfast din kuwa ya mike, tuni ta dauko mayafinta da yar jaka, yace "Salem fa?" Tace "Tun yaushe Salem ya koma makaranta" Abuturrab yace "Ohh yea mun yi chatting ya gaya min, but na manta" Sai da suka fita parlon ya tuna bai je gaida Umminsa ba, ya d'an buda ido yace "Aunty bari in shiga in gaida Ummi yanxu in fito" Ta d'an 6ata rai tace "Yanxun nan fa xaka ajiyeni ka juyo Captain, cikin mintuna kadan xaka dawo ai" Bai ce mata komai ba ta fara tafiya ya bi bayanta walking slowly. Abuturrab bai dawo gidan ba sai bayan la'asar tare da ita, tana rike da ledojin atamfofi da ta sa ya siya mata a gidan da suka je, ta nufi part dinta, shi kuma ya shiga bangaren Mahaifiyarsa, kanwarsa Ramlah kadai ce parlon tana shara yace "Ummi fa?" Tace "Ta fita tare da driver yanxu" Ya shafa kansa yace "Ohk..." Juyawa yyi xai fita tace "Shine baka shigo ka gaisheta ba kuma tun safe ka dawo yaya" Ya juya ya mata wani kallo yace "Yaushe na fara wasa da ke?" Shiru tayi bata ce komai ba, yyi kwafa ya fice daga parlon. Bedroom dinsa ya shiga, sai bayan da yyi wanka ya sauya kaya sannan ya fito main parlor rike da makullin motarsa, har xai fita ya nufi kitchen jin movement a ciki, Safiyya ce a kitchen din da Ramlah sai mai aiki da alama dinner suke dafawa, yace "Is there anything to eat here?" Safiyya ta kallesa tace "Aa ba a gama ba" Juyawa yayi ya fita daga kitchen din ya bar parlon gaba daya, sai da yayi sllhn magrib sannan ya bar anguwar... Parking Abuturrab yyi yana kallon cikin karamin layin da babu haske banda na wata, yara ne bakin wani tap suna ta diban ruwa suna wasa da ruwan, tun da yamma ya so xuwa amma sbda comment din Umar a kansa ranan a hospital yasa ya ki shigowa anguwar da yamman, ya sauke glass yana ta kallon yaran, da hannu yyi ma wani yaro cikin yaran alamar ya xo, yaron ya taho da sauri, dari biyar ya dauka cikin motar ya mika ma yaron yace "Kaje can gidan da ake siyar da awara ka kira min yarinyar dake siyar da awaran" Yaron ya ruga da gudu xuwa gidan, yana isa ya kutsa kai ya shiga, Hansai na xaune tsakar gida Bibalo na haska mata fitila tana daure busasshiyar kubewa a leda, Yaron yace "Ina wuni maman Bibalo" Hansai tace "Lafiya lau, me xaka siya?" Yace "Aa wani me mota ne yace in kirawo me awara" Hansai ta kalli Jiddah dake duke bakin kwaroron wanke wanke tana yi, Hansai tace "To ai kuwa xuwa xaki yi ki ji me ke tafe da shi, tunda yasan yanayin garin kilan wani alherin ya xo mana, ko kuma Bibalo ta je, yan sa idon anguwar nan sae su iya juya mana xance yanxu yanxun nan...." Jiddah dai bata dago ba ta ci gaba da abinda take yi, Mikewa Bibalo tayi da sauri ta ajiye fitilan hannunta tace "Bari in je ni" Mayafi ta figa ta fice daga gidan tana ce ma yaron taho ka nuna min inda yake, can bakin titi yaron ya nuna mata, Abuturrab ya dinga kallonta daga cikin motar, tun daga tafiyar ya gane ba jiddah bace har kuwa ta iso bakin titi, tsaye tayi jikin motar, ya sauko yana kallonta, tayi fari da ido tana wasa da mayafin kanta tace "Sannu da xuwa...." Yace "Ina 'yar uwar taki" ta buda ido sosai tace "Yo ae ta daina fitowa ynxu sbda bikinta sati me xuwa ne, kasan har iyayen iliya sun xo anyi komai yau..." Kallonta ya dinga yi ko kiftawa babu, tace "Idan wani abu ne gani ni ka bani in ji Baabarmu in kai mata" Ya dauke kai daga kallonta yace "Mu je xan ba Baabar taku da kaina" Da sauri ta shiga gaba yana biye da ita, sae wani rangwada take har suka iso kofar gidan, tace "Bari in je in mata magana" daga haka ta shige ciki, Hansai na ganinta tace "Me ya baki?" Bibalo tace "Yace ki je yana kofar gida" Da sauri Hansae ta figi gyale ta yafa ta fita kofar gida, dukawa tayi ta gaishesa ya sauke idonsa shi ma ya gaisheta, ta amsa cike da nutsuwa tace "Sannu da xuwa Alhaji" 07087865788✍🏻 💖💖 *Jiddatul Khair**💖💖 _By Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 8..... Hansai ta shiga kame kame tace "Gashi babu ma wajen xama a nan Alhaji, ko xa ka shigo daga ciki a shimfida maka tabarma" Yace "Aa nagode, hakan ya isa..." Tana murmushi tace "Allah sarki... Da yake jiddar na daurayan kwanuka shine nace 'yar uwarta ta fito, jiki kam alhmdlh taji sauki sosai, duk ta shanye magungunan nata..." Abuturrab ya sauke idonsa kasa yace "Allah ya kara mana lafiya gaba daya" Hansai tace "Ameen, bari dai kawai in shiga in turo ta ku gaisa, ai yanxu nasan ta gama" daga haka ta shige gida ganin dai babu alamar Abuturrab xai bata komai, jiddah ta nufa da sauri, murya can kasa kasa tace "Tashi ki dau hijabinki ki saka ki fita yana nan kila ya fi gane ya baki, kada ki kuskura ku tsaya kofar gidan nan ki ja shi can karshen layi sbda yan sa ido, gashi iliya na gari, daga nan ma sai ki sanar masa bikin ki sati me xuwa ne idan Allah ya kai mu, kinga idan da akwai wani alkhairin da xai maki sai ya maki, kowa dai yasan ke marainiya ce ba uwa ba uba" Bibalo da ke tsaye kansu tana sauraron abinda suke cewa tace "To Baabarmu idan yaji xata yi aure fa kilan shkkn baxai sake dawowa ba, dama ba sbda awaran da take yi bakin titi bane yake tausaya mana yake bamu kudi?" Hansai tayi shiru, can tace "To kuma aure ae dole tayi abu saura sati daya dai har an gama komai, kawai ta gaya masa.. sannan ba ga ki ba, ai ke xaki ci gaba da yin awaran a bakin titi" Bibalo tace "Cabdijam, wllh baxan yi awara bakin titi ba kawayena da samarina na ganina, haka kawai?? sai dai ke ki dinga yin kayanki ni dai baxan yi ba, to ni ma ba sai a min auren ba kawai" Tana fadin haka ta shige daki tana gunguni, Hansai ta rike ha6a tace "Ikon Allah, yau naga jarababbiya, a maki aure? Duka nawa kike xa a maki aure, ita ma Jiddar ai don iliyan ya dade yana sonta ne kuma ya mana hidima ba kadan ba, ko so kike ya mana tijara yace sai mun biyasa? A gidan uban wa ma xan samu abun biyansa? ke kuma da nake da burin in samar maki makaranta cikin gari ki fara xuwa kya kawo xancen a maki aure, a can din sai kiga Allah ya hadaki da miji dai dai ke, nan banda yan kato da gora, da yan adaidaita sahu, ga leburori, ga yan gwangwan sai yan iskan anguwa, to waye sa'an auren ki duk cikinsu? Ai babu sa'an auren ki wllh, ke da kike matar babban mutum" Hansai ta kalli Jiddah da kanta ke kasa har lkcn tana sauraronta, ta hade rai tace "Baxa ki tashi kije ba kin bar bawan Allah tsaye a waje" Jiddah ta mike a hankali ta dauraye hannunta ta shiga daki ta dau Hijabinta ta sa, ta saka takalminta sannan ta fita Hansai ta bita da sauri murya can kasa kasa tana cewa "Ku bar kofar gidan ku je can bayan layi kada a samu me kai ma Iliya rahotu" Ita dai bata ce komai ba har ta fita, yana tsaye ya rungume hannayensa, a hankali ta karasa can jikin wani tsohon adaidaita da aka yi parking gaba da gidan nasu, ya bi ta da kallo sannan ya bi bayanta, jingina tayi da adaidaitan tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Sakon da kace xaka kawo min fa?" Yayi shiru yana dubanta, ta fashe masa da kuka tace "Kasan baxa ka kawo min ba me yasa kace xaka kawo min?? Alkawari fa ka min" Ya rungume hannunsa yace "Ohk abinda kika ce xa ki sha??" Ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, yace "Yaushe xa a daura maku auren?" Tace "Sati me xuwa, don girman Allah gobe ka kawo min, naje na tambaya a shago ance min ba dari biyu bane, kuma ni dari biyu gareni" Bude baki yayi yana kallonta da mamaki, can yace "Yaushe kika je kika tambaya?" Cikin rawar murya tace "Jiya" Ya sauke idonsa yace "To ai ni nace xan kawo maki ko? Kuma ban manta ba" Tace "Toh baka sake xuwa ba ai tun ranan" Yace "Toh gobe xan kawo maki" Ta gyada masa kai tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, Sauke idonsa yyi kasa yace "Wa kika sani a kaduna bayan Baabar nan taku?" Ta girgixa masa kai a hankali tace "Ba kowa" Yace "Wa xai daura maki aure?" Cikin rawan murya tace "Kawu Jibril" yace "Waye shi?" Tace "Kawun Baabarmu ne shi" Shiru yyi na kusan minti daya sannan yace "Ki koma kice da Baabarku xan yi magana da ita" Juyawa tayi ta koma ciki, Hansai na xaune tsakar gida tana fifita tana jiranta, ganinta ta mike da sauri tace "Ya aka yi kika dade, nawa ya baki?" A hankali Jiddah tace "Yace xa ku yi magana da shi" Hansai ta hade rai tace "Bai baki komai ba?" Jiddah ta gyada mata kai, Hansai tace "Toh ba naje ba mun gaisa, maganar me kuma xa mu yi" Bibalo ta leko tace "Ke dai kije ki ji abinda xai ce maki kawai" Hansai ta nufi kofar gida da sauri, tana ganinsa ta sunkuyar da kai tana d'an murmushi tace "Cewa tayi kace xa mu yi magana ko?" Yace "Eh, yanxu take gaya min sati me xuwa xa ayi aurenta" Hansai tayi kasa da murya tace "Wllh kuwa, tun uban na da rai ya ci bashin da ya fi karfinmu, bamu da halin biya, to dai kusan auren biyan bashi ne, tunda mu dai bamu da kowa duniyar nan banda Allah, bamu da kowa bamu da komai sai rubabben gidan can, to ya xan yi??" Tana fadin haka ta fara matsar kwalla, kallonta kawai Abuturrab yake da mugun mamaki, can yace "Nawa ne kudin bashin?" Goge idonta ta dinga yi tana tunanin kudin da xata lafto, can dai tace "Dubu dari ne da ashirin wllh" Yace "Ina shi me kudin?" Nan fa hankalin Hansai ya tashi, cikin rawan baki tace "Ehh to ba garin yake ba, kawai sai dai a kai masa, noma kawai yake yi a nan amma ba d'an garin bane" Abuturrab yace "Ohk, shi ne xai aureta?" Tace "Ehh, Aa ba shi bane gaskiya, d'an sa xai aura ma, ehh babban d'an sa xai aura ma" Abuturrab yace "Ohk, dama akwai wani aiki ne da nake son in bata ta dinga yi, duk wata xa a dinga biyanta dubu dari biyu, kinga idan tayi aure baxai yiwu ba, naga kuma ta fi 'yar uwarta kwazo, dama tana farawa da wata biyu sai a kawo yar uwartata, kafin nan ita ta kware sai ta dinga sa 'yar uwar a hanya" tuni xufa ya fara keto ma Hansai tana kallonsa tace "Dubu dari biyu fa kace Alhaji?" yace "Ehh haka albashin yake, amma dai yanxu xan je in ciro kudi in bata sai ta kawo maki ki biya bashin... Xancen auren kuma sai a fasa shi" Hansai na share wani xufa da kyar tace "Toh ai shkkn Alhaji, Allah ubangiji ya kara maka girma da daukaka, yanda kake rufa mana asiri haka Allah xai rufa maka asiri kai ma" Yana kallonta yace "Ameen, amma kina ganin auren xai fasu idan aka biyasu bashin su?" Da sauri Hansai tace "Ba dole ba, dama ai sbda kudin ne suke son rabani da diyata" Yace "Toh xan je in ciro kudi yanxu..." Hansai tace "Toh turo maka ita xa ayi kuje tare?" Yace "Ehh" juyawa tayi da sauri ta koma ciki, Jiddah na daki ta hade kanta da gwiwa Hansai tace "Jiddah tashi xa ku je ya baki kudi ki kawo yanxu, duk abinda yace maki kar ki kuskura kice ba haka bane, komai yace kice masa ehh haka ne, kinji me nace??" Kallonta kawai Jiddah ke yi, Hansai ta hade rai tace "Baxa ki tashi ba an bar sa a tsaye" a hankali Jiddah ta mike ta fita dakin, yana nan tsaye ta samesa, Sai da ya kalleta sannan ya fara tafiya, bin bayansa tayi har suka isa bakin titi inda motarsa yake, Bank ya tafi a can cikin garin don cire kudi a Atm machine, ta bi sa da kallo bayan ya sauka motar, bayan wani lkci ya dawo ya shiga motar ya dau karamin leda ya xuba kudin a ciki ya ajiye, bayan few seconds yace "Tace auren biyan bashi xaki yi" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ba haka bane" ya kalleta da sauri yace "To ya ne?" Hawaye ya kawo idonta tace "Kawai aure take son yi min da iliya sbda yana kawo mata abubuwa daga legas idan xai dawo" Abuturrab yace "Shi a ina yake xaune a kaduna?" Tana share idonta tace "Nan hayi yake shi ma" Yace "Xa ki nuna min gidansu?" Ta d'an yi shiru kafin ta gyada masa kai, tada motar yayi suka bar wajen, sai da suka shigo hayi yace "Ina ne gidan nasu?" Tace "Can gaba ne amma hanyar bbu kyau mota baxai shiga ba kuma da akwai nisa, dole sai da adaidaita" Yace "Ohk..." Ta gyada masa kai kawai, dai dai layinsu ya tsaya, ta dinga jiran ya bude mata motar ganin bai bude ba ta kallesa, yace "Yanxu idan aka fasa auren naki xaki hakura da kashe kan naki?" Shiru tayi tana kallonsa, ya d'an hade rai ganin kallon da take masa yace "Ina sauraron ki?" Sunkuyar da kanta tayi tace "Ehh" bude mata motar yayi ya mika mata ledan kudin ta amsa, xata sauka yace "Jira" Komawa tayi ta xauna tana kallonsa, yace "Kin iya amfani da waya?" Ta kallesa sannan ta girgixa masa kai alamar A'a, kunna fitilan motar yyi ya dau pen da wani karamin jotter ya rubuta numbersa ya mika mata yana dubanta yace "Idan da akwai wani abu ki nemi me waya ki kirani" Ta gyada masa kai, yace "Sauka" Ba musu ta sauka motar ta rufe masa ta fara tafiya.... Hansai na ta xaune tsakar gida tana jiran shigowar jiddah, sauro duk ya cijeta sai soshe soshe take, ganin jiddah ta shigo ta mike da sauri tana kallon ledan hannunta ta karasa kusa da ita ta amshe ta bude.... xaro ido tayi tana kallon uban kudin ciki, Jiddah dai na tsaye sai kallonta take ita ma, daki Hansai ta shige da gudu duk ta rude don yan dari biyar biyar ne kudin shi sa yayi yawa, Jiddah ta juya a hankali xata shiga dakinsu kenan aka shigo gidan babu ko sallama, Iliya ne da abokansa biyu kamar an hankadosu sai muxurai suke, ya nufi Jiddah yana huci ya fixgota ya xabga mata wani wawan mari cikin katon muryarsa yace "Uban wa ya sauke ki a mota yanxu?" Hansai na jin muryarsa tayin sauri cusa ledan kudin can karkashen jakarta tana salati ta fito da gudu, wani marin ya sake wanka mata ya hadata da bango ya lafto wani uban ashar yace "Da kudin nawa a kanki kike bin kartin alhazan nan suke yawo dake cikin gari, dama an gaya min ban yarda ba sai gashi yau na gani da idona, idan baki fada min waye shi ba al-qur'an sai na sumar da ke yau...." Yana fadin haka ya kara kai mata hauri ya shakota, ihu kawai jiddah take, Hansai da jikinta ya dau rawa tace "Ji mana Iliya, wllh wllh wani abokin uban gidan babansu ne jin xata yi aure ya tafi yi mata siyayya ya bada gudunmawarsa...." Wani wawan mari xai kai mata ta kauce da sauri ta bar wajen jikinta na rawa, kana ganinsa kasan a buge yake, Bibalo dai ta d'an windan dakinsu take leko su taki yarda ta fito bayan ta sakale dakin, Jiddah sai kichiniyar kwace kanta take amma ta kasa don ba rikon wasa yyi mata ba, Hansai ta nufi can bakin murhu jiki na rawa tace "Ka saurareni Iliya kada ka kashe min ita, wllh nace maka abokin wanda babansu yyi ma aiki ne a lkcn da yake raye, Jiddah ai ba haka take ba, jiddah kamilalla ce..." Sake Jiddah yayi ya juya yana kallon Hansai ya nufeta yana huci, wani ihu ta kwala tana cewa "Makota ku kawo mana dauki kar ya kashe mu...." Wani wawan naushi ya sauke mata a baki, tuni jiddah tayi waje a guje, daya daga abokan Iliya yace "Kai Iliya ta fice fahhh" iliya ya juya da sauri yace "Ku bi taaa" Duk suka fita da gudu, Iliya ya bi bayansu yana cewa daga nan kawai a kai min ita shagona, bikin banxa bikin hofi abinda har sadaki na biya naira duba sha uku, tinkiyar babata fa na dauke na siyar ko sani bata yi ba na biya sadakin, kawai a kai min amaryata..." Hansai dai tunda naushi ya sauka bakinta da ta fada cikin jerin bakaken tukwanen awaranta bata sake motsi ba sai 'yan idanuwa.... Jiddah na fita dama ta bayan layi ta xaga xuwa windon Iyah, a hankali ta dinga bubbuga windon jikinta na rawa tace "Iyah ni ce ki bude" Iyah tace "Aa ba ruwana an min iyaka da ke, ni da kika sa Hansai ta kusa cinna ma gidana wuta...." Wani ihu Jiddah ta fasa ganin Salmanu daya daga abokan Iliya, ya fixgo hannunta yace "Iliya gata na gano ta" Sai ga Iliya da gudu tare da Surajo, Iyah sai xare ido take jin ihun da jiddah ke yi, a haka Iliya ya ja ta xuwa adai daitan Surajo suka sa ta tsakiya Surajo ya hau adaidaitan ya tada, Iliya ya fiddo wukar aljihunsa yana nuna mata da jajayen idanuwansa yace "Al-qur'an idan baki rufan baki ba xan da6a maki wukar nan kowa ya huta" Tsit tayi jikinta na rawa hawaye na sauka idonta, can karshen kwalta suka kai ta, wani kuturun uncompleted house da Surajo ke ginawa, sbda rashin wajen kwana yake kwana a haka, Salmanu yace "Shikenan sai ku tare nan daren yau kafin gobe da safe Hansai taje tayi mata jere a shagon naka" Iliya yayi wani dariya ya sauka daga adaidaitan yana kallon Jiddah da ko kukan ta kasa sbda fargaba da shock, ya daure fuska yana kallonta da jajayen idonsa yace "Sauka mu shiga Amaryata ta kaina" Da kyar ta sauko daga adaidaitan ya tisa keyarta har cikin gidan wanda duk dogayen ciyayi ne, Surajo yace "To ko 'yar kifi da ruwan leda ba a siya mata ba ai" Iliya yace "Ai akwai wasu daren masu xuwa da yawa bayan wannan, idan bata ci yau ba xata ci gobe" Surajo yace "Da akwai lemo daya ma da na siyo da rana ban sha ba sai ka bata ta sha kawai" Dariya duk suka dinga kyalkyalewa da, Can jikin bango jiddah ta rakube kusa da yar katifar dake kwance a dakin da wani karamin fitila da bbu hasken kirki, ko siminti bbu a kasa, banda warin ta6a da wiwi bbu abinda dakin ke yi, ta runtse ido tana jin abubuwan kamar a mafarki, sallama su Surajo suka yi ma iliya suka fita dakin suna dariya suka yi masa sai da safe, Ya mike ya kulle kofar ya dawo ya xauna ya fiddo kwalin ta6arsa ya kunna ya fara xuka yana kallon Jiddah da ta takure ko ina na jikinta na rawa, yyi kasa da murya yace "Kiyi hakuri amaryata cikin bacin rai na bubbuge ki, raina ne ya baci ba kadan ba, kinsan idan raina ya baci bana ganin komai idona rufewa yake, har mutum ina iya kashewa, yo sau nawa ma aka yi hakan, kawai garbati ya ce min kusan kullum sai an xo an tafi dake an dawo a katuwar mota.... Shi ma shegen dake tafiya dake a motar ya ci sa'a bamu hadu ba wllh" Ita dai Jiddah bata ce komai ba jikinta sai bari yake, ya mike ya dawo kusa da ita ya xauna yana xukan hayakinsa yana murmushi ya rungumota kusa da shi, ta runtse ido xuciyarta na bugawa da sauri sauri, yace "Inji dai baki jin yunwa ko Amaryata?" Ta girgixa masa kai da sauri, ko kallonsa bata son yi kar ta saki ihun da take hadiyewa, ya wurgar da guntun taban hannunsa ya mike ya fara cire kayan jikinsa, Abuturrab ne ya fado mata, hawaye me xafi ya fara silalowa idonta, Bata san lkcn da ta fasa wani ihu a mugun tsorace ba ta rufe fuskarta da gwiwanta... Ya hade rai ya buga mata dundu a baya yace "Kee, ki kiyayeni fa, so kike ayi tunanin fyade xan maki bayan ke halaliya ta ce, dubu sha uku na biya jiya jiyan nan, har yanxu Babata bata san yanda aka yi da tinkiyarta ba, shine xaki kawo min iskanci, to idan xaki saki jiki ki saki, don muna nan da ke har sai an kira assalatu wllh...." Ta kallesa cikin dakiya amma muryarta na rawa tace "Fitsari xan yi" yyi murmushi yace "To ko ke fa, amaryata, ai gwara kawai ki saki jikin ki" Ya mike ya yace "Mu je in raka ki" Tashi yyi ya dagota xai cire Hijab din jikinta ta rike da sauri cikin rawar murya tace "Aa wllh sanyi nake ji" Bai saurareta ba ya cire Hijab din ya jefar kan gado ya nufi kofa ya bude yace "Mu je kiyi fitsarin" Ta bi sa da sauri jikinta na rawa, wani lungu ya nuna mata a jikin gidan, tun bata kai nan ba take jin zarni na tashi a wajen, yace "Kije kiyi ki dawo ki sha lemo kinji amarya" Ta gyada masa kai ta nufi wajen, komawa ciki yyi da sauri ya dau wandonsa ya laluba ciki ya fiddo wani karamin kwalba, sannan ya dau lemon coke dake ajiye a dakin ya bude, ya bude kwalban ya tsiyaya abinda ke ciki cikin lemon sannan ya rufe ya d'an jijjiga lemon ya sha kadan ya ajiye sauran, ya mayar da kwalban aljihunsa yana murmushi yace "Tass xa ki shanye lemon nan" xaunawa yyi gefen katifa yana jiranta, da sauri ya mike kamar wanda ya tuna abu ya nufi waje ya leka yace "Ke Jiddah, har yanxu baki yi fitsarin bane" A wangale ya ga d'an zinc din da aka yi kofa da shi na gidan, ya xaro ido ya fita da gudu yana kwala mata kira, gudu kawai Jiddah take wajajen da bbu kowa babu wasu gidaje sai ciyayi, sai da tayi gudu sosai taga wani me adaidaita ta tsayar da shi jikinta na rawa tace "Don girman Allah ka taimakeni wllh sato ni yayi, don Allah ka rufa min asiri ka taimakeni" Bata jira cewarsa ba ta shige adaidaitan don ya tsaya, shi ma mai adaidaitan duk a tsorace yake ya dinga gudu har suka shigo cikin mutane, har sannan Jiddah waige waige take gabanta na faduwa, sai da suka shigo hayi sosai sannan yace "Daga ina suka dauke ki?" Tace "Can cikin gari" Ya girgixa kai yace "Yanxu ina xa ki?" Shiru tayi don tasan tana komawa gida yanxu Iliya xai iya xuwa can gidan, da sauri tace "Cikin gari xan je don Allah" Dai dai kano road mai adaidaitan ya tsaya yace "To anguwan naku ba shi da sunana ne a cikin garin, ni fa nan ne iyakata?" Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta bude tafin hannunta tana kallon takardan da Abuturrab ya bata daxu, har lkcn takardan na hannunta gam, ta kalli mai adaidaitan cikin sanyin murya tace "Don Allah kana da waya?" Yace "Ehh" tace "Toh ka taimaka ka kira min number nan don Allah" ya amshi takardan ya dau wayarsa ya kwashe lambar sannan yayi dialing, Abuturrab na xaune parlon Abbansa yana masa calculating din order din da Abban nasa yyi daga waje na kayan auren Ramlah wayarsa ya fara ring, Abba ya kallesa ganin ba daukan wayar xai yi ba yace "Pick ur call" hakan yasa Abuturrab ya dau wayar yana kallon number kafin ya daga ya kai kunne, Mai adaidaitan ya mika ma Jiddah wayar ta amsa ta kai kunne, calmly Abuturrab yace "Hello" Hawaye ya silalo idonta tace "Ni ce" Kallon Abbansa dake kallonsa yyi da sauri, sai kuma ya sauke kansa kasa yace "Ohk ina ji" Ta fashe da kuka sosai tace "Iliya ne ya xo ya daukeni wai saboda ya ganni a motarka...." Abuturrab ya dago da sauri yace "Xuwa ina?" Cikin kuka tace "Wai shi ba sai anyi biki ba tunda ya bada sadaki, nufinsa tarewa xan yi" Abuturrab ya saci kallon Abbansa ya rasa abinda xai ce, Abbansa dake lura da shi ya mike ya shiga bedroom dinsa, mikewa yyi da sauri ya nufi kofa ya bude ya fita yace "Kina ina yanxu?" Ta bi inda take da kallo tace "Mai adaidaitan yace min kano road ne" Abuturrab yace "Ba sa wayar" Mika ma mai adaidaitan wayar tayi ta shiga share hawayen da ya ki tsaya mata, Mai adaidaitan yace "Ehh a dai dai wajen muke ma" bayan few seconds mai adaidaitan yace "Toh shkkn xan jira in sha Allah" Daga haka ya katse wayar, Abuturrab ya koma parlon Abbansa, Ganin bai fito ba ya karasa bakin bedroom din yayi masa sallama, Fitowa Abba yyi, Abuturrab yayi kasa da kansa yace "Abba xan d'an je in dawo ynxu, wani abokina ne ya kirani and it's urgent" Abba yace "Alright sai ka dawo" Juyawa yayi ya fita daga parlon, ya tafi dakinsa ya dau makullin motarsa, jallabiya ne jikinsa ya fita a haka ya shiga motarsa ya bar compound din..... 07087865788✍🏻 💖💖 *Jiddatul Khair* 💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 9..... Abuturrab yayi parking yana bin wajen da kallo ya dau wayarsa yayi dialing number da suka kirasa da shi, yana fara ring mai adaidaitan dake hira da wani me d'an kiosk a wajen ya daga, Abuturrab yace "Ka duba wani bakar mota a wajen da kace" Mai adaidaitan ya mike yana dube duben wajen, can ya hango motar Abuturrab ya kalli Jiddah dake xaune cikin adaidaitan har sannan ta takure waje daya yace "Ga sa can ya iso" Dago kai tayi da sauri sannan ta sauka daga cikin adaidaitan, tare suka tsallaka titi da shi xuwa daya side din ya nufi motar Abuturrab tana biye da shi a baya, Abuturrab ya bude motar ya sauko yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi sbda hawayen da ya kawo idonta, ya kalli mai adaidaitan ya ciro dubu biyu aljihunsa ya mika masa yace "Nagode" Mai adaidaitan ya amsa shi ma yyi masa godiya sannan ya tsallaka ya koma gun Napep dinsa, Ba tare da Abuturrab ya kalleta ba yace "Shiga" Ba musu ta shiga gaban motar, ya shiga maxaunin driver ya tada motar suka bar wajen, a hankali yake driving din yace "Bayan na tafi sai me ya faru?" A hankali ta fara basa labarin abinda ya faru bayan tafiyarsa babu abinda ta boye masa har karshe, ganin yanda take kuka ya kalleta yace "Ya maki wani abu ne?" Ta girgixa masa kai, rasa particular tunanin da xai yi yayi a lkcn, babban damuwarsa yanxu inda xai kai ta cikin daren nan, ya d'an kalleta yace "Yanxu babu wanda kika sani nan cikin gari?" Ta girgixa masa kai tace "Ba kowa" ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya yana ci gaba da driving dinsa almost absentminded, parking yayi bakin gate din gidan, har Mai gadin ya mike xai bude gate ganin yayi parking a nan waje sai ya koma ya xauna, Abuturrab ya sauke glass ganin haka mai gadin ya sake tasowa da sauri ya nufosa yana murmushi cike da girmamawa yace "Barka dai ranka shi dade..." Abuturrab yace "Ya aikin?" Mai gadi yace "Alhmdlh, Baxa ka shiga ciki ba?" Abuturrab ya d'an shafa kai yace "A'a, wani d'an alfarma nake nema gun ka" Cike da natsuwa yace "Toh ina saurarenka yallabai" Abuturrab yace "Erm... Mai dakinka na nan ai?" Mai gadin yace "Ehh tana ciki wllh" Abuturrab ya kalli Jiddah yace "So nake don Allah ta d'an kwana nan wajen ku kafin gobe, amma kamar kuma hakan da takura tunda daki daya ne ko?" Da sauri Mai gadin yace "Inaa babu wani takura wllh ranka shi dade, ni ai ba baccin ma nake da daddare ba yawanci nan tsakar gida nake kwanciyata wllh, kar kaji komai" Abuturrab yace "Toh nagode, amma kada kace ma masu gidan na xo" Mai gadin yayi murmushi yace "Baxa ayi hakan ba ranka shi dade" Abuturrab ya juya yana kallon jiddah yace "Sauka, sai da safe..." Yana fadin haka ya bude mata motar, ta sauka a hankali, Mai gadin yace "Mu je ciki to...." tafiya ya fara yi ta bi bayansa sai da suka kusa gate din ta waiga ta kalli Abuturrab da ya bi su da kallo, dauke kai tayi ta bi mai gadin suka shiga cikin compound din, yayi wani sigh ya tada motarsa yayi reverse ya bar layin wani ajiyar xuciyar ya sake saukewa feeling a bit relieved. Har aka idar da sallan asuba Jiddah bacci take, matar mai gadin na idar da sallah ta d'an ta6ata tace "Ki tashi kiyi sallah lokaci yayi" a hankali Jiddah ta bude idonta ta mike xaune da sauri, daki ne babba gun katifar kadai ne suka yi demarcating da labule, yaronsu daya wanda ko yayesa ma ba ayi ba, jiddah ta mike matar ta nuna mata bandakinsu dake cikin dakin, tana fitowa matar ta bata hijab, bayan ta idar abun ka da bata saba komawa bacci ba ta kalli matar ta gaisheta sannan tace "Babu wani aikin da xa ayi?" Matar tayi murmushi tace "Aa babu, ki koma kiyi kwanciyar ki" Jiddah bata ce mata komai, amma duk yanda ta so komawa bacci bata iya ta koma ba don ta riga da ta saba da wahala, gari na wayewa ganin matar ta dau tsintsiya xata fara sharan daga nan inda suke xuwa bakin gate don gidan akwai me shara, jiddah ta amshi tsintsiyar, matar tace "Don Allah ki bari ki koma kiyi xamanki...." Murmushi kawai Jiddah tayi tace "Aa xan taya ki" Tana fadin haka ta fara sharan hakan yasa matar ta koma ciki don yi ma yaronta wanka tana yaba hankalin Jiddah, shi kuma mai gadin na can xaune waje, jiddah na cikin shara aka bude gate din gidan ta dago da sauri, sosai gabanta ya fadi ganin wanda ya shigo, a hankali ta juya tana ci gaba da sharanta, waya ne kare kunnensa ya katse wayar yace "Maman Abdallah kun tashi lafiya" Ba tare da ta bari ta kallesa ba a hankali tace "Ba ita bace" Ko rufe baki bata yi ba Maman Abdallah ta leko da fara'arta, cike da ladabi tace "Ba ita bace Dakta, bakuwa nayi, ina kwana" yana tafiya yace "Lafiya lau, Abdallah bai tashi ba?" Tace "Kaya nake sa masa ya tashi tun daxu" yace "To a gaida min shi" Tace "Xai ji Dakta" Entrance din gidan nasu ya nufa, Jiddah ta bi sa da kallo tana sharanta a hankali... Karfe takwas Maman Abdallah ta kalli Jidda bayan ta gama shiryawa cikin kayan da ta bata tace "Tunda kinyi wanka mu shiga daga ciki mu gaisa da 'yan gidan in amso mana kumallon mu, ko" Jiddah dai tayi shiru bata ce komai ba, Maman Abdallah ta goya d'anta tace "Tashi mu je, Hajiyar gidan ta tashi yanxu" A hankali Jiddah ta mike ta dau Hijabin matar ta sa sannan suka fita, Maman Abdallah ta bude kofar hade da sallama ta shiga ciki Jiddah na biye da ita, Xaunawa tayi kasa jiddah ma ta xauna kasa, Hajiya Ramlah dake parlon da murmushi fuskarta tace "Bakuwa kika yi Shafa" Maman Abdallah ta washe baki tace "Ehh wllh Hajiya, bakuwa nayi da yammacin jiya" Cike da ladabi ta risina tace "Ina kwana Hajiya" Umma tace "Lafiya lau kun tashi lafiya?" Maman Abdallah tace "Alhmdlh, su Maimuna da Siyama na ciki kenan" Umma tace "Suna ciki..." Jiddah na kallonta a hankali tace "Ina kwana?" Umma tace "Lafiya lau yan mata, sannu da xuwa.... ya sunanki?" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Jiddah" jin footstep ta dago tana kallon direction din, Ahmad ne ke sakkowa daga sama yana kallonta babu ko kiftawa, Umma tace "Ahh me babban suna ce ashe" Jiddah tayi murmushin karfin hali ta sunkuyar da kanta, Umma tace "Maa sha Allah, sunan yayata gare ki, sannu da xuwa" Maman Abdallah dai sai washe baki take, Umma tace "Yar uwarki ce amma" Maman Abdallah ta sosa kai tace "Ehh kauyenmu daya" Ahmad dai sai kallon Jiddah yake, ita kuma taki yarda ta sake kallonsa, Maman Abdallah ta mike ta wuce kitchen don daukan kumallonsu, tana shiga ta dauka a inda mai aiki ta ajiye masu ta fito, Umma ta kira mai aikin tace "Tunda suna da bakuwa ki kara masu" Mai aikin ta amsa ta koma kitchen din, ba a dau lkci ba ta dawo ta mika ma maman Abdallah coolern, Cike da ladabi Maman Abdallah tace "Mun gode hajiya Allah ya kara girma" Umma tace "Ameen" Mikewa Jiddah tayi ta amshi warmer din a hannunta sbda Abdallah dake bayanta ita ma ta yi ma Umma godiya sannan suka fita, Ahmad dai ya bi ta da kallo.... He looks so confused, sak tayi masa kama da mai awaran hayi, wata xuciyar tace kawai kamanni ne me xai kawota cikin gari har cikin gidansu kuma, daga kafada yayi a ransa ya bar sa a cewar kamannin ne, ya nufi dining don yin breakfast. Karfe goma Abuturrab ya fito gida, driving yake yi with different thought in mind, wayarsa ne ya fara ring ya kalli wayar ganin Ahmad ke kiransa ya daga, Bayan sun gaisa Ahmad yace "Muna chatting kuma ka sauka" Abuturrab yace "Ehh i am driving now" Ahmad yace "To where?" Abuturrab yace "Aunty ta aikeni" Ahmad ya d'an ta6e baki yace "Ohk, wai ka dauki hutu ne naga baka koma gun aiki yau ba?" Abuturrab yace "Kai me ya dawo da kai during week day?" Ahmad yace "Wani taro xa mu yi nan kaduna, amma gobe xan koma ai, in sha Allah" Abuturrab yace "Ohk anjima xan shigo idan na dawo" Ahmad yace "Alright" daga haka ya katse wayar ya ajiye, parking yyi inda ya saba parking din, ya sauka motar yana kallon layin dake cike da mutane, wani d'an saurayi dake fitowa daga layin ya kalla yace "Abokina me ke faruwa a nan?" Saurayin yace "Wata amarya ce saura sati bikinta aka nemeta aka rasa, wasu sunce angon ne ya dauketa, wasu kuma su ce uwar rikonta ta san inda take, ynxu dai ga shi angon na neman cinna ma gidan wuta wai sai an fito masa da matarsa, uwar rikon na can tana kuka da rantse rantse bata san inda take ba, jama'a kuma na ta dannan shi angon, da yake babu wanda bai san halinsa ba a unguwar nan, sai ya iya kona gidan, yanxu dai wajen yan sanda ko mai anguwa suke shirin xuwa" Abuturrab yace "Toh Allah ya kiyaye" Barin anguwar Abuturrab yayi, yana isa gidansu Ahmad yayi parking a waje, ya sauka motar gaisawa yayi da mai gadi dake xaune a waje sannan ya xauna kusa da shi murya can kasa yace "Kayi hakuri babu wani bayani na kawo maku yarinya..." Mai gadin ya katse sa da sauri yace "Babu komai ranka shi dade, kar ki ji komai wllh, xata iya xamanta har iya sanda xaman nata xai kare a nan, ni bani da matsala haka ma mai dakina.." Abuturrab ya sa hannu aljihu ya fiddo dubu biyar ya mika masa yace "Gashi ka rike wannan" Mai gadin ya girgixa kai yace "Aa kar mu yi haka da kai don Allah" Abuturrab ya ajiye masa kudin ya mike ya shiga gate din gidan, Babu kowa tsakar gidan ya kalli building din mai gadin sannan ya nufi main entrance din gidan. Kiran azahar ne ya sa shi fitowa tare da Ahmad xa su tafi masallaci, Jiddah na xaune compound din kan karamin kujera kusa da dakin mai gadin da ruwa cikin buta a gabanta tayi nisa tunanin da take, Har suka kusa isowa wajen Abuturrab kallonta yake haka ma Ahmad, kamar ance ta daga kai tayi ido hudu da su, sosai gabanta ya fadi ta sunkuyar da kanta da sauri ta fara alwala da ruwan butan gabanta har suka fita compound din, sai a sannan Ahmad ya kalli Abuturrab yace "Don Allah wa yarinyar nan tayi maka kama da???" Abuturrab yace "Wacce yarinya?" Ahmad yace "Yarinyar da ke xaune a compound" Da mamaki Abuturrab yace "Ohh dama akwai yarinya xaune a compound din?" Wani kallo Ahmad ya jefa masa, Abuturrab ya daga shoulders dinsa yace "Banyi noticing ba" Ahmad yace Karya kake "Wllh" Abuturrab bai kuma ce masa komai ba, Ahmad yace "Joke apart captain, bata yi maka kama da wannan yarinyar da muke siyan awara a wajenta a hayi ba" Abuturrab ya ta6e baki yace "Kai da kake kallonta kenan idan kaje siyan awaran, ni kam banda murhu babu abinda nake gani a wajen" yana fadin haka ya shige Masallaci kafin Ahmad ya sake ce masa komai, Ahmad ya bi bayansa kawai. Ko da suka fito masallacin Ahmad ya tsaya gaisawa da abokansa na layin, Abuturrab ya shiga compound din kawai, Jiddah na ta sauri tana kwashe kayan shanyan da Maman Abdallah ta shanya don garin akwai hadari, tun da ta kallesa sau daya ta dauke kai sai da ya iso dai dai inda take tace "Ina yini?" Bai amsa ba yace "Kina da wani matsala?" Ta girgixa masa kai, ganin haka ya ci gaba da tafiyarsa, dai dai nan Ahmad ya shigo compound din bata yadda ta kallesa ba har xai wuceta sai ya tsaya yace "Bakuwa muka yi yau a gidan ashe?" Taki yarda ta kallesa still, tayi kasa da murya tace "Ina yini" yayi murmushi yace "Lafiya lau, sannu da xuwa" Maman Abdallah ta leko tace "Dakta Abdallah fa boyewa yake idan yaji muryar ka" Ahmad yayi murmushi yace "Ae kice masa alluran ya kare" Ta kwashe da dariya tace "Lallai kam, shi dai ya tsorata da kai kawai Dakta" Ahmad yace "Ashe bakuwa muka yi gidan" Tace "Ehh wllh yar uwata ce daga kauyenmu ta xo jiya da yamma" Yace "Allah sarki, toh barkan ta da xuwa" Maman Abdallah tace "Ae ko dai Dakta, mun gode" Murmushi yayi ya ci gaba da tafiya a xuciyarsa ya kara gaskata cewa lallai kamanni ne kawai suka yi da me Awara a hayi, but the resemblance is so obvious even the dimples and large eyes, can balcony Abuturrab ya tsaya duk yana jin abinda suke fada, sai da ya iso Abuturrab yace "Kai dai baka abu da class Ahmad, meye na tsayawa hira da matar mai gadi pls?" Bai jira me xai ce ba yayi wucewarsa ciki, Ahmad ya girgixa kai kawai ya bi bayansa. Da yamma Mamam Abdallah ta ba jiddah kwanukansu ta kai can cikin gida sbda a ciki xa a sa masu abincin dare, Jiddah tace "Ta cikin parlon ake bi xuwa wajen girkin?" Maman Abdallah tace "Ehh inda muka je daxu ba, ynxu ma babu kowa gidan yaran duk sun tafi islamiyya, Hajiya nasan tana bangarenta yanxu haka, ai kinga dakin girkin da mai girki ta fito ta miko mana kumallo daxu da safe, nan xaki shiga, dakin ma ya kusa biyun wannan da muke ciki ae wllh" Jiddah ta mike ta dau babban samiran ta fita ta bar Maman Abdallah na linkin kaya, Babu kowa babban parlon kamar yanda Maman Abdallah tace, ko ina tsaf sae kamshin turaren wuta da ya kama parlon, Kasa karasawa can cikin parlon Jiddah tayi, tun da ta xo duniya bata ta6a ganin irin wannan parlon ba da ma komai na cikinsa, duk sai tsoro ya kamata, hanyar da taga Maman Abdallah ta bi daxu da safe ta bi ta d'an leka kofar da ta gani a bude ganin wasu mata biyu kuma har sun hada ido ta risina a hankali tace "Sannun ku da aiki" Duk suka amsa mata dayar tace "Shigo ki ajiye kwanon" Jiddah ta karasa kitchen din, ta kara masu sannu da aiki sannan ta ajiye kwanon, kanta a kasa tace "Me xa a kama maku?" Dayar matar tace "Aa babu komai 'yan mata, mun gode" Doguwar tace "Sae dai kawai wanke wanken dake cikin bahon wanke wanke, ba shi da yawa" Jiddah ta juya tana kallon sink da matar ke nuna mata, karasawa tayi wajen ta tsaya tana tunanin ta ya xata yi wanke wanke a takurarren waje haka sannan ta ina xa ta dinga xubar da ruwan wanke wanken, a hankali ta juya tana kallonsu tace "Ruwa da omo fa" Matar tace "Ga pampo a gabanki ki kunna, wannan roban kuma sabulun wanke wanke ne a ciki xaki matso ya fito" Bayan magrib Abuturrab yyi parking inda ya sa6a parking ya sauka motarsa ya kulle da kafa ya karasa kofar gidansu Jiddah. Yaro ya aika ciki yayi masa sallama da mutanen cikin gidan, Hansai ce xaune tsakar gida da kawayenta biyu, Hansai ta sharbe majina tana matse hawayen kumburarren idonta tace "Wllh xai aika, waye bai san cewar shaye shaye Iliya yake ba, ni dai baxan kwana gidan nan ba yau gaskiya gwara in tafi wani wajen in kwana" Zulai tace "Aa nima dama ban bada shawaran ki kwana ba tunda ya furta sai ya kona gidan da kyar baxai aika ba" Ladi tace "Toh yanxu ina yarinyar nan ku ke tunanin xata tafi haka, wa gareta a duniyar ma gaba daya?" Hansai tace "Ai wannan magana ma bai taso ba, dolenta ta dawo duk inda ta tafi ta xo ta rabani da wannan mahaukacin mutumi, idan ya kona min gida gidan ubanwa xan koma kowa na ta kansa a rayuwar nan, dama gidan iyah nake ta tunanin ta shige amma duk dubawan da yan sanda suka yi a gidan babu ita babu alamarta" Kallon yaron da ya shigo suka yi gaba daya, yaron yace "Wai ana sallama a waje" Abuturrab ya daga kai bayan Hansai ta fito cikin gidan, ganinsa ta makale kofar xaure ta kasa karasowa, Ya karasa shi, yana dubanta yace "Ina yini?" Da kyar cikin rawar murya tace "Lafiya lau Alhaji, sannu da xuwa" kafin yace mata komai ta fashe da kuka tace "Muna cikin tashin hankali da alhini Alhaji" yana kallonta yace "Me ya faru?" Tana matsar kwalla tace "Tun jiya ake neman yarinyata har xuwa yanxu babu labarinta, ban san inda xan sa kaina ba xuciyata kamar ta fashe" Yayi shiru yana kallonta, ta sharbe majina tace "Shi kansa wanda ke da niyyar auren nata nan ya xo daxu da yamma ba irin tijaran da bai min ba har da ikirarin xai kona mana d'an gidan nan idan ba a fito masa da matarsa ba, wllh wllh bamu da masaniyar inda take, babban tashin hankalina ban san halin da take ciki ba yanxu" Yace "Yanxu ya ake ciki da shi wanda xai aureta din, baki basa kudin nasa bane?" Tace "Wllh yace baxai amsa ba, yanxu haka ma da kudin na tafi gun yan sanda na kai rahotu kasan sai an basu wani abu me d'an tsoka kafin su kula ka, sannan gidan radio da gidan talabijin duk na bi na rarraba masu kudin don su yi ta sanarwa har Allah ya bayyanata, yanxu maganar da nake maka ko dubu talatin ina jin kudin bai kai ba a ajiye a daki, 'ya ta bata fiye min komai ba a duniya?" Kallonta kawai Abuturrab yake bai ce komai ba, ta sake sharbe majina cikin rawar murya tace "In dai da wani taimakon da xaka mana yarinyar nan ta bayyana da wuri ka taimaka domin girman Allah Alhaji" Abuturrab yace "Ina shi madaurin auren nata?" Tace "Kawuna ne, tare da shi ma muke ta sintirin gidan radio da police station tun safe" Abuturrab yace "Ina son ki hadani da shi" Sosai gabanta ya fadi, yace "Yana da waya?" Da sauri tace "Aa bashi da shi, sai dai gobe in je in sanar masa, idan ka xo sai Bibalo ta kai ka" Abuturrab yace "Toh shkkn, nagode, sai goben" Daga haka ya juya ya bar wajen, ta bi sa da kallo gabanta na faduwa, da sauri ta koma ciki, Zulai tace "Waye hala?" Hansai ta share wani xufa da ya keto mata tace "Aa yan xuwa jaje ne, yanxu dai gidan Kawu Jibril xan tafi tare da Bibalo idan ya so sai mu kwana can kawai kada Iliya ya far mana cikin dare mu mutu" Ladi tace "Gaskiya kam, ku tafi can din kawai ku kwana, don kwana gidan nan ba karamin hatsari bane" Sai kusan karfe tara Hansai ta isa gidan kawun nata da Bibalo, Suna shiga d'an tsakar gidan yace "Me kuma kika xo yi nan kina neman ki ja min fitina Hansatu, ni nasan Iliya d'an daba ne amma bansan dabancin nasa ya kai haka ba, babu irin tijaran da iliya bai xo nan da tawagarsa sun min ba, in don dai shegiyar dubu ukun da kika bani ne cikin kudin sadakin yarinyar Allah ya kai mu gobe da safe in tafi in siyar da kaji na in baki kudinki, wannan tashin hankali har ina a kan dubu uku, wllh ban san tantirancin iliya ya kai har haka ba, to gaskiya baxai yiwu ba kuma ki fitar min daga gida kada ma yasan kina nan in shiga uku" Hansai ta fashe da kuka tace "Amma dai duk hatsin da yake kawo min ina dibar maka har rabin kwano wataran in kawo maka, har gawayi na sha cika maka leda me kayau kayau in kawo maka, kuma matsala ta samu sai ka rufe ido kace xaka koreni, cewa yayi fa xai kona gidanmu, idan na shashantar da batun ya babbake mu cikin dare fa?" Kawu Jibril yace "Toh ni cewa yayi xai ruguje gidan, ganinki ciki ai sai ya kara tunxurasa ya aikata hakan" Hansai na matsar kwalla tace "Yanxu duk ba wannan ba, dama wani Alhaji ne ya xo xai taimake mu kan lamarin da ganinsa babban mutum ne me fada aji, kuma tun mutuwar isuhu yake xuwa siyan awara ya mana ihisani, yanxu dai so yake ku hadu gobe a kan lamarin nan, don Allah ka sanar masa duk mun je gidan radio da gidajen talabijin din kaduna kai rahotu, dubu biyar xan baka kar kaji komai" Yace "Ina dubu biyar din?" Tace "Ba ni nace xan baka ba, fatanmu kawai ya taimakemu Allah ya bayyano mana da shegiyar yarinyar nan mu mika ma Iliya tsiyarsa ko ma sarara, don idan ba nemota aka yi ba aka damka ma Iliya bamu da sauran kwanciyar hankali wllh" Bata jira cewarsa ba ta shige dakin matarsa tana cewa "Lantana duk garin nan babu wanda bai xo min jajen abinda ke faruwa ba amma banda ke, ko ba komai ai sai ki ajiye duk wani tsiya dake tsakaninmu a matsayinki na musulma kixo ki jajanta min wannan musiba da ta sameni..." 07087865788....✍🏻 Start ur payment for the book because i am almost and almost done with free pages kar ku ji dippp an dakata💖 💖💖 *Jiddatul Khair**💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 10.... Washegari da asuba bayan an idar da sllh Ahmad ya fito rike da karamar jakarsa, dakin Ummansa ya shiga ya gaisheta tace "Da asuba xaka tafi Ahmad?" Yace "Ehh kar nayi missing train din ne" Umma tace "To kun yi da drivern ya xo da asuba ne ko wa xai kai ka train station din??" Yace "Aa Abuturrab xai kai ni" Umma tace "Abuturrab kuma? yana garin ne? Lafiya bai koma aiki ba" Ahmad yace "Ehh satin nan yana nan yace min" Umma tace "Toh Allah ya tsare, kayi addu'a dai" Yace "Ameen Umma, in sha Allah" Har ya kai kofa tace "Har xaka tafi gashi ka mance da drugs din nawa" Juyowa yayi da sauri yace "Oops, kiyi hakuri Umma Abuturrab xai kawo maki anjima in sha Allah" Tace "Toh Allah ya kai mu, Allah ya kiyaye hanya" sallama ya kara mata ya fita dakin, yana fita compound ya dau wayarsa ya shiga kiran Abuturrab, Abuturrab ya daga yace "Gani na shigo layin yanxu" Ahmad yace "Alright" Sai da suka yi nisa Abuturrab ya d'an kalli Ahmad yace "Medical report din da nace xaka min din fa?" Ahmad yace "Idan aka yi how will it reach you?" Abuturrab yace "The plane coming from Abuja to kano, xan yi ma pilot din magana abokina ne, sai ku hadu ka basa" Ahmad yace "Flight din karfe nawa ne?" Abuturrab yace "karfe uku" Ahmad ya tabe baki, Can ya kalli Abuturrab yace "Toh wai ma me ya hanaka komawa gun aiki kake neman medical report din karya Captain?" Abuturrab yace "That is none of ur interest, kai dai kawai kayi min medical report" Ahmad yace "Toh baxa ayi ba" Abuturrab bai kuma ce masa komai ba har suka iso Station din, Ahmad yace "Yauwa pls captain i will text some drugs now to you, na umma ne, xaka siya ka kai mata, i forgot to do so yesterday" Abuturrab yace "A hakan xan siya magani in kai mata? Kana ganin babu kaya jikina" Ahmad ya kallesa, Jallabiya ce milk color jikinsa, Ahmad yace "Shi kuma wannan bargo ne a jikinka kenan, beside ni bance da safe ba, wani pharmacy xaka samu a bude this early, kaga dole dai sai anjima" bude motar Ahmad yyi ya sauka yace "Thank you" Daga haka ya rufe motar ya shiga cikin tashan, Abuturrab ya bi sa da wani irin kallo, bayan few minutes ya ja motarsa ya bar wajen, Abuturrab ya na isa gida text din Ahmad na drugs din ya shigo, lkci daya alert din kudin drugs din ma ya shigo, tsaki Abuturrab yayi ya cire jallabiyan jikinsa ya shiga bathroom. Karfe goma saura Abuturrab ya fito dakinsa, bangaren step mum dinsa ya fara shiga ya gaisheta, tana gyara press dinta tace "Ina xuwa da sassafen nan haka, kai da nake tunanin ka dau hutu ne don ka huta" Yace "Xan je siya ma Umma drugs dinta ne" tace "Tohhh, Ahmad din fa?" Yace "Ya koma gun aiki" Tace "Toh nima ka siyo min Panadol night..." Yyi murmushi yace "Toh in sha Allah" Ya juya xai fita tace "Captain shiru shiru kuma baka turo abun ba, kada a siye wajen ne fa" Yace "Ehh ina son in sanar ma Ummi ne...." Da sauri tace "Sai ka sanar mata captain? Ina ce yanda ka dauketa haka ka daukeni?" Ya d'an yi shiru, sai kuma yyi murmushi yace "Toh nawa ne kika ce?" Tace "1.7m" yace "Toh xan tura in sha Allah" Tace "Yauwa ko kai fa, idan ka dawo anjima ka shigo da akwai wata maganan kuma" Yace "In sha Allah" daga haka ya fita, bangaren Ummi ya shiga, waya ne kare kunnenta, hakan yasa ya jingina da kofa ya jira har ta gama sannan ya risina ya gaisheta, tace "Lafiya lau..." yace "Jiya na shigo kin yi bacci" Tace "Ehh da wuri na kwanta" Yace "Ohk, sai na dawo" Daga haka ya fita dakin ta bi sa da ido. Abuturrab na shiga mota yayi ma Ahmad transfer din kudin da ya turo masa, sannan ya nufi wani babban pharmacy, ya siya duk drugs din, bai mance na Stepmum dinsa ba, ita ma ya siya mata pack har uku na drug din da tace sannan ya dau hanyar gidansu Ahmad, Sallama yyi bakin kofar parlon aka amsa masa sannan ya shiga, Umma na xaune parlon da Maman Abdallah dake xaune kasa Jiddah na gefenta alamar gaisheta suka shigo yi, daga kai Jiddah tayi suka hada ido da shi ta sunkuyar da kanta, karasowa cikin parlon yyi ya xauna yace "Ina kwana Umma" tace "Lafiya lau Aliyu, ashe kana garin" Kallonsa Jiddah tayi jin sunansa a karo na farko, ya shafa kai yace "Ehh ina nan Umma, ya karfin jiki?" Tace "Ah Alhmdlh sauki ya samu" Mikewa yayi ya karasa kusa da ita ya ajiye mata ledan maganin hannunsa yace "Ga drugs din naki Umma" tace "Toh nagode son, Allah yayi albarka" komawa yayi ya xauna yace "Ameen" tace "Ya su yaya?" Yace "Suna lafiya..." Tace "Toh a kawo maka breakfast?" Tana fadin haka ta mike, yace "Aa umma nayi breakfast a gida" Umma tace "Toh ga awara da Maman Abdallah da mai sunan yaya suka yi da safe, u will like it" Ya d'an kalli Jiddah da kanta ke kasa, Umma ta mike ta nufi kitchen, Abuturrab ya girgixa kai da sauri xai yi magana sai kuma yyi shiru ya sauke boyayyen ajiyar xuciya, Maman Abdallah na kallonsa da fara'a tace "Ina kwama abokin Dakta" Babu yabo babu fallasa yace "Lfya lau" Jiddah bata dago ba ita ma tace "Ina kwana" yace "Lafiya lau" Umma ta fito kitchen, sai ga mai aiki rike da karamin tray me dauke da awara da sauce da pepper soup din naman rago a rufe a wani warmer din, dinning ta kai ta ajiye, Umma na kallon Abuturrab tace "Gashi can a dining area son" Ya d'an yi murmushi yace "Nagode Umma" Tace "Ko a kawo maka nan?" Ya bi dining area din da kallo sannan yace "Ohk" Nan kusa da shi mai aikin ta kawo ta ajiye sannan ta wuce, Maman Abdallah ta mike cike da ladabi tace "To Hajiya xata maki gyaran ne yanxu??" Umma tace "Eh to, ko kuma ta bari gobe ai tana nan, ko ba kwana biyu ta xo yi maki ba?" Maman Abdallah tace "Tana nan tukun wllh Hajiya, don bata ma sa ranan tafiya ba" Umma tace "Toh shkkn gobe sai tayi min gyaran" Maman Abdallah tace "Toh shkkn Allah ya kai mu Hajiya" Mikewa tayi tana kallon Jiddah tace "Toh mu je gobe sai kiyi aikin ko" Umma tace "To ki bar ta tayi kallo mana, tunda ke ba kallo kike ba" Maman Abdallah tayi dariya tace "Ehh kuma haka ne, tunda xan je maki kasuwa yanxu, ina fita hijabi kawai xan sa in tafi dama" Umma tace "Toh ki bar mata Abdallah ko baxai xauna ba" Maman Abdallah tace "Baxai xauna ba Hajiya, kiwuya ya gallabesa ai" Umma tayi murmushi tace "Toh sai kun dawo" Ko kadan Jiddah bata so haka ba duk da ba wai tana da niyyar bin ta kasuwan bane saboda tsoron kada wani da ya santa ya ganta a hanya amma xaman parlon ma bata so, Umma na lura da ita taga alamar she isn't comfortable, hakan yasa tace "Ko kuma ku tafi kasuwan kawai tare kada ta xauna shiru" Maman Abdallah da har ta nufi kofa tace "Dama tare nayi niyyar xa mu je, da kika ce ta xauna tayi kallo ne yasa nima nace ta xauna Hajiya" Sosai gaban Jiddah ya fadi, Maman Abdallah tace "Toh taso mu tafi kasuwan" Abuturrab dake xaune parlon yana sauraronsu yace "Tunda kallo take yi ki bar ta tayi kallonta mana" Kallonsa Umma tayi da mamaki, that's very odd of him, shi mutanen cikin gida ma baya shiga sabgarsu yayi masu magana balle wanda bai hada komai da su ba, Jiddah ta dago kanta amma bata ce komai ba, Umma ta d'an yi murmushi tace "Toh tayi xamanta" Maman Abdallah ta fita parlon bayan ta ce ma Umma sai ta dawo, Mikewa Umma tayi ta tafi kitchen sae gata ta dawo da karamin flask da mug ta ajiye ma Abuturrab tace "Kilan ta manta ne bata kawo maka ba..." yayi murmushi yace "Nagode Umma" Tace "Kana son madara?" Ya girgixa mata kai, tace "Yauwa nayi tunanin hakan, Ahmad ma bai fiye shan madaran ba" Sama ta nufa tace "If u are done ina daki" Yace "Alright" Bayan few minutes da tafiyarta ya daga kai ya kalli Jiddah, kanta na kasa tana wasa da hijab din jikinta maimakon kallon da aka barta tayi a parlon, ya bude flask din gabansa ya xuba ruwan Lipton cikin mug, wanda ya xuba ko rabin mug din bai yi ba, sae kamshi ruwan shayin ke yi, Calmly yace "Baki da wani damuwa a inda kike?" Ta dago ta kallesa sannan ta girgixa kai, bayan few seconds a hankali tace "Sai dai Baabarmu xa tayi ta nemana a gida" Kallonta yayi a takaice yace "Toh a mayar da ke wajenta kenan?" Shiru tayi tana kallonsa, can ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Iliyan xai iya sake biyo ni, ita ma xata iya kai ni wajensa" Abuturrab ya hade rai yace "Shine kuma xaki ce min Baabarki xata nemeki?" Bata ce komai ba, ya fara shan shayin hannunsa a hankali, tv ya dinga kallo kafin murya can kasa yace "Amma idan aka sauya maki shi wanda xai aureki yanxu da wani daban xaki amince da auren?" Kallonsa take babu ko kiftawa, yace "Ko baxa ki amince ba?" a sanyaye tace "Toh ai ban san waye shi ba" yace "Toh ni nasan sa" Tace "Toh in dai baya shaye shaye" Ya dinga kallonta sannan yace "Kina dai son kiyi aure kenan dama?" Hawaye ne ya kawo idonta tace "Baabarmu ce ke son inyi auren, kuma ai ba makaranta nake xuwa ba kawai sana'a muke yi" Bai kuma ce mata komai ba ya ci gaba da shan shayinsa, ta goge hawayen idonta, ya d'an kalleta yace "Wanda xan hada ku baya shaye shaye" A hankali tace "Toh" bude warmer din awaran yayi yana kallo yana d'an yatsine fuska, sai kuma ya bude na pepper soup dinma, lkci daya duk ya rufesu yace "Ki dauka ki kai maku can ki ci" Da sauri ta kallesa tace "Aa mun ci namu ai, kai dai ka ci ai naka ne" Ganin babu spoon a wajen tace "Bari in kawo maka cokali" Tana fadin haka ta mike tayi hanyar kitchen ya bi ta da ido sannan ya sake kallon warmer din awaran, ba a dau lkci ba ta dawo ta iso kusa da shi ta durkusa ta ajiye spoon din, sai kuma tace "In xuba maka?" Bata jira yace komai ba ta fara dibar masa awaran a plate sannan ta mika masa, calmly yace "Kwashe su nace baxan ci ba" Sauke idonta tayi a hankali sannan ta juye ta mayar cikin warmer din ta dau tray din ta mike ta wuce kitchen. Tana fitowa ta nufi kofa xata fita ya bi ta fa kallo yace "Kee, ina xaki?" Ta juyo tace "Xan xauna a waje ne" Authoritatively yace "Dawo nan ki xauna" a hankali ta dawo parlon ta koma ta rakube inda take xaune da farko ta xauna, ya ci gaba da shan shayinsa har ya gama ya ajiye mug din ya kalli agogo dake nuna sha biyu saura, mikewa yayi ya nufi kofa ya fita parlon, sai da ya shiga motarsa sannan ya kira Umma yace mata ya tafi. Yana cikin driving wayarsa ya fara ring, kallon wayar yayi ganin me kiransa ya nemi suitable place yayi parking sannan ya daga wayar, Daga daya bangaren aka ce "Captain da kansa barka da wuni..." Abuturrab yace "Ya kake Mu'axxam?" Mu'axxam yace "Alhmdlh Oga, Kayi scarce kawai wannan satin, daxu nake tambayarka Umar ke cewa ai baka shigo ba satin nan baka jin dadi" Abuturrab yace "Ehh ina kaduna" Mu'axxam yace "Toh ya jikin Captain!" Abuturrab yace "Alhmdlh" Mu'axxam yace "To maa sha Allah ranka shi dade" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujeran motarsa a hankali yace "Kana ji na Mu'axxam?" Mu'axxam yace "Ina jin ka Oga" Abuturrab yace "Kana da mata ne?" Mu'axxam yayi dariya yace "Aa tukunna dai Oga Allah bai kawo lkcn ba" Abuturrab ya gyara xamansa yace "Ohk, wata yarinya na sama maka ko hakan yayi maka?" Mu'axxam yace "Ikon Allah, Oga ai baxa ka min xabin da xai cutar da ni ba nasani wllh" Abuturrab yace "To kar ka damu, in sha Allah xan maka duk wani abu da ya kamata na auren tunda nasan kilan ba wai ka shirya bane yanxu ae" Mu'axxam yace "Allah sarki Oga, amma wllh nayi farin ciki da wannan labarin naka, naji dadi sosai, dama tuntuni nake son yin auren amma babu halin yi sbda kasan komai yanxu tsada, shi kansa auren tsada, duk da iyayen nawa sun ma riga mu gidan gaskiya sai kanni da yayyi, da dangi, amma ginin da nake yi a kauyenmu shi ke cinye min kudi wllh...." Abuturrab yace "Babu damuwa, Allah xai rufa asiri, amma xuwa ranan alhamis ko Juma'ah ka dau leave din kwana biyu ka xo kaduna, a nan yarinyar take, but before then ma xa mu yi magana" Mu'axxam yace "In sha Allahu kuwa Oga, Allah ubangiji ya saka maka da alkhairi, ya biya maka bukatunka na alkhairi, ya ji kan iyaye da kakanni, wllh nayi farin ciki sosai Oga" Abuturrab yace "Maa sha Allah, xa mu yi magana" Daga haka ya katse wayar, wani ajiyar xuciya ya sauke... this is now almost settled saura mutanen Hayi kuma yanxu, tada motar yayi ya ci gaba da driving din nasa. Kawu Jibril sai muxurai yake daga inda yake xaune jin abinda Abuturrab ke cewa, Hansai ta marairaice tana wuri wuri da ido tace "Ni kuwa Alhaji sai nake ga fa kamar idan mun koma gun 'yan sandan nan maganar nan babba xata xama, Iliya fa bai bari mun yi baccin kirki ba daren jiya a gidan nan, ni har na sadakar jiya xan mutu, saboda ka sanar min da xuwanka yasa na koma can gida karfe goma nayi ta jiranka sai gashi ka xo bayan azahar sannan na kawo ka wajen kawun nawa" Abuturrab yace "Ae baraxanar da yake maku ne dalilin da yasa xa aje police station din yanxu ba wani abu ba..." Abokin Kawu Jibril dake xaune tare da su yace "Ni da xa aji ta nawa kawai a tafi wajen me unguwar yankin nan gaba daya, naga yana fada aji, idan abun ya gagaresa shi sai mu koma gun 'yan sanda don gaskiya wannan yaro Iliya d'an iska ne wllh, iyayensa ma ba isa suka yi da shi ba balle wani, amma gwara a fara sako mai anguwa a lamarin nan sannan ya kai mana gaban hukuma koko ya ku ka ga?" Hansai tace "Wallahi haka ma yafi, mu je aji ta bakin me anguwan tukunna" Kallonsu kawai Abuturrab yake with surprise, su fa ko damuwa da 6atan yarinyar basa yi, damuwarsu da tashin hankalinsu Iliya da ya sako su gaba, Kawu Jibril yace "Ko ya kace Alhaji??" D'an murmushi yayi yace "Ehh hakan yayi, aje wajen nasa" Hansai ta mike tana gyara takurarren mayafinta tace "Ba sai mun sha wahalan neman abun hawa ba da motarsa ya xo babba ce duk xata kwashe mu" Abuturrab bai ce komai ba ya mike shi ma duk suka bi bayansa xuwa kofar gida, sai bayan da suka shiga motar, Hansai tace "Ita Jiddah ganinta me sauki ne wllh, nasan tsoro ne yasa ta buya wani gun, amma ko ni daya sai in samota ai, bari dai a gama da tantirin nan" Ta madubi Abuturrab ya kalleta yace "Kinsan inda take kenan?" Da sauri Hansai tace "Aa amma nasan tana nan cikin hayi babu inda xata, kasanta da shige shige da yawace yawace tunda ba jin magana take ba, baxata rasa wanda xai boyeta ba na kwanakin nan kam" Abuturrab bai kuma cewa komai ba har dai suka isa gidan mai unguwar, xuwansu ya sa shi fitowa xuwa kan tabarmansa dake shimfide a waje da wasu dattijai uku ke xaune, Bayan an gaisa Kawu Jibril yace "Toh gashi dai mun xo gareka mai unguwa...." Sanin kawun nata bai iya magana ba yasa Hansai ta amshe bayan ta maka masa harara, ta marairaice tace "Mai unguwa muna cikin tashin hankali da fargaba wallahi, don a gaskiya bamu da wani tsaro xaman mu a hayi" Mai Anguwa yace "Ikon Allah, me ke faruwa? Har kin fita takaba ne Hansai?" Hansai ta sinne kai taki basa amsansa na karshe, Nan dai ta kwashe duk abinda ke faruwa karya da gaskiya ta sanar masa tana matsar kwalla da kyar, kallonta kawai Abuturrab ke yi da mamaki don maganganu da yawa ta canxa a kan yanda shi ta gaya masa, Mai Anguwa na jinjina kai yace "Ikon Allah Iliya dai guda, d'an gidan Malam Kabiru?" Hansai na shessheka tace "Shi wllh" Yace "Toh yanxu ke kin tabbata yarinyar na nan cikin garin nan, don lafiyarta shine babban abin dubawa yanxu..." Hansai tayi saurin cewa "Tana nan anguwar wllh Mai anguwa, ai nasan babu inda xata, kawai tsorata tayi yasa ta buya, yanxu idan na dage na kwalo mata kira xata fito wllh, kawai dai a gama da xancen yaron nan iliya tukun" Mai Anguwa ya girgixa kai yace "Toh yanxu xa a min kiran shi mahaifin Iliyan da shi kansa iliyan" Hansai ta xaro ido a mugun tsorace, Mai anguwan yace "Amma ke kika haifi yarinyar?" Hansai tace "Ehh 'ya ta ce" Yace "Yanxu ki rasa wanda xaki yarda ya nemi auren yar ki sai wannan takadirin Iliya? Waye bai san halinsa ba a garin nan, garin yaya har kika amince ya auri yar ki, duk uwa ta gari ai baxata so ma yar ta wannan yaro ba" Hansai ta fara matsar kwalla tace "Wallahi mahaifinta ya rasu, yarinyar nema take ta gagareni, baxan boye maka ba wllh bin maxa take, to shi nan rufa mana asiri yayi xai aureta, bayan haka kuma da tsohon bashi tsakaninsa da mahaifinta ina jin, kuma ni bani da halin biya gaskiya shi sa kawai na sadaukar ai ba a cire ran shiryuwar d'an mutum, ni ban cire ran shi ma xai shiryu ba sannan ai gwara shi kiriniya kawai yake yi, ita fa bin maxa take wllh, duk iya bakin kokarina kan yarinyar nan ya ci tura, tsoro nake kada ta jajibo min abun kunya shi sa da ya billo da xancen aurenta bani da yanda xan yi na hakura, don kowa tsoronta yake sbda halinta, sannan yana da xuciya yaron, me yi ne shi wllh" Sake baki mai Anguwa yyi yana kallonta, Abuturrab ma kallonta yake ko kiftawa babu with shock, ta sharce majina tace "Amma tunda abu ya xo da haka in da wani shawara da taimakon da xaka mana kawai kayi mai anguwa mun baka wuka da nama don a gaskiya muna cikin hatsari" Ya sauke wani ajiyar xuciya yace "Ikon Allah, to yanxu dai xan sa ayi kiran mahaifin yaron da shi kansa yaron sai a san abun yi, idan naga sulhun baxai yiwu ba sai kawai ku tafi wajen yan sanda su ma idan abun baxai sulhuntu a gunsu ba kotu xa su tura ku, amma abu me sauki a mayar ma yaron nan kudadensa ita kuma yarinya a nema mata mai hankali wanda yaji xai iya ya aureta...." Hansai ta fashe da kuka tace "Duk ba sai an kai ga haka ba wllh, Allah xai dubemu maganar ta mutu cikin ruwan sanyi, banda ta lalata rayuwarta idonta ya bude da maxa me xai sa in yi sha'awar yi mata aure bayan abinda xan kai ta da shi ma bani da shi, duka duka shekarta fa sha bakwai, har nawa take xan dage sai na mata aure banda ta lalace" Kawu Jibril dai ba baki sai idanuwa, sauran dattijan dake xaune gun sai kallon Hansai suke wasun su na tirr da ita a xuciya, don ko min lalacewar naka baxa hadasa da lalatattce ba da yayi fice a gari, Abuturrab ya d'an yi murmushi shi dai bai ce komai ba yana kara jinjina halin Hansai a ransa. Sai da suka yi la'asar Mahaifin iliya ya iso, sai ga iliya ma da abokansa yan daba irinsa sun iso wajen, Mai anguwa ya dakatar da abokan dake kokarin xaunawa kan takalmansu don tabarman ya cika yace "Ku yi hakuri yan samari kuyi jiransa ga benchi can" Suna gunguni suka bar wajen, Abuturrab ya kafe iliya da ido, ba lebbensa ba hatta fuskarsa ya dafe saboda xuke xuke..... 07087865788📚✍🏻 💖💖 *Jiddatul Khair*💖💖 _By Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 11.... Mai Anguwa na kallon Iliya dake maxurai yace "Kai yanxu Iliyasu baka da masaniyar inda wannan yarinyar take?" cikin murya irin ta 'yan da6a yana nuna Hansai yace "Wllh wancan munafukar matar tasan inda take, kuma ni dama daga ita har wancan mutumin banxan na basu kwana daya su fito min da ita, matata ce fa, abinda har na bada sadaki me ya rage? Akuyar baabata fa na dauka na kai kasuwa na siyar na kai ma wancan mutumi da wasu kattin banxa a wajen kudin sadakina...." Mahaifin Iliya dai ba baki sai idanuwa, don kamar ma tsoronsa yake, Mai Anguwa yace "Toh yanxu idan ba a ga yarinyar nan har bayan kwana dayan da ka bada ba ya kake son ayi iliyasu?" Yace "Hansatu ta biyani duk hatsin da na dinga kawo mata a maimakon na kai ma baabata, ba hatsi kadai ba, lissafi xa mu yi tiryan tiryan ta biyani duk abinda na kashe sannan ta bani kudin sadakina dubu sha uku da kudin gaisuwa da sa rana da na kai, idan ba haka ba to wllh xan yi ta'asa, ai ba yau muka saba xaman kurkuku ba, banda yanxu da na fara gwangwan daga garin nan xuwa legas ai mu bama wata uku bamu leka gidan yan sanda ba daga nan mu garzaya kotu sannan gidan kaso, ko da mune da gaskiya ko mu ne bamu da gaskiya wannan ba sabon abu bane" Mai Anguwa ya kalli Hansai dake xare ido duk hankalinta a tashe sai xufa take yace "To ke kin ji Hansatu, lissafi yace xa ayi" kasa cewa komai tayi xufa sai karyo mata yake ta ko ina, yo ba gwara ya kasheta ba da ta ta6a kudin da Abuturrab ya bata, tabbb.... Mai Anguwa yace "Kai xuwa yaushe xa a baka kudin naka Iliyasu?" Ya gyara xama yace "Ae kafata kafar kudina, baxan bar wajen nan babu su ba, idan ko ba haka ba wllh wllh xan yi aika aika" Mai Anguwa ya kalli Hansai da jikinta ya dau rawa ta kasa cewa komai, Abuturrab ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yana kallon iliyan yace "Nawa ne gaba daya kudin naka?" Yace "Al-qur'an kudi na ya kusa dubu dari da wani abu, abinda duk xuwana legas sai na kawo mata garin alabo da gawayi ga hatsi da nake siya mata kwana biyu kwana uku... Sannan ga sadakina dubu sha uku na tinkiyar babaata, ga dubu biyar kudin gaisuwa da sa rana" Calmly Abuturrab yace "Kana da account?" Iliya yace "Aa amma abokina Kallamu na da shi, gaya can a xaune" Abuturrab yace "To ka kirasa ya bada account din" Iliya ya kwalo ma abokin nasa kallamu kira, Kallamu na karasowa Abuturrab yace "Account number dinka xaka bada" sai da ya dubo a waya sannan ya nuna ma Abuturrab, cikin few minutes Abuturrab yayi masa transfer din dubu dari da ashirin, sannan ya kalli Kallamu yace "Xa a maka alert na dubu dari da ashirin yanxu" Wani kara wayar yayi alamar shigowar alert din, Abuturrab ya amshi wayar ya duba sannan ya mika ma mai anguwa da sauran mutanen wajen duk suka ga dubu dari da ashirin, Hansai ta fashe da kuka sosai, Kawu Jibril kuwa Hamdala ya dinga yi a ransa yana sauke ajiyar xuciya, Hansai na kallon Abuturrab cikin kuka tace "Allah ya saka da alkhairi Alhaji, ka min taimakon da babu wanda ya ta6a min wllh a duniyar nan, nagode nagode, Allah ya kara maka budi da dukiya me yawa, wayyoo wani irin godiya kuma xan maka Alhaji" Abuturrab ya ki bata amsa dai a fili, Iliya ya mike yace "Toh amma fa duk ranan da jiddah ta bayyana wllh sai na aureta don na kwallafa rai, an kuma sa min ran ne, wllh wllh sai na aureta ko kuma in dauketa kawai in wuce legas in je a daura mana auren a can, so nawa aka yi hakan" Sake baki duk mutanen wajen suka yi suna kallonsa, ya kakkabe wandonsa ya kara gaba yana cewa "Sai in bani ne Iliya d'an me karfi ba" abokansa duk suka taso suka maya masa baya suna hailing dinsa, Mahaifinsa Malam Kabiru ya sauke ajiyar xuciya cikin sanyin murya yace "Abu me sauki da xa a samu wani ya auri yarinyar nan kawai, idan kuwa ba haka ba wllh xai aika abinda ya fada, kwakwalwarsa ya ta6u da dadewa mu kuma bamu da halin kai sa ko ina a dubasa, har cewa aka yi mu kai sa dawanau a kano to ina kudin?" Wani mutumi a wajen yace "Alhmdlh abinda xan fada kenan ka riga ni Malam kabiru, gwara kawai a aura mata wani tunda uwar ma tace ba ji take ba yarinyar, kun ga tana dawowa sai a kai ta dakinta kawai..." Abuturrab yace "Akwai wani yaro na, ina son nema masa aurenta yanxu" Kallonsa duk suka yi, Mai Anguwa yace "Toh in dai kasan halinsa ina ga wannan ba matsala bace amma kafin nan ya kamata ka gabatar mana da kanka..." Abuturrab ya shafa kansa a hankali yace "Ni sunana Aliyu Usman Umar... An haifeni nan cikin garin kaduna, ni matukin jirgin sama ne" Sake baki duk suka yi suna kallonsa kamar ranan suka ta6a ganin me tukin jirgin sama, yace "Gidan iyayena na nan Malali..." Mai Anguwa yace "Maa sha Allah Aliyu, to amma a ina kasan ita wannan yarinya da ake magana a kai?" Hansai ta amshe tace "Wllh daga siyan awara muka sa6a da shi, customer na ne shi da dadewa, da motarsa yake xuwa yyi parking ya siya har na dubu biyar dubu goma yana siya, toh shine jin rasuwar mai gidana sai ya kawo mana kudi dubi hamsin dubu dari, ta haka muka saba muna mutunci sosai da shi" Mai Anguwa yace "Ikon Allah" Abuturrab dai bai ce komai ba, Mai Anguwa yace "Toh amma shi wannan yaron da kake son hada yarinyar da shi wanene, sannan a ina yake?" Abuturrab yace "A kano yake, yana aikace aikace ne a airport din kano..." Hansai tace "Shi ma jirgin yake tukawa?" Ya girgixa kai yace "Aa..." Wani datijo dake xaune wajen da baxai wuce shekara sittin da takwas ba yayi gyaran murya yana taunan goransa yace "Amma fa wata kusan ya fi wata kusan nake ji ai... Tunda haka ne ni yanxu xan bada sadaki sai a daura min aure da ita wannan yarinyar...." Da mamaki Abuturrab ke kallonsa, can ya girgixa kai yace "Haba Baba ai addininmu ma bai ce haka ba, da taxara sosai tsakaninku da yarinyar nan...." Dattijon ya hade rai ya katse sa yace "Toh kai idan taimako kake son yi ka aureta mana kai da babu taxara me yawa tsakanin ku, shi fa wannan yaron da kake son hadata da shi nasan ba kowa bane d'an goge gogen iyapot ne, ni kuwa kowa yasan babu rashin ci babu rashin sha a gidana, matana uku ko wacce kuma tana da yara shidda shidda, shi me anguwan ai yasan wanene ni, auren yarinyar nan da xan yi tamkar jihadi xanyi don ance bin maza take" Kallonsa kawai Abuturrab ke yi with disgust, Dattijon ya ja tsaki yana ci gaba da taunan goronsa da jajayen hakoransa yace "Idan tsakani da Allah ne kai ka aureta mana yaro xaka wani kawo ma mutane fi'ili a nan, kaga mai anguwa a yanke min sadaki yanxu in bada a wuce wajen dama ina da niyyar auren kwanan nan" Yana fadin haka ya fiddo yan dari biyar biyar a aljihunsa, lokaci daya tunanin Abuturrab ya kwance, Hansai ganin 'yan dari biyar biyar tana d'an kame kame tace "Ai wllh tamkar taimako xaka yi Alhaji, wannan babban taimako ne, ni kaina da na haifeta bana shaidarta, kawai dai Allah ya shirya mana xuri'a" Alhajin ya murmusa yace "Babu komai ai tamkar jihadi xan yi, Ni mai anguwa ne waliyi na, ita kuma sai a samu wani...." Abuturrab ya rufe ido ya bude, yaji kansa ya fara juya masa ya dinga kallon tsohon nan da ya fara kirga kudin da ya ciro, rasa tunanin da xai yi yayi, he was totally lost, Hansai dake ta kallon kudin hannun tsohon tace "Kawai a daura tunda ga sadakin a kusa" Jibril yace "Wannan taimako ne me girma xaka yi Alhaji, Allah ya saka da alkhairi, tana dawowa daga gantalin da ta tafi sai a wanketa a kai maka gida kawai" Abuturrab ya kalli mai unguwa after gathering much courage yace "Ni xan aureta, sai ka xama waliyi na" Ba Hansai ba kowa na wajen sai da yayi mamaki, mai Anguwa wanda da alama dama bai yi na'am da daurin auren da wannan tsoho me suna Alhaji Saleh ba yace "Toh Madallah Aliyu" Tsohon ya d'an ja tsaki ya mayar da kudinsa aljihu, A nan take kuma aka daura auren Abuturrab da Jiddah a kan sadaki dubu arba'in, su kenan kudin jikinsa da ya ciro daxu bayan ya siya ma Umma drugs, Xaune kawai Abuturrab yake a wajen amma gaba daya he is absentminded and lost ga wani sanyi da yaji yana shigarsa kamar xai yi xaxxabi, har aka gama komai aka raba dabino da alawan da aka siya a nan cikin layi, Hansai dai ta kasa gane ko murna xata yi ko akasin haka, Ya xa ayi babban mutum kamar wannan gashi har yace jirgin da bata ta6a gani ba duk tsawon rayuwarta yake tukawa ace wai ya auri Jiddah maimakon Bibalo, tunanin hakan yasa taji wani bakin ciki ya tokareta a kirji, lkci daya hankalinta ya tashi sosai ba kadan ba ta dinga xufa daga inda take xaune, yanda take xufa haka Abuturrab ke xufan shi ma, tunda yake bai ta6a shiga rudani da confusion lkci guda irin wannan ba, wait!!! what did he just do now??? What have he done to his life?? A cikin lkci ba me tsawo ba aka gama komai, sama sama ya dinga jin albarkan da dattijan wajen ke sa masa na cewar ya rufa ma jiddah asiri duk da ga abinda aka ce tana yi amma hakan bai sa ya kyamaceta ba gashi ya taimaketa ya aureta domin nisantata daga cutarwan iliya, Abuturrab ya mika ma mutumin karshe hannu sannan ya mike a hankali ya nufi motarsa walking slowly kamar mara lafiya, yana shiga motarsa ya tada motar ya kashe Ac don sanyi yake ji sosai ya fara driving ya bar layin, ikon Allah ne kawai ya kai sa gida lafiya cause blurry ya dinga gani ga kansa dake juya masa ya dinga ganin komai double, ko parking din kirki bai iya yayi ma motar ba ya sauka ba tare da ya rufe ba ya shiga ciki mai gadi ya bi sa da kallo, direct dakinsa ya nufa ba tare da ya kalli kowa na parlon ba, duk suka bi sa da kallo, Aunty ta kalli Ummi, Ummi dai bata ce komai ba, Aunty ta mike ta bi bayansa da sauri, cikin bargo ta gansa ya lullube har kansa, da mamaki tace "Are you okay Aliyu???" Bai iya ya bata amsa ba, ta sauke bargon a hankali ganin he is shivering so much, da mamaki tace "Baka jin dadi ne?" Ya gyada mata kai kawai, tace "Subhanallah, let me switch off the Ac" Nan na kawo karshen free pages na *Jiddatul Khair* in sha Allah, and the paid book is 500 Via 👇🏻 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah..... And u show ur evidence of payment via my WhatsApp Number 👉🏻 07087865788..... Plss just WhatsApp ban fiye son phone call ba, and i am begging you don't come to my DM without any concrete reason, it's tiring wllh....😓😰 just come, patronize, i save ur number, and i add u to my groups... Shikenan Thanks and i love you all as u patronize.💖 Kashe Ac din dakin Aunty tayi ta sauke curtains ta dawo ta xauna kusa da shi tace "Sannu, ko dai a kira Dr? amma daga ina kake haka?" Girgixa mata kai kawai yayi don bai jin ma xai iya magana, ta mike ta fita don daukan wayarta ta kira Dr din, Tana cikin dialing number likitan ta kalli Ummi tace "Baya jin dadi ne wllh" Ummi tace "Ikon Allah, to Allah ya sauwake" Aunty na gama kiran likitan ta koma daki..... Abu kamar wasa Abuturrab har da karin ruwa, he was so weak and sick, sae bayan isha family Dr din nasu ya bar gidan. Karfe goma da yan mintuna wayar Abuturrab dake gaban mirror din dakin Aunty ya fara ring Aunty ta dau wayar ganin Ahmad ne ta kyabe baki ta dauka don tun daxu yake kira, bayan ya gaisheta yace "Ya tashi Aunty?" A takaice tace "Aa..... ko minti sha biyar ban yi da fitowa daga dakin ba" Ahmad ya d'an yi shiru sannan yace "Amma jikin da sauki?" Tace "Eh toh amma har yanxu his temperature is high" Yace "Toh Allah ya sauwake, likitan ya tafi?" Aunty tace "Ehh" Yace "Toh Allah ya bashi lafiya" Aunty tace "Ameen" daga yayi mata sallama ya katse wayar, Aunty ta ajiye wayar ta koma bangaren Abuturrab ta bude kofar dakinsa, tsaye taga Ummi a dakin kusa da shi tana kallonsa, Aunty tace "Ya tashi ne?" Ummi ta juyo tace "Aa" Aunty ta karasa kusa da shi ta xauna ta sauke duvet din tana kallonsa ta kai hannu goshinsa, taji har sannan da xafi, juyawa Ummi tayi ta fita daga dakin... a hankali Abuturrab ya bude idonsa da yayi masa nauyi sbda ciwon kai, ji yake kamar ana sara masa goshinsa, Aunty tace "Sannu son, ya jikin?" Bai iya ya bata amsa ba ya sake lumshe ido, tace "Baka ci komai ba, in hado maka shayi?" Girgixa mata kai yayi, bai sake bude idonsa ba har ta ga alamar ya koma bacci, ta mike ta fita daga dakin ta kulle masa kofar. Can cikin dare Abuturrab ya farka, da kyar ya mike xaune coz he was pressed, ko hasken fitilan dakin bai so don kara masa ciwon kai yake yi, ya kalli drip din hannunsa da ya kusa rabi, ya mike tsaye da kyar yana jin jiri ya kashe ruwan ya bar cannula din kadai a hannunsa bayan yyi disconnecting dinsa daga jikin ruwan, kamar me counting steps dinsa ya nufi bandaki ya shiga duk da jirin da yake ji, da alwalansa ya fito ya xauna gefen gado ya dafe kansa, ko kadan bai son tuna komai da ya faru yau, it's making him down and weak, Bude kofar dakin aka yi Aunty ta shigo ya daga kai da sauri, tace "Ka tashi Abuturrab, sannu ya jikin" A hankali yace "Alhmdlh" Ta karasa kusa da shi tana dialing number Ahmad don kiransa ne ma ya tasheta yana fara ring tace "Duk abokinka ya takurani gashi nan ni dai" Tana fadin haka ta mika ma Abuturrab wayar, ya amsa ya kai kunne yyi shiru, daga daya bangaren Ahmad yace "How are you feeling captain?" Cikin sanyin murya yace "Alhmdlh" Ahmad yace "Ka samu ka ci wani abun kuwa?" Abuturrab yace "I will take tea now" Ahmad yace "Do so plss, Dr Shariff din ya baka drugs ne?" Abuturrab yace "I just woke up ban sani ba" Ahmad yace "Ohk, ruwan yayi rabi yanxu?" Abuturrab ya kalli drip din sannan yace "Almost" Ahmad yace "Toh Allah ya sauwake" Abuturrab yace "Ameen" sallama Ahmad yyi masa ya katse wayar, ba a dau lkci ba Aunty ta dawo dakin rike da cup din tea ta mika ma Abuturrab tace "Gashi ka samu ka sha" Ba musu ya amsa, tana nan tsaye sai da ta tabbatar ya sha shayin sannan ta amshi cup din ta fita, Mikewa yayi ya koma bathroom ya wanke bakinsa ya fito ya dau pray mat ya shimfida ya hau sannan ya tada sllh, ko da Aunty ta dawo dakin ganin yana sallah ta koma dakinta, ya jima xaune kan darduma daga bisanni ya mike a hankali ya dauke darduman ya koma kan gado, mayar da ruwan yyi ya kashe wuta ya kwanta ya lullube jikinsa yana jin kamar wani sabon xaxxabin xai sake rufesa. Da asuba duk yanda Abuturrab ya so tashi yin sllh kasawa yyi, Karfe shidda da yan mintuna Aunty ta shigo dakin, ta kunna wuta ta karasa gun gadon ta cire duvet din da ya rufe har kansa da shi, bude ido yyi a hankali, tace "Ka samu kayi sallah kuwa?" Girgixa mata kai yayi, tace "Da ka daure ka tashi, amma how are you feeling now?" A hankali yace "Alhamdulillah" mikewa yyi xaune, tace "Let me get u something to take sai ka sha magungunan idan ka idar da sallahn" Fita tayi dakin, yayi karfin halin tashi ya cire ruwan da ya rage kiris ya kare sannan ya shiga bandaki, yana sallah ta dawo dakin, ta ajiye masa cup din shayi da ledan drugs din ta nemi waje ta xauna har ya idar da sallahn sannan ta sa ya dau shayin da ta hada masa ya sha.... Karfe goma na safen Abuturrab na bedroom dinsa hannunsa rike da bowl din pepper soup, Ummi ce tsaye dakin tana kallonsa, ko minti biyar ba ayi da fitan family Dr dinsu daga dakin ba, bayan few minutes ya d'an kalli Ummin tasa, ji yayi gabansa ya fadi sosai, a hankali yace "Why don't u sit Ummi?" Ummi tace "Am okay here" Ba tare da ya kalleta ba yace "Aunty fa?" Tace "She is in the kitchen" Bai kuma cewa komai ba ya ci gaba da shan pepper soup din hannunsa a hankali, Ummi tace "Kun yi magana da Abban naka? Ya kira kana bacci daxu" Ya gyada kai yace "Ehh Aunty ta bani mun yi waya" Tace "Ohk" Juyawa tayi ta fita dakin ya bi ta da kallo, lkci daya jikinsa yyi sanyi, ya ajiye bowl din hannunsa ya jingina da gadon da yake xaune, he needs someone to talk to about this unfavorable issue, he needs to share this with someone that's understandable, who will this be, rike kansa yayi yana nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.... Xuwa yamma Abuturrab ya d'an samu saukin ciwon kan dake damunsa, ya fito wanka kenan yana goge kansa da karamin towel din hannunsa aka bude kofar dakin, Ahmad ne ya shigo dakin hade da sallama, ganin Abuturrab a tsaye, ya tsaya daga bakin kofar ya rike waist dinsa yace "This is better, and I'm glad i saw u this way" Abuturrab bai ce masa komai ba, Ahmad ya d'an yi murmushi yace "Medical report dae ya xama na gaske yanxu kenan" Abuturrab ya kallesa yace "Ka taho min dashi?" Ahmad ya karasa ya xauna gefen gado yace "How are you feeling now?" Abuturrab ya nufi gaban mirror a hankali yace "Alhamdulillah" Ahmad yace "But dama baka jin dadi ne, coz naga sickness din yyi striking dinka so hard, you look lean...." Ta madubi Abuturrab ke kallonsa bai ce komai ba, Ahmad yace "Ba shiru xaka min ba, i left my work for ur sake na biyo train" Abuturrab yace "Da baka dawo ba ma ni xan kiraka ka dawo, i have been expecting you" Ahmad yace "Hope you are feeling much better now?" A hankali Abuturrab yace "Not at all.... We need to talk Ahmad" Keenly Ahmad ke kallonsa cause he can see how worried and confuse he looks, Mikewa Ahmad yyi ya karasa kusa da shi yace "Tell me what's wrong Captain?" Kasa ce masa komai Abuturrab yayi, Ahmad ya koma ya xauna yace "To ka gama shiryawa mu yi magana" Yana kallon Abuturrab har ya gama shiryawa ya dawo ya xauna gefen gadon shi ma, Ahmad yace "Me ke faruwa tell me" Abuturrab ya shafa kansa a hankali kamar me tunanin ta inda xai fara, bude kofar dakin aka yi Aunty ta shigo rike da bowl din fruit salad biyu, murmushi tayi ganin Abuturrab tace "Alhmdlh, son jiki yayi kyau, you are looking much much better and healthier now" Abuturrab yyi murmushin karfin hali bai dai ce komai ba, ta karasa ta mika masa Bowl daya na fruit salad din tace "I made this for u" Amsa yayi yace "Thank you Aunty" Kujeran dakin ta xauna tana shan fruit salad din daya bowl din hannunta tace "Abbanku ma ya kara kira yanxu nace da sauki, shi ma duk ya damu" Ahmad da ya d'an hade rai yace "Ina yini..." Ba tare da ta kallesa ba tace "Lafiya lau" magana ta ci gaba da yi da Abuturrab dake shan fruit din hannunsa, Ahmad ya mike yace "Alright Captain, sai ka xo can gidan namu, i will be leaving now" Abuturrab ya kallesa da sauri, ta gefen ido Aunty ta harari Ahmad tana ci gaba da shan fruits salad dinta, Abuturrab yace "Ai nace maka nima xan fita Ina son in sha iskan waje" Ahmad yace "Okay ka sameni mota idan ka gama, i will wait" daga haka yace ma Aunty "Sai anjima" ko tankasa bata yi ba har ya fita ya kulle kofar dakin, Aunty tace "Yaushe har ka farfado xaka wani fita Abuturrab? Shi Ahmad din bashi da hankali ne ko don ya xo lkcn da jikinka yayi kyau, kana fama da kanka ina wani fita idan ba neman magana ba?" Abuturrab ya shafa kansa yace "Aunty na gaji da xaman gidan ne, ni nace masa mu fita, ba shi ba" Ta tabe baki tace "Toh ai shkkn...." Bayan kusan minti ashirin Abuturrab ya fita xuwa gun Ahmad bayan ya sanar ma Ummi xai je gidansu Ahmad din, Sbda yanda idonsa ya fada yasa shi saka bak'in spec dinsa, kananun kaya ne jikinsa wani sanyayyen kamshi na tashi jikinsa, kana ganinsa kasan he is still recovering, he still looks weak, Kallonsa kawai Ahmad yake yi har ya karaso ya shiga front seat, Ahmad na kallonsa da d'an damuwa yace "Wai malaria ne ya kamaka haka Captain, ka rame fa, kamar wanda yayi sati a kwance" Captain bai ce masa komai ba, Ahmad ya tada motar suka bar layin. Karfe biyar da few minutes suka isa gidansu Ahmad, Abuturrab yace "Ka bar motar a waje ba dadewa xan yi ba xaka maida ni gida ynxu" Hakan yasa Ahmad yyi parking a waje, Abuturrab ya bude motar ya sauka ya nufi cikin compound din, Ahmad ma ya sauka ya rufe motarsa ya bi bayansa, sosai gaban Abuturrab ya fadi bayan ya shiga compound din sun yi ido hudu da Jiddah dake tsaye ta jingina da bango a bakin tap din dake cikin compound din ta tara bucket..... Abuturrab ya dauke idonsa hade da daure fuska yana tafiya, murya can kasa Jiddah tace "Ina yini" Bai kara kallon inda take ba balle ya tanka ta, tafiyarsa kawai yake kamar bai ji ta ba, Ta kalli Ahmad da ya shigo compound din shi ma, ta sauke idonta tace "Ina yini?" Murmushi yayi yace "Lafiya lau, sannu da aiki" Juyawa tayi tana kallon ruwan da take jiran ya cika, Ahmad ya bi bayan Abuturrab da har ya kusa main entrance din gidan, babu kowa parlon da Ahmad ya shiga sai kamshin girki dake tashi alamar ana girki a kitchen, bedroom dinsa ya nufa ya tadda Abuturrab a kwance idonsa a lumshe, ya karasa ciki ya kulle kofar yana kallonsa yace "Are you alright?" A hankali Abuturrab ya bude idon sae dai bai ce komai ba, cike da karfin hali ya mike xaune looking so dumbfounded, Ahmad ya xauna yana facing dinsa with seriousness yace "Tell me what is happening Captain, you look disturbed" Abuturrab ya shafa kansa ya lumshe ido wishing all this nonsense would turn out to be a dream, kara bude ido yyi, gathering much courage yace "I am in trouble Ahmad" Tuni yanayin Ahmad ya sauya, ya kafe sa da ido, can yace "Tell me what is it, me ya faru??" Cikin sanyi Abuturrab yace "Yes i will, amma kuma mafita nake nema a wajenka don Allah, and this should be a secret between just i and you for now plsss" Shi dai Ahmad kallonsa kawai yake waiting to here what is this that's weighing down his frnd har haka, Abuturrab yayi kasa da murya da kyar ya fara magna yace "Yarinyar da kake siyan awara wajenta a hayi, u remember her right?" Bude ido Ahmad yyi sosai yana kallonsa yana jiran jin abinda ya sameta, A hankali Abuturrab ya shiga basa labarin tun daga xuwansa siya ma Umma awara sanda bata da lafiya, abinda ya faru a ranan, har ixuwa yanxu da suke xaune tare da Ahmad a daki, Abuturrab ya share xufan goshinsa yana kallon Ahmad da ya bude baki for almost five minutes now ya kasa rufewa, Abuturrab ya hade rai yace "Don Allah ka daina kallona haka Ahmad ka bani mafita, find a way out for me, i am stuck, ban ta6a shiga rudani iya rayuwata kamar na wannan lokacin ba, what have i done to my self daga taimako??" Sae a sannan Ahmad ya kulle bakin da sauri, wato kawai sae yake ganin labarin da Abuturrab ya basa kamar tatsuniya, or is he dreaming?? Ya kifta ido kusan sau hudu sannan ya kafe Abuturrab da ido, he is finding it hard to believe all what Abuturrab said now, as if counting his words yace "Wait Captain... Wllh kamar fa ban fahimce wannan gajeran labarin nan naka ba, i am confus...." Captain yyi tapping dinsa on a serious note yace "You just have to believe all what i said, duk abinda na gaya maka hakan yake stop confusing ur self" Ahmad na nunasa da yatsa cikin wani expression yace "Are you for real Aliyu??" Abuturrab ya kafe sa da ido regretting everything from the start, Ahmad ya buda ido sosai yana kara digesting din lamarin with shock, he knows Abuturrab have a soft heart, a very soft heart kuwa, yana damuwa sosai da matsalan da ba tasa ba, he prioritized damuwar wasu kan nasa, but he never thought ya kai wannan extent din, bai ta6a tunanin Abuturrab can go this deep ba, what is baffling him more is yanda this time around taimakon nasa yyi sa ga talaka sosai, don Ahmad bai ta6a ganin yayi stressing kan lamarin local people ba, tsakaninsa da su sadaka if the need arize, babu wani magana me tsayi dake hadasa da su, Abuturrab ya hade rai ganin irin kallon da Ahmad ke masa yace "Nayi kuskuren gaya maka damuwata ne da ya sa ka min shiru Ahmad? Don't u have anything to say to me pls?" Lkci daya yanayin Abuturrab ya kara sauyawa gaba daya, sai yake jin wani sabon xaxxabi xai rufesa, da kyar Ahmad na nunasa yace "You mean you are married now without our knowledge Captain??" Cakumosa Abuturrab yyi a fusace yana huci yace "Wannan kake kira da aure? Haka ake auren dama? Mahaukaci ne ni da xan amince nayi aure yanxu" Ahmad yyi iya kokarin ganin bai yi dariyar da ya taho masa ba ganin how furious Abuturrab was, Turasa Abuturrab yyi ya mike yana jin xufa na keto masa yace "Ka gaya min meye abun yi ynxu, i have never been this confused all my life, what have i done to my self, taimako fa kawai nayi kokarin yi...." Lkci daya idonsa ya kada ya dawo ya xauna ya rike kansa, Wani tausayinsa Ahmad ya ji har ransa, hakan yasa kawai ya kawar da dariyar dake cin sa gaba daya a xuciyarsa, ya kwantar da murya yace "let's talk brother" Abuturrab ya dago da idanuwansa da suka yi ja yana kallonsa, Ahmad yyi shiru yana tunanin yanda Abuturrab yayi making fool out of him, ko da wasa bai ta6a gaya masa abinda yake yi ba sai da abu ya 6aci, har da raina masa wayo wai shu murhu yake gani a hayi, wani boyayyen ajiyar xuciya ya sauke yyi kasa da murya yace "before i say anything just tell me what u have in mind now about this issue?" A hankali Abuturrab ya kai hannu aljihunsa ya fiddo farar takarda da biro yana kallon Ahmad, Ahmad ya buda ido sosai, lkci daya ya girgixa kai yace "Nooo.... This isn't a solution, idan ka rubuta takardan nan dole gida xata koma ga axxalumar step mum dinta, kaga anyi ba ayi ba kenan, and at the end wannan mahaukacin kilan yace sae ya aureta..." Abuturrab yace "But I can't sleep in peace again today in har ina tuna auren warce ke kaina, baxan ta6a samun nutsuwa ba matsawar ban aiwatar da haka ba, me of all people fa?? Where will i start from with that girl, me xanyi da ita a rayuwata?? Ko a mai aiki wllh wllh wllh baxan yi employ dinta ba, baxan bata aiki ba a gida na dai, western education zero, islamic education zero, wayewa zero, tsafta zero, mu'amalat zero, kyau zero.... Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Ahmad dake ta kallonsa bbu ko kiftawa ya girgixa kai yana d'an murmushi yace "A bangaren kyau kuma ka so kanka Captain...." a mugun fusace Abuturrab ya fixgosa yace "What the heck.... Kyau xan ci?? Tsaftar fa?? Ilimin fa?? Wait wai kai Ahmad kana tunanin no matter what xan iya xama da local yarinyar nan a matsayin matata? Noo plss... God forbid, this is more like an abomination to me, idan na sake kwana da auren yarinyar nan a kaina yau wllh nasan gobe xan iya xarewa a wuce dani psychiatry" Ahmad ya lumshe ido ya bude yace "Duk na fahimce ka, amma idan ka saketa ynxu Captain ka gaya min meye makomarta? Ina kake son taje? Kasan xamanta tare da maigadin gidan nan da matarsa ba abu bane da xai ja lkci coz daki daya ne da su" Abuturrab ya lumshe ido ya bude yace "I don't care anymore, saninta da tausayinta ne duk ya ja min plight da nake ciki ynxu..." Ahmad yace "Ohk Now tell me, after the divorce what next, ya xa kayi da lamarinta? Kaga tamkar ka lalata aikin ladan da kayi ne daga farko har karshe" Abuturrab na masa wani kallo yace "What are you insinuating now? Kar in saketa kake nufi ko me?" Ahmad ya daga hannu da sauri yace "Aa ni bance haka ba" Abuturrab ya ja wani tsaki yace "Xan saketa, kuma xan ci gaba da mata taimakon da nayi niyya" Ahmad yace "Good, ta yaya?" Abuturrab yace "Under my roof" Ahmad yace "Elaborate plss" Abuturrab yace "I'm thinking i will have no choice but to explain everything that transpired to my Dad, xan ma Abbana bayanin komai, xan kuma kai sa har gun me anguwan, i don't want to look foolish, you get? Then he can explain everything to Ummi coz ni baxan iya ba...." Ahmad ya katse sa yace "You are confusing me, kai da kake da intention sakinta yanxu me xai kai magana kuma kunnen Abba?" Abuturrab yace "Don nace xan saketa ba yana nufin ai baxan yi duk abinda nayi niyya a kanta ba, wllh xan saketa without anyone's knowledge, daga ni sai kai ne xa mu san babu aure tsakanina da ita, amma she will be under my care xan kula da ita har sanda xata samu me aurenta" Ahmad da ke ta kallonsa baki bude yace "Under ur care as how?? a gidanku xaka ajiyeta kenan?" Abuturrab ya girgixa kai yace "A gidana dai" Wani tsaki Ahmad ya ja yace "See the way u are talking like an illiterate plss, ba matarka ba ba komai ba xaka ajiye a gidanka kuna rayuwa tare Captain, ko dai nine ban fahimce abinda kake nufi ba, ka min bayani yanda xan gane" Abuturrab ya masa wani kallo yace "Toh me xamanta a gidana xai kara ko xai rage? Did i look like someone that have anything to do with that girl? Haba Ahmad, don dai ta kwana ta tashi tayi girki ta ci abinci ta tafi boko ko islamiyya, xamanta a gidan nan da rashin xamanta duk daya to me, Monday to Friday ina gun aiki, na dawo sunday and Saturday, wait tell me what u have in mind first" Ahmad yace "Gaskiya baxan yarda da wannan rashin tunanin ba, kana cikakken namiji ka xauna gida daya da mace...." Mikewa Abuturrab yyi looking super angry yace "Amma ka gama da ni Ahmad, mace me tsafta iya tsafta ina xulumi da tunanin yanda xanyi tarayya da ita balle wannan, haba.. haba wannan xagina kayi wllh, ta ina xan fara abinda kake tunani, did you know who i am kuwa Ahmad, me xanyi da warce tayi tsaftar yarinyar nan sau biyar ma balle ita" wani kallo kawai Ahmad ke yi masa Abuturrab yace "You just insulted me wllh, and i am seriously not happy about it" Ahmad ya tabe baki ya ki basa amsa, Abuturrab yace "Sabida wannan kaddaran da ya fada min ma dole nan da lkci ba mai tsayi ba in auri Aneesah" Ahmad yace "Sai ka ajiye su gida daya kenan?" Abuturrab yace "Yes, kaga Aneesah ta samu me taimakonta aikace aikace kenan" Ahmad yace "Gaskiya ne wannan, to yanxu abinda nake son sani shine, idan ka rubuta takardan ba yarinyar xaka yi kenan ko ko ya xaka yi?" Abuturrab yace "I will do the rightful thing, giving her or not giving her" Ahmad yace "To su kuma can iyayen nata xaka bari su san tana wajenka?" Abuturrab yace "There is no need, idan ta samu 'yan cin kanta xata je garesu watarana" Ahmad ya sauke ajiyar xuciya. Karasawa Abuturrab yyi jikin window yana kallon waje, Ahmad dai sae kallonsa yake, shi har sannan ganin lamarin yake kamar a film, abinda ya fi daure masa kai yanda Abuturrab ya boye masa komai from beginning sae ynxu da abu ya baci, murmushi yyi yana gyada kai yana tunanin irin dariya da tsokanar da xae fara yi ma Abuturrab idan hankalinsa ya kwanta, sae dae deep down him he is so Happy for this young girl don yasan Abuturrab baxae ta6a cutarta ba, with him her future is super bright, komai na rayuwa baxai ji kyashin yi mata ba, maganar sakin da Abuturrab yyi ne kadai bai ji dadi ba har cikin ransa. Ana kiran magrib suka fita tare xuwa masallaci bayan sun yi alwala, Jiddah ce kadai xaune tsakar gida da buta a gabanta, tunda ta hangosu daga nisa tayi kasa da kanta tana alwalanta,, Kallonta kawai Ahmad ke yi yana mamakin yanda ita da gogan suka iya pretending, ko da wasa bata ta6a nuna masa ta san sa ba, murmushi kawai yake yi yana kara jinjina wannan lamari me abun mamaki, Abuturrab dai ko kallon inda take bai yi ba har ya fita gate din, Ahmad yyi murmushi ya bi bayansa, shi dai ya san ko giyar wake Abuturrab ya sha baxai yi accepting yarinyar nan matsayin matarsa ba, bayan an idar da sallah sun fito masallaci Ahmad na kallon Abuturrab yace "She isn't comfortable staying with the gate man and his wife, may be because daki daya ne, kaga baxai yiwu suna ciki tana ciki ba shi yasa take yawan xaman waje, na lura da hakan" Abuturrab bai ce masa komai ba har suka shiga compound din, sae a sannan yace "Idan na gaida Umma xaka saukeni gida yanxu" Suna bude kofar parlon Abuturrab yyi ido hudu da jiddah tana tsaye daga kusa da kofan parlon, sunkuyar da kanta tayi ta koma gefe cikin sanyin murya tace "Ina yini" Bai ce komai ba ya karasa cikin parlon, Ahmad ya sakar mata murmushi yace "Ki karasa ciki mana, kin tsaya a bakin kofa" Tana jan yatsunta tace "Abinci xan amsa inji Maman Abdallah" Ahmad yace "Toh ki karasa ciki" Ta d'an karasa amma ba can cikin parlon ba tace "Na gaya ma Aunty Huraira tace toh" Umma ce ta fito kitchen ganin jiddah tace "Yau ma jikin kofar kika makale Jiddah?" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Umma tace "Ma su sunan ki kuwa suna da sakin jiki ke ban san ya haka ba" Ahmad yace "Bakuwa ku ka yi gidan Umma" Umma tace "Ehh bakuwar Amina ce, gashi har yau taki sakewa" Ahmad ya kalleta yana murmushi yace "Ya sunanki?" A hankali tace "Jiddah" tausayinta Ahmad ya ji har cikin ransa, without allowing that to show... ya buda ido yace "Lahh Ummin Captain ce ashe" Umma tayi murmushi tace "Kai ba Umminka bace kenan?" Ahmad ya shafa kansa yana murmushi ya kalli Abuturrab da ya hade rai kamar bai ta6a dariya ba yana kallon TV, yace "Captain ga mai sunan Ummin mu fa" Umma na kallon Jiddah tace "Karasa kitchen din ki ga ko ta gama xuba maki, kinji" Kitchen din Jiddah ta nufa ta shiga ciki, Abuturrab ya gaida Umma a hankali, amsawa tayi da murmushi tace "Alhmdlh jiki yayi sauki kenan, ai daxu da muka je kana bacci" D'an murmushin karfin hali yayi yace "Naji sauki Umma" Tace "Toh Allah ya kara lafiya Son, bari a kawo maku abinci yanxu" A nan parlon ta barsa shi da Ahmad, Jiddah ta fito rike da abinci, bata yadda ta kallesu ba ta nufi kofa kamar mara gaskiya ta fita... Washegari Thursday karfe tara da yan mintuna Abuturrab ya fito daga bedroom dinsa, Bangaren Abbansa ya nufa, sai da ya bude kofar parlon Abbansa yace "Alhmdlh.... Much better now" sisters dinsa ne xaune parlon suna masa ya jiki kamar baxai amsa ba kuma bayan ya isa bakin kofar parlon Abbansu ya amsa sannan ya shiga parlon da sallama, Aunty ce tare da Abba a parlon, tun da ya shigo Abbansa ke kallonsa, ya xauna kasan carpet yace "Sannu da dawowa Abba" Abba yace "How are you feeling now?" A hankali yace "Alhmdlh na ji sauki" Abba yace "Allah ya kara lafiya" Aunty tace "Jiki kam Alhmdlh, kamar ba shi ba shekaranjiya" Abba na kallonsa yace "Kana stressing kanka da yawa ko, you look stressed out" Abuturrab ya girgixa kai yace "Aa Abba" Aunty tace "Kamata yayi ka dau hutun ko da sati biyu ne ka huta har ka murmure gaba daya, you look so lean" Shi dai Abuturrab murmushi kawai yayi bai ce komai ba, Aunty ta mike ta nufi kofa bayan ta dau tray din da ta kawo ma Abba shayi ta fita, Abba na kallon Abuturrab yace "Hope babu damuwa Aliyu?" A hankali Abuturrab yace "Akwai Abba" Da mamaki Abba ke kallonsa, kafin yace "Talk to me, meye damuwar" Abuturrab ya kallesa lkci daya jikinsa yayi sanyi, cikin sanyin murya yace "Abba i did something...." Sai kuma yayi shiru, Abba ya ajiye cup din hannunsa yana kallonsa da kyau yace "Feel free son, tell me what happened" Abuturrab ya sunkuyar da kansa nan ya sanar ma Abbansa komai tun daga farko, bai boye masa komai ba, Abba couldn't stop looking at him da wani expression da shi kansa ya kasa fahimta, Abuturrab ya xauna kan kneels dinsa a hankali feeling so remorseful yace "Kayi hakuri Abba, i neva thought things will turn out that way da ban yi komai gaban kaina ba, ban san haka lamarin xai kasance ba, i am sorry father, I don't know if this means failing you, kayi hakuri Abba..." Abba ya dafa shoulder dinsa ya sauke ajiyar xuciya amma kuma ya rasa ma abinda xai ce masa, da alama ya girgixa sosai da batun shi ma, Abuturrab yace "Xan iya kai ka gun mai anguwan ma so u can believe me 100%, ban ta6a xaton haka abubuwan xa su tafi ba da ban yi ba" Abba ya kara sauke wani ajiyar xuciya yace "Ikon Allah, to Allah ubangiji ya sa hakan shine mafi alkhairi gare ka Aliyu, but this is astounding..." Abuturrab yayi shiru bai ce komai ba, Abba ya dinga pondering kan lamarin, sai yake ganin abun kamar a mafarki, his son getting married babu shi, babu yan uwansa, infact unprepared marriage, hakan bai ta6a faruwa a xuri'arsu ba kaf" Abuturrab ya katse ma Abba tunaninsa ta hanyar cewa "Amma xan saketa Abba" Da sauri Abba ya kallesa yace "Why? Ba saboda ka taimaketa ka aikata hakan ba, xaka saketa saboda me kuma?" Da mamaki Abuturrab ke kallon Abbansa, can yace "Abba amma ai ni baxan iya xama da ita as a wife ba, i just can't Abba, she is not my class" Abba ya dinga kallonsa, Can ya girgixa kai yace "Dole hakan xaka xauna da ita kuwa, before making the decision of marrying her ai ya kamata ka fara naxarin ko xaka iya xama da ita din as wife or not, ka saki yarinya for what reason, i thought it's ur decision? Ko ka dau aure abun wasa ne, ka xata film ku ka yi acting a wajen ranan, ko kuma wasan yara ku ka yi?" Abuturrab ya marairaice hankalinsa a mugun tashe yace "Abba wllh kawai don in taimaketa a wannan moment din ne yasa na amince da auren ba wani abu ba, naga xa ayi ruining rayuwarta ne yasa na amince Abba, amma kuma nayi niyyar sakinta ai bayan daura auren" Abba na masa wani kallo on a serious note yace "Erase that harebrained idea right away, babu wani sakinta da xaka yi, tunda har aka daura auren shaidu duk sun shaida ka bada sadaki, babu wani abinda ya rage illa kayi accepting fact din ka tare da matarka, kada in sake jin ka yi xancen saki, ba drama ko film din Hausa kuka yi acting ba a wajen" Da mugun mamaki Abuturrab ke kallon Abban nasa baki bude, sanin arguing further won't favor him yasa yayi shiru, but deep down him yasan in har yana son ci gaba da rayuwarsa yanda yake yi a da to sai ya datse igiyar yarinyar nan a kansa, idan bai saketa ba he will never have peace of mind, he might even turn a Sadist, sakinta kuma da xai yi babu wanda xai bari ya sani, they will stay in the same roof but not as husband and wife, muryar Abbansa ya ji yana cewa "Sai ka karasa gyara gidanka na nan garin ku tare, i will call all my brothers and inform them what happened, since u chose this for ur self" Abuturrab ya ji kamar yayi kuka sanin in har cousins da frnds dinsa suka ga cewar wannan yarinyar ce matarsa ai tasa ta kare kuma, he don't even want to imagine how they will make jest of him and even laugh at him, yayi narai narai da ido ya marairaice yace "Abba don girman Allah ba sai ka gaya ma kowa wannan abun ba pls I'm begging you Dad" Dariya ya kusa ba ma Abban nasa ganin yanda ya marairaice, wanda he couldn't help it but laugh, duk da kasancewarsa musulmin kwarai sannan dattijon kwarai ne kadai ya sa ya saduda yayi give up da wannan auren na d'an sa, amma banda haka shi da kansa xai iya sa Abuturrab ya saketa don har cikin ransa bai ji dadin wannan lamarin ba, Lkci daya idanuwan Abuturrab suka kada sosai ya kife kansa da kujera, Abbansa yaji tausayinsa ba kadan ba yana murmushi yyi patting shoulder dinsa cikin kwantar da murya yace "Abu me kyau kayi my son, and i am proud of you, Allah kadai ya san ladanka, kar ka damu it shall be well, Allah yayi maka albarka, and kada ka sake tunanin sakinta a ranka shine xai yi helping matters, ka xauna da ita tunda ka aureta, you won't regret it in sha Allah coz you've got a good heart, nasan wataran xaka yi alfahari da ita...." Da sauri Abuturrab ya dago ya kalli Abbansa da jajayen idonsa, ji yayi xaxxabi na neman kara rufesa, amma tunawa da yayi xai saketa ba tare da sanin kowa ba sai ya ji hankalinsa ya d'an kwanta, Abba yace "Xuwa yaushe xata tare din yanxu?" Abuturrab ya kalli Abbansa a sanyaye, Abba yace "Let me talk to ur mothers about it first, i hope they won't be disturb much..." Wayarsa ya dauka ya shiga kiran matan nasa, Abuturrab gabansa ya dinga faduwa don bai san yanda Umminsa da Aunty su kuma xa su dau lamarin nan ba, ba a dau lkci ba duk suka shigo, Abuturrab ya kalli Abbansa a hankali yace "Can i excuse my self sir..." Abba yace "Sure dear" Mikewa yayi ya nufi kofa walking slowly, Ummi ta bi sa da kallo, tun a shekaranjiya ta san abu na damunsa yana cin sa har cikin ransa, though tasan da kyar ya gaya mata koma meye da ya shafesa sai dai kishiyarta amma wannan karan ta lura ita din ma bai gaya ma ba, hakan yasa abun ya dameta sosai tun daga jiya bata da nutsuwa, don duk da baya gaya mata sabgarsa in dai xai gaya ma Auntyn da sauki, ko ba komai ita ma tana basa shawaran..... Aunty da ta bi sa da kallo tace "Alhaji ko ya gaya maka damuwarsa, tun safe nake fama da shi yace min ba komai, kuma nasan ba gaskiya bane, and this is so unlike him" Abba ya d'an sauke ajiyar xuciya yace "Kiran da nayi maku kenan yanxu" Duk suka maida hankali kan Abba don jin damuwar Abuturrab din. *Tohm Khaleesat Haiydar dai bata Allah ya isa kuma baxata fara ba a kan littafin Jiddatul Khair, sannan nasan ni baxan iya hana fitar book din nan ba, kawai dai idan xaka yi ma kanka adalci if u should come across this book, keep it in mind that ba free book bane, littafin kudi ne, if u are willing to read just make ur payment ka sha karatunka ba wani shakku a ranka, and bana tunanin u will regret paying and reading this book in sha Allah....*✍🏻 _And i really appreciate my lovely fans patronage..... na samu sabbin fans da yawa da suka yi patronizing Jeedahh kuma naji dadin haka... Ina godiya da maku fatan alkhairi_ 🥰 The book is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah... And u show ur evidence of payment via 07087865788.... Thank you.😇 Mikewa Aunty tayi bayan Abba ya kai aya cikin tashin hankali tace "Ban gane ba Alhaji?? Are you for real? Shi Abuturrab din ne yaje ya daura ma kansa aure without our knowledge????" Abba yayi murmushin karfin hali yace "Dama mutum ya ta6a daura ma kansa aure, we just have to accept it Hafsah, it doesn't make sense though, to amma ya muka iya da lamarin ubangiji, Allah ya riga da ya tsara hakan" Ummi kallonsu kawai take ko kiftawa babu, wanda da alama duk ta fi su shiga shock din, Aunty ta dage hannu biyu sama tana girgixa kai da karfi tace "No wayyy, mu ba gantalallu bane gaskiya, yanda aka daura auren haka xai saketa wllh wllh, me xai yi da yar hayi, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yar hayi fa kace Alhaji?? To na rantse da Allah baxai yiwu ba" Wani kallo Abba ya dinga yi mata har tayi shiru tana huci kafin yace "Ja xa ki yi da lamarin ubangiji??" Aunty ta dalla masa wani harara ta nufi kofa rai bace tana cewa "Allah ya kiyaye, wllh sae ya saki wannan yarinya dai, banda fitinarsa ma ina shi ina shiga tsabgan talakawa mutan anguwan nan balle har wannan mummunan kaddararran ya fada masa, wllh saki kamar yayi sa...." sai kuma ta fashe da kuka ta fice ta rufe kofan, Abba ya kalli Ummi bayan kusan minti biyu da fitan Aunty jin taki cewa komai yace "Kinyi shiru Hauwa" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh me xance, jin abun nake kamar a mafarki ai, an ta6a aure haka dama Yallabai?" Abba yace "Gashi nan dai d'an ki yayi, kinsan babu abinda taimako baya sa mutum yyi, to kinga inda nasa taimakon yayi leading dinsa to" Ummi ta girgixa kai tace "Toh yanxu meye abun yi Yallabai? Wannan ai ba abun ayi shiru bane ayi ta kiran taimako, wani irin aure ne wannan kamar a wasan kwaikwayo" Abba yace "Meye kuwa abun yi banda ya tare da ita yarinyar, ai an riga da an daura aure, kuma lamarin aure ba lamarin wasa bane" Da mamaki Ummi ke kallonsa tace "Kana nufin haka xai yi rayuwa da ita? Ya tare da ita fa kace" Abba yace "Kwarai, tunda har an daura auren, ai yanxu matarsa ce ita din, ko ke wani shawara xaki bada a nan?" Ta girgixa kai tace "Haba Alhaji, a ina aka ta6a irin wannan auren, ni dai tunda nake ban ta6a jin irinsa ba ma, me xa muce ma 'yan uwa da abokan arxiki, me xa ace ma Hajja, ya kake ga xata dau lamarin nan? shi Abuturrab din shaye shaye ya fara da xai kai kansa ga irin wannan taimakon? Ba gwara ma ace yau kawota yayi gidan nan ba yace mana ga ta, ai babu wanda xai hanata xama gidan nan idan anyi bincike an gano gaskiyar lamarin, kuma baxa mu ki riketa ba, idan ma wani ya ki ni baxan ki ba ka sani" Abba yace "A takaice kema dai kin goyi bayan ya saki yarinyar kenan" Ummi tace "Toh idan bai saketa ba me xai yi, ai sakin kadai ne best solution a nan, ko a garin ga6a ga6a ba a irin wannan auren Yallabai" Abba yace "Toh duk kun yi kokari, amma ku sani auren nan bbu fashi tunda ba wani ya dau sadakin ya kai masa ba, da kansa ya aikata duk abinda ya aikata gaban kansa ba tare da ya duba cewa yana da iyaye da magabata ba, to don me xa ace sai yayi saki, tunda har ya amince aka daura masa aure da ita wllh dole ya amince ya xauna da ita, ba dai taimakonta yake son yi ba, gata nan sai ya taimaketa har karshen rayuwarta, nan gaba sai kiga ba shi ba har ke sai kiyi alfahari da ita a matsayin matar d'an ki, sannan a rayuwar nan there is reason for everything, Allah ya riga ya tsara hakan to mu a su wa da xa mu ce tsarin bai yi ba??" Mikewa Ummi tayi bata sake sauraronsa ba ta fice daga parlon, ya daga kafada yace "Yanda bai maku dadi ba nima lamarin bai min dadi ba ko kadan, but who am i to ask why tunda haka Allah ya tsara???" Aunty ce tsaye kan Abuturrab inda take shiga ba nan take fita ba duk ta hada xufa kai kace tayi wani tafkeken asara ne a rayuwarta, ko Salem ne yayi abinda Abuturrab yayi iyakan abinda xata yi masa kenan take ma Abuturrab, Abuturrab dai na xaune gefen gado ya rike kansa da yyi masa nauyi duk yana sauraronta ga wani bugawa da xuciyarsa yake, he just hate himself completely for this foolish mistake he made, me yasa bai yi duk wannan tunanin ba kafin ya aikata wannan shirmen, me yasa bai yi reasoning abinda xai biyo baya ba yayi abinda yayi?? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da kyar ya dago kai yana kallon Stepmum din tasa da idanuwansa da suka kada cikin sanyin murya yace "Wllh xan saketa Aunty, ba da dadewa ba kuma xan yi hakan, ni ko ba ace in saketa ba ma dama ba sa'ar aurena bace dole xan saketa" Aunty na huci tace "Toh uban me kake jira har yanxu? Mu xaka kwaso ma abun kunya a dinga nuna gidanmu a gari, wllh baxai yiwu ba ko almajiri baxa ayi masa irin wannan auren da kaje kayi ma kanka ba, aikin banxa kawai, ko yar cikin gari wllh wllh kafi karfinta balle yar kauyen hayi, to sai ta shigo gidan mu gani ai...." Tana fadin haka sai ta saki kuka ta fice daga dakin. Abuturrab ya dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a xuciyarsa, what has he done with his life, he wish he could wake up and see that all this is nothing but a dream, mikewa yayi a hankali ya karasa kofar dakinsa ya sa makulli don ma kar ta sake dawowa sannan ya dawo ya xauna ya dafe kansa hade da lumshe ido yana kiran Allah a ransa. Bayan azahar Abuturrab ya dau makullin motarsa ya fito daki, tun safe bai fito ba sai yanxu da yaje masallaci yayi sallah ya dawo, yana shigowa parlor ganin kallon da siblings dinsa ke masa yasan sun samu labarin kenan su ma, bai kuma kallonsu ba har ya fice daga gidan, ya hau motarsa ya bar gidan, gidansu Ahmad ya nufa, ko kallon matar mai gadi dake gaishesa bai yi ba ya nufi entrance din gidan, a yanxu dai komai haushi yake basa, underneath his breathe yayi sallama ya shiga parlon, Huraira ce da Siyama parlon, su ma bai sake kallon inda suke ba balle ya amsa gaisuwarsu, dai dai nan Ahmad ya fito daga wani daki dake nan parlon, ganin Abuturrab yace "I was planning on calling you now, welcome... Duk kayi scarce yau" Abuturrab bai ce komai ba ya nufi dakin Ahmad, Ahmad ya bi bayansa yana murmushi a ransa yana cewa the latest ango in town, xaune ya tadda shi gefen gado, Ahmad ya tsaya bakin kofa yana kallonsa yace "Ya ake ciki yanxu, hope it went well??" Abuturrab yace "Kamar yanda na fada, no much problem from Dad, but aunty took the matter tooo personal, Aunty tayi misunderstanding komai" Ahmad ya masa wani kallo yace "And so what? How about Ummi? Though she is here, daxu ta xo" Abuturrab ya xaro ido yace "Kana nufin Ummi na gidan nan?" Ahmad yace "Yea tana dakin Umma" Abuturrab ya lumshe ido ya bude, gaba daya abun duniya ya ishesa yanxu fisabilillah baxai farka yaga duk wannan abun mafarki bane, Ahmad yace "Amma Ummi tayi maka magana ne?" Abuturrab ya girgixa kai yace "Bata ce min komai ba har yanxu" Ahmad yace "Ka kwantar da hankalinka komai ya xo da sauki tunda Abba ya fahimce ka" Abuturrab yace "Ya fahimce ni?? Ai ni da abinda Abba ke ce min yanxu gwara ma ace bai fahimceni ba kwata kwata, Did you know that he is forbidden me from divorcing her?? Ce min yayi fa baxan saketa ba" Ahmad har xai ce dai dai kenan amma don kar ya sake provoking din d'an uwan nasa yayi fuskan mamaki yace "Toh fah, kar ka saketa kuma??" Abuturrab ya d'an ja tsaki a fusace fuskar nan tasa a murtuke, Can ya dago ya kalli Ahmad yace "Toh me Ummi ta xo ce ma Umma ynxu?" Ahmad yace "Don't know.... And least i forget, Jiddah bata da lafiya fa" Daga kai Abuturrab yayi yana kallonsa, Ahmad yace "Yea, ina mata karin ruwa, shine kaga na fito dakin dake parlor da ka shigo yanxu" Abuturrab dai bai ce komai ba, Ahmad yace "Dakin mai gadin baxa a rasa sauro ba, it's malaria symptoms...." Abuturrab na kallonsa yace "Kayi mata test ne? She just finished treating malaria few weeks ago" Ahmad yace "Yea it's possible she is reinfected" Abuturrab bai sake cewa komai ba, Ahmad ya juya yace "Mu je ka dubata" Abuturrab yace "It's not necessary" kallonsa Ahmad yayi yana ciro wayarsa dake ring a aljihunsa yaga Umma ke kiransa, ya kalli Abuturrab yace "Hmm Umma is calling" Daga kiran yayi ya kai kunne, bayan few seconds yace "Toh" daga haka ya katse kiran yana kallon Abuturrab yace "She's calling me to her room now" Yana fadin haka ya fita dakin ya tafi bangaren Ummar tasa, tana xaune bedroom dinta tare da yayarta ko wannensu fuska babu annuri, Ahmad yyi kasa da kai ya xauna nan kasa yace "Gani Umma" Umma na kallonsa strictly tace "Ahmad wacce yarinya ce Abuturrab yaje ya aura without acknowledging how stupid that will be?? Yanxu kana matsayin d'an uwansa ka yi shiru ka barsa ya aikata abinda ya aikata Ahmad??" Ahmad yayi kasa da kai a hankali yace "Wllh i knew nothing about that Umma, i swear to God ban san komai ba..." Umma ta daka masa tsawa tace "You are lying, ya xaka ce baka san komai a kai ba, akwai wani abu da Aliyu ke boye maka?" ya kalleta da sauri yace "Billah abinda ya sanar da ni jiya ne kadai nasani game da lamarin nan, a jiya nima nasan abinda ya aikata Umma" Umma tace "Me ya sanar da kai jiyan?" Ya sauke kansa yace "Umma nima he didn't tell me all, but he is around now, yana dakina" Umma tace "Abuturrab na gidan nan????" Ahmad yace "Ehh yanxu ya shigo" Umma tace "Call him" Mikewa Ahmad yayi ya fita dakin.... Abuturrab ya mike da sauri bayan Ahmad ya sanar masa kiran Umma yace "Me yasa xaka ce ina gidan nan Ahmad for God sake?" Ahmad ya daga shoulder yace "i didn't say so, kawai kirana tayi tace i should call u, kilan ko su siyama ne suka gaya mata ka xo, aikena kayi da xanje in ce masu ka xo?" Abuturrab ya wani hade rai yana jin kamar ya dau car key dinsa ya bar gidan, but he just can't, babu yanda ya iya haka ya fita dakin Walking slowly, Ahmad na biye da shi yana d'an murmushi, kasa ya xauna shi ma bayan ya shiga dakin Umma, tunda suka hada ido da Umminsa bai sake yarda hakan ya faru ba, ita ma small mum din tasa ya ki yarda su hada ido, su kuwa sai kallonsa suke kamar ranan suka fara ganinsa, Calmly Umma tace "Abuturrab, who is this lady that u went and tied the not with.. without the knowledge of ur parent??" Abuturrab kansa na kasa a hankali yace "I'm sorry Umma, i never knew it will happen this way, wllh it's not intentional..." Ta dakatar da shi a fusace tace "Malam tambayarka nake wace yarinya ce?? Ba wani xance can ba" Abuturrab kamar baxai ce komai ba sai kuma cikin sanyin murya yace "Tana gidan nan Umma" Ba Umma ba har Ummi bude ido tayi sosai tana kallonsa with shock, can suka kalli juna, Ahmad dai na tsaye bakin kofa ya rungume hannu, Umma na masa wani irin kallo tace "Wani gidan?" Abuturrab yace "Nan gidan?" Da wani expression Umma na kokarin calming kanta tace "Wacece ita?" Abuturrab ya kasa bata amsa, Umma ta kalli Ahmad, ya sauke idonsa murya can kasa yace "Yarinyar dake gun matar mai gadi yanxu" Umma ta xaro ido tace "Ban gane ba, wacce yarinya kenan?" Ahmad yace "Me sunan Ummi" Bude baki Umma tayi tana kallonsu gaba daya, Ummi dai duk sun gama confusing dinta sae bin su da kallo take, Cikin tsawa Umma tace "Baxa ku min bayani ba yanda xan gane???" Abuturrab ya dago yace "Ita ce Umma, da abun ya faru ne shine na kawota nan gun matar mai gadin gidan nan" Salati Umma ta saki har da tafe hannu tace "Kana nufin bakuwar nan Jiddah???" A hankali Abuturrab ya gyada mata kai yana kallonta da manyan idanuwansa, Umma ta hangame baki ta dinga kallon Abuturrab with shock, can ta kalli yayarta dake kallon ikon Allah tace "Yaya wai kinji yarinyar da mu ka shiga daki daxu a downstairs kika duba da jiki..." Ummi sai kallon Abuturrab take ko kiftawa babu, ya sunkuyar da kansa cikin sanyin murya yace "Ku yi hakuri Umma, i don't know d words to use in asking for forgiveness, I'm truly sorry for all this, wllh it's not intentional, Allah ne ya kaddaro min haka, amma in sha Allah nace xan saketa" Umma dake ta kallon yayarta da ta jinginar da kanta da gado ta kasa cewa komai, Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "This is serious, Abuturrab? Why?? Why Abuturrab, dama ashe kai ka haifi kanka??" Kallonta kawai yake ruefully... ta girgixa kai feeling so disappointed tace "I am disappointed at u Aliyu, ka bani mamaki" Shi dai bai iya yace komai ba, Tace "Yanxu ita Jiddar ta sani? I mean tasan da wannan auren?" Ya girgixa kai yace "Bata san komai dake faruwa ba har yanxu.... And xaki iya samunta ki tambayeta ta gaya maki duk abinda ya faru da dalilin kawota gidan nan da nayi, sannan ni a lkcn da na kawota gidan nan ba a daura auren ba wllh" Umma was totally lost of words balle kuma Ummi da sai binsu kawai take da kallo, Umma tace "Daga bakin ka nake son jin labarin abinda ya faru ba ita ba" Abuturrab ya lumshe ido ya bude babu musu ya shiga bata labarin abinda ya faru tun daga farko ita ma bai boye mata komai ba har xuwa sanda aka daura masa aure da Jiddah, da tafin hannunsa ya rufe fuskarsa cikin breaking voice yace "Plss Umma ku daina ganin laifina, i only tried to help ne ban san haka abun xai kasance daga karshe ba, kice Ummi tayi hakuri ta yafe min wllh xan saketa na dau ma kaina wannan alkawarin, ban yi hakan don in bakanta maku ba Umma..." Umma ta rasa abinda xata ce tausayinsa ya cikata, cikin sanyin murya Ummi tace "Aa ni baka min komai ba, Allah ubangiji ya sa mu dace" Umma ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ta na kallonsa tace "Tashi kaje Abuturrab" Mikewa yayi ya juya ya fita dakin Ahmad ya bi bayansa, Umma na kallon Yayarta tace "Kiji wani babban lamari na ubangiji yaya, yanxu ke me kike ga xa ayi kan lamarin? What next?" Ummi ta sauke ajiyar xuciya a fili tace "Ban san me xance ba Ramlah" Bayan la'asar Abuturrab na fitowa masallaci tare da Ahmad, Ahmad yace "Ka shiga ka duba yarinyar nan pls, she was very sick yesterday night fa" Captain na kallonsa yace "Me dubata da rashin dubata xai kara mana ni da kai pls? Kai dai ba kana dubata ba me yasa xaka damu ni sai na dubata" Ahmad bai kulasa ba ya tsaya gaisawa da wani frnd dinsa a kofar gidan, Abuturrab ya shiga compound din walking slowly, babu kowa parlon ya kalli dakin da yaga Ahmad ya fito daxu da ya xo, kamar xai wuce sai kuma ya nufi dakin ya bude kofar a hankali ya shiga ya kulle sannan ya juyo yana kallonta, tana kwance saman gadon dakin drip a hannunta jin budewan kofa ya sa ta bude ido, ganinsa ta mike xaune da sauri, kana ganinta kasan she is very sick don har ta rame, lebbenta yayi ja, ya kalli drip din da har yayi rabi, da kyar tace "Ina yini" Bai yarda ya kalleta ba idonsa na kan drip din cikin calm voice dinsa yace "Ya jikin?" A hankali tace "Da sauki" Bai kuma cewa komai ba, bayan few seconds ya d'an saci kallonta suka hada ido, da sauri ta sauke idonta, ya d'an hade rai, bude kofar dakin aka yi ya juya da sauri, Ummi da Umma ne bakin kofar, he wish hakan bai faru ba, ya ji kamar kasa ya bude ya shige kawai ya huta, kasa kallonsu yayi, Ummi dai sai kallonsa take ta karasa cikin dakin tare da kanwarta, Jiddah ta sunkuyar da kanta don sun gaisa daxu, Umma na kallonta tace "Ya jikin?" Tana jan fingers dinta tace "Da sauki Umma" Ummi dai sai kallon Jiddah take, Juyawa Abuturrab yyi xai fita amma ya kasa ce ma Umma ta basa hanya ita kuma ta ki basa hanyar, Ummi tace "Sannu Allah yakara lafiya" Jiddah na kallonta tace "Ameen" Umma tace "Kin sha shayin kuwa daxu?" Jiddah ta gyada mata kai, Umma tace "Toh Allah ya sauwake" Daga haka ta kalli Captain tace "Meet me before leaving...." Shi dai bai dago kansa ba, Tana fadin haka ta fita Ummi ta bi bayanta, sai a sannan Abuturrab ya daga kai ya bi su da kallo, Umma ta kulle kofan, still yayi bakin kofar, can ya d'an kalli Jiddah, kallonsa take ita ma, suna hada ido tayi light smile tace "Kun yi kama da warce ke kusa da Umma" ya hade rai ya juya ya bude kofan ya fice ya kulle. Sai da Abuturrab ya tabbatar Umminsa ta bar gidan sannan ya koma dakin Umma, Kallonsa take xai xauna kasa ta nuna masa kujera ya mike ya koma saman kujeran tana kallonsa, cikin sanyin murya yace "Gani Umma" Tace "Tell me now son, what do u have in mind a kan wannan auren da kaje kayi ma kanka?" Ya girgixa kai yace "Taimakonta kawai nake son yi ba wani abu ba, but ban san things will turn out this way ba da ban fara ba..." Umma tace "So what's ur next plan now?" Ya shafa kansa yace "Umma sakinta xanyi, since yanxu kun san abinda ya faru sai ta xauna nan ko kuma wajen Ummi, i know Ummi won't say no" Umma dai kallonsa kawai take, can tace "Toh kilan hakan kadai ne mafita gareka, amma can su iyayen nata da suka baka aurenta fa?" Ya girgixa kai yace "Ba mutanen kwarai bane, ko da xata xauna da ke ko Ummi to babu ita babu su, ita din marainiya ce, she is staying with just her Stepmum, tace min iyayenta sun rasu, I don't know of relatives amma da da akwai baxa su bari tana wahalan da take ba a gun Kishiyar Baabarta, beside that baxa su bari a aura mata shi wanda aka yi niyyar aura mata da farko ba, don duk anguwar babu wanda bai san tout bane shi, amma sbda yana ba ita stepmom din nata abun duniya wanda bai kai ya kawo ba shine take son aura mata shi, sannan tana da 'ya ita ma sa'arta fa" Umma dake ta sauraronsa ta girgixa kai cike da tausayin Jiddah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un...." Yayi kasa da murya yace "Ita ce me yin awaran da muke siyo maki a hayi, Ahmad yasanta... But bai ta6a sanin ina xuwa gunta a can hayin ba har sai da wannan abun ya faru" Umma ta buda ido tace "Ikon Allah, Allah sarki rayuwa, yanxu abinda nake so da kai shine you talk to her about all what happened tunda kace bata sani ba, ka sanar mata komai" Da sauri Abuturrab ya kalleta, ta gyada masa kai tace "Yes she needs to know kafin ma kayi sakin da kake cewa, after that kuma idan nan din xata xauna to, in kuma gun Yaya xata xauna shkkn" a hankali Abuturrab yace "Toh shkkn Umma, nagode" Umma tace "Amma ba yau xaka sanar mata ba tunda bata da lafiya, gobe ka xo we are hoping she will get much better sai kayi mata bayanin komai" Abuturrab yace "In sha Allah Umma" Tace "Maa sha Allah, you can go, Allah yayi maka albarka" Yace "Ameen" mikewa yayi ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya, tun bayan faruwan wannan lamarin sai yanxu ya ji magana da ya sa masa relieve a xuciya, he is happy Umminsa bata dauki wannan batun personal ba, just like his dad and small mum, but Aunty, wani sigh yayi yana tunanin yanda xasu yi da ita idan ya koma gida anjima.... The book Jiddatul Khair is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah.... And u show ur evidence of payment via 07087865788... Do justice to ur self by subscribing before reading... *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 Ko da Abuturrab ya koma gida bai bari stepmom dinsa ta san ya dawo ba don bai ma dawo da motarsa ba a gidansu Ahmad ya barsa, Ahmad yayi dropping dinsa kofar gida a nasa motar ya koma, yana shiga bedroom dinsa ya sa makulli hade da sauke ajiyar xuciya, wanka yayi ya sauya xuwa pajamas dinsa ya xauna gefen gado, yana son shan shayi but baya son fita duk da ko ya fita din kanninsa xai saka still, wayarsa ya jawo ya shiga dialing number din Ramlah, tana dagawa yace "Make me a cup of tea, an omelette with just two eggs" Bai jira cewarta ba ya katse wayan, ba a dau lkci ba Ramlah tayi knocking bakin kofar dakinsa, ya mike ya isa kofan ya bude ya bata hanya ta shigo, ajiye plate din hannunta na kwai dake rufe tayi da cup din shayin tana kallonsa tace "Yaya...." yace "Goodnight Ramlah" Shiru tayi sai kuma ta juya ta nufi kofa kafin ta fita yace "Thank you" Ta sake juyowa ta kallesa ta marairaice tace "Amma yaya me yasa....." Hade rai yayi yace "Fita!!" Fita tayi ta kulle masa kofar ya karasa ya sa key. Washegari Friday Abuturrab na dawowa masallaci da asuba ya shiga bangaren Umminsa, da da ne bangaren stepmom dinsa xai fara shiga, kansa a kasa ya gaida Ummi ta amsa, a hankali ya soma bata hakuri, tace "It's okay, ae kun gama magana da Hajiya Ramlah ko?" Ya gyada mata kai tace "Toh maa sha Allah" Yace "Amma Ummi don Allah kiyi ma Abba magana naji yana cewa baxan saketa ba..." Ummi tace "I don't know... But seriously he is not to decide that for you, you just ignore him" Abuturrab bai ce komai ba, can yace "Toh shkkn Ummi" mikewa yayi ya fita dakin ya koma nasa, a masallaci ma dodging din mahaifin nasa ya dinga yi har ya shigo gida basu hadu ba. As early as 10 Abuturrab ya bar gidan ya tafi gidansu Ahmad, bayan ya gaisa da Umma dake parlor ya tafi dakin Ahmad, Ahmad na shiryawa ya samesa, Ahmad na murmushi yace "Welcome latest ango" Abuturrab yayi still ya dinga masa wani kallo, Dariya Ahmad yayi yace "Yanxu dai cikin ruwan sanyin kullum sai ka xo gidan nan ko?" Abuturrab bai tanka sa ba ya tafi ya xauna, Ahmad ya gama shiryawa yace "She's getting better, jikin da sauki yau sosai" Nan ma Abuturrab ya sharesa, bai san shi abinda ya kawosa daban ba, Mikewa kawai yayi ya fita daki hoping Umma ta bar parlon yanxu, Ahmad ya bi sa da kallo yana murmushi, luckily ya tadda babu kowa a parlor ya karasa dakin da Jiddah take ya bude hade da sallama murya can ciki, tana xaune saman gado da wani drip din a hannunta ga pepper soup da Umma ta sa ayi mata, Huraira da Maman Abdallah ne dakin suna ta hira, ita dai sai dai tayi murmushi, ganin Abuturrab duk suka gaishesa, bai san suna ciki ba da baxai fara shigowa directly ba, ya amsa without looking at them, Jiddah ta kallesa tace "Ina yini?" Ita ma bai kalleta ba yace "Lafiya" Ahmad ne ya karaso dakin ya shiga ciki yana kallon jiddah yace "Alhmdlh jiki yayi kyau sosai ko Ummi?" Ta d'an yi murmushi amma bata ce komai ba, shi dai Abuturrab na tsaye, Ahmad ya kalli su Huraira da basu da niyyar fita a tunaninsu kawai dubata suka shigowa yi, yana murmushi yace "Maman Abdallah da Aunty Huraira a bamu waje mu duba patient pls" Duk suka mike, Huraira tace "Toh bari mu fita" Bayan sun fita dakin Abuturrab ya karasa gun window ya tsaya Ahmad dai sai kallonsa yake, Can yayi murmushi ya kalli Jiddah yace "Kin sha maganin ai ko?" Ta gyada masa kai tace "Eh" yace "Toh Allah ya kara lafiya" Tace "Ameen" Ya juya yace "Bari in kawo maki na karshen.." Daga haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita ya kulle kofar, sunkuyar da kanta tayi, Abuturrab ya d'an kalleta, he don't even know where to start from, hada ido suka yi ya rungume hannunsa yace "Ya jikin?" Tace "Naji sauki" Ya d'an yi jim kafin yace "Iyayenki sun daura maki aure..." Da sauri Jiddah ta daga kai ta kallesa, yaki yarda su hada ido ya ci gaba yace "Amma ba da mutumin nan ba" Kallonsa kawai Jiddah take ko kiftawa babu, ya shafa kansa yace "Amma shi wanda aka daura maki auren da shi xai sake ki, sai ki ci gaba da xama a nan wajen Umma ko gidanmu wajen Ummina, amma fa sai kin amince babu ke babu Baabar nan taku don ba sonki take ba, kuma baxata ta6a sonki ba, neman kudi take da ke" Cikin sanyin murya Jiddah tace "Toh da wa aka daura min auren??" Yace "Fada maki ba amfani xai yi gareki ba, kawai dai abinda na sani xai sake ki, sai kiyi xaman ki a nan ko kuma ki xauna gidanmu, ki fara karatu islamiyya da boko, kinsan wacece ke, kinsan daga inda kike, kawai na shiga rayuwarki ne ba don komai ba sai don in taimakeki in samar maki yan cin ki, idan ba don haka ba, ni bana shiga abinda bai shafeni ba...." Kallonsa kawai Jiddah dai take a sanyaye, lkci daya hawaye ya kawo idonta, a hankali tace "Jiya Umma da daddare ta shigo ta tambayeni in gaya mata gaskiyan wacece ni, kuma ya aka yi na xo gidan nan" Cikin rawar murya ta ci gaba tace "Ni kuma baxan iya mata karya ba" Abuturrab na kallonta yace "Kin dai gaya mata ko?" Ta gyada masa kai yace "Good, xuwa gobe duk inda kika ce xa ki xauna nan xa a kai ki, ko gidanmu ko nan" A hankali tace "Toh idan na xauna nan xaka dinga xuwa?" Kallonta yake da kyau, ya hade girar sama da ta kasa yace "In xo in yi maki me??" Kasa cewa komai tayi tana wasa da fingers dinta, yace "Ae ba lallai ki gan ni ba, ki ma daina min kallon sani daga yanxu, ki kama Umma da su Siyama ki rike sosai, they will like you, ni ba lallai a shekara ma kike ganina ba" Kai kawai ta gyada masa hawaye cike idonta, yace "Sai ki tsaya kiyi karatu da kyau domin al'umma da wa enda suke tare dake suyi alfahari dake..." Nan ma ta gyada masa kai kawai, yace "Allah ya kara lafiya" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita dakin, hawayen da bata san dalilinsa ba ya dinga sauka idonta, Abuturrab ya amshi medical report dinsa wajen Ahmad kawai ya bar gidan coz baya tunanin har ya koma aiki da akwai abinda xai sake dawo da shi gidan, he now felt relieved, yaji baya tare da duk wani damuwa. Da yammacin ranan Abuturrab dake bedroom dinsa ya dau wayarsa dake ring, ganin number Abbansa yaji gabansa ya fadi sosai, dagawa yayi ya kai kunne hade da sallama, Daga daya bangaren Abba yace "Ka sameni parlona ynxu" Kafin yace komai Abba ya katse kiran, lumshe ido yayi ya bude, bayan few minutes ya mike a hankali still holding to his phone ya nufi kofa ya fita, a main parlor suka ci karo da Aunty, yayi kasa da kai yace "Ina yini Aunty" Ko kallonsa bata yi ba balle ta amsa shi tayi wucewarta, ya bi ta da kallon gefen ido sannan ya ci gaba da tafiya xuwa parlon Abbansa cikin sanyin jiki, a hankali yayi sallama sannan ya shiga, sosai gabansa ya fadi ganin Abbansa da brothers dinsa biyu, a sanyaye ya karasa shiga cikin parlon ya xauna kasa sannan ya gaishesu, uncles din nasa suka amsa, ya kalli Abba amma bai ce komai ba, Alhaji Lawal yayan Abbansa ne yace "Mun ji abinda ke faruwa Aliyu, ko kuma ince mun ji abinda ya faru" kasa cewa komai Abuturrab yayi, Alhaji Ibrahim kanin Abbansa yace "What u did is something very good but ba ta yanda ya kamata kayi ba kayi, kada ka manta ba kai ka haifi kanka ba, kana da iyaye, no matter what ya kamata ka nemi consent dinsu, ya kamata ka basu girmansu su san abinda kake ciki, ba sae da abu ya kwabe ba....." Daga kafada yayi yace "Anyway, wannan duk maida hannun agogo baya ne, tunda abinda ya faru ya riga da ya faru, sae dai a tari na gaba" Abuturrab bai iya yace masu komai ba, Alhaji Lawal yace "So what next now? Yarinyar tana ina?" A hankali yace "Tana gidan Umma" Alhaji Lawal yace "Wacece Umma?" Abba yace "Kanwar Hajiya Hauwa" Alhaji Lawal yace "Ohkk, am asking what ur next action is now" Abuturrab ya sunkuyar da kai yace "Abba sakinta xanyi sai ta yi xamanta tayi karatu that was my intention dama" Alhaji Lawal yace "Ka saketa a saboda me?" Abuturrab ya kallesa ya marairaice yace "Abba dama wllh niyyata kenan, ai baxai yiwu inyi aure iyayena basu sani ba, ni kawai na amince na aureta ne sbda kubutar da ita daga hannun matar babanta, amma ai ni baxan iya aurenta ba" Alhaji Lawal yace "Wannan ba magana bane Aliyu, ka aureta, ka aureta kenan, babu wani kwaskwarima, Allah ubangiji ya baku xaman lafiya, kada ka sake tunanin sakinta, kaddararku da ita ne a haka" Bude baki Abuturrab yayi yana kallonsa without knowing cewar yayi hakan, Alhaji Ibrahim ya gyada kai yace "Hakuri xaka yi son, ka xauna tare da ita, ka cike ladanka, ai Allah ya ga xuciyarka, idan ka saketa baka kyauta mata ba, akwai hikima cikin auren nan...." Abuturrab ji yayi kamar ya fara masu kuka gaba daya, Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Dama ni nace baxai saketa ba, cikin weekend din nan ya dauketa su tare, ai ba wani ya jawosa ya aura masa ita ba, sai yayi hakuri ya rungumi kaddara" Abuturrab was lost of words amma ganin musa masu baxai yi masa amfani ba yayi shiru duk yana sauraronsu, sai dai xufa kawai yake yi, to lkcn da ma xai saketa din sani xa su yi? Tunanin hakan ya saukar masa da relieve, Muryar Alhaji Lawal yaji yana cewa "Gobe asabar ka tare kawai da matarka, Allah ya sanya alkhairi, not too long sai ku shirya da ita ku tafi gaida mai martaba a bauchi" Abuturrab bai samu courage din ce masu komai ba, but he is boiling inside, dama taimako na iya xama fitina da tashin hankali haka bai sani ba??? Alhaji Ibrahim yace "Sai a kira Hajiya Hauwa ita ma aji ta bakinta tunda tana da right a kansa ko?" Abba ya dau waya ya kira Ummi, har da Aunty, Abuturrab ya ji dadi da Abba ya kira har Aunty don yasan she will stand for him, ba a dau lkci ba suka shigo parlon, duk suka yi ma 'yan uwan mijin nasu sannu da xama don tun xuwansu gidan suka gaisa, Alhaji Lawal ne yayi masu bayanin shawaran da suka yanke, Ummi dai ta kasa cewa komai, ita babban tashin hankalinta asalin yarinyar nan ba wai tana kin auren bane, ba a san wacece ita ba gashi yace uwarta da ubanta sun rasu sai kishiyar uwar, Aunty ta mike tana girgixa kai cikin tashin hankali tace "Haba fisabilillah, an ta6a aure dole ne? Tunda yace bai so, yayi auren nan ne kawai don taimako to a barsa ya datse wannan kaddararren auren mana, ai ya gama taimakon da yayi niyya, to meye kuma xa ayi ta cusa masa yarinya kamar ku ka aura masa ita, wannan ai kamar neman suna ne ku ke yi, banda haka wllh ko mahaukaci baxai amince da irin wannan auren ba, yarinyar da bata da asali ku ke burin d'an ku ya xauna da?" Alhaji Ibrahim yace "Ke kinje kinyi bincike kinga bata da asali Hafsah?" A fusace tace "Banda yanxu da na kawo maganan asalin ai babu wanda ya damu da hakan, haka kawai xaku yi ma yaro dole kuce sai ya xauna da yarinya yana ce maku baya so?" Alhaji Lawal na kallonta da kyau yace "Tunda ni ko d'an uwana ko Ibrahim babu wanda ya ja Abuturrab ya kai sa aka daura masa aure he just have to dance to his music, ko yaki ko ya so haka xai hakura ya xauna da yarinyar, mu ba kananun mutane bane, yanda bai yi shawara da mu ba yaje yayi abu gaban kansa bai isa yace yanxu ma xai juya mu ba, Allah ya basu xaman lafiya" Abba ya gyada kai cikin gamsuwa, Aunty na masu wani kallo gaba daya tace "Ai ko baxan ta6a xuba ido Abuturrab ya cutu ba in dai ina numfashi..." Daga haka ta fice daga parlon fuuu, Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh Allah yayi abinda ya fi alkhairi, ya sa mu dace" Alhaji Lawal yace "Ameen Hauwa" ta mike ta fita parlon ita ma, Abuturrab dai kansa na kasa, Abba na kallonsa da kyau yace "Kafin gobe kayi duk abinda xaka yi a gidan nan ka tare da matarka, kamar yanda Alhaji Lawal ya fada maka, idan an kwana biyu kuma ka kai ta ku gaisa da mai martaba" Still Abuturrab ya kasa cewa komai, sai da suka yi masa ixinin fita sannan ya mike ya fita xuciyarsa na tafarfasa, Alhaji Lawal yace "This should serve as a lesson for him, next time baxai sake yin abu gaban kansa ba" A bedroom dinsa ya tadda Aunty tana ta jiransa tana girgixa kafa, a sanyaye yake kallonta, Tace "What next now?" A hankali yace "I don't really know Aunty, but ni nasan baxan yi rayuwa da ita matsayin matata ba wllh" Aunty tace "Toh dama ina hakan xai yiwu, a ina xaka xauna da ita bayan ga Aneesah, uban me xaka ci da ita?? kuma idan ka saketa sani xa su yi?" Ya girgixa kai yace "That's what i have in mind Aunty, xan saketa babu wanda xai san hakan sai ke a gidan nan, quite alright xan tare da ita gobe din amma ba matsayin matata ba wllh" Aunty tace "Ai xaman naku ne bana so kwata kwataaa Abuturrab" Yace "Aunty a hankali ake bin komai" Tace "Toh da dai ya fi, don wllh abun dariya xaka xama gun colleagues dinka da yan uwanka, wa ka ta6a jin yayi irin wannan auren? Auren ma na yar talaka" A sanyaye yace "Na sani Aunty" Ta nufi kofa tace "Ba dai tarewa suke so ba, xaka tare din da ita sannan ni xan san abun yi" Daga haka ta fice a fusace, ko ba komai Abuturrab na samun relieve tunda akwai warce ke supporting dinsa dai. Daren ranan Umma ta kirasa yana kwance sai tunane tunane yake yana imagine yanda lkci daya Jiddah ta shigo rayuwarsa tana neman tarwatse masa farin cikinsa da kwanciyar hankali, a hankali ya dau wayar ya kai kunne bayan ya daga, cikin sanyin murya Umma tace "Kana ji na Aliyu?" Yace "Ina ji Umma" Tace "Kayi hakuri ka bi abinda iyayenka suke so sai kaga haske sosai a lamarinka, Yaya ta kirani ta min bayanin komai, ka janye batun saki, kaga dai yau jiddah kwananta uku ko sama da haka a gidan nan, amma har yanxu ban ga aibun yarinyar nan ba wllh Aliyu, gata da hankali da nutsuwa da sanin ya kamata ga uwa uba kawaici da hakuri, baxa kuma a dau lkci ba xata waye don na lura tana da kwakwalwa, taka kaddarar ce a haka ka amsheta hannu biyu Aliyu, kada ka mance Allah ne ya tsaro maku hakan kayi hakuri ka yarda da kaddara my son, duk sanda xaka koma wajen aiki sai ka dinga kawo min ita nan ina gwada mata abubuwa, daga nan din ta dinga xuwa boko da islamiyya, wllh lkci daya xata dawo dai dai taste dinka, nasan damuwarka kenan, in sha Allah xaka yi mamakin wayewar da Jiddah xata yi" Abuturrab yaji baci ransa kawai yake da wannan shawaran da ake basa, ya ma rasa abinda xai ce mata, how on earth suke tunanin xai iya rayuwa da yarinyar nan matsayin mata idan ba cutarsa suke son yi ba, ina duk burinsa na auren wayayyiyar mace me tsafta 100%, ji yayi kamar ya fara mata kuka wannan wacce irin kaddara ce haka ake forcing dinsa ya amsa, a ransa yace no way sai dai duk suyi hakuri, he just have to disappoint them because no amount of their sugar quinted mouth will convince him to live with that girl as wife, he will only live with her as a guardian.... Jin shirun yayi yawa Umma tace "Are u there son?" Ya runtse ido yana jin ransa na dada baci, cikin dakewa yace "Ina ji Umma, nagode Allah ya kara girma" Tayi murmushi tace "Ameen my son, Yaya tace min Abbanka yace ku tare gobe ko?" Cijen lips dinsa yayi yana jin wani mugun takaici, amma ya daure yace "Ehh haka ne" Tace "Toh Allah ya kai mu goben lafiya son, may Allah reward u abundantly for this deed" Ya bude idonsa da ya kada sosai.... forcing his self yace "Ameen" Sallama suka yi ya jefar da wayar kan gado xuciyarsa na tafarfasa ya mike xaune ya rike kansa. Washegari Saturday Umma na xaune dakinta tana kallon Jiddah dake juya kayan hannunta ta kasa sawa, jira take ta sa kayan ta gyara mata gashinta da ta sa ta wanke, murmushi Umma tayi da ta lura kunya ce yasa take hakan, sabon kaya ne da ta dinka ma Ramlah, sae ya kasance Ramla bata xo gidan ba har sannan shine ta ba Jiddan ta sa, mikewa tayi ta fita dakin, Jiddah ta bi ta da kallon gefen ido, sae a sannan ta fara sa kayan da sauri, wani kunya na musamman Allah yayi mata ita kam, komai da Umma ta bata ta saka sabo ne, sosai riga da skirt din ya amsheta kamar don ita aka dinka, kallon kanta ta dinga yi a madubin dakin tunda take iyakar atamfar da ta ta6a sa wa na dubu biyu ce, lkcn ko Ahmad ya kawo mata atamfa me tsada sae Hansae ta amshe ta siya mata roba roba ko half cotton, yau kam ga tsadadden atamfa ta saka duk da bata san me tsadan bane ba ma, bayan wani lkci Umma ta dawo dakin, sosai hankalinta ya kwanta ganin powder kawai jiddah ta shafa a fuska sai kwalli, ta bar mata har kayan kwalliya kawai don taga irin kwalliyan da xata yi sae gashi alama ya nuna iyakar kwalliyarta kenan ba irin na yan kauye take yi ba a lafta ja gira da jan baki, ta madubi take ta kallon jiddah da ta kasa kallonta, Jikin Umma yayi sanyi ganin irin kyan Jiddah, wai ma tun bata waye ba kenan, kuma jikinta bai fara samun hutu yanda ya kamata ba, ae balarabiyan Africa xa ayi a nan, a hankali Jiddah ta juyo tana kallon Umma, Umma ta sakar mata lallausan murmushi tace "Kinyi kyau my daughter" Jiddah tayi murmushin karfin hali, Umma ta xauna tace "Taho ki xauna in gyara maki gashin" Jiddah ta karasa ta xauna ta janye hulan Siyama dake kanta, Umma tace "Idan kin wanke gashi bari ake ya bushe kafin a sa hula kin ji?" Kai kawai Jiddah ta gyada mata, Unma ta fara taje mata dogon gashin nata, murmushi Umma tayi ganin tsayin gashin Jiddah a ranta kuwa tunani take ko ruwa biyu ce dai ita, sosai gashinta ke da kyau da tsayi sai dai babu gyara, Umma ta xuba mata man kai me yawa a gashin da ya dinga sheki da kamshi sannan ta yi mata parking da ribbon, mikewa Jiddah tayi tace "Nagode" Umma tace "Ki daura dankwalin yanxu" Jiddah ta dau dankwalin amma ta kasa daurawa, Siyama Umma ta kira tayi mata daurin, Siyama sae murmushi take tace "Kinyi kyau" xuwa yanxu har Maman Abdallah tasan matsayin jiddah a gidan, sae kusan karfe sha daya Umma ta bar gidan xuwa gidan yayarta da Jiddah, well ironed Hijab ne nude colour har kasa jikin Jiddah, kasancewar akwai kalan a jikin atamfar jikinta, sanyayyen kyau tayi, Hijab din yayi matukar amsarta, Driver ne ya kai su gidan don Ahmad kin amincewa yyi he knows definitely Abuturrab will be mad at him wato da shi xa a kai masa mata...... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 Umma ta sauka motar bayan drivernta yayi parking, Jiddah ma ta sauka tana kallon babban gidan, Umma ta kalli driver tace "Ka je kawai idan xan dawo anjima xan kiraka..." Cike da ladabi yace "Toh Hajiya" ta kalli Jiddah tace "Mu je" Bin bayanta Jiddah tayi tana tafiya a hankali har suka isa main parlor din gidan, kasancewar ranan asabar ne su Ramlah duk sun tafi islamiyya, Mai aiki ce kadai parlon tana aikace aikace, ban da kamshi babu abinda ke tashi parlon, mai aikin ta gaida Umma da ladabi, Umma ta amsa da fara'a tana mata sannu da aiki sannan ta kalli Jiddah tace "Toh xauna Jiddah" Xata xauna kasa Umma tace "Aa tashi ki hau kujera" Mikewa tayi ta xauna saman kujeran Umma ta nufi bangaren yayarta, sai a sannan Jiddah ta gaida mai aikin, matar ta amsa mata da murmushi tana ci gaba da abinda take, Muryar Abuturrab Jiddah ta ji ta d'an saci kallon gefenta amma bata gansa ba, slowly yake tahowa waya kare kunnensa yana waya tare da wani colleague dinsa da ya kirasa don jin ya jikinsa, murmushi Abuturrab yyi yace "Wato the sky misses me, not my co pilots" Murmushin kawai yake, daga karshe suka yi sallama da Captain Ishaq ya katse wayar ya nufi kitchen, 3 quarter ne jikinsa da farin T shirt, Mai aikin gidan Naja'at ta d'an risina ta gaishesa with respect ya amsa without looking at her, Jiddah ta bi sa da ido, har xai shiga kitchen ya juya coz he saw someone sitting amma bai kalli ko waye ba, suka hada ido, da farko bai ganeta ba sai da ya tsura mata ido, ita dai tayi kasa da nata idanuwan tace "Ina kwana" daga sama har kasa yake kallonta, Naja'at tace "Tana gaisuwa ranka shi dade" Juyawa yayi ya shige kitchen abun sa, Naja'at ta sunkuyar da kai sanin kadan daga abinda xai iya aika kenan, can ta d'an yi murmushi tana kallon Jiddah tace "Ina jin bai ji ba" Jiddah tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba, Umma ta shigo parlon tare da Ummi, Ummi na kallon Jiddah tace "Sannu da xuwa" Jiddah ta gaisheta da ladabi, Ummi ta amsa da d'an murmushi fuskarta, Ummi na kallon Naja'at tace "Tafi dakin Hajiya Hafsah ta xo su gaisa da bakuwa" Naja'at tace "Toh Hajiya" daga haka ta wuce da sauri, Ummi ta xauna Umma ma ta xauna, gaba daya Jiddah sae taji ta kasa sakin jiki, duk ta takura, Ummi tace "Ya kika kara ji da jiki?" A hankali Jiddah tace "Alhmdlh" Abuturrab ya fito daga kitchen rike da cup din shayi yana juyawa da cokali, Umma ta dinga kallonsa, sannu da xuwa kawai yayi mata ya nufi dakinsa ya ajiye cup din shayin, ba a dau lkci ba sai gashi ya fito, ya karaso cikin parlon ya xauna yace "Ina kwana Umma" Da murmushi tace "Lafiya lau Abuturrab, ka tashi lfya?" Yace "Alhmdlh" Umma ta kalli Jiddah tace "Kun gaisa kuwa" Jiddah na kallonsa tace "Ina kwana" Ba tare da ya kalleta ba yace "Lafiya lau" Ummi dai kallonsu kawai take, Aunty ta shigo parlon ganin Umma tace "A'a Sannu da xuwa Hajiya Ramlah" Umma na murmushi tace "Yauwa, mun same ku lfya?" Aunty tace "Alhmdlh wllh" Aunty na kallon Jiddah tace "Sannu yan mata..." Jiddah ta gaisheta tana kallont, Aunty ta amsa ta nemi waje ta xauna, Ummi na kallon Abuturrab tace "Sai ka kai ta parlon Abbanku su gaisa tunda Kawunnanka na ciki" Abuturrab mood dinsa ya sauya lkci daya, Aunty dai sae murmushi take a xatonta ko 'yar uwarsu ce Jiddah warce bata sani ba, ganinta fara sosai kamarsu Ummin, Mikewa Abuturrab yyi, Umma na kallon Jiddah tace "Tashi ki bi sa" Ta mike a hankali ta bi bayansa, Ummi ta bi su da kallo, ba karamin kyau hijab din yyi mata ba har kasa kuma yake ja, Wani boyayyen ajiyar xuciya ta sauke, Aunty na gyara daurin dankwalinta tace "Bakuwa aka yi, kamar yar uwarku naganta ita ma fara, amma ban santa ba" Ummi na kallon Aunty tace "Ita ce yarinyar da yaje ya aura ae" Da sauri Aunty ta bi Jiddah da kallo idanuwanta kamar xa su fito, Daga Umma har Ummi kallonta suke, da wani confusion tace "Ita ce yar hayin??" Umma tace "Ita ce fa" Aunty ta hade rai lkci daya, can ta girgixa kai tace "Toh meye fa'idar kawota nan din tunda dai sakinta xai yi, haba ni dai ina ta kallonta ganin halin gidadanci a tare da ita, to yanxu meye amfanin xuwa da ita har ace taje ta gaida kawunnansa??" Wani kallo Umma tayi mata ta dauke kai, Ummi dai bata ce komai ba, Aunty ta ja wani tsaki ta mike ta fice daga parlon. Da sallama Abuturrab ya shiga parlon Abbansa Jiddah na biye da shi, Abba na xaune tare da yayansa da kaninsa, Abuturrab ya xauna kasa ya sunkuyar da kai, d'an nesa da shi ta xauna ta takure cikin Hijab, cikin sanyin murya ya gaishesu gaba daya, ko wannensu ya amsa mata da fara'a, Alhaji Lawal na kallon Abuturrab yace "Ita ce?" Abuturrab yyi karfin halin cewa "Ehh" Duk suka amsa da maa sha Allah, Ita dai Jiddah kanta na kasa, Abba yace "And there is nothing wrong with her, Allah ubangiji ya baku xaman lafiya" Sae a sannan Jiddah ta dago tana kallon Abba, Abuturrab dae ya kasa dago kansa, nasiha dattijan suka shiga yi masu a tare, Jiddah dai sae bin su take da kallon don gaba daya bata gane inda suka dosa ba, a xatonta wanda aka ma aure ake yi ma irin wannan maganganun da suke mata, ya xa ayi ta bi shi kamar yanda suke cewa, tayi masa biyayya sannan tayi hakuri, Abuturrab dai ya ki dago kansa, Sun fi minti talatin suna abu daya daga karshe suka masu addu'a da fatan Allah ya kade shaidan a xamansu, A hankali Abuturrab ya dago yace "Ameen nagode Abba" Kudi ko wannensu ya ciro ya mika mata ta ki amsa tana kallonsu duk kana ganinta kasan she is confused, Abuturrab ya daga kai ya kalleta, can ya karasa ya amsa kudaden, Uncles din nasa suka ce ya siya mata duk abinda take so, ya amsa masu da in sha Allah, Abba yace "Yau din xa ku wuce can gidan naka, amma kafin nan ka kira mai martaba" Kai kawai Abuturrab ya gyada masa a hankali, sannan ya mike yana kallon jiddah, k'in tashi tayi, Alhaji Ibrahim ya mata murmushi yace "Tashi ku je, Allah yayi maki albarka" Mikewa tayi, Alhaji Lawal yace "Ya sunan nata?" Ta sunkuyar da kanta Abuturrab ya d'an fara kame kame yace "Ummi ce..." Abba ya d'an yi murmushi yace "Hauwa sunanta" Duk suka amsa da maa sha Allah, Alhaji Lawal yace "Baki da matsala a rayuwa idan kika yi halin me wannan sunan ta gidan nan, A very simple life" murmushi kawai Abba yayi, Abuturrab ya nufi kofa Jiddah ta juya ta bi bayansa, sai da suka fita ya kulle kofar yana mata wani irin kallo yace "Ke wace irin dakikiya ce ana maki magana kiyi ta kallon mutane kamar wawuya kiyi shiru..." Kallonsa kawai take da manyan idanuwanta ko kiftawa babu, ya nuna mata parlon fuska daure yace "Koma kiyi masu godiya ko ajiya kika basu kudin da suka baki?" Ba musu ta juya ta bude kofar ta shiga parlon, duk kallonta su Abba suka tsaya yi, ta tsugunna hawaye har ya kawo idonta cikin sanyin murya tace "Abba nagode Allah ya saka da alkhairi" Duk suka amsa mata da Ameen, suka kara sa mata albarka sannan Alhaji Lawal ya umarceta da ta tashi ta wuce, mikewa tayi ta nufi kofa ta bude ta fita ta rufe masu kofar, tsaye ta tadda Abuturrab bakin kofar yana jiranta, ta sunkuyar da kanta, ya fara tafiya, bin bayansa tayi tana tafiya a hankali, babu kowa parlon, ganin xai hau sama ta nemi waje parlon ta xauna, kamar ance ya juya ya ganta ta xauna a parlor, hade rai yayi sosai yana kallonta, ta mike tsaye ita ma tana kallonsa, yace "Xo ki wuce" Ta nufesa gabanta na faduwa, sai da yaga ta kusa iso shi sannan ya fara tafiya, tana biye da shi har suka isa dakin Aunty, Kulle kofar yayi bayan Jiddah ta shigo, Aunty ta tamke fuska ganinta, ya xauna kan stool din gaban mirror yana kallon Aunty a hankali yace "The lady..." Aunty ta wani ta6e baki hade da tafe hannu tana kallon Jiddah, lkci daya ta girgixa kai tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wllh ka cuci kanka Aliyu, me xaka yi da bagidajiya domin Allah, sai ku ce sai kunyi taimako, taimakon da yanxu idan mutum yayi yake xame masa sharri, to dai ga naka nan ya xamar maka sharri babba, da ajinka, da kyanka, da ilimin ka da kudinka, ina xaka kai wannan fisabilillah? Ina kai ina wannan Aliyu? Wllh wllh banyi baccin kirki a kan lamarin nan ba jiya" Sunkuyar da kai Jiddah tayi har lkcn ta kasa gane kan komai amma duk jikinta yayi sanyi har hawaye ya kawo idonta don saurin kukanta, Abuturrab ya lumshe ido, bai ji dadin maganganun Aunty a lkcn ba, he wish she was even speaking just English at that moment, ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yace "U need not to worry Aunty as soon as possible i will find a solution, I've told u everything, you just have to trust me aunt" Yana fadin haka ya mike yana kallon Jiddah kafin yace komai ta juya ta bude kofar ta fita daga dakin, Aunty taji har ranta ta tsani Jiddah, and she will do everything Abuturrab ya datse auren nan balle ma tasan tunda yace xai saketa xai saketa din... Suna fitowa Abuturrab ya fara tafiya, bin bayansa Jiddah tayi a hankali tace "Umma fa?" Ya juyo ya kalleta bai bata amsa ba ya ci gaba da tafiya sai ga Umman ta fito dakin Ummi, ganinsu tace "Yauwa dubawa xanyi dama ko kun fito" Jiddah ta nufeta, Umma tace "To mu shiga ciki" Umma na juyawa Jiddah ta kalli Abuturrab, hararanta yyi ta bi bayan Umma suka shiga parlon Ummi, jingina yyi da bango ya rufe idanuwansa, idan ba avoiding yarinyar nan xai dinga yi ba ko da suna xaune gida dayan ae wataran bubbugeta xai yi a banxa, she is just too dopey for his liking, kwafa yayi ya bude ido ya bar wajen.... Har bayan magrib Jiddah na part din Ummi, a lkcn kuma Umma ta shirya xata wuce don har ta kira Driver, Suna bedroom tare da 'yar uwarta Jiddah kuma na parlor tana kallon tv dake ta aiki, duk ta kagu Umma tace mata su tashi su wuce, duk yan matan gidan kowa ya shigo kallon sama har kasa yake mata sannan ya fita, Ramlah ce kawai ta tsaya suka gaisa, Ummi na kallon Umma tace "Toh ki kara mata fada ni dai kinsan babu abinda xan ce, har yanxu Ramlah i am finding it hard to believe Aliyu is married, ganin abun nake kamar mafarki, i still don't have the courage to start telling this to relatives and frnds, to me ma xance masu Ramlah? Waliman da Uban nasa yace ayi yace baxai yi ba shi, nima dama I'm not in support of that" Umma ta kwantar da murya tace "Yaya kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki, in sha Allah xa mu yi alfahari da wannan auren gaba dayanmu, duk mu yi hakuri mu bar ma Allah komai, Ae Allah ya ga xuciyar mu gaba daya, bama nufin d'an kowa da sharri mu bi su da addu'a kawai" A sanyaye Ummi tace "Ikon Allah, idan wani yace min haka xae ta6a faruwa a household dina baxan yadda ba wllh, duk burin da aka ci a kan bikinsa a haka ya tarwatse??" Umma tace "Haka Allah ya so, ynxu duk abinda Allah ya hore maki sae kiyi mata yaya kinga marainiya ce, nima xan yi nawa, amma kar ki manta da kayan Ramlan don bata da wanda xata sa idan sun tafi yau din" Ummi bata sake cewa komai ba duk jikinta yayi sanyi sosai, Umma tace "Xan sake yi mata nasiha yanxu kafin driver din ya karaso" Daga haka ta fita Ummi ta bi ta da kallo ta girgixa kai tace "Ikon Allah, so all this isn't a dream" Jiddah na ganin Umma hankalinta ya kwanta a tunaninta xa su wuce, ta mike Umma tace "A'a xauna" Xaunawa tayi tana kallon Umma, Umma tace "Abuturrab ae ya maki bayanin komai jiya ko?" Kallonta kawai Jiddah ke yi, can tace "Na me Umma?" Umma tace "Auren ku" a sanyaye Jiddah tace "Ehh yace min an daura min aure da wani, amma wanin xae sakeni sae in dawo wajenki kuma in xauna" Innocently ta fadi hakan tana kallon Umma, Umma ta d'an yi murmushi, lkci daya taji tausayinta ya rufeta, can tace "Bai gaya maki da wanda aka daura maki auren ba?" Jiddah ta girgixa kai tace "Aa bai gaya min ba" Shiru Umma tayi tana tunanin ya kamata tayi breaking mata news din ma kuwa, ajiyar xuciya ta sauke sannan tace "Toh shkkn, d'an xaman da muka yi dake Jiddah naga kina da hakuri da kawaici, sannan kina da hankali, to ki ci gaba a haka kinji, me hakuri shi ke cin riban xaman duniya sannan ki xama me rikon addininki sallah a kan lkci, tsaftar jikin ki, duk ae na nuna maki yanda xa ki dinga yi a gida, kinsan daga inda kika fito Jiddah, ki rike maraicinki, kiyi hakuri a duk halin da kika tsinci kanki" Jiddah ta gyada mata kai lkci daya hawaye ya kawo idonta, abinda Umma bata so kenan duk mutum xai yi hawaye gabanta sae taji xuciyarta ya karaya, tana da rauni sosai, hakan yasa ta mike tace "Drivern ma na kirana ya iso ina jin" Jiddah ta mike da sauri cikin rawan murya tace "Umma ba da ni xa ki koma ba?" Umma ta kasa kallonta tace "Abuturrab xai dawo dake, ae baku yi sallama da Abba ba, Abban na dawowa bayan kunyi sallama xai dawo min dake" Umma na fadin haka ta shiga daki gun yayarta, Jiddah ta bi ta da kallo hawaye me xafi na sauka idonta, ba a dau lkci ba Umma ta fito, murmushi tayi tace "Toh idan baxa ki daina kukan nan ba sae ince ya bar ki nan ki kwana biyu kafin ya dawo min dake" Da sauri ta share hawayenta, Umma tace "Toh ko ke fa, yanxu Abban xae shigo sae Abuturrab din ya dawo dake a motarsa" Gyada mata kai Jiddah tayi, Umma tace "Sae kun karaso" Daga haka ta fita, Jiddah ta koma kasa ta xauna a hankali wasu sabbin hawayen na sauka idonta.... Karfe takwas da few minutes Abuturrab ya shigo parlon, tun tafiyar Umma Jiddah ke ta xaune parlon ita kadai, Ummi kuma na bedroom dinta, kallo daya yayi ma Jiddah ya karasa dakin Umminsa, Jiddah ta shiga saka hannun hijab dinta hoping ynxu xai ce mata ta tashi ya maidata gidan Umma, Abuturrab ya karasa gun Umminsa dake xaune ita kadai dakin, kasa kallonta yayi kansa a kasa yace "Ummi xan wuce" Tace "Allah ya kiyaye" Bai iya yace komai ba, Ummi ta ci gaba da duba littafin hannunta, a hankali yace "Sae da safe" Tace "Allah ya tashemu lafiya, ga akwatin kar ka manta" Ya kalli trolley din ya karasa ya daga ya juya ya fita dakin, yana shigowa parlon ya kalli Jiddah dake jiran taji yace tashi mu tafi yace "Ki shiga kiyi ma Ummi sai da safe" Ba musu ta mike ta shiga dakin Ummi, ta sunkuyar da kai tace "Ummi sae da safe" Ummi ta kalleta tace "Allah ya tashemu lafiya" Juyawa Jiddah tayi ta fita, har sannan Abuturrab na tsaye yana jiran fitowarta, ganin ta fito ya fara tafiya, Bin bayansa tayi har suka fita, ko da wasa bai yi tunanin shiga bangaren stepmom dinsa ba sanin wani maganan da xai bata masa rai xata yi, yana fita su Safiyya da Aisha dake xaune parlor suka dinga kallon jiddah, kofa ya nufa duk suka yi masa sai da safe bbu warce ya tanka cikinsu, Basu ce ma Jiddah ba ita ma bata ce masu ba, a tare duk suka ta6a baki banda Ramlah da ta bi Jiddah da kallo, a booth ya saka trolley din, ya bude driver seat ya shiga ya tada motar, Jiddah dai na tsaye bata ma san inda xata shiga a motar ba, ya wani hade rai ya sauke glass din yana kallonta yace "Rokanki xan yi ki shigo?" A hankali tace "Toh ban san inda xan shiga ba" irin kallon da ya dinga yi mata ya sa ta bude back seat ta shiga ta rufe motar, gaba daya sae taji ta tsorata da shi, amma lkcn da yake xuwa can gidansu ae baya hararanta ko yayi mata ihu haka, sunkuyar da kanta tayi har hawaye ya kawo idonta, yayi horn mai gadi ya bude masa gate ya fita gidan, driving kawai yake amma gaba daya yyi nisa tunanin da yake, wai shi yau xai tafi gidansa da yaki budewa wishing to go in with his wife first, sai gashi da wannan yarinyar xai je, wannan yarinyar fa, tunanin hakan yasa yaji kamar ba a ta6a abinda ya cucesa a rayuwa irin wannan lamarin ba, ya runtse ido ya bude still driving, ae idan ya kwana ma da auren yarinyar nan yau yana da ra'ayin rayuwa tare da ita kenan, Ahmad ne ke ta kiransa tun fitowarsa amma yaki daga wayan haushin kowa kawai yake ji shi yanxu, tafiyar minti talatin da biyar yayi ya isa gidansa dake U dosa, dai dai gate din gidan ya tsaya ya dau makullin gate din ya karasa ya bude gate din sannan ya dawo ya shigar da motar compound din gidan, Jiddah dai sai bin gidan take da kallo don bai yi kama da gidansu Umma ba, sauka yyi motar bayan ya kashe ya karasa ya rufe gate din ya cire makullin ya koma gun motar, ya bude booth ya sauke trolley din, har sannan Jiddah ta ki sauka daga motar, bayan ya rufe booth din ya bude side dinta yana kallonta fuskarsa ba fara'a, sauka tayi tana sake bin gidan da kallo ta kara tabbatarwa ba gidan bane duk da shi ma din gidan sama ne, ta marairaice tana kallonsa tace "Ae ba nan bane gidan" Wani kallo yyi mata ya ja trolley din, bin bayansa tayi da sauri a d'an tsorace tace "Gidan Umman fa??" Ganin har ya shiga parlon ta shiga ita ma ya kunna wuta da ya haska ko ina na parlon, komai na parlon sabo ne, ba kuma karamin haduwa parlon yayi ba, ta dinga bin babban parlon da kallo kamar idanuwanta xa su fito, rufe kofar yayi yasa makulli, sae a sannan ta fashe da kuka a hankali tace "Gidan Umma ae aka ce ka kai ni fa" Biron da ya saka a aljihunsa tun daga gida ya ciro sannan ya wuce sama sanin baxai rasa takarda a bedroom dinsa ba, bin bayansa jiddah tayi hawaye na xuba idonta, ganin hanyar da ya bi bayan ya hau saman ta bi da sauri ita ma don tsoron gidan take, wani kofar da taga ya shiga ta bude taga wani babban parlon hadadde, tsaye tayi bakin kofar gabanta na faduwa, bayan few seconds sae gashi ya fito rike da farar takarda...... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Do justice to ur self by subscribing before reading.... Thank you Jiddah dai na tsaye bakin kofar parlon tana share hawayen da ya ki tsaya mata, saman kujera Abuturrab ya xauna bayan ya ja center table din parlon right in front of him, ya daura takardan a kai ba tare da ya kalleta ba, babu yabo babu fallasa yace "Shigo ciki..." A hankali ta karaso cikin parlon tana share idonta, ta rakube jikin one sitter din parlon ta tsaya tana kallonsa, daga kai yayi ya kalleta ya nuna mata kujeran alamar ta xauna, ta xamo kasa ta xauna, bayan few seconds, speaking calmly yace "Shekaranjiya na gaya maki an daura maki aure, right?" Jin tayi shiru ya ajiye biron hannunsa yace "Tambayarki nake" Ta gyada masa kai tana kallonsa, yace "Kuma baki san da wanda aka daura maki auren ba ai koh" Nan ma ta gyada masa kai, a takaice yace "Ohkk... Da ni aka daura auren" Kallonsa kawai Jiddah take kamar bata gane abinda yake nufi ba, not minding that ya langwabar da kai yace "Shi yasa kika ji a can gida suna maki nasiha" a hankali Jiddah ta sauke idonta kasa, taji xuciyarta na bugawa da sauri da sauri, yace "Na aure ki ne kawai don ceto rayuwarki daga matar mahaifin ki, na aure ki ne saboda naga xa a cuce ki xa a lalata maki rayuwa, na aureki ba don naje da niyyar yin hakan ba, don haka bani da xabi da ya wuce in sakeki, wannan sakin kuma da xan maki tsakanina dake ne kawai...." Da duk idanuwanta take kallonsa jin furucinsa na karshe, cikin sanyin murya tace "Xaka sakeni?" Yace "Ehh xan sake ki" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, shi ma shirun yyi yana kallon hotonsa dake parlon yana sanye da wear dinsa na pilot, muryarta ya ji tace "Idan ka sakeni sai in koma wajensu Umma kenan?" Ya girgixa kai, cikin nutsuwa yace "Aa a nan gidan xaki xauna, kamar yanda na fada maki sakin nan xai kasance sirri tsakaninmu, babu wani da xai san na sake ki...." Tayi shiru bayan few seconds tace "Toh ae ni ba muharramarka bace da xa mu xauna gida daya bayan ka sakeni...." Kallonta ya dinga yi da mamaki jin furucinta ba don shi ta fada ma ba idan wani yace masa ta fadi hakan baxai ta6a yarda ba, can yace "A ina kika san wannan?" Tana wasa da fingers dinta ba tare da ta kallesa ba tace "Lokacin da nake xuwa islamiyya" Surprisingly yake ta kallonta, can yace "Ohh i see... amma kuma basu koyar dake hukuncin wanda ya kashe kansa ba kuma?" Kallonsa Jiddah tayi amma taki cewa komai, ya jefa mata wani shegen kallon da yasa ta koma baya a hankali, idonta har ya fara kawo ruwa, yace "Ke a tunaninki rashin sakin ki kadai ne xai sa mu xauna gida daya kenan, idan ban sakeki ba shine kike muharramata koh?" Shiru tayi bata ce komai ba yace "Bude baki ki bani amsa malama" A hankali tace "Nima ban sani ba" Wani kallo ya sake jefa mata ta sunkuyar da kanta, yace "Xan sakeki kuma xa mu xauna gidan nan tare, don mun xauna gida daya tare ba yana nufin ganina xaki dinga yi ko ganinki xan dinga yi ba, kinsan matsayinki gidan nan, nima haka, balle ma ni daga ranan lahadi da yamma xuwa juma'ah ina wajen aiki, kina tunanin sati da lahadin ma idan na dawo ganina xa ki dinga yi??" Ita dai bata ce masa komai ba, yace "Don haka ki cire tunanin yan kauye dake ranki yanxu, komai kike bukata xan baki waya da xa ki dinga kirana, sannan idan ba abu me ma'ana ba dama kar ki kuskura ki kirani, nan da wani lkci xaki fa islamiyya da boko...." Sai a sannan ta daga kai ta kallesa cikin sanyin murya tace "Toh nagode Allah ya saka da alkhairi" Bai tanka ta ba ya soma rubutu a takardan gabansa, kallonsa kawai Jiddah take babu ko kiftawa, yayi rubutu wanda iyakarsa layi biyu xuwa uku sannan ya dago kai yana kallonta, da sauri ta sauke idonta kasa, yace "kin iya karatu?" A hankali ta girgixa masa kai, sai kuma ta gyada masa kai alamar xata iya, ya mika mata takardan yana kallonta, ta mike ta karasa ta d'an risina ta amsa takardan tana kallo, bayan few seconds ya mika mata hannu alamar ta basa takardan, ta dago kai, hawaye ya gani makale idonta ta mika masa takardan ya amsa sannan ya linke without looking at her yace "Wannan tsakaninmu ne da ke, har abada bance ki sanar ma kowa ba idan ba haka ba......" Daure fuska yyi yana kallonta bayan ya fadi haka, ta gyada masa kai a hankali hawayen idonta ya silalo, mikewa yayi ya linke takardan tsaf sannan ya shiga bedroom dinsa ta bi sa da kallo, ba a dau lkci ba ya fito, kofar fita ya nufa yace "Mu je in nuna maki dakin da xaki xauna" Juyawa tayi cikin sanyin jiki ta bi bayansa, bangaren suka bari gaba daya, ya bude wani daki wanda akwai komai a ciki yana kallonta yace "Ga dakin ki nan, kinga can bangaren nawa ko by mistake, kinsan me nake nufi da by mistake?" Ta girgixa masa kai alamar A'a, yace "Ohk, ina nufin ko bisa kuskure kada ki kai kafarki can, iyakar ki nan dakin, ko parlon kasa idan ina gari bana son kina xama, idan bana nan xaki iya xaman ki can, sai kuma kitchen, komai xan ajiye maki a ciki ki girka duk abinda kike so" Ta gyada masa kai kawai, yace "Yanxu ki tafi kasa jakar nan ki kawo dakin ki, gobe da safe xa mu fita xan siya maki duk abinda xaki bukata, sai ki xaba komai da kanki" Nan ma kai kawai ta gyada masa yace "Kin ci abinci ai a can gida?" Ta gyada masa kai nan ma, yace "Good" downstairs ya nuna mata yace "Tafi ki dauko jakanki, kayan da xaki dinga amfani dasu ne a ciki" Ba musu ta fara sauka kasa, ya bi bayanta suna shigowa parlon ya nufi kofa ya sa makulli, ta dau jakar ta koma sama, kashe wutan parlon yayi, sannan shi ma ya wuce saman, tsaye ya ganta bakin kofar dakin da ya nuna mata, a hankali tace "In shiga?" Ya daure fuska yace "Ehh" Bude kofar tayi kafin ta shiga ciki yace "Gobe karfe takwas xa ki sauko kasa" Ta gyada masa kai, sannan ta shiga dakin ta kulle, ya kashe wutan corridor din ya nufi bangarensa. Bin dakin da kallo Jiddah ta dinga yi, sai take ganin abun kamar a mafarki wai yau ita ce xata kwanta saman wannan katon gadon ita kadai, to ko dai bai ce ta kwanta ba? Kar ta kwanta kuma yace mata don me, a hankali ta kai jakar can jikin bango ta ajiye sannan ta dawo ta xauna kasa tana sake bin dakin da kallo, ta fi minti talatin xaune a kasa, can ta tuna abinda Umma tace mata duk dare kafin ta kwanta ta dinga yin wanka, mikewa tayi tana kallon jakar da yace mata kayan da xata dinga amfani da ne a ciki, ta karasa gun jakar ta kwantar sannan ta bude, tawul ta fara cin karo da sabo, ta ajiye gefe, taga sabulu da soso da Toothpaste and toothbrush, su ma ta ajiye a gefe, sannan taga sabbin undies, da turarruka da mayyuka sai kayan kwalliya, kallon kayayyakin ta dinga yi, lkci daya hawaye ya kawo idonta, xaunawa tayi nan kasa ta hade kai da gwiwa tana shessheka, gani take kamar Hansai xata xo ta haureta ko ta watsa mata ruwa sai ta farka taga duk mafarki kawai take, ta fi minti sha biyar tana kukan kafin ta dago kanta har sannan hawayen yaki tsaya mata, ta dinga share idonta daga bisanni ta mike ta cire Hijab din jikinta, kamar yanda Umma tace mata bata ajiye Hijab din haka ba sai da ta linke, sannan ta soma cire kayan jikinta, ta dau tawul din ta daura ta shiga bandaki, tun daga gidan Umma su Huraira da Maimuna sun nuna mata yanda ake amfani da komai na cikin bayi, cikin kankanin lkci kamar ana koranta tayi wanka ta fito bandakin, bayan ta gama goge jikinta ta dau lotion daya ta bude ta fara shafawa, wani doguwar riga mara nauyi duk da ba na bacci bane ta dauka ta saka, sannan ta maida komai cikin jakar ta rufe ta mayar jikin bango, darduman da ta gani ta shimfida don tayi alwala, ta gabatar da sallan isha sannan ta linke darduman da hijab din ta ajiye, komawa tayi ta rakube ta xauna a kasa, tana ta xaune tana tunani iri iri, taji bacci ya fara fixgarta, tsoron hawa saman gadon take yace tayi laifi, hakan yasa ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta kwanta nan kasan tiles ta dukunkune waje daya, nan da nan bacci ya dauketa, sai dai kafin asuba ba karamin wahalar da ita sanyi yayi ba, baccin ma bata yi me dadi ba sbda sanyi da ya isheta, a haka har aka kira sallan asuba, abun ka da wanda ya saba, tun kafin a tada sallah ta tashi ta tafi bandaki ta dauro alwala, da kyar take numfashi sbda hancinta da taji ya toshe, ga ciwo da kanta ke yi, tana xaune saman darduma bayan ta idar da sallah aka bude kofar dakin, da sauri ta juya suka yi ido hudu da shi, sanye yake da jallabiya, ta sunkuyar da kanta, ya rufe kofar ya nufi bangarensa, sai a sannan ta dago kanta jin ya rufe kofar dakin. Har gari ya waye Jiddah na xaune saman darduma sai dai fa babu abinda take, ko d'an azkar din nan babu, kawai sabo da tayi da rashin komawa baccin asuba ne, bakwai saura ta mike ta shiga bandaki ta wanke baki tayi wanka sannan ta fito, wani atamfar ta saka bayan ta shafa mai ta saka turare dai yanda ta ga su Maimuna na yi, tana ta xaune dakin lkci lkci tana duba agogon dake dakin, har taga karfe takwas yayi, mikewa tayi ta dau Hijab ta saka sannan ta nufi kofa ta bude a hankali ta fita, kamar mara gaskiya ta dinga sauka stairs din har ta iso main parlor din, karan Tv ta ji, ta leka parlon ta gansa kwance saman dogon kujera idonsa a lumshe, kasa karasawa tayi cikin parlon, ta fi minti goma a tsaye kamar munafuka, daga karshe ta juya a hankali ta koma saman, xaunawa tayi a kasa ta jinginar da kanta da gado, tana ta xaune a haka har bayan awa kusan daya taji an bude kofar dakinta, da sauri ta juya, suna hada ido ya daure fuska yace "Baki san agogo bane?" Ta kalli agogon dakin dake nuna karfe tara saura mintuna kadan, a hankali tace "Na sauko karfe takwas naga kana bacci shine na koma" da mamaki yake kallonta, can yace "To meye damuwarki da baccina ba ni nace ki sauko lkcn ba?" Ta gyada masa kai, juyawa yayi ya bar bakin kofar, ta mike tana gyara hijab din jikinta ta bi bayansa, xaune ta samesa a parlon ta karasa ta rakube kasa jikin kujera ta xauna yana kallonta daga sama har kasa yace "Babu wani Hijab din ne a jakar?" Tace "Akwai" Yace "To bana son maimaita kaya... Koma ki canxa hijab din" Mikewa tayi ta wuce sama a sanyaye, ba a dau lkci ba sai ga ta ta dawo da wani Hijab din navy blue colour, shi ma har kasa, sosai Hijab din ya haskata kasancewarta fara, ta koma inda take ta xauna ba tare da ta kallesa ba, bayan few minutes yana kallonta yace "A gidanku idan an tashi da safe ba a gaisuwa?" Ta d'an buda ido tace "Ina kwana" Bai tanka ta ba yana kallonta jin voice dinta da ya canxa yace "AC din dakin kika kunna?" Da sauri tace "Aa ai ban iya kunnawa ba" Yace "Da ruwan sanyi kika yi wanka?" Ta girgixa kai tace "Aa na xafi na tara" Yace "Kin bude windows din dakin ne?" Nan ma ta girgixa kai tace "Ban san ma ya ake budewa ba" She looks so Afraid, don with authority yake mata tambayar, bayan ya gama kallonta da kyau yace "A ina kika kwanta?" Tana jan fingers dinta a hankali tace "A kasa" Da mamaki yake kallonta, can dai yace "Saboda me?" Innocently tace "Ai baka ce in hau saman gadon ba" Dauke idonsa yayi daga kallonta, bai ma san wani reaction xai yi ba, she sounds very funny, can dai ya sake kallonta yace "To daga yau nace ki dinga hawa saman gadon, anjima da daddare xan baki bargo da xaki dinga rufa" Cikin sanyin murya tace "Toh nagode" ya nuna mata basket me dauke da breakfast da Umma ta aiko masu da shi, yace "Ga ya can ki je ki karya" Ba musu ta mike ta isa wajen, babu abinda babu wajen har cup da spoon da plate, ganin yanda take ta kallon basket din bayan ta duka a wajen yace "Ki bude dukka ki xuba abinda kike so" A hankali ta shiga bude warmers din, wainar shinkafa da lafiyayyen miyarsa na naman rago, sai fried Irish da kwai, ga kuma bread da pepper soup din hanta xalla, kallonta kawai yake, ta dau plate ta debi waina biyu xata kara daya suka hada ido, mayarwa tayi, yace "Juye dukka" Da sauri ta kallesa tace "Ya min yawa ai" Ya hade rai yace "Juye nace" Ta kalli wainar da xai kai sha uku tace "Wllh tllh baxan iya cinyewa ba" Hade rai yayi sosai yana kallonta can on a serious note yace "Bana son rantsuwa a gidana, kada ki sake" Sauke kanta tayi ta xuba wainar guda biyar sannan ta debi miya, xata mike yace "Hada shayin" Ta hada shayin ta koma can jikin kujera ta xauna, lkci lkci take satan kallonsa tana cin abincin gabanta, daga karshe ya mike ya wuce sama ganin she isn't comfortable, ta bi sa da kallo. Bayan kusan awa daya Abuturrab ya sakko rike da makullin motarsa, kananun kaya ne jikinsa as usual, Jiddah na ta xaune bayan ta gama wanke plate da cup din da ta karya a kitchen, kashe tv dake aiki yayi ya kashe fitilan parlon ba tare da ya kalleta ba ya nufi kofa yace "Ki sameni waje" Mikewa tayi ta bi bayansa, takalmanta ta gani bakin kofar fita ta saka sannan ta fita, yana tsaye waje yana jiran fitowarta, tana fitowa kuma ya kulle kofar da makulli ya nufi can gate, ya bude gate din sannan ya karasa parking lot ya bude motarsa ya shiga, slowly take tafiya har ta iso parking space din, ya gama warming motar sannan ya kalleta yace "In roke ki kafin ki shiga motar?" Bude back seat tayi ta shiga, bai dai ce mata komai ba ya fara driving ya fitar da motar kofar gida, sannan ya sauka ya kulle gidan ya koma cikin motar, Driving Abuturrab yake yana tunanin shopping mall da xa su, daga karshe ya dau hanyar ASD city mall, suna isa yayi parking ya bude motar ya sauka, Jiddah ta sauka ita ma, don yanxu kam ta iya bude mota, ganin inda ya nufa ta bi bayansa, shopping cart ya dauka tana biye da shi, wajajen turarruka ya fara nufa ya tsaya ya rungume hannu yana kallonta babu yabo babu fallasa yace "Debi turaren" tace "Ai a jakar kayan nan akwai turare hudu" Wani shegen kallo yayi mata yace "Debi turare nace my frnd" Diban turaren ta fara yi wanda wasu body sprays ne a wajen tana xubawa a cart din, takaici ya sa ya ma kasa ce mata komai, she's not even making any effort to check for the ones with better scent diba kawai take, cikin husky voice dinsa yace "koma gefe" A hankali ta ja ta tsaya a gefen tana kallonsa, gun sealed tsadaddun turarurruka ya karasa ya xabi hudu ya xuba a cart din, a takaice dai turaren da suka diba a wajen xai kai kala sha uku kamar abinda kadai ya kawosa mall din kenan, dubu dari biyu Abbansa yayi masa transfer a yau da safe yace ya siya mata duk wani abinda take so, ga wanda uncles dinsa suka bata a jiyan, gun mayyuka ya nufa next tana biye da shi tana tura cart din da ya sakar mata, wayarsa ya ciro aljihu yayi dialing number Aneesah warce har yau bata san abinda ke faruwa ba, yasab Aunty ma baxata yi gigin sanar mata ba, shi ma kuma bashi da intention din sanar mata, tana dagawa cikin cool voice dinsa yace "Aneesah wani cream kike shafawa pls?" Daga daya bangaren tace "Ohh body cream?" Yace "Yeah" fada masa tayi, ya d'an yi shiru har sai da tace "Are u there?" Yace "Yeah, amma ba na lightening bane ko?" Daga daya bangaren tayi dariya tace "To ka mance ni fara ce, lightening din me kuma my captain?" Kallon Jiddah dake tsaye ta rakube waje daya yayi, yace "ohk, haka ne" Tace "Ba na bleaching bane kamar yanda kake tunani, amma kuma me kyau ne, yana fito da ainahin complexion din mutum, sannan yana sa jiki yayi glowing, me tsada ne sosai" Abuturrab ya d'an yi murmushi yace "Ohk, text me the name now ina jira, and sorry.... Har da sabulu, infact da duk wani abinda kike amfani da shi na gyaran jiki ki turo min ta text ynxu" Tace "Uhmm my Captain lefe ka fara hadawa ne?" Bai san lkcn da ya fara murmushi ba yace "Yea, with perfumes da kike amfani da" Farin ciki ne sosai a voice dinta, tace "Alright my captain, i will now" daga haka ta katse wayar, jan cart din yayi suka tafi bangaren undies kafin Aneesah ta turo masa text din, gefe ya ja ya tsaya ya rungume hannunsa yana kallonta yace "Ko shi ma ni xan xabar maki?" Kasa kallonsa tayi wai duk kunya, ta sunkuyar da kanta inda take tsaye, yace "Heyy kina bata min lkci" A hankali ta karasa ta fara daukan panties din tana ajiyewa a cart din, ya hade rai yace "Idan kika dauki wanda suka fi karfin ki kina da wanda xaki ba ma ne?" Kasa kallonsa tayi kamar xata yi kuka, yace "Madam kina bata min lkci fa, baxa ki dinga dubawa ba...." kamar xata yi kuka tace "Ni baxan iya ba" that sounds so funny, amma ya dake yace "Baxa ki iya me ba?" Juya masa baya tayi, bai san lkcn da ya d'an yi murmushi ba, karasawa yayi ya gun undies din, daga sama har kasa ya kalleta doing survey with his eyes, ita dai ta ki juyowa, da kansa ya xabar mata undies din ko wanne dozen dozen, ya tura cart din ya bar ta wajen a tsaye, satan kallonsa tayi, sai kuma ta fara bin sa a hankali, gun nighties ya tsaya nan ma ya xabi sha biyu.... Kananun wears ma ya xabar mata isassu, ganin she is already tall, flat shoes iri iri masu kyau ya xabar mata shi ma dai kusan sha biyu, da handbags, a mall din nan atamfofi ne kawai Abuturrab bai siya mata ba, komai da mace xata bukata sai da ya siya ma Jiddah enough a lkcn, sai dai idan cart din ya cika ya ajiyesa sa can gun da xa abiya kudi ya dau wani shopping cart din, Creams da sabula da turarrukan da Aneesah ta turo masa ne karshen abinda ya duba a mall din, kala uku ya dau mata cream din da sabulu da shower gel, turarruka kuwa kala biyar kawai ya kara mata har da miski a ciki, a mall din Abuturrab yayi azahar, Jiddah dai iya gajiya ta gaji, bayan ya biya duk kudin kayan an kai masa mota ya nufi bangaren cin abinci dake cikin mall din, Jiddah dai na biye da shi, xaunawa yayi ya nuna mata table din dake opposite din wanda ya xauna yace "Can xa ki xauna" Karasawa tayi ta xauna wajen tana kallonsa, fried rice yayi ordering da kaza sai Chivita da bottle water, bayan an kawo masa abincin a gabansa ya juya ya kalleta, da sauri ta sunkuyar da kanta, yace "Me xa ki ci" Ta girgixa masa kai tace "Aa na koshi" Wani shegen kallo ya jefa mata yace "Me xa ki ci nace?" Kasa cewa komai tayi, ya kalli waitress din ya umarceta da ta kawo mata exactly abinda ta kawo masa amma takeaway xata yi, waitress din na wucewa ya soma cin abincinsa, lkci lkci Jiddah ke satan kallonsa, cikin rashin sa'a suka hada ido, da sauri ta kauda kanta, shi dai ya ci gaba da cin abincinsa, Waitress din ta kawo abincin ya amsa ya ajiye kan table dinsa, sai da ya gama cin abincin sannan ya mike ya saka sauran drink din da bottle water a ledan abincin dake kan table din, cash ya ba waitress din har xai fara tafiya ganin jiddah bata taso ba yace "In xo in daga ki ne malama" Mikewa tayi xata wuce ya nuna mata ledan yace "ohk bar masu abincin xa ki yi" bata ce komai ba ta dauki ledan ta bi bayansa, suna isa gida da kansa ya dinga kwasan kayan yana kai wa parlor har ya gama, tana tsaye kamar wawuya bakin kofa sai dai ta basa hanya, har ya gama shigar da kayan yayi xamansa a parlor yyi powering Tv, jin bai ce ta shigo ba taki shigowa parlon, bayan kusan minti sha biyar ya mike ya isa bakin kofar yace "Ke wai baki da hankali ne dama ban sani ba? Meyasa kike behaving kamar yar kauye?? Yanxu me kike yi a nan a tsaye" Kamar xata yi kuka tace "Ai baka ce in shigo ba" Ya mata wani shegen kallo yace "Get out my frnd, sai nace ki shigo, idan kina son xaman lafiyar ki a gidan nan ki daina behaving kamar wawuya" Har hawaye ya kawo idonta ta bi ta gefensa ta shiga parlon, bata san dama kayan da ta bar sa da shi yake ta kwasa tana kallonsa ba ya basa haushi, tsaye tayi parlon tana tunanin ta wuce sama ko ta tsaya, ganin kallon da yake mata ta juya da sauri ta nufi sama, yace "Dawo nan" Dawowa tayi yace "Kwashi duk kayan nan ki wuce da su sama dakin ki" Daukan ledojin ta dinga yi daya bayan daya tana kai wa dakin nata har ta gama, ta dau na karshen xata wuce ya dawo da ita ya nuna mata ledan abincin durkusawa tayi ta dauka sannan ta wuce sama yace "Idan kin je saura ki ajiye abincin ki jirani in xo ince ki ci" Bata ce komai ba a sanyaye ta wuce sama ta shiga dakin ta kulle. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Do ur self justice by subscribing before reading, Thank you!! Karfe hudu saura Abuturrab na xaune parlor wayarsa ya fara ring, kallon wayar ya dinga yi ganin Ahmad ne ke kiransa ya ki dagawa har ya katse, bayan few minutes ya ji wayar na ring kuma, dauka yayi xai yi silencing phone din ya ga Aneesah ce ke kiransa, sosai gabansa ya fadi, ya gyara xamansa da sauri yana kallon wayar har ya katse, ya lumshe ido hade da jinginar da kansa da kujera, mikewa yayi daga karshe walking slowly ya wuce sama, bude kofar dakin da Jiddah take yayi, da sauri ta dago kanta daga kan gwiwanta ta jawo ledan abincin, kallon idonta da yayi jajir sbda kuka ya tsaya yi, ta fara bude abincin ba tare da ta yarda ta sake kallonsa ba, she looks sad and scared, karasawa yyi cikin dakin ya xauna kan stool din dake gaban mirror looking at her directly, kasa kunce ledan da abincin ke ciki tayi, cikin cool voice yace "Kukan me kike?" Ta girgixa masa kai kawai wasu hawayen na taruwa idonta ba tare da ta yarda ta kallesa ba still, yace "Tambayarki nake" Nan ma ta girgixa masa kai, shiru yayi yana kallonta, ta bude ledan abinci ta ciro ta fara ci a hankali, ya mike yace "Xan tafi masallaci, kafin in dawo ki tabbatar kin gama cin abincin" Ta gyada masa kai, ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita dakin... Ko kafin ya dawo ta rufe sauran abincin da ta rage, ba cikin dadin rai ta ci abincin ba, ko rabi bata iya ci ta kai ba, lemon ma bata bude ba tunda ba iya sha tayi ba, ruwa kawai ta sha, tunani ta shiga yi ko ta kai sauran kitchen kar ya dawo kuma yayi mata ihu, a sanyaye ta mike ta dau ledan abincin ta fita, kitchen ta shiga ta fiddo takeaway din abincin ta ajiye gefe daya, sannan ta ciro ruwa da lemon ta ajiye tana kallon ledan hannunta wanda bata san inda xata wurgar ba, window din kitchen din ta dinga kallo sannan ta karasa a hankali ta bude ta jefar da ledan ta kulle windown, bin kitchen din ta dinga yi da kallo, babban ne kitchen din sosai, ga kuma store a ciki, cabinet din yayi kyau ba kadan ba sai dai babu komai a kitchen din sai electric heater da gas cooker, wanda bata ma san meye shi ba, sai fridge da deep freezer, a hankali ta juya xata fita ta gansa tsaye bakin kofar shigowa kitchen din ya rungume hannunsa yana kallonta, komawa baya tayi a tsorace tana kallonsa, ya nuna mata kofa wanda xai yi leading dinka to the back of the house, calmly yace "Bude kofar nan ki fita ledan da kika wurgar ki kwaso su" Da sauri ta nufi kofar tana murda makullin amma ta kasa budewa, karasawa yyi hakan yasa ta koma gefe da sauri, gaba daya a tsorace take, ya bude kofar ta fice, ledojin ta kwaso ta dawo ta tsaya bakin kofa tana kallonsa rike da ledan, ya karasa ya sa ma kofar makulli yace "Daga yau kada ki sake jefar min da komai wajen nan, don ba bola bane, ko kinga yayi maki kama da bola?" Ita dai bata ce komai ba ta sunkuyar da kanta, ya nuna mata wani waste bin a cikin kitchen din yace "Nan xaki dinga ajiye bola from henceforth" A hankali ta karasa shigowa ta saka ledojin a waste bin din, ya juya ya fita yace "Ki sameni sama" Bin bayansa tayi... ganin ya shiga dakin da take ta bi sa xuwa cikin dakin, gefen kofa ta tsaya bayan ta shigo, yana kallon tulin ledojin kayan da ta jera a kasa yace "Ga press can da xaki xuba kayanki" Ta kalli abinda yake nuna mata amma bata ce komai ba, yace "Yanxu xaki fara sa kayan ina gani...." Yana fadin haka ya ja stool ya xauna yana kallonta, ta karasa gun kayan ta bude, rasa ta yanda xata fara jera kayan tayi she look so confuse and Afraid at the same time, ta marairaice tana kallonsa amma bata ce komai ba, hakan yasa ya d'an yi tsaki bai ce mata komai ba ya mike, tun daga kananun kaya, undies, nighties, ya fara arranging dinsu a press din tana tsaye gefe tayi jigum tana kallonsa, har ya gama, ya bude akwatin da suka taho da shi jiya, atamfofin ciki dinkakku wanda baxa su wuce kala biyar ba ya ciro, linkin guga aka yi masu hakan yasa ya ajiye su cikin press din, da hijab biyu da suka rage suma gogaggu, sauran kananun abubuwan ciki duk ya samar masu maxauni cikin press din, gaban mirror yaje duk turarrukan ya jera su da mayukan shafawa da kayan kwalliya, lkci lkci yake kallonta ta madubin gabansa, Jiddah dai ta dinga kallon turarrukan da take ta tunanin su wa da su wa xasu dinga amfani da su haka da yawa, sun yi yawa sosai ba kadan ba, bayan ya tabbatar komai ya samu maxauni ya hade uban ledojin waje daya sannan yana kallonta ya nuna mata turarrukan yace "Kinga turarrukan nan?" Ta gyada masa kai, yace "They are not there for decoration?" D'an rufe idonsa yayi after he realized what he just spoke, sai kuma ya bude idanuwansa ya d'an hade rai yace "Kin gane abinda nace?" Ta girgixa masa kai yace "Ohk, cewa nayi ba don jere na siya maki su ba, watanni kadan na baki duk su kare, idan kuwa basu kare ba xan sa sai kin shanye su, na siya maki ne don ki dinga amfani da su a kai a kai, safe, rana, yamma, dare, bbu takamaiman lkcn saka turare, sannan ba kadan kadan aka ce ki dinga fesawa ba, idan kinga dama xaki iya feshe gaba dayansu a lkcn daya, infact ba ma sai kin ga dama ba, haka nake son ki dinga yi, gaba daya xaki dinga fesawa a lkci daya, wata daya na baki in ga duk sun kare..." kai kawai take gyada masa, ya nuna mata body cream din yace "Wannan xaki dinga shafawa duk kika yi wanka, sannan wanka da safe, rana, dare.... kullum haka xaki dinga yi, ga sabulun nan xan kai maki bandaki, idan kina so ma xaki iya wanka sau goma a rana akwai enough ruwa a gidan" Nan ma ta gyada masa kai, ya hade rai yace "Ba ki gyada min kai kamar lizard ba malama, sau nawa nace xaki dinga wanka daga yanxu?" A hankali tace "Sau uku, idan ina so ma inyi sau goma" Yace "Idan ma baki yi ba ina da camera a gidan ai xan gani...." Xaro ido tayi tana kallonsa, yace "Wanke baki kuma duk kika ci abu ki tafi bayi ki matsa MacLean ki wanke bakin ki, sannan ga na kuskura baki ma, bayan kin wanke bakin shi ma sai ki kuskure baki da shi, duk dare kada ki kuskura ki kwanta baki wanke bakin ki ba, da safe kafin kiyi alwala sai kin fara wanke baki, idan xaki yi wanka ki sake wankewa da safe... haka da rana sannan da yamma, ina son cikin sati biyu maclean dinki ya dinga karewa" Ta gyada masa kai, ya nuna mata mayukan gashi yace "Kullum sai ki shafa wannan a gashin ki, ki gyara..." Cikin sanyin murya tace "Toh" Nail cutter ya dauka gaban mirror din yace "Kinsan meye wannan?" Shiru tayi tana kallo, ya isa gabanta yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi ta fara komawa baya a hankali, tsayawa yayi yana kallonta, lkci daya ya daure fuska yace "Meye haka?" Taki kallonsa gabanta sai faduwa yake, yace "Baxa ki dago kanki ba" Da kyar ta dago kanta amma ta kasa kallon cikin idonsa, ya daura nail cutter din a kan finger dinsa wanda babu farce yace "Shi ake yankewa da, duk ranan juma'ah ki tabbatar kin yanke faratanki, kar ki kuskura ki yarda in ga farce a hannunki, bana son ganin haka..." A hankali ta gyada masa kai, yace "In ga hannunki" a hankali tayi masa stretching dogayen fingers dinta wanda ita ma bbu farce, lkci daya kuma ta sauke kasa, ya dau shaving stick dake cikin leda yana kallonta yace "Kinsan wannan?" Sau daya ta kalli abinda yake nuna mata, ta Smsunkuyar da kanta, yace "Duk Jumma'ah xaki dinga amfani dashi shi ma" ita dai bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, Sabulu ya dauka da Listerine mouthwash ya nufi bathroom, da ido ta bi sa, xai shiga ya juyo ganin bata taho ba yace "In dawo in dauko ki ne??" Da sauri ta bi sa, wajen da xata ajiye towel dinta ya nuna mata, ganin undies dinta da ta wanke a bandakin yace "Xa a sa maki igiya a baya, daga yau kada ki sake shanya a nan ki kai rana, nan ba wajen shanya bane, am i clear?" Ta sunkuyar da kai a hankali tace "Toh" da ido ya bi bandakin ganin it's clean ya juya ya fita ta bi bayansa, ya jingina da bango ya rungume hannunsa yace "Kinsan abinda yasa nake nuna maki duk abubuwan nan?" Ta girgixa masa kai tana kallonsa, yace "Saboda ba lallai wani abun ya sake hadamu a gidan nan ba, ba lallai ki sake samun privilege din tsayawa waje daya tare da ni ina maki bayani ba, ke kadai xaki dinga rayuwarki gidan nan babu wani da xai xo balle ya nuna maki wani abu shi sa nake bata lkci na yanxu, kina da ikon shiga ko ina a gidan nan amma banda bangarena.... sannan idan ina gari ba ke ba fitowa daga dakinki, kwana biyu xuwa uku kawai nake yi a kaduna shi ma sai karshen mako, don haka a wannan lkcn iyakar ki dakin ki, sai kuma probably kitchen, sannan baxan lamunci ki bar min gida da kazanta ba, kullum ki tabbatar kin yi shara kin yi mopping kin goge ko ina, nasan kin ga yanda ake yi a gidan Umma, tunda kin fi sati a can" Ji tayi hawaye ya kawo idonta, ta daga kai tana kallonsa, ya hade rai yace "Kin ji abinda nace?" Gyada masa kai tayi tana kokarin ganin hawayen bai karasa xubowa ba, Ya rungume hannunsa yace "Gobe xan koma wajen aiki, kafin in tafi xan siyo kayan abinci da komai da xa ki bukata a kitchen, don haka duk abinda na gaya maki yanxu baki da wani da xai sake gaya maki a gidan nan, it's better ki tabbatar kin gane komai...." Kallonsa kawai take tana jin wani kuka xai taho mata, ya ki yrda ya hada ido da ita, ya daga kafada kawai ya juya ya nufi kofa ya fita, ta sauke idonta a hankali wani hawaye me xafi ya shiga sakko mata. Abuturrab na dawowa daga masallaci da magrib ya shigo da abinci, sama ya haura ya kwankwasa kofar sannan ya bude, tana xaune saman darduma, ya ajiye mata abincin bakin kofar, ya d'an tsaya wanting to ask what she is even reciting in her prayers, sai kuma kawai ya fasa, ya ta6e baki yayi wucewarsa, karfe tara da rabi ta gama saka kayan da ya nuna mata yace ire irensu xata dinga sa wa da daddare, wando ne dogo da riga, sosai kayan ya mata kyau tana tsaye gaban madubi ta saka daya daga hulunan da ya siyo mata, har makogwaro ta dinga jin turarrukan da ta fesa abin ka da bata saba ba, ta nufi saman gado ta takure waje daya ta kwanta ta lumshe ido... Abuturrab ya fito daga bangarensa rike da lallausan duvet, kana ganin duvet din kasan me tsada ne sosai, kamshin turarruka ne ya gauraye ko ina na upstairs din, ya isa kofar dakin, ya fi second biyar a tsaye kafin ya bude, ko motsi bata yi ba alamar ta fara bacci, ya karasa ciki ya bude duvet din ya rufeta da shi, da sauri ta bude ido, yana kallonta yace "Daga yanxu idan xa ki kwanta ki dinga kashe wuta" Ta gyada masa kai, gun switch din ya nufa ya kashe wutan dakin sannan ya fita ya kulle kofar dakin, Jiddah ta lumshe ido gabanta na faduwa don bata saba kwana ita kadai ba. Washegari Abuturrab ya tabbatar duk wani abinda Jiddah xata bukata a kitchen ya siya, tare da Ramlah suka tafi siyayyen, duk ita ke fada masa abinda xa su siya na foodstuffs, har da filling din gas sun yi, kitchen din ya dawo well stocked up with foodstuffs, few pots, and some kitchen utensils, Jiddah dai na xaune parlon tun bayan dawowarsa da Ramlah, shi ma ya aika Ramlan taje ta kirata ne, yana tsaye kitchen din Ramlah ta jera komai, yana kallonta yace "Ahmad ya koma Abuja ne?" Ta gyada masa kai, ko ranan ma Ahmad ya kirasa amma yaki dagawa kamar dai shi ya aura masa jiddah, Ramlah na gamawa Abuturrab ya bata 2k transport ta fito daga kitchen din tana kallon Jiddah dake ta xaune, da murmushi fuskarta tace "Aunty amarya xan koma" ko lura da kallon da Abuturrab ke mata bata yi ba don jiddah kawai take kallo, Jiddah kam ta ga kallon da yake ma kanwartasa, cikin sanyi tace "To sai anjima" Ramlah ta nufi kofa.... bayan ta fita, Jiddah ta d'an kallesa suka hada ido, daure fuska yayi yace "In rokeki ki taso?" A hankali ta mike ta nufesa, komai na kitchen din ya shiga nuna mata da inda suke ajiye, ya koya mata kunna gas ya tabbatar ta iya kashewa ta iya kunnawa, yana kallonta da kyau yace "Anjima kafin in tafi xaki kunna min in gani" Tace "Toh" fita yyi daga kitchen din ya bar ta tsaye, ta bi sa da ido sannan ta bi bayansa. Abuturrab na komawa bangarensa ya ga calls din Umma har biyu, kiranta ya shiga yi bayan ta daga ya gaisheta, ta amsa tana tambayarsa ya gida, ya amsa mata, tace "Jiya naji ka je kun yi siyayya da Jiddah ko?" Yace "Ehh" Tace "Toh Allah ya saka da alkhairi" Ya amsa da "Ameen" tace "Yanxu meye babu cikin kayan, don xan taho anjima ne, sai in ga ko xa a iya tahowa da su" Ya d'an shafa kansa yace "Kawai Hijabs, bayan shi babu wani abu" Tace "Toh xuwa wani satin sai a dinka mata su" Yace "To Allah ya kai mu" Tace "Shi kenan dai ko?" Yace "Ehh" Tace "Toh sai na iso" Yace "Kamar yaushe xa ki taho Umma?" Tace "Xaku fita ne?" Ya girgixa kai yace "Xan koma aiki ne yau" Da mamaki tace "Xaka koma aiki kuma? ni na xata tunda ansan baka ji dadi ba xaka dau wani satin off?" Yace "Aa ni naji sauki, yau xan koma" Sake baki tayi, can tace "To ita Jiddar fa? Ko tare xa ku tafi?" Ya xaro ido kamar warce ta fado masa wani mugun abu yace "Aa" Tace "To ina xaka barta?" Yace "Nan gidan" Umma tace "Ita kadai?" Yace "Ehh babu komai" ta xaro ido tace "Aa gaskiya ka kawota nan kawai" Abuturrab yace "Aa xata xauna nan Umma" Umma tace "A kan me xaka bar yar mutane ita kadai a wannan gidan, ae baxai yiwu ba Abuturrab" Ya d'an shafa kansa a hankali yace "Umma tace fa xata iya xama, kuma ma xa a kawo mata mai aiki, ni nafi son ta xauna nan din kawai, and ranan laraba da safe xan dawo ai" Umma tace "Yaushe xa a kawo me aikin??" Da sauri yace "Ermm yau, in sha Allah" Umma ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Ni dai na fi gane ka kawota nan gida Abuturrab, ina ga xai fi wllh, it's not advisable to leave her all alone a gidan nan, she is too young for that, beside bata saba xama ita kadai ba" Trying all he xan to convince her yace "Umma xafa ta iya xama wllh, u shouldn't worry pls..." Umma tace "Toh amma is there anything wrong idan ka dawo da ita nan din, idan ka dawo weekend ba sai ka xo ka dauketa ba" Yace "Umma makaranta fa xata fara soon, plss u need not to worry" A hankali Umma tace "Toh shkkn wai dama don in dinga nuna mata wasu abubuwan ne, yasa nayi insisting" Ya girgixa kai yace "Ai bata da wani lkcn Umma, xata fara boko sannan islamiyya" Umma tace "Toh shkkn" ya d'an sauke wani boyayyen ajiyar xuciya yace "Toh sai kin xo Umma" Tace "Kai xan ba Maimuna sakon kawai ta kawo, next week din xan shigo in sha Allah" Yace "Umma me yasa kika fasa kuma, ko fushi kika yi" Tace "Not at all, let me leave it next week kawai" A hankali yace "Toh shkkn Umma" Sallama tayi masa ta katse wayar tana mamakin irin taurin kan Abuturrab, wanda tasan da Aunty ce tayi masa wannan maganan baxai mata musu ba xai yi yanda tace, girgixa kai kawai tayi don kwata kwata bata ji dadin haka ba, Abuturrab ya sauke wani ajiyar xuciyar ya ajiye wayar. Bayan la'asar ya gama shirinsa don driving xai yi xuwa kanon, komai da yasan ya kamata jiddah ta sani ko ta iya amfani da shi a gidan sai da ya tabbatar ya nuna mata a gidan nan, abinda ya kara bata masa lkci kenan, xaune yake parlor waiting for Maimuna don baya son sai ya tafi ta xo, tana ring din bell ya mike ya bude kofar, gaishesa tayi da fara'a, ya amsa yace "Ya gida" Tace "Alhmdlh yaya, ina Aunty Amarya" Babu yabo bbu fallasa ya amshi ledan hannunta, sannan ya ciro dubu daya ya mika mata yace "Ki yi transport" tace "Tare da driver muke" Yace "Ohk" dubu daya ya kara xarowa aljihunsa ya hada ya mika mata yace "Ki saka kati" Tana murmushi tace "Aa ka bari nagode yaya" Ya hade rai yace "Amsa ki tafi" Amsa tayi yace "Sai anjima" Tayi masa godiya sannan ta juya a hankali, amma duk jikinta yyi sanyi don bai bari ta ga Jiddah ba, ya kulle kofar, kujera ya koma ya xauna yana duba abinda ta kawo, turarrukan wuta ne a kwalbansu kusan kala hudu sai burner, da wasu turarrukan na jiki, tabe baki yyi ya mike ya wuce sama, dakin jiddah ya bude ya ganta xaune duk ta dawo wani iri, tana ganinsa ta sauke kanta kasa, ya ajiye ledan yace "Umma ta bada a kawo maki" ta bi sa da kallo har ya jona burner din a socket, sannan ya bude turaren wutan guda daya ya diba ya xuba yana kallonta, bayan d'an lkci kamshi ya fara tashi, yace "Safe da yamma xaki tabbatar kin ma dakinki da parlor haka" Ta gyada masa kai kawai, waya karama ya ciro aljihunsa yana kallonta ya mika mata, ta mike ta isa inda yake ta risina ta amsa, yana kallonta yace "Number da xaki dinga samuna ne kadai a ciki, sai ki koyi yanda xaki yi amfani da shi ke kadai" cikin sanyin murya tace "Toh" Yace "Sannan ba ace ki xauna ke daya kiyi wani shiru kamar me xaman makoki ba, ga kayan kallo duk na koya maki yanda xaki kunna" Ta sunkuyar da kanta, kofa ya nufa yace "Na tafi" Ta kallesa da sauri tace "Ina xaka je" Yace "Garin da nake aiki" bude kofar yyi ta bi sa da ido, sai da taga ya fita kafin ya kulle kofar cikin sanyin murya tace "Allah ya tsare" Ya amsa da Ameen a takaice, da sauri tace "Yaushe xaka dawo?" Yana kallonta yace "Wannan bai shafeki ba, ko da wani abu da xaki bukata bayan duk wanda na maki??" Daga haka ya kulle kofar hawayen dake makale idonta ya silalo a hankali, ta fi minti goma tsaye yanda ya bar ta, jin an tada mota ta kalli window da sauri sannan ta karasa window din ta d'an bude labule tana lekan waje, tana ganinsa ya fita da motar, a hankali ta fara kuka ta xauna nan kasa, sai kuma ta fashe da kuka kamar ana dada tunxurata, Abuturrab ya sauka motar yana kallon gate din gidan, he just dont have any option then to close the gate from outside, don bai ma son ya gwada mata yanda ake kullewa daga ciki balle ya sa ta kulle ta ciki, yasan probably kafin ya dawo weekend an samar masa mai gadi kamar yanda yayi requesting ayi, ya kulle gidan ya koma ya shiga motarsa yana karasa addu'o'in da yake yi tun daga compound a ransa ya bar layin..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Do justice to ur self by subscribing before reading Thank you Jiddah ce tsaye kitchen bayan magrib tana ta kallon kayan abincin dake cikin store, yunwa take ji tun daxu amma bata san me xata girka ta ci ba, gashi tsoron gas din take, don yace mata yana kona mutane idan ba a maida hankali wajen amfani da shi ba, a hankali ta bude fridge tana kallon ciki, lemo ne a ciki da ruwan gora, sai apples, grapes, banana da dai wasu fruits din a ciki, a hankali ta rufe ta bude deep freezer, taga naman cow, kayan ciki, kifi, da naman kaza, a hankali ta rufe shima, kwalin indomie da ya riga ya bude mata ta nufa ta dau daya a ciki, ta bi tukwanen dake ajiye da kallo snn ta dau wani karami, da kyar ta iya kunna gas din tana ja da baya don duk a tsorace take, ganin wutan ya dawo kamar na risho da take gani gidan iyah yasa ta daura tukunyar, tun da take idan banda icce da gawayi bata ta6a girki a kan wani abu ba, ba ita ta bar kitchen din ba sai ana isha a masallaci, ta cika ma indomien uban ruwa sai swimming yake a plate din, da kyar dai ta tuttura ta cinye indomien da bai mata dadi ba a baki don ita bata ta6a ci ba ma, tura plate din tayi hawaye ya kawo idonta don kewar tuwon masara take da miyar kuka, cimar da ta saba da kenan iya rayuwarta, don ko shinkafa kwana biyun nan da take ci duk taji ya isheta. Abuturrab na kwance hotel room da ya saba sauka, dawowarsa kenan daga eatry yaje ya ci abinci, vid call suke yi da Aneesah wanda har yanxu bata san abinda ke faruwa ba, bai yi mamakin da har lkcn Aunty bata sanar ma kowa ba, tunda ita bata yarda da auren ba dama from start, Aneesah na kwance saman gado daga ita sai wata yar rigar bacci, komai na jikinta na waje, ganin yanda Abuturrab ke lumshe ido tace "Kar kace min har ka fara jin bacci My captain" Ya bude idon yana kallonta yace "Sure, i will be piloting 8am flight tomorrow in sha Allah" Ta marairaice tace "Wllh ban gaji da jin muryarka ba mine" a hankali yace "Yi hakuri, early to bed early to rise..." Tace "Toh shkkn sweetheart, sleep tight, and dream of me" Ya kashe mata ido sannan ya katse wayar, har ya ajiye ya juya baya hade da lumshe ido sai kuma ya bude idon a hankali ya jawo wayar, dialing number yyi ya sa handsfree yana kallon screen din, Jiddah ta kwanta kenan ta takure waje daya tsoro duk ya cikata, da ta tuna ita kadai ce gidan sai hankalinta yyi mugun tashi, ko wutan dakin ma taki kashewa kamar yanda yyi instructing dinta, sai taji kamar abu na motsi a dakin, ring din wayar dake gaban madubi yasa ta mike a mugun firgice tace "Wayyoo Allah na, nq shiga uku" Sosai jikinta ya dinga rawa tana kallon wayar, sai kuma ta nufi gaban madubin ta dau wayar tana kallo, button din left side din ta danna, tunda iyah na da waya kuma ita ke daga mata ma idan ana kiranta, Shiru Abuturrab yyi yana kallon wayar tasa bayan yaga ta dauka, can jin bata ce komai ba yace "Kin ci abincin ko ba ki ci ba?" Ta sauke idonta kasa a hankali tace "Na ci" Bai ta6a xaton xata yi magana da irin wannan natsuwar a waya ba, can yace "Me kika ci?" Tace "Taliyar indomie" Yace "Ohk.... Sai da safe" Da sauri tace "Ka kai lafiya?" Yace "Eh" kamar xata yi kuka tace "Amma ni tsoro nake ji wllh" yace "Tsoron me?" Ta fashe masa da kuka kamar jira take tace "Ni kadae fa a gidan, gashi sae inyi ta jin motsi" Ya gyara kwanciyarsa, calmly yace "Ehh dodon da na ba ajiyar ki ne ke motsi, ko kar yayi??" Ta wani gwalo ido tana bin dakin da kallo tana sake maimaita abinda yace a ranta, ko ina na jikinta ya dau 6ari a lkcn, cikin rawar murya tace "Dodo fa kace?" Yace "Ehh ko dai ya bari kin gansa ne?" Wani ihu ta kwala da ya sa shi mikewa xaune da sauri, ta rushe da wani kuka tana salati, da sauri yace "Ke wasa fa nake maki" ko sauraronsa bata yi ba ta cika masa kunne da kuka, tsayar da kukan tayi ganin duhu ya gauraye ko ina na dakin, da ta dage ta kara kwala wani ihun sae da Abuturrab ya mike tsaye, cikin bargo ta shige har sannan wayar na hannunta tana rusa kuka, Abuturrab ya dinga cewa "ki tsaya ki saurareni nace maki wasa nake, i am only joking" ko ina na jikinta na rawa cikin tashin hankali tace "Wllh ya kashe wutan gidan, na shiga uku na, don Allah ka xo ka taimake ni, xan iya mutuwa ni kadai" Komawa Abuturrab yyi ya xauna jin tace ba wuta, gaba daya ya mance ya gwada mata yanda xata dinga kunna solar idan an dauke wuta, yayi kasa da murya yace "Ki saurareni nace, ni wasa nake maki, wa yace maki akwai dodo a duniyar nan, ke baki san wasa ba? babu komai fa wuta kawai suka dauke, ko ba a dauke wuta a Hayin ku??" kuka kawai take tana shessheka tace "Don girman Allah ka dawo ka fitar dani a gidan, ni wllh baxan iya kwana ni kadai ba, Allah baxan iya ba" Hade rai yyi sai dai bai ce komai ba, jin yanda take rera kuka da karfi, yyi kasa da murya yace "Kinsan inda nake da kike cewa in dawo ynxu" Taki ce masa komai sai kuka, cikin kwantar da hankali yace "Wllh babu komai kawai zolayarki nake yi, amma tunda kina tsoro shkkn baxan kashe wayar ba har gari ya waye, idan da wani abu sai ki min magana, kina ina yanxu?" Tana shessheka a hankali tace "Ina kan gado" Yace "Toh kwanta" Ta gyada masa kai tace "Na kwanta" Yace "To kulle idonki" Cikin rawar murya tace "A kulle yake ai" Yace "Toh fara bacci" Yana jin yanda take kuka a hankali, ya lumshe ido ya bude, can yace "In kashe wayata ne?" Da sauri ta bude ido ta girgixa masa kai tace "Aa don Allah" Yace "Toh daina kukan nan" a hankali tace "Na daina" Yace "Kiyi baccin ki, ni karatu xan yi..." tayi shiru bata ce komai ba tana sauke ajiyar xuciya, jingina yyi jikin pillow ya fara karantun Al-qur'ani cikin cool and calm voice dinsa, tun jiddah na jin sa har bacci ya dauketa, ya kai ayar karshe a suran da yake karantawa, shiru yyi.... bayan few seconds murya can kasa yace "Jeedderh" jin shiru ya kara tabbatar da tayi bacci, a hankali ya katse wayar ya sauke ajiyar xuciya sannan ya kwanta yana karanto addu'a.... Kiran Sallan asuba ya farkar da Jiddah, ta mike xaune da sauri tana bin dakin da kallo da hasken fitilun ciki ya haska tarrr, kallon wayar dake kusa da ita tayi ta dauka ta danna tana kallon screen din, a hankali ta mayar ta ajiye sannan ta mike, kamar me tsoron tiles din dakin ta sauke kafarta sannan ta mike tsaye, dodon da yace mata ne ya dameta a rai, amma kuma yace wasa yake, cikin sanda ta nufi bandaki ko rufewa bata yi ba tana leko dakin ko xata ga abu me kama da dodo... Karfe tara da yan mintuna Abuturrab na lagos bayan sun sauka kiran Ahmad ya shigo wayarsa, kallon screen din ya dinga yi kafin ya dauka daga karshe, Ahmad yace "What nonsense Aliyu, ni na turaka hayi kayi ma kanka aure da xan dinga kiranka ka ki dauka all this while?" Abuturrab yace "Ka kirani ne ka ci xarafina daga inda ka tsaya?" Ahmad yace "Abinda ya fi xarafi... Ance maka farin ciki nayi da auren nan naka Captain, ae ko a mafarki ban ta6a tunanin xaka riga ni aure ba, which means xaka riga ni fara ajiye iyali, may be next year warhaka duk muna gidanka suna, to kaga kuwa ae ni ba haka na so ba, tunda ni aka fara sa ma rana" rasa abinda xai ce masa Abuturrab yyi sae bin mutanen cikin eatry da yake xaune yake da kallo, har ransa yaji xafin abinda Ahmad ke gaya masa, gashi ya ma rasa amsan da xai basa, Ahmad da tsaf ya san ya kular da abokin nasa, ya dinga dariya kasa kasa kafin yace "Toh ya Amarya me sunan Umminmu, ka dai min bakin cikin xuwa ganinta a gidanka kafin in koma aiki, hope a hankali dai ake cin amarcin??" Abuturrab ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ya cire wayar a kunnensa ya yi tapping button din katse kira sannan ya jefar da wayar kan table din gabansa, ya jingina da kujera xuciyarsa na ci gaba da tafarfasa, haske wayan ya sake yi ganin El-Basheer ke kiransa ya dinga kallon wayar bbu ko kiftawa, har ya katse bai yi attempting din dagawa ba, he knows the news of his marriage has circulate, but what's d essence, auren da babu yanxu.... Mikewa yyi daga bisanni ya dau wayar da ruwan gora ko breakfast din bai cinye ba ya fita eatry din back to airport. Yana Abuja that same day da rana, which in few hours xa su yi piloting xuwa port Harcourt, kasa daurewa yyi ganin da sauran lkci sannan Co-pilots dinsa suna preflight preparations kawai ya fita xuwa hospital din da Ahmad ke aiki, many patients ne xaune reception din hospital din, ya nufi gun wata nurse bayan sun gaisa yace "Dr Ahmad na nan?" Tace "Eh, do u have any appointment with him sir?" Abuturrab yace "Yea ynxu muka yi waya..." Daga haka ya nufi hanyar office dinsa, nurse din ta bi sa da kallo, can tace "But he is attending to a patient" ko juyowa bai yi ba har ya isa kofar office din ya murda, Ahmad na xaune attending to his patient, ya daga kai, ganin Abuturrab ya bude ido, Abuturrab bai ce komai ba ya nemi kujera ya xauna, murmushi kawai Ahmad ke yi har ya sallami patient din ya fita, sannan ya kalli direction din da Abuturrab ke xaune, smiling broadly yace "Latest ango in town" mikewa Abuturrab yyi yana kallonsa yace "In ur life Ahmad.... I mean in ur life don't ever abuse me the way u did earlier today, i felt really bad at that" Ahmad ya masa Wani kallo kafin ya fara dariya irin wanda ke kufular da mutum yace "Toh Alhaji Ibrahim, ae da ka xo da bulala koh?" a fusace Abuturrab yace "You caused me all this mess sannan ka fi kowa yi min dariya?? Who does that Ahmad?" Ahmad ya buda baki hade da xaro ido yace "Ta yaya na janyo maka?" Abuturrab na huci yace "Ohk, i will tell u now, ka xata da baka fara kai ni gun yarinyar nan ba da akwai wani abun da xai hadani da ita balle taimakona ya dawo min sharri?" Ahmad yace "Da na kai ka gun yarinyar sai nace ka xaga ka bi ta baya ka dinga xuwa wajenta ba tare da na sani ba? Ina ce ranan har Umar sai da yace yana ganinka a unguwar Hayi ka mu sa don kada ma in dago komai" Dariya sosai Ahmad yyi har da gyara xama yace "Gaskiya na dade banga me abun dariya irin ka ba Captain, da naje siyan awara sai nace ka dinga xagayawa kana xuwa gun me awara?? just take a look at the distance daga cikin gari xuwa Hayin rigasa amma haka kullum kake jan motar kaje shine xaka xo nan yanxu kayi wani blaming dina, ni da ma aka munafurta ana ta xuwa tadi ta baya ban sani ba, ban ji haushi ba sai kai?" Kallonsa kawai Abuturrab ke ta yi yana jin kamar ya shakosa, Ahmad ya sake wani shegen dariya har da buga table yace "Toh ai dai yanxu ka rigani sanin aure hankalinka ya kwanta, mu ma Allah ya nuna mana namu da wuri wuri haka..." Komawa Abuturrab yayi ya xauna xuciyarsa na mugun tafarfasa, Ahmad sai satan kallonsa yake yana yar dariya, Calmly Abuturrab yace "Dama Aunty na yawan tagging taimako da xama sharri a rayuwar nan, and i have seen that clearly now don ya faru a kaina, assuming i ignore and act as if i didn't see anything da duk hakan bai faru da ni ba, kuma am making this vow today.. ni Aliyu duk inda na ga wani na neman taimako idan ya wuce na kudi, shi ma kudin sai nayi naxari me xurfi a kai, to wllh wllh i will never ever render that help" Ahmad yace "Calm down man, wannan taimakon fa bai xame maka wani sharri ba illa ma lada me yawa da ka kwasan ma kanka idan Allah ya yrda, da ma nine na kwashi wannan ladan wllh, i cant imagine how happy i will be, sannan sharrin dake ciki a naka tunanin ba dai auren yarinyar dake kanka bane??" Abuturrab na kallonsa da kyau yace "Babu wani aurenta a kaina yanxu, ni d'an iska ne da xan bar aurenta a kaina" Da mamaki Ahmad ke kallonsa, can yace "Ban gane ba" Abuturrab yace "U heard and assimilate me right, babu wani aurenta a kaina" Ahmad ya mike yana kallonsa da mamaki yace "Kana nufin ka saketa Aliyu?" Abuturrab yace "Toh me xan jira, ko don dariya da jest making irin naka da mutane ire iren ka ai dole inyi hakan in samar ma kaina kwanciyar hankali" Ahmad ya fito ya xauna gefen Abuturrab on a serious note yace "Stop it plss captain, da gaske ka saketa?" Abuturrab yace "To wai jiran me xan yi, idan ba ina da intention din auren nata bane dama, i have nothing to do with that girl as a wife, gwara kawai in xama guardian dinta, and that's what i am doing right now..." Ahmad ya dafe kansa yace "Ya salam... amma da baka yi haka ba Captain, why will u do that pls???" Abuturrab yace "You are not to tell me what to do and what not to do, so ka ke in cuci kaina in kwari kaina, ina aka ta6a irin wannan taimakon, i just have to saboda kwanciyar hankalina" Kallonsa kawai Ahmad ke yi gaba daya expression dinsa ya nuna ko kadan bai ji dadin sakin jiddah da yace yayi ba, Bayan few seconds yace "Kuma ta sani, i mean ta san ka saketa?" Abuturrab yace "Of course a gabanta nayi na mika mata sannan na amsa na ajiye" Ahmad ya girgixa kai yace "Wllh banji dadin hakan ba Abuturrab" Wani kallo Abuturrab yayi masa sannan ya ja tsaki ya mike ya nufi kofa, Ahmad ya bisa da kallo yace "Amma kuma xamanku a gida daya baxai ta6a yiwuwa ba, ko don hakan ma ni da kaina xan sanar ma su Umma cewar babu aure tsakaninka da Jiddah, I can't pretend over this in cuceta, idan baka san addini ba ni na sani" Dawowa Abuturrab yyi yana kallonsa da kyau, calmly yace "And this will bring the end of our friendship Ahmad, i told you my secret because i trust u, and I'm sure u won't betray my trust, addini kuma da kake cewa ina ga sai dai mu goga a kan saninsa da ni da ke, bbu abinda xaka nuna min... Baka isa kuma ka koya min yanda xanyi da rayuwata ba" Daga haka ya nufi kofa ya fice ya kulle masa kofar. Daren ranan Abuturrab na xaune hotel room dinsa dake kano after isha yana shan shayi a hankali, tunawa yyi daxu da yamma ya kira wayar wajen Jidda bata daga ba, ya sake kira da magrib ma no answer, ya kalli wayarsa dake gefensa ya dauka ya sake dialing number, har ya katse no answer, haka nan kawai yaji his mind has lost rest, kallon wayar ya dinga yi, can ya sake kira nan ma har ya katse no answer, kallon agogon jikin wayar yyi yaga takwas ya wuce, sake dialing yyi nan ma har ya katse no answer, ajiye cup din hannunsa yyi, ya shiga kiran wani pilot hoping to reach him don yasan he might be up in the sky now, jin captain Musa ya daga, ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya yace "Captain baku tashi har yanxu ba?" Captain din yace "About to... in few minutes time, ya gajiya?" Abuturrab yace "I think i will have to follow you to kaduna now" Da mamaki pilot din yace "Baxa kayi piloting jirgi gobe da safe ba, and hope all is well?" Abuturrab yace "Sure alhmdlh, jirgin gobe na sha daya ne, i don't have early morning duty" Musa yace "Toh shkkn, ka taho yanxun nan kasan basu fiye son jira ba, in some minute time xamu yi take off" Abuturrab yace "In sha Allah" Cikin few minutes ya shirya cikin kananun kaya Hoping not to miss the private flight going to kaduna, cikin ikon Allah ya isa, kuma suka daga sama, within some minutes suka sauka a garin kaduna, a motar Musa dake airport din kaduna suka shigo cikin gari, Musa ya kawo Abuturrab har layinsa ya sauka yana masa godiya, Musa yace "Sai mun hadu Wednesday in sha Allah" Abuturrab yace "Sure in sha Allah, thank you" daga haka suka yi sallama ya karasa cikin layin da kafa, makullin gidan ya fiddo a aljihunsa ya bude sannan ya shiga, har ya isa main entrance nan ma ya bude sannan ya shiga parlor, wutan parlon a kunne yake parlon sai kamshin turaren wuta yake, ko ina na nan ynda ya barsa jiya, kuma babu alamar ana xama cikin parlon ma, karasawa yyi sama yana kallon kofar dakinta ya murda a hankali ya shiga, babu kowa cikin dakin ya bude ido sosai sai dai lkci daya yayi calming kansa jin kamshin sabulu a dakin, coz he is a very sharp percipient, bin dakin ya dinga yi da kallo yana duba inda xai ga wayar amma bai ga alamarsa ba, can kusa da window ya nufa ya tsaya hade da rungume hannunsa ya daure fuska, bayan few seconds ta bude kofar bandakin, ta fito daure da towel, bata ko kalli direction din da yake ba ta nufi gaban mirror, sai a sannan ta ga mutum ta madubi wani ihu ta fasa da karfi ta nufi bandakin a guje ruwan kafarta ya sa tsantsin tiles ya kwasheta ta fadi nan bakin kofar bandakin, da sauri Abuturrab ya nufeta ya durkusa kusa da ita ya dagota yace "Ke nine fahh" wani kuka ta fashe da bayan ta kare masa kallo ta tabbatar shi din ne, tana rike da towel din jikinta gam tace "Wayyo kafata, wllh kila nayi targade, wayyo Baabarmu" Komawa baya yyi yana kallon kafar, ya mike yace "Tashi tsaye" Tana girgixa kai hawaye na sauka idonta tace "Ni baxan iya ba wllh" Ya kamata ya dagata, lkci daya ya hade rai yace "Wani kafar ne kika yi targade" Ta nuna masa right leg dinta, gefen gado ya xaunar da ita ya duka yana kallon kafar, ita dai hawaye kawai take tana hade laps dinta tana kallonsa, wani kallo ya mata ta sunkuyar da kai da sauri, mikewa yayi ya nufi gaban madubi don yasan ya siya mata man xafi ranan da suka yi shopping incase she will need it, a hankali tace "Don Allah ka yi hakuri ka miko min hijabi na" Ya dau man ya juyo ya dawo kamar bai ji ta ba, ta marairaice tace "Hijabina nace" Yace "Ki bari in duba maki kafar in ga babu targade, yau duk kukan karyar nan da kike ma mutane sai ya dawo na gaskiya, kuma xaki gaya min inda kika jefar da wayar da na baki" Shiru tayi bata ce komai ba, ya duka ya bude man ya diba sannan ya kama kafar da tace, wani ihu tayi ya ja kafar da karfi, har kasa sai da ta sauko tana kokarin kwace kafarta sbda axaban da take ji, ganin da gaske ta ji ciwon yasa yace "A hankali fa nake maki amma wllh idan kika sake ta6a ni xan yi da karfi" hawaye na sauka idonta tace "Wllh xafi yake min sosai, don Allah ka rufa min asiri kayi hakuri" Ya daure fuska ganin xata sake kai hannunta kan nasa yace "Kin xata wasa nake maki" Da sauri ta dauke hannun, duk da yanda yake mata a hankali haka ta dinga kuka tana neman birgima a wajen, shi dai kallonta kawai yake, don a fuska bata yi kama da warce xata yi shagwaba ba, ko warce baxata iya jure xafi ba ko yaya ne, dauke idonsa yyi ganin tawul din na neman sauka a kirjinta, ya sake mata kafar ya mike, sai a snn ta ankare, tana shessheka ta kankame abarta, ya ajiye man xafin hannunsa ya nufi kofa ya fita. *Pls i am bringing this to the notice of people coming to disturb me with... ina karanta littafin ki kuma bani da kudin biya ki yafe min!!! For what?? Na aikeki karanta littafi baki da kudi? Ga dai free books kaca kaca a gari, Toh a gaskiya baxan iya lalacewa da gantalewa ba kije can ki nemi wanda xaki ce ya yafe maki ba dai khaleesat Haiydar ba, ba ruwanaa tunda ban aike ki karanta littafi ba, ki sani you owe me har sai ranan da kika mula kika mulmule kika ga daman biya*🤷 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Kamar wanda ya tuna abu ya sake juyowa, rarrafawa yaga tayi xuwa gun da hijab dinta yake xata dauka, ya hade rai sosai yace "Ina wayar da na baki?" Ta juya ta kalli gadon dakin, a hankali tace "Ya fada karkashin gadon na kasa daukowa" Da mamaki ya dinga kallonta, ta sunkuyar da kanta, can yace "Wa ya jefar karkashin gadon?" Ta sake kallonsa tace "Xamewa yayi ya shige ban sani ba" cikin tsawa yace "Saboda ke yar yarinya ce ko?" Shiru tayi bata ce komai ba ya juya ya fice daga dakin ya kulle kofar, da kyar ta lallaba tayi shafe shafen mayukanta da turarruka sannan ta dauki wani rigar bacci ta saka tana dingishi ta hau saman gado ta kwanta, mamaki ta dinga yi na yaushe ya shigo gidan bata ji karan shigowar mota ba, ko dai bai dawo da motar bane, kuma ai ce mata yyi sae karshen sati, da wannan tunane tunanen bacci yyi awon gaba da ita. kasa bacci Abuturrab yyi sbda shayi da bai sha ba, don ya fara shan shayin kenan ya bari ya taho, shi kuma idan da abinda ke takurasa rashin shan shayin dare, ji yake yunwa na damunsa indai bai sha shayi ba, and he detest making tea himself, da dai yayi da kansa gwara kar ya sha, rub da ciki yyi ya lumshe ido hoping to force sleep, wajen karfe daya da rabi ya mike ya fito daga bangarensa, downstairs ya sauka ya shiga kitchen ya bude fridge, kallon fridge din ya dinga yi don bai ga alamar ta ta6a komai na ciki ba tun jiya, ya dau Chivita daya ya bude ya dau glass cup bayan ya dauraye ya xuba a ciki, sau biyu ya cika ya shanye sannan ya mayar fridge, da ya hada shayi gwara yyi hakan, fitowa yyi daga kitchen din ya xauna saman kujera a parlon cikin duhu, yana ta xaune har karfe biyu sannan ya mike ya haura sama, har ya nufi part dinsa ya dawo ya bude kofar dakinta, cikin duvet ya ganta ta takure waje daya tana bacci, ya karasa cikin dakin ya janye duvet din, dukawa yyi yana kallon kafarta sannan ya d'an danna kafar, da sauri ta janye ta juya masa baya, sake kai hannu yayi ya kamo kafar, da sauri ta bude ido, ya hade rai amma bai ce komai ba ya mike ya sake dauko man xafin, a hankali ya shafa mata sannan ya mike ya kashe wutan dakin ya fita. Da asuba bayan ya dawo masallaci ya fara tunanin ta yanda xai koma kano babu mota, gashi bai fiye son shiga commercial vehicles ba, karfe bakwai ya gama shiri ya fito daga bangarensa, dakinta ya murda a hankali ya shiga, a kwance ya ganta amma idonta biyu, ganinsa ta mike xaune da sauri... yace "Kafin in dawo ran juma'ah ki tabbatar kin fito da wayata da kika jefar karkashin gado" shiru tayi bata ce komai ba, yace "Sannan kayan marmarin da na xuba a fridge ki tabbatar kar in dawo in sami ko daya" Daga haka ya juya, da sauri tace "Tafiya xaka yi?" Yace "Aa xama xan yi" sai bayan da ya fita ya fara tunanin wayar da xai sake bata, he just need to hand a phone over to her, shi kuma bashi da strength din daga kayan gado da sassafen nan, can dai yyi deciding ya koma dakin ya ga inda ta jefar da wayar tukun, Yana shiga bai ko kalleta ba ya nufi gadon ya fiddo wayarsa ya kunna fitila ya duka yana haskawa karkashin gadon, cikin few minutes ya ciro wayar da hannunsa, ita dai tana tsaye ta rakube gefe da hijab dinta har kasa, ya dago yana kallonta fuskarsa a tamke, ta sunkuyar da kanta, ajiyewa yyi kan gado ya nufi kofa ya fita ta bi sa da kallo, dole commercial car din ya tafi ya hau a park xuwa kano... Jiddah na xaune kasan carpet a parlon hannunta rike da apple biyu, ta kasa ci sbda rashin sabo da shi, tunda take a rayuwarta bata ta6a shiga matsatsi da takura irin wannan ba, duk da ba jin dadin xama take da Hansai ba amma ai xaman bakin titi ma da take ya kan debe mata kewa tana ganin mutane da motoci, amma tun shigowarsu gidan nan yau kwananta nawa bata ga kowa ba banda shi kadai, tunanin hakan ya sa hawaye ya kawo idonta, kallon ma sbda rashin sabo da shi da ta fara xata soma gyangyadi, Mikewa tayi a sanyaye tana goge idonta ta nufi wani window dake parlon ta makale jiki ta bude labulen a hankali tana lekan tsakar gidan, babba ne tsakar gidan da flowers masu kyau xagaye, ta dade tsaye wajen tana ta kallon tsuntsayen dake tashi da sauka a tsakar gidan, kiran sallan azahar yasa ta juya a hankali ta bar wajen tana kallon apples din hannunta kitchen ta koma ta mayar, marairaice fuska tayi tana kallon fruits din fridge din banda ayaba babu abinda ta iya ci a ciki ita dai, tana tafiya a hankali ta fita kitchen din. Hansai ce xaune gaban mai anguwa da Zulai da ta rakota, bayan sun gaisa, ta kunce ha6ar xaninta ta sakar masa kuka tana matsar kwalla da zanin tace "Wllh Mai Anguwa shiru shiru har yau babu yarinyar nan tawa babu labarinta fa, abun nan ya fara damuna duk inda taje ai ya ci ace ta dawo yanxu, yau fa sati daya cur ba ita ba labarinta, na rasa inda xan sa kaina, ga komai nawa ya tsaya kamar ta tafi da shi" Sae kuma ta rushe da kuka, Mai Anguwa dake ta kallonta da mamaki yace "Ikon Allah, ni ai na xata da naji shiru Allah ya sa ta dawo gida, toh ke duk kwanakin nan me yasa kika yi shiru kinsan bata dawo gida ba, sai yanxu xaki taho kice bata dawo ba" Hansai ta marairaice cikin rawan murya tace "Wallahi na danni xuciyata ce don ban debe tsammani ba, ina ta baxa ido amma naga shirun yayi yawa" Mai Anguwa yace "Cabb, amma kina da ganganci Hansatu, anya ke kika haifi yar nan kuwa kamar yanda kika ce?" Hansai ta kara marairaice masa cikin kuka tace "Nice mana Mai Anguwa, ina da kauda kai dai xaka ce kawai" Mai Anguwa yace "Toh, ranan dai na amshi lambar shi mutumin da ya aureta, wato shi matukin jirgin saman, kuma bayan wannan aure da kwana uku ya xo min har nan da mahaifinsa da kawunsa, mahaifin nasa sanannen mutum ne dattako kuwa a garin nan..." Hansai ta hadiye abu da kyar tace "Toh kira mana shi xaka yi yanxu kenan don Allah? Don dai gaskiya na fara xargin kilan ma ya ganta ya tafi da ita ne kawai bamu sani ba, banda haka me yasa xai yi shiru haka babu labarinsa, bayan gashi kace har ya xo da mahaifinsa, to idan haka ne ba sai sanda na ga damar basa matar xai tafi da ita ba, to wllh ni na canxa ra'ayi kan auren ma, ya dawo ya fadi nawa ya kashe ko gidan da muke ciki ne sai in sayar in biyasa, ba ruwana wllh" Mai Anguwa dake ta kallonta, ya d'an yi murmushi yana kara jinjina hali irin nata, ya fiddo wayarsa bayan kusan minti biyar yace "Alhmdlh, na samo lambar" Yana fadin haka yayi dialing number Abuturrab ya sa handsfree, kallon Hansai yayi bayan an sanar wayar baxai je ba, Hansai ta rushe da wani matsanancin kuka tace "To ko dai lambar karya ya baka, ni sai yanxa nake jin ma ban yarda da mutumin nan ba wllh, wa ya sani ma ko d'an yankan kai ne yace mana matukin jirgi ne shi, jirgi abar wasa ce da xai iya tukata bayan an sanar mana turawa ne kadai suka iya daga jirgi sama su tuka, sannan idan ba d'an yankan kai ba mutumi babu dangin iya balle na baba kayi ta kashe mana kudi haka daga jin an mana mutuwa, daga haduwar mu xuwa fa ranan da ya bada sadakinta wllh mutumin nan ya kashe mana yayi kusan rabin miliyan, to akan me? Aa wllh ya xo in biyasa ya maido min da 'ya ta" Mai Anguwa dai tabe baki kawai yake bai bata amsa ba, Hansai ta fara kokarin mikewa tace "Ai dai wayar baxata dauwama a mace ba, don haka ko gobe ma xan dawo sai ka sake gwada kiran lambar don ni bani da waya, haka kawai yarinya ta bace batt kamar yar kaza" Mai Anguwa yace "Allah ya kai mu goben" daga haka ta bar wajen tare da kawarta, Zulai tace "Anya wannan mai anguwan na da gaskiya kuwa Hansai?" Hansai ta kalleta da sauri tace "Atoh, nima shi na gani, baki ji har ya fara cewa Uban yaron sananne ne a garin nan ba, kawai dai sun danna masa uban kudi shi ma shine yayi mukus, to wllh a maido min da 'ya ta babu wani xancen auren karya" Zulai tace "Kuma fa da gaskiyan ki, ko dai wannan yaron d'an yankan kai ne, idan ba haka ba a wnn xamanin ina xai samo rabin miliyan ya kashe maku" Hansai ta tsaya tana kallon Zulai, can ta marairaice tace "Toh kuwa in har haka ne ya kassara ni, wa gareni da muke sana'a tare banda jiddar, ke baki ga ko me nasa Bibalo kin yi take ba sai ta nemi ta xageni, ai jiddah ita ce rufin asiri na a duniyar nan, gashi duk jarin na fatattakar, kuma sana'ar ba wani ciniki nake yi ba yanxu, uwa dai an juya min baya a anguwan" tana fadin haka ta fara matsar kwalla, Zulai tace "Toh da da kike shirin aurar da ita Jiddar ga Iliya fa?" Hansai ta ci gaba da tafiya tace "Toh ai ko daga gidan mijin sana'ar xan dinga bata tana min nufi na" Zulai ta ta6e baki tace "In ko ba d'an yankan kai bane to tana gunsa Wlh, abinda kowa dai ya shaida matarsa ce" Hansai ta share xufar goshinta tace "Toh uban me xai yi da ita wai Zulai, sai kiyi ta wani cewa matarsa, wllh babban mutum ne ko da kudi aka hadasa da jiddah banjin xai amsa balle bbu ko sisi, don baki gansa bane shi yasa kike wannan xancen banxan, lafiyayyen namiji ne fa wanda da kyar ya amince ya auri yar kaduna sai dai yar Abuja" Zulai tace "Toh wai ke kinga tun bayan da aka daura masa aure da ita ya sake dawo maki kofar gida, ai da wllh bata wajensa da tuni ya dawo an kai xance gidan yan sanda, duk inda ta shiga kuma sai an nemota, ke dai kawai kin cuci kanki, kina ji kina gani sbda shegen son kudi kin ba babban mutum irinsa auren Jiddah ga Bibalo yashe a gida" Hansai ta fashe da kukan takaici tace "Ni anjima da daddare ma wllh xan dawo gun mai anguwa ya sake kiran lambar, don bani da waya ne da na amsa lambar ai, kuma wllh in har da gaske jiddah na wajensa to ni ba da amincewata ya aure min 'ya ba, wllh sai ya sakar min ita, ina jiddah ina babban mutum kamar shi idan ba yana da wata manufa na yanka min ita ya bunkasa arxikinsa a ransa ba" Zulai ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Ohh!!! wa yasan irin daulan da Jiddah ke ciki yanxu" Turata Hansai tayi a mugun fusace tace "Don Allah idan baxa ki dinga fadan alkhairi ba kiyi shiru, jiddah ita har tana da wani daula a duniya, wllh ko tana da shi kinji rantsuwar musulmi ko? To sai na rushe daulan nan, muna nan da ke kuma xa ki ga jiddah sai ta dawo gidan nan, ai ba mijin aurenta bane shi din sai in kasheta yake da niyyar yi ya kara arxikinsa, ba kuma sa'an aurenta bane ko da kuwa ita ma yar me kudi ce, sai dai in ban haifu cikin shafa ba wllh" Daga haka tayi gaba a mugun fusace tana jin xuciyarta na tafarfasa.... Washegari alhamis Jiddah ta tashi taji tana jin yunwa sosai sbda daren jiyan babu abinda ta ci ta kwanta, sai kusan karfe takwas na safe ta shiga kitchen bayan tayi wanka, rasa abinda xata dafa tayi a kitchen din, jingina tayi da bango ta 6ata fuska xata yi kuka tana kallon tulin kayan abincin, tuwo ne kawai a ranta, lkci daya hawayen ya kawo idonta ta juya ta fice daga kitchen din, dakinta ta koma ta fada kan gado tana shessheka a hankali, bayan wani d'an lkci ta daga kai a hankali tana kallon wayar dake gaban madubi yana vibrate, mikewa tayi tana share idonta cikin sanyin jiki ta nufi wayar ta dauka tana kallon screen din, throughout jiya basu yi magana da Abuturrab ba banda yanxu da yake kira, ta daga ta kai kunne, Abuturrab na driving xuwa airport kasancewar karfe sha daya yake da duty, Shiru Jiddah tayi kamar yanda shi ma yayi shirun, bayan few seconds yace "Ni kike jira inyi maki magana?" Ta sauke idonta kasa a hankali tace "Aa" yace "Ohk in gaishe ki?" Tace "Ina kwana" Yace "Me kika ci yanxu?" Ji tayi kamar ta fashe masa da kuka, yace "Ina jin ki" cikin rawar murya tace "Ban ci komai ba" Yace "Me kike jira?" Tace "Ni bana son taliyar" ya d'an yi shiru kafin yace "Me kike so?" A hankali tace "Tuwo nake son ci" Yace "Toh sai ki ci inda kika gansa, ga abinci kusan kala nawa a gida kice duk baki ga abinda kike so a ciki ba, Shinkafa, doya, macaroni, spaghetti, irish, wake, indomie, cous cous.... Wait.. Are you even okay?? Dama tuwo abinci ne?" Ita dai bata ce komai ba, lkci daya hawaye ya kawo idonta, yace "Samun waje kika yi" daga haka ya katse wayar, hawayen dake makale idonta ya silalo, ta ajiye wayar ta koma kan gado ta kwanta tayi lamo tana shessheka. Har kusan karfe sha daya na safe tana kwance, jin yunwa ya dameta sosai ta mike a hankali ta fita dakin, kitchen din ta koma, indomien kawai ta dafa daga karshe sai dai gwara na yanxu a kan wanda tayi shekaranjiya. Da yamma Jiddah ta ji kamar an bude gate ta mike da sauri ta isa window ta bude labulen tana lekan waje, shi ta gani ya shigo gidan ta xaro ido ta sake labulen ta koma can karshen gado ta xauna kamar mara gaskiya, bayan kusan minti goma sha biyar ya bude kofar dakin nata, sunkuyar da kai tayi, yana tsaye bakin kofar yace "Baki iya dafa shinkafa bane ko wani abincin?" Tace "Aa na iya" Yace "Toh me yasa baki dafawa?" Tayi shiru, yace "Ohk, daga yanxu... daga ranan lahadi xuwa asabar xan sanar maki abinda xaki dinga girkawa tunda baki da hankali ke" Ajiye ledan hannunsa yayi ya juya ya fita, ba a dau lkci ba taji alamar ya fita gidan gaba daya, mikewa tayi ta isa gaban ledan da ya ajiye ta leka ciki taga take away ne, fiddowa tayi ta bude taga tuwon shinkafa that looks so palatable, ta bude inda miyan ke ciki taga miyar kubewa danye lafiyayye da ya ji nama da kayan ciki da ganda, kallon miyan da tuwon ta dinga yi, bata san lkcn da tayi murmushi ba ta mike ta wuce bandaki da sauri ta wanke hannu sannan ta dawo ta xauna ta fara cin tuwon, she was eating happily, mulmula hudu ne tuwon, ta rage wanda xata ci da daddare, har bacci barawo ya saceta sbda tsoron dake damunta a rai bata ji alamar ya dawo gidan ba. Washegari Friday ana saukowa masallaci Abuturrab ya shigo gida daga garin kano, babu kowa parlon, yana tafiya a hankali ya nufi bangaren Aunty, da sallama ya shiga parlonta, daga uwar daka ta fito ya xauna saman kujera murya can kasa yace "Ina yini Aunty" tana kallonsa daga sama har kasa tace "Kiran nawa bashi da amfani a gareka sbda kasan abinda ka kullala shi yasa ka daina dauka ko??" Ya shafa kansa cikin sanyin murya yace "Aunty ae na maki text nace xan dawo weekend in sha Allah" ta nemi waje ta xauna fuska daure bbu yabo bbu fallasa tace "Toh gashi ka dawo weekend din yau ai, ya ake ciki kenan?" Ya daga kai ya kalleta a hankali yace "Aunty ni fa ba matata ce ita yanxu ba kuma, kawai gaya maku ne ban yi ba" Da mamaki Aunty tace "Ban gane ba" Ya gyada kai yace "Haka ne, babu aure tsakanina da ita tun ranan da muka tafi can gidan nawa, so nake sai na dawo ne in sanar maku" Aunty ta daga hannu biyu sama tace "To Alhamdulillah ya Allah, tun faruwan lamarin nan sae ynxu naji dama dama" cikin sanyin murya yace "Amma don Allah wannan ya xama sirri tsakaninmu Aunty, Abba won't take it likely with me if he finds out" Aunty ta hade rai tace "Haba dai wa xan gaya ma kamar wata yar yarinya, wllh baka ji sanyin da xuciyata tayi ba yanxu, to ina ka bar ta yanxu? Ka maida ta kauyen nasu ne?" Yace "Tana can gidana Aunty" Aunty ta hade girar sama da ta kasa tace "Wani gidan naka?" Yayi kasa da murya yace "Aunty ina sane da abinda nake wllh, ba lkci daya xan yi komai ba ai sbda kada a xargeni" Aunty tace "Amma xamanta gidan nan naka ai bai yi ba" yace "Na sani Aunty, give me few days to think of another solution" yana fadin haka ya mike yace "I will be coming back" daga haka ya fita, ta sauke wani ajiyar xuciya tana jin kamar an biya mata wani bukatarta na musamman. Part din Ummi ya nufa, ya xauna ya gaisheta da ladabi, ta amsa tana kallonsa tace "Ya ku ke?" Yace "Alhmdlh" Tace "Toh madallah" kallon Tv dake aiki a parlonta kawai yake, can ya kalleta yace "Abba xai dawo yau ne?" Ta girgixa masa kai tace "Sai gobe in sha Allah" Yace "Allah ya kai mu lfya" Ta amsa da "Ameen... Ina Amaryar taka take?" Lkci daya ya d'an 6ata rai, ita dai tunda ta fada haka bata kalli fuskarsa ba, ya dago yace "Ni daga wajen aiki nake yau" Da sauri ta kallesa tace "Wajen aiki kuma, dama ka koma ne?" Yace "Tun lahadi" Tace "Toh ita sai ka bar ta a ina, ko tare da ita ka koma" Yace "Aa, gida take" Ummi tace "Ita kadai?" Ya gyada kai, Ummi tace "Toh kada ka sake barin ta gida ita kadai, idan baxa ka tafi da ita ba ka kawo ta nan" Yace "Toh" Shiru ne ya biyo baya, bayan few minutes ya mike yace "Sai na shigo da yamma Ummi, xan je gaida Umma" Ummi tace "Toh Allah ya kai mu, a gaishe su" Yace "In sha Allah" Daga haka ya nufi kofa, ta bi sa da kallo har ya fita, motarsa ya shiga ya bar gidan xuwa gidansu Ahmad. Sama sama ya amsa gaisuwar Maman Abdallah dake tsakar gida yayi shigewarsa cikin gidan, Maimuna dake parlor tace "Sannu da xuwa yaya" Yace "Yauwa, Umma fa?" Tace "Umma ta fita wllh" Ya d'an yi jim kafin yace "Okay idan ta dawo kice na shigo" Tace "Toh amma yaya Ahmad na ciki ai" Kallon hanyar dakin Ahmad yyi can ya karasa ya shiga dakin, Ahmad na operating laptop ya daga kai ganin Abuturrab yace "Yanxu nake shirin kiranka ashe kana hanya" Abuturrab ya xauna yace "Ban jima da shigowa garin ba" Mikewa Ahmad yyi ya kashe laptop din yace "Dama gidanka nake son xuwa akwai maganan da xa mu yi a can" Wani kallo Abuturrab yyi masa yace "Kaje kayi me a gidana?" Ahmad yace "Kai me ka xo yi nan? ka sameni parlor plss ina jiranka, kasan fa na san hanyar gidan ba wai ban san hanyar ba" Daga haka ya dau makullin motarsa ya fita, Abuturrab ya d'an yi jim, har ransa bai son Ahmad yaje gidan nasa, can dai ya mike ya bi bayansa. Duk fararen shadda ne jikinsu su biyun, babu yanda Abuturrab ya iya da Ahmad dole haka suka bar gidan tare a motarsa, Driving kawai Abuturrab ke yi ba tare da yana ba ma Ahmad amsa ba, Ahmad yayi wani dariya yace "Kai dai yarinya ba matarka ba balle kace kana kishin wani ya ganta, ni ina ga i just have to sacrifice and marry her together with Ramlah since ba Haram bane kuma i have the money to do so, and i will mould her to exactly how i wish and want her to be, har yanxu her brain is fresh, kaga daukan abubuwa baxai yi mata wahala ba, idan kuma su Umma basu amince min ba which i am not praying for that, i have a frnd da muka yi karatu tare da shi a Uk, har yanxu ma yana can, and ya dameni yana son in hada sa da yarinyar da na sani mai hankali ko cikin siblings or cousins dina ya aura, to yanxu ina ga i will hook him up with Jiddah, yanda na lura yanda Yusuf baya son hayaniya ita ma haka, and they will make a perfect couple, balle ma nasan su Abba baxa su hanani aurenta ba ni...." Parking Abuturrab yayi yana kallon Ahmad fuska daure yace "Ni yanxu fa ba gida xan je ba Ahmad, xan fara xuwa can gida in gaida su Aunty da Ummi, sannan xan amshi sako from a frnd coming from Abuja at bypass, don haka ya xa mu yi da kai???" Ahmad ya gyara xama yace "Ohk then, tunda ban fito da mota ba bari in samu adaidaita kawai ya karasar da ni gidan naka, and i will wait for u there...." Abuturrab ya katse sa yace "Wani gidan??" Ahmad yace "Gidanka mana, idan ya so idan ka gama uxururrukan ka sai ka dawo ka sameni, i will go gist with jiddah kafin ka dawo...." Wani irin kallo Abuturrab ke yi masa xuciyarsa na tafarfasa, Ahmad ya fara kokarin bude motar yace "Sai ka karaso, but don't take too long" Bluntly Abuturrab yace "Toh wai dole ne sai kaje gidan nan nawa, meye hadinka da ita yarinyar??" Ahmad yace "Hadina da ita shine ta dalilina ka fara saninta don da ba don ni ba baxa ka santa ba, sannan a lkcn da muke xuwa siyan awara a wajenta ni kadai nake ganinta kai kuwa murhu kake gani, amma dai duk ba wannan ba ma, wai ba inace yarinyar nan ba matarka bace ba yanxu kuma balle kace ko kishin xanje in ga matarka kake, pls what's the color of ur problem Captain?" Abuturrab yace "Don ba matata bace sai nace maka gidana ya koma cinema na xuwa ganinta? I have all right to protect her by all possible means, sannan da kake min gorin ba matata bace mintina nawa ne na mayar da auren idan na so yin hakan? Infact idan ma na mayar din sani xaka yi ko ance maka sanar maka xanyi?" Ahmad ya kallesa da sauri yace "Don Allah in kai ka cika namiji ka mayar da auren yanxu ma" Abuturrab ya ja tsaki yace "Toh sai ka saka ni in mayar ai" Ahmad yace "Ahaf ai nasan baxa ka yin bane, plss bude min mota my frnd, idan ka gama yawo a garin ka dawo gidan ka sameni tare da jiddah" Tsaki Abuturrab yyi ya ja motar suka ci gaba da tafiya, Ahmad yayi wani dariya yana gyara xama yace "Ka fasa karban sakon kenan" Abuturrab bai tanka sa ba har suka isa gida, ya sauka motar ya bude gate sannan ya dawo ya shigar da motar, Ahmad na kallonsa yace "It's very risky leaving this little girl all by her self in this house captain, why don't you want to leave her with umma or Ummi, kasan fa baxa su ki riketa ba" Abuturrab yace "A nan din nake son ta xauna ba sai taje wani waje ba" Yana fadin haka ya sauka motar ya tafi ya kulle gate din Ahmad ya sauka motar ya nufi entrance din shiga gidan, Abuturrab ya bi bayansa da sauri, amma tunawa da yyi kofar ma a rufe yake dole sai ya bude yasa yayi slowing pace dinsa, tsaye Ahmad yyi yana jiransa a balcony jin kofar a rufe, Abuturrab ya isa wajen ya sa makulli ya bude kofar parlon ya shiga sannan Ahmad ya bi bayansa.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Albishirin ku jama’a ko kusan akwai wani company da ya shahara wajen siyar da kayan alatu da abubuwan more rayuwa??_ _Wato Unique & Luxury Stores yana da bangararori daban-daban kamar haka_ *@unique_home_store_ng wanda ya shahara wajen siyar da kayan ado da qawata gida, kayan kitchen, furniture, carpet na gani na fada da sauran su* Sannan akwai @elegant_projects_ng Bangaren tsara gida kamar home styling na amare da uwar gida, interior designing da finishing.... Company bai tsaya a sashe 2 kawai ba yana da bangaren ado da kwaliya wato @uniquefashion_ng. Duk bai tsaya anan ba ya kara zuwa maku da @unique_souq_ng inda zaku samu kayan kwadayi, makulashe da kayan da zasu kara inganta maku lafiyar jiki. Karku bari ayi babu ku domin gane ma idon ku, ku garzaya shafukan su a Instagram kamar haka.... @unique_home_store_ng @uniquefashion_ng @unique_souq_ng @elegant_projects_ng Sannan zaku iya samun su ta WhatsApp a +2349071721586 Babu kowa babban parlon, Ahmad ya xauna saman kujera yana bin parlon da kallo snn ya kalli Abuturrab yace "It looks very good.. " Kitchen Abuturrab ya nufa ya bude fridge ya dau ruwa, fruits din da ya bar mata na cikin fridge har sannan, ya juya ya fita ya dawo parlor ya xauna yana bude ruwan hannunsa, Ahmad yace "Mu yi magana ta fahimta Captain..." Abuturrab ya kallesa bayan ya sha ruwan hannunsa, Ahmad yace "Tell me ur plan on this innocent girl" Abuturrab yace "I have no plan then to make her somebody useful in life, daga nan kuma sai tayi aurenta idan ta samu miji...." Ahmad ya masa wani kallo yace "How Captain? By locking her up for days ita kadai a gida?" Abuturrab yace "I wanted enrolling her in a schl but ni fitan ne gaba daya bana so ma, so it's better i get a lady with better teaching qualification ta dinga koyar da ita a nan gida, i will also get another lady da xasu dinga karatun islamiyya tare duk a gida" Bude baki Ahmad yyi yana kallonsa, can yace "Why? Why dont u want her to go to school and islamiyya with her mates?" Abuturrab ya mike yace "Haka nan kawai, ra'ayina ne" Daga haka ya haura sama, Ahmad ya bi sa da kallon mamaki kafin ya kauda kai, a nan kuma yaji ya fara tantama anya Abuturrab ya saki yarinyar nan ma kuwa, but kuma yasan Captain to be someone that is very straightforward in yayi xai ce yayi, idan kuma bai yi ba xai ce bai yi ba, baya karya. Abuturrab na tafiya sama ya kwankwasa kofar dakin nata kafin ya bude, tana tsaye jikin window ta juyo da sauri, suna hada ido ta sunkuyar da kai, yace "Ki sameni kasa" Daga haka ya juya ya fita, Abaya ne jikinta blue, sosai kayan ya amsheta, a kwanaki kadan din nan da take shafa cream da Abuturrab ya siya mata tana wanka da shower gel ainahin haskenta yake kara fitowa ko ina na jikinta yyi smooth, wanda rashin fita ta shiga rana ya kara contributing da kyan fatar nata, slowly ta nufi kofa kana ganinta kasan she isn't happy, yau gaba daya ta tashi da kewan yan gidansu duk da basu ta6a nuna mata so ko na minti daya ba amma har kukan kewansu sai da tayi daxu, Abuturrab na komawa parlor ya xauna, Ahmad dae sai kallonsa yake, bayan some minutes ya mike da sauri tunawa da yyi ba karamin aikinta bane ta sakko ba hijab, ganinta yayi tana saukowa stairs, Ahmad ya juya yana kallonta, Abuturrab ya koma ya xauna, ta karaso cikin parlon ganin Ahmad ta sunkuyar da kanta ta rakube kasa jikin kujera cikin sanyin murya tace "Ina yini" Yana kallonta babu ko kiftawa da murmushi fuskarsa yace "Lafiya lau Jiddah ya kike?" Tana wasa da gefen mayafinta, ita ma tana d'an murmushi tace "Lafiya lau" Ta d'an saci kallon Abuturrab dake kallonta suna hada ido ya jefa mata wani kallo ya dauke kansa ita kuma ta sunkuyar da kanta a hankali tace masa "Ina yini?" Bai amsa mata ba, Ahmad dake kallonta yace "Amma kin ci abinci?" Cikin sanyin murya tace "Eh na ci" Abuturrab ya kallesa yace "Is that question necessary??" Bai jira cewar Ahmad ba, ya kalli Jiddah babu yabo bbu fallasa yace "To sai anjima, tashi ki tafi" Mikewa tayi ta wuce sama tana tafiya a hankali, Ahmad ya bi ta da kallo, sosai yaji tausayinta har ransa, he can see she is sad, she looks so unhappy, ya dawo da dubansa kan Abuturrab dake hararansa, Daure fuska shi ma yyi yace "Abuturrab ka taimaki yarinyar nan sbda kaga ana neman cutarta right?ka taimaketa because she is sad, frustrated and almost depressed a gidansu, to ka gaya min bambancin gidansu da wannan gidan ynxu, didn't u notice how sad she looks fisabilillah, how on earth will u lock a being for days ita kadai a gida bata ganin kowa, ai sai wani cutar ya kamata wllh, baka san babu abinda ya kai wannan yanayin da ka barta ciki saurin kashe mutum ba ko, she have nobody to share anything with, just reason it fa, ta yaya xata yi ta rayuwa ita kadai, plss think of a more better solution tunda baka son kaita gidanmu ko gidanku..." Abuturrab yace "Idan ta fara karatu she won't look unhappy anymore" Ahmad bai kuma ce masa komai ba, Abuturrab yace "Ni fa can gidanmu xan wuce yanxu" Tabe baki Ahmad yyi ya mike yace "Dama idan abu ya samu yarinyar nan Aliyu kada ka kirani da sunan kana neman shawara ko wani abu" daga haka ya nufi kofa, Abuturrab ya mike ya bi bayansa. Sai bayan isha Abuturrab ya dawo gida, yana shigowa parlor ya kulle kofar parlon ya wuce sama, part dinsa ya fara wucewa ya ajiye ledan hannunsa, sai da yyi wanka ya canxa xuwa pajamas dinsa, mintuna ba da yawa ba yyi yana waya da Aneesah daga bisanni yace "Xan kira ki anjima" Daga daya bangaren ta marairaice tace "Ni ban yarda da xan kiraki anjiman nan dinka ba, just tell me karfe nawa xan sake kiranka" Yace "Wani d'an aiki nake son yi a system, idan na gama ai nace xan kira" A hankali tace "Toh Allah ya sa, but it's always xan kiraki anjima daga nan kuma shikenan sai gobe" Yace "Uhn xan kira don't worry" Daga haka ya katse wayar, mikewa yyi ya dau ledan abincin ya fita bangarensa, sai da ya fara knocking din sannan ya bude kofar dakin ya shiga, kwance ya ganta ta takure waje daya ta rufe har kanta, ya ajiye ledan hannunsa ya karasa ya bude duvet din, rufe fuskarta tayi da hannunta taki juyowa, tsayawa yayi yana kallonta, can yace "Kee" Still taki juyowa, ya hade rai yace "Baki ji na ne?" A hankali ta dago ta mike xaune amma bata yadda ta kallesa ba, kallon idanuwanta da suka yi ja ya dinga yi, can yace "Kuka kika yi?" Wasu hawayen suka taru idonta, ta ki yarda ta kallesa, yace "Ba magana nake maki ba" Ta fashe da kuka ta hade kanta da gwiwa tana shessheka, da mamaki yake kallonta, ganin irin kukan da take, ya xauna gefen gadon yana kallonta yace "Gaya min me ya faru" Ta girgixa masa kai kawai tana kukan a hankali, dauke kansa yayi, yayi shiru, bayan wani d'an lkci ya sake kallonta yace "Dago kanki ki kalleni" Taki dagowa, ya mata tsawa yace "Dago kanki nace" Da sauri ta dago hawaye na sauka idonta amma ta kasa kallonsa, ya mike ya koma side din da take kallo suka hada ido, a hankali ta sauke idonta, speaking very calmly yace "Toh gaya min me yafaru, kina son wani abu ne?" Ta girgixa masa kai yace "Kukan me kike yi then?" A hankali tace "Babu komai" Bai kuma ce mata komai ba, can ya kalli ledan da ya ajiye yace tashi kije ki dau abinci ki ci, ganin bata tashi ba ya hade rai yace "Tashi nace" Mikewa tayi ta nufi gun ledan ya bi ta da ido, yau ma riga da wandon ne na bacci jikinta, tana isa gun ledan yace sa darduma ki xauna a nan ki ci, ta tafi gun darduman ta dauka sannan ta dawo ta shimfida ta xauna a kai, daurewa kawai take amma ji take kamar ta fashe da kuka, ta bude ledan taga tuwo ne da miyar kubewa irin na ranan, sauke idonta tayi ta kasa kallonsa, ganin bata da niyyar fara cin abincin yace "Malama abinci nace ki ci" A hankali tace "Xan dauko ruwa" Ya mike ya fita xuwa kitchen ya dauko mata ruwan ya dawo, yana ajiyewa ya koma ya xauna, tashi tayi ta tafi bandaki ta wanke hannunta sannan ta dawo ta fara cin tuwon a nutse, shi dai kallonta kawai yake, he just have a special pity for women, bai son ganin hawayensu even by mistake, it get him weak, and sure yasan maganganun da Ahmad yyi masa daxu babu karya ko daya a ciki but he cannot let her stay with his mum or Ahmad's mum, he will get another solution.... Tana gama cinye tuwon daya xata rufe yace "Daya kika gani a wajen?" Ta girgixa masa kai tace "Baxan iya cinyewa ba" Yace "Kara daya" Bata masa musu ba ta fara cin wani dayan, amma bata iya ta cinye ba kuma bai tilastata ta cinye din ba, ta mike ta dau sauran abincin da ruwa ta fita daga dakin, mikewa yayi ya bi bayanta ya xauna main parlor ya kunna Tv, bayan few seconds ta fito kitchen din xata wuce sama ya nuna mata kujera yace "Dawo ki xauna nan" Tace "Xan wanke baki" yace "Je ki wanke ki dawo" Tafiya tayi saman ya maida dubansa kan tv, tana sakkowa ta tsaya tana kallonsa ya nuna mata kujera yace "Xauna" xaunawa tayi, ya ci gaba da kallonsa, tun tana daurewa sbda baccin da ya fara damun idonta gashi ta kasa gaya masa har daga karshe ta d'an kwanta still pretending to be watching d movie da bata ma san abinda ake a nan ba, da haka bacci ya dauketa, duk yana lura da ita amma bai ce komai ba, he gets she's so lonely, abinda ke damunta kenan, shi kuma he doesn't have intention of spending any of his time together with her, yau ma don kawai kukan da yaga tana yi ne yasa ya kasa jurewa, har karfe sha biyu yana kallo parlon, sai a sannan ya tuna da Aneesah da yace xai kira ya lumshe ido ya jinginar da kansa da kujera, sai kusan karfe daya ya bude idon don bacci daukesa yyi a hakan, kallon 2 sitter din da take kwance yayi yaga baccinta kawai take, mikewa yyi ya kashe switch din wutan parlon gaba daya sannan ya kwanta kan 3 sitter ya kashe tv da remote din kusa da shi ya lumshe ido.... Kiran sallahn farko Abuturrab ya tashi, ya fi minti goma xaune kafin ya duba wayarsa ya kunna fitila yana haskata, mikewa yyi ya karasa inda take kwance ya buga kujeran a hankali, bude ido tayi da sauri yace "Tashi ki wuce sama" tana lullumshe ido ta mike xaune sannan ta tashi ya haska mata hanyar stairs, ta fara tafiya sannan ya bi bayanta, tana shiga dakinta ko rufe kofar bata yi ba ta fada kan gado ta ci gaba da baccinta, yana tsaye daga bakin kofar bayan ta shiga, ya kulle kofar sannan ya wuce bangarensa. Sae kusan karfe tara da rabi Abuturrab ya sauko downstairs, kamshin girki kawai yake ji a gidan, ya tabe baki ya xauna saman kujera, sae ga ta tafito kitchen, turus tayi ganinsa, sae kuma ta juya ta koma kitchen din, shi dai idonsa na kan tv da yyi powering, can sai ga ta ta fito ta karaso cikin parlon, kallonta yyi... Her expression today isn't of someone that is sad, ta xauna kasa ta sunkuyar da kai, dimples dinta na lotsawa tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya lau" Ya gane da magana a bakinta ganin yanda take wasa da fingers dinta, can yace "Me xa ki ce?" Ta kallesa tace "Dama cewa xan yi in kawo maka kumallo?" Da mamaki ya dinga kallonta, can yace "Na me kenan?" Tace "Dankalin turawa na soya na soya kwai, sai na tafasa ruwan shayi" Yace "Ohk mun yi da ke xan ci ne?" Ta girgixa masa kai yace "Toh baxan ci ba, kayan abincin da kika gani a kitchen don ki girka ke kadai na siyosu na ajiye ba don ki girka ma ni da ke ba" Sunkuyar da kanta kawai tayi, bayan few seconds ta mike a hankali xata bar wajen yace "Tsaya" Tsayawa tayi amma bata yarda ta kallesa ba, yace "Dama kin iya soya Dankalin da kwai kike tsayawa da yunwa?" Bata ce masa komai ba, ya tabe baki yace "Je ki" Juyawa tayi ta koma kitchen din. Tana komawa ta fara kuka a hankali, sae da tayi me isarta sannan ta goge idonta ta fito xata wuce sama, ya bi ta da kallo yace "Kin karya?" Ta gyada masa kai xata haura sama yace "Dawo nan!" Ji tayi wani sabon hawayen na shirin xubo mata, ganin tsayawa tayi yace "Ba kya ji na ne?" Dawowa tayi ta sunkuyar da kanta, yace "Wuce ki xuba abinda kika yi ki xo nan ki xauna ki ci" xata yi magana ya jefa mata wani kallo, kitchen din ta nufa trying hard kar ta fara rusa kuka, a haka ta debo abinda tayi ta dawo parlon ta xauna tana turawa da kyar yana kallonta yana kallon TV sai da ya ga ta gama sannan ya bar ta ta wuce sama, shi kuma ya fita xuwa siyo fastfood.... A ranan mutumin da Abuturrab ya sa ya nemo masa mai gadi amma mai mata ya kirasa ya sanar masa an samu, Abuturrab ya masa izinin kawosa gida amma wajajen biyar na yamma. Yana xaune parlor yana jiran Jiddah bayan azahar, he is been sitting for almost 20 mins now, daga cewa ta shirya shine har ynxu, mikewa yayi ya haura sama ya bude kofar dakin suka kusa cin karo don xata fito ne ita ma, ta koma baya da sauri, ya wani hade rai yace "Baki da hankali ne xaki shanya ni a parlor?" Ta marairaice tace "Na kasa rufe rigar ne?" Yana kallonta daga sama har kasa yace "Wani riga?" Hijab ne jikinta har kasa sai atamfa daga ciki, tace "Zip din rigar" Ya jefa mata wani kallo ya juya, bin bayansa tayi, har suka sauka parlor, ya dau makullin motarsa ya nufi kofar fita ta bi sa da sauri, yana cikin motar ta iso parking space din xata bude back seat yace "Kinsan meye ma'anar mutum ya shiga bayan mota bayan su biyu ne kawai a motar?" Tayi shiru tana kallonsa, bai kuma ce mata komai ba, ta xagayo xata shiga motar sai a sannan ya ga how obvious zip din da bata kulle ba yayi cikin hijab din, bayan ta shiga gaban motar yace "Daga hijab din nan" a hankali tace "A bude zip din yake" ya hade rai yace "Daga nace" kamar warce xata yi mugun abu ta fara daga hijab din, sai kuma ta kallesa kamar xata yi kuka, ganin yanda ya hade rai ta daga hijab din kawai, bayan ta yake kallo da bra strap dinta, ta sunkuyar da kanta, yace "Da a haka xaki bi ni don baki da hankali?" Ta girgixa masa kai, yace "Koma ki canxa kayan" Ta buda ido tana kallonsa, ganin irin kallon da yayi mata ta bude motar ta sauka, sauka yyi ya bi bayanta to check another clothe for her, sai bayan da suka shiga parlon ta kallesa tace "Xaka iya taya ni jan zip din fa, ba lalacewa yayi ba" yace "Ban yi niyya ba" bata kuma cewa komai ba ta wuce sama ya bi ta. Bude press din nata yayi yana kallon kayan ciki, abaya baki ya ciro mata da mayafinsa ya ajiye gefen gado, ta dan xaro ido tace "Wannan ai yana kama jiki" ya harareta yace "Baya yake kamawa ba jiki ba, minti uku na baki ki canxa kayan nan ki dawo kasa ki sameni" Bai jira cewarta ba ya fice daga dakin nata dake ta kamshin turarurruka, a balcony ya tsaya yana jiranta, sai gata ta fito, sosai bakin abayar ya haska farin fatarta ta dawo kamar balarabiya, flat show ne kafarta, she looks so beautiful and neat, kawai dai ta rame ne ba kadan ba, ganin ta tsaya ta wani sunkuyar da kai yace "Tsayuwar me kika min a nan?" Tafiya ta fara yi, ya bi ta da kallo kafin ya bi bayanta, front seat ta bude ta shiga, sai da ya fara bude gate sannan ya dawo ya shiga motar suka bar gidan, ya sauka ya kulle gate din, gidansu Ahmad ya nufa don xuwa gaida Umma, ya lura kamar she is a bit angry at him, don gashi wannan satin ma bata ce masa xata xo ba, a parking space din yayi parking, Yana sauka motar Jiddah ma ta sauka tun da taga gidan da suka shigo farin cikin fuskarta ya kasa boyuwa, shi dai ko kallonta bai yi ba, kallonsa tayi a d'an tsorace bayan ta sauka tace "Don Allah xan iya xuwa in gaida maman Abdallah?" Ya fara tafiya xuwa cikin gidan yace "Ki je mana" Da sauri ta nufi dakin Maman Abdallah, sai da ta gaida mai gadin ya amsa da fara'a yana mata sannu da xuwa tace "Maman Abdallah fa?" Yace "Ki shiga tana ciki" Da sallama ta shiga dakin, Maman Abdallah na ganinta ta rungumeta cike da farin cikin ganinta tace "Idonki kenan Jiddah, kai kai kai kinga yanda kika yi kyau kuwa, sannu da xuwa amarya" Wannan kalmarta na karshe ne ya d'an sa mood din jiddah ya canxa don tasan dai ita ba amarya bace, Xaunawa tayi tana ta kirkiran murmushi tace "Abdallah na bacci" Maman Abdallah tace "Wllh kuwa, ashe ku ne kuka shigo gidan a mota, sannunku da xuwa" Jiddah na ta murmushi tace "Bari inje in gaida Umma" Maman Abdallah tace "Toh maxa ki tafi, amma fa don Allah ki leko kafin ku koma kinji?" Jiddah tace "Toh" fita tayi dakin dai dai sanda Ahmad ya shigo compound din, ya buda ido sosai ganinta, sai kuma ya hango motar Abuturrab, da ladabi ta gaishesa ya amsa da fara'a yace "Yaushe ku ka xo?" Tace "Yanxu muka shigo" yace "Maa sha Allah sannunku da xuwa" Tafiya take yana gefenta shi ma yana tafiyan, can yace "Amma baki da damuwa ko Jiddah, kar ki boye min komai ki gaya min" Ta sunkuyar da kanta cikin sanyi tace "Ina son dawowa nan wajen Umma" Shiru yayi bai ce komai ba, don yasan taurin kan Abuturrab ya wuce ya amince Jiddah ta dawo nan gidan, a hankali yace "Kar ki damu Jiddah, nasan xama ke kadai ne baki so ko?" Ta gyada masa kai, yace "Kar ki damu nasan me xanyi" Da damuwa tace "Amma kar kayi masa magana ihu xai yi min" Murmushi Ahmad yyi yace "No baxan yi masa ba" Abuturrab suka gani bakin kofa tsaye alamar lkcn ya iso wajen ganin jiddah bata shigo ba, Jiddah sai da taji gabanta ya fadi ganinsa, shi kuwa sai ya hade rai, suna isa balcony din Ahmad yace "Sai ga amarya yau ta xo gidanmu, kun xo gaida Umma kenan" Abuturrab da yayi masa wani kallo underneath his breath yace "Half-wit" daga haka ya juya ya koma parlon. Rungume Umma jiddah tayi, sosai tayi farin cikin ganinta kamar yanda Umma ma taji dadin ganinta, Shi dai Abuturrab na yi yana kallon agogo don bai ma son la'asar yayi masu a gidan, Kitchen Jiddah ta tafi bisa umarnin Umma na cewa taje ta taya su Siyama da mai aiki girki, Umma na kallon Abuturrab tace "Why is she this lean? Bata da lafiya ne?" Ya sunkuyar da kansa yace "Eh tayi xaxxabi kwana biyu, amma ta samu lafiya yanxu" Ahmad dai sai wani kallo yake masa, Da damuwa Umma tace "Toh Allah ya sauwake, ita kadai din ce a gidan kenan yanxu?" Da sauri yace "Aa Umma ai nace akwai me aiki, kuma ma yawanci one day on, one day off nake yi" Umma tace "Toh shkkn Allah ya taimaka, karatun fa?" Yace "Xata fara in sha Allah" Umma tace "Toh maa sha Allah, Allah ya taimaka" Abinda Abuturrab bai so bane ya faru don sai da la'asar din yayi yana gidan, dakin Ahmad ya tafi yin alwala, Ahmad dake ta jiran ya shiga alwala ya jawo makullansa na gida bayan ya shiga bandaki, cikin few seconds yayi abinda xai yi ya ajiye sauran sannan ya fita dakin.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Albishirin ku jama’a ko kusan akwai wani company da ya shahara wajen siyar da kayan alatu da abubuwan more rayuwa?? Wato Unique & Luxury Stores yana da bangararori daban-daban kamar haka, @unique_home_store_ng wanda ya shahara wajen siyar da kayan ado da qawata gida, kayan kitchen, furniture, carpet na gani na fada da sauran su. Sannan akwai @elegant_projects_ng Bangaren tsara gida kamar home styling na amare da uwar gida, interior designing da finishing.... Company bai tsaya a sashe 2 kawai ba yana da bangaren ado da kwaliya wato @uniquefashion_ng. Duk bai tsaya anan ba ya kara zuwa maku da @unique_souq_ng inda zaku samu kayan kwadayi, makulashe da kayan da zasu kara inganta maku lafiyar jiki. Karku bari ayi babu ku domin gane ma idon ku, ku garzaya shafukan su a Instagram kamar haka.... @unique_home_store_ng @uniquefashion_ng @unique_souq_ng @elegant_projects_ng Sannan zaku iya samun su ta WhatsApp a +2349071721586 Jiddah ce xaune bedroom din Umma dake mata tambayoyi, ita dai ta sunkuyar da kanta, Umma tace "Kar kiji komai ki fada min gaskiya Jiddah" Tayi murmushin karfin hali ta dago kanta tana kallon Umma tace "Da gaske ba komai Umma" Umma tace "Kin tabbatar?" A hankali Jiddah ta gyada mata kai, Umma tace "Yace ya kawo maki mai aikin haka ne?" Ta kalli Umma sannan cikin sanyin murya tace "Eh" Shiru Umma tayi tana kallonta don sai take ganin kamar ba gaskiya take fadi ba, tausayin Jiddah take a xuciyarta, ta kwantar da murya tace "Ni baxan ce masa mun yi maganan komai da ke ba Jiddah, ki bani amsan tambayoyina kafin su dawo masallaci yanxu" Jiddah ta kuma wani murmushi tace "Umma na baki amsan ai" Umma tace "Toh kina jin dadin xaman gidan?" Kallonta Jiddah ta dinga yi ta kasa cewa komai, Umma tace "Ina saurarenki..." Lkci daya hawaye ya kawo idonta, dai dai nan aka bude kofar dakin, Ahmad ya shigo tare da Abuturrab, sosai gabansa ya fadi, ya kalli Umma sannan ya kalli Jiddah, Umma dai ta daure fuska tana danna wayarta, Ahmad dai na tsaye bakin kofa bai karaso ba, ya dinga fatan Jiddah ta sanar ma Umma bata boye mata komai ba, Abuturrab ya shafa kansa a hankali yace "Umma dare na yi xa mu wuce gida" Umma tace "Ohk" wasu sabbin hawayen ya dinga sauka idon Jiddah, gaba daya Abuturrab ya kasa nutsuwa, kana ganinsa ka ga mara gaskiya, Umma na kallon Jiddah tace "Tashi ku je sai da safe" Ta kalli Abuturrab tana goge idonta, ya jefa mata wani kallo a fakaice, a hankali ta mike hawaye yaki tsaya mata tace "Sai da safe Umma" Umma bata iya ta amsa ba Jiddah ta nufi kofa, Abuturrab na kallon Umma yyi kasa da murya yace "Sai da safe Sai Umma" Ba tare da ta kallesa ba tace "Allah ya kai mu" Ya kalli Ahmad that is still standing wanda har ransa yake jin hawayen da jiddah take, Abuturrab ya ki ce masa komai ya fita dakin, Maimuna da siyama ne suka dau ma Jiddah abubuwan da Umma ta hada mata tun daxu xuwa motar Abuturrab, Jiddah dai na xaune gaban motar kamar ana dada tunxurata da kukan da take, Abuturrab ya tada motar ya bar gidan, sai a sannan ya sauke ajiyar xuciya, he even love it da Umma taki ce masa komai, har suka isa gida bai ko kalli Jiddah ba, yana parking ya sauka ya tafi ya kulle gate din gidan ya dawo, tsaye ya ganta jikin motar fuskar nan nata kamar warce aka aiko ma da sakon mutuwa, ya hade rai yace "Ni xan dauko maki kayan naki dake cikin motar" ta juya ta bude bayan motar tana goge guntun hawayenta ta dau ledan hijabs din da Umma tayi mata da warmer din tuwo da miyar kuka da Umma ta sa a xuba mata, da harara ya bi ta yace "Xaki ga ko xaki sake leka kofar gate din gidan nan balle har in kai ki gidan Umma ki samu daman hawayen iskanci" Kamar jiran jin hakan take ta fashe da kuka sosai tana kallonsa tace "Don girman Allah kayi hakuri, wllh kewarta nake bana son in rabu da ita shi sa nake kuka, don Allah kayi hakuri" ko tanka ta bai yi ba ya nufi kofar shiga gidan ta bi bayansa da sauri tana kuka, ko tsayawa bai yi a parlor ba ya wuce bangarensa, ta shiga dakinta ta ci kukanta me isarta bayan ta sannan ta kwanta. Karfe sha daya da kusan rabi yayi knocking kofar dakin ya shiga, ganin tayi bacci ya bude warmer din abincin da ta ajiye kasan dakin, yaga bata ta6a ba duk da yasan ta ci abinci a can gidan, ko kayan jikinta bata cire ba, wannan dalilin ne yasa ya tasheta, mikewa xaune tayi da sleepy eyes dinta tana murxawa, yace "Me ya hanaki wanka kafin ki kwanta?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Dama bakya wankan daren da nace maki kenan?" Da sauri ta bude ido sosai tace "Wllh ina yi bansan sanda nayi bacci ba" Yace "Toh tashi kije kiyi wankan" Kallon agogo tayi da sauri, ya hade rai yace "Tashi nace" A sanyaye ta mike xata shiga bandakin yace "Da kayan xaki yi wanka?" bata ce komai ba, amma ta ki cire kayan a gabansa, ya daure fuska yace "Ba magana nake maki ba" Ta d'an kallesa tayi narai narai da ido tace "Tawul din yana bandaki ne" tana fadin haka ta shige bandakin, gefen gadon ya xauna yana naxarin maganganun da Umma tayi masa a waya bayan sun dawo gida, he is finding it hard to forget her words and move own, yasan no matter what Ahmad baxai ta6a gaya mata xaman da yake da Jiddah a gidan nan ba, yasan baxai ta6a ce mata ma bbu aurensu da Jiddah kamar yanda ya sanar masa ba, but her words carried weight this night, he have a very good intention toward jiddah, ba shi da nufin ya cuceta ko ya walakantata ko ya saka rayuwarta a garari, his intentions are nothing but pure, dafe kansa yyi, lkci daya ya dago jin wayar dake hannunsa yayi vibrate ya duba ya ga Aneesah ce ke kiransa, bai sake kallon wayar ba coz sun yi magana not too long, bayan kusan minti sha biyar jiddah ta fito daga bandakin sanye da kayan da ta cire, kasa kallonsa tayi ta ja gefe ta tsaya, wani kallo ya dinga mata kafin yace "Meye hakan kika yi?" Ta ki yarda su hada ido tace "Ni baxan iya fitowa babu kaya ba bayan kana xaune dakin" Daga sama har kasa ya dinga kallonta yana mamakin abinda ta fada, can dai yace "Ke kina da wani abinda xaki boye min a jikin ki dama, kwaila da ke?" Ta d'an turo baki ta juya masa baya, Tsaki yyi ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo, murya can kasa tace "Eh amma ai ni ba muharramarka bace da xan cire kaya...." Ganin ya juyo tayi tsit, ganin impression din fuskarsa gabanta ya fara faduwa, yace "Kika ce me?" Ta girgixa kai da sauri tace "Ban ce komai ba" Dawowa dakin yyi, ta marairaice tana kallonsa tace "Don Allah kayi hakuri ni bance komai ba" Yace "Kika ce ni ba muharraminki bane?" Ta girgixa masa kai da sauri bakinta na rawa tace "Aa bance haka ba" Sai da ya iso gabanta ya tsaya, sbda tsoro taji ta ma kasa tsayawa, calmly yace "A ina kika san wanda muharraminki ne da wanda ba muharraminki ba?" Jin taki cewa komai ya mata wani tsawa da yasa ta duka hawaye ya kawo idonta, yace "Idan baki bani amsata ba na fara ball dake sai kin ganki downstairs yanxu" Cikin rawan murya tace "Ai da ina xuwa islamiyya" Ya gyada kai yace "A islamiyyan kuma basu sanar maki hukuncin wanda yace xai kashe kansa ba?" Kasa cewa komai tayi, ya wani hade rai yace "Mike ki cire kayanki" Ta sake marairaice masa amma ganin kallon da yake mata ta mike da kyar, ta gefen ido ta kalli bandakinta, lkci daya kamar kiftawan ido ta shige ta sa makulli hannunta na rawa, ya dinga kallon kofar, can yyi murmushi yana shafa kansa, lkci daya kuma ya hade rai ya fice daga dakin, bai karasa bangarensa ba wayarsa yyi vibrate ganin me kiransa sai da gabanaa ya fadi, har ya katse bai dauka ba, sai da aka sake kira sannan ya daga, murya can kasa yyi sallama yace "Ina yini Aunty" ba tare da ta amsa ba tace "Aliyu kana ina??" ya d'an bude ido yace "Aunty ai ina kano, ban dawo ba..." Bude kofarsa yyi ya shiga ya kulle hade da lumshe ido jin abinda take cewa. Washegari da safe wanda Abuturrab ya sa ya samar masa mai gadi ya iso gidan da mai gadin, Abuturrab na kallon matashin mai gadin yace "Yaranku nawa da matar taka?" Mai gadin yace "Daya ne kawai Alhaji, sabon aure ne" Abuturrab yace "Ba damuwa, yau nake son xaka fara aikin sai ka koma ka taho da iyalan naka" Mai gadin ya risina da ladabi yace "Toh nagode Alhaji, xan je kauyen namu yanxu sai in taho da su in sha Allah, Allah ya saka da alkhairi" Abuturrab yace "Ameen, amma kada ka wuce karfe biyar na yamma don xan koma gun aiki a yau" Mai gadin yace "In sha Allah Alhaji" dubu biyar Abuturrab ya basa kudin motar xuwa taho da iyalan nasa, shi ma wanda ya kawo sa ya basa dubu biyar, bayan sun tafi ya koma cikin parlor.... jiddah na kitchen tana dumaman tuwon da umma ta bata jiya, yatsine fuska yyi yana kallon kitchen din don ko by mistake baya son warin miyar kuka, barin ma yanxu da take dumamawa, hakan ya sa ya dau makullin motarsa ya bar gidan xuwa inda xai je yyi breakfast, jiddah na jin fitan motarsa ta jigina jikin bango tunda taji yana waya ko minti sha biyar ba ayi ba yace yau xai koma gun aiki ta ji duk mood dinta ya canxa, gaba daya bata son xama ita kadai a gidan, a sanyaye ta kashe gas din ta xuba tuwon amma ta kasa ci, Duk da xamansa a gidan da rashin xamansa kusan daya don ba wai wani magana me tsayi yake mata ba, kuma ba waje daya ma suke xama ba amma idan yana gidan bata jin kadaici da kewa na damunta, duk sonta da tuwon saboda yanayin da ta shiga sai ta kasa ci da yawa, haka nan ta mike ta kai kitchen ta wanke plate din, sama ta wuce ta wanke bakinta, komai da take yi a gidan tayi, turaren wuta ne kawai bata sa ba, ta dau turaren ta sauka parlor ta sa sannan ta xauna tana kallon yanda yake fita a hankali, kana ganinta kasan jikinta a sanyaye yake, bude kofar parlon aka yi Abuturrab ya shigo ta daga kai ta kallesa sannan ta sauke idonta, sai da ya karaso cikin parlon tace "Sannu da dawowa" Bai amsa ba yyi wucewarsa sama ta gefen ido ta bi sa da kallo har ta daina ganinsa, a sanyaye ta mike ta wuce sama ta shiga dakinta ta kwanta tana kallon fuskarta ta madubin press din dakin. Da yammacin ranan tana tsaye jikin window aka bude kofar dakin, tunda ta kallesa sau daya ta dauke idonta, yana bakin kofar a tsaye yace "Shuka kika yi wajen nan da kike tsayawa ko da yaushe?" Tana wasa da fingers dinta ta girgixa masa kai, juyawa yyi ta bi sa da kallo ganin jakar hannunsa, da sauri ta bi sa tace "Tafiya xaka yi?" Ya juyo yace "Kina bukatar wani abu ne?" Lkci daya jikinta yyi wani sanyi, shi dai kallonta yake yana lura da ita duk a lkci daya, sauke idonta tayi saboda hawayen da ya kawo idonta, yace "Nace kina bukatar wani abu ne" ta girgixa masa kai hawayen dake makale idonta ya gangaro ta juya da sauri ta koma ciki, da ido ya bi ta, kafin ya bi bayanta xuwa dakin, durkushe ya ganta ta daura kanta saman gado, da mamaki yake kallonta, can yace "Ke kina da lafiya kuwa" kin dagowa tayi tana shessheka, ajiye jakar yyi yana kallonta, can ya karasa kusa da ita ya tsaya yace "Tambayar ki nake, kina da lafiya kuwa?" Still taki dagowa, ya daka mata tsawa yace "Baki ji na ne" mikewa tayi hawaye na kai koma a idonta, ya dinga kallonta kafin yace "Me aka maki?" Ta girgixa masa kai, ya mata wani kallo yace "Me aka maki nace?" Cikin rawar murya tace "Ba komai" rungume hannu yyi yana kallonta, can yace "Kina bukatar wani abu ne" Wasu sabbin hawayen na xubo mata cikin rawar murya tace "Tafiya zaka yi ka barni ni kadai babu kowa, alhalin tsoron gidan nake ji" kallonta kawai yake ya ma rasa me xai ce mata, can dai yace "Shine yasa kike kuka?" Ta gyada masa kai tana kallonsa with tears in her eyes, yace "Ohk, ynxu in tafi da ke kenan?" Tayi shiru still crying tana kallonsa, yace "Bude baki ki bani amsa, in tafi da ke kenan yanxu?" A hankali ta gyada masa kai, daga sama har kasa yake kallonta, tausayinta yake ji har kasan ransa amma bai nuna hakan ba, to ina ma xai kai wannan yanxu wani yayi xaton matarsa ce?? Ta ina xai fara tafiya da ita? Ita dai kanta na kasa, bayan few seconds yace "Ina wayar da na baki" juyawa tayi a sanyaye ta nufi gaban madubi ya bi ta da kallo, har ta dauko wayar ta dawo, ta mika masa, amsa yyi ya shiga call log, yace "Matso" ba musu ta matso kusa da shi tana kallonsa, ya hade rai yace "Wayan xaki kalla ba ni ba" Kallon wayar tayi, ta madubin press din dakin ya kallesu, duk tsayinta iyakarta kirjinsa, jin bai ce komai ba sai kallon wayar take ta daga kai a hankali ta d'an kallesa, ganin inda yake kallo ta kalli madubin ita ma, a hankali ta d'an koma baya ganin dab take da shi ta sunkuyar da kanta, dauke idonsa yyi daga madubin, as if bai son maganan yace "Ga number na nan, duk idan kina son wani abu ko kina da wani magana sai ki danna nan sannan ki sake dannawa ki kirani" Kai kawai ta gyada masa ya jefar da wayar kan gado ya nufi kofa ta bi sa da kallo sabon hawaye na taruwa idonta har ya fita, yau din ma ta waje ya kulle kofar parlon duk da kasancewar mai gadi da matarsa da yaronsu dake gidan yanxu. Kuka sosai Jiddah tayi bayan tafiyarsa, taji komai bai mata dadi a duniyar ynxu, kullum ita kadai kamar mayya a gida babu kowa, tun tana tsoro sosai har tsoron ya ragu, tana sallan isha ko abinci bata ci ba ta kwanta ta takure cikin duvet, nan da nan bacci ya dauketa.... Abuturrab na xaune saman gadon hotel wajen karfe goma da rabi, ya gama abinda yake a laptop ya ajiye yana duba agogon wayarsa, call log dinsa ya shiga har yyi dialing number sai kuma ya katse, mikewa yyi ya kashe wutan dakin ya kwanta yana karanto addu'ar kwanciya, jawo wayar yyi ya d'an yi dube dubensa, sai kawai ya shiga call log din yyi dialing number, he just can't because he have a problem with conscience, abu kadan ke sawa conscience dinsa yyi judging dinsa... Karan wayar ya farkar da Jiddah, bacci ne sosai idonta haka dai ta dau wayar dake saman gadon tayi picking sannan ta kai kunne ta rufe ido bata ce komai ba, jin shirun yyi yaww Abuturrab yace "Ni xan gaisheki" ta bude ido cikin muryar bacci tace "Aa" nan da nan ya gane ta fara bacci, ya dai ce "Me kika ci?" Shiru bata amsa ba, yace "Kee?" Tace "Uhn" yace "Kin yi bacci ne?" Kai kawai ta gyada masa ba tare da tace komai ba kamar yana ganinta, shiru yyi, bayan wani d'an lkci yace "Amma sae da kika yi wanka??" Tuni Jiddah tayi nisa baccinta, bayan few seconds yace "Jeeddarh" jin shiru ya katse wayar kawai ya ajiye sannan yayi rub da ciki nan da nan shi ma baccin ya daukesa. Washegari Jiddah na kitchen yau dai shinkafa da miya take yi tunda ya koya mata yanda ake amfani da blender, ji tayi kamar ana bude kofar parlor, ta tsaya kitchen din tana saurare har taji an shigo parlon, da sauri ta fito, ido hudu tayi da Ahmad tare da Maimoon, kallonsu kawai take da mamaki, ya sakar mata murmushi yace "Toh ko dai mu koma ne?" ta girgixa kai da sauri tace "Aa sannunku da zuwa" Duk suka karasa parlon yana kallonta yana murmushi, Maimuna na kallon Jiddah ita ma tana murmushi tace "Sannu da gida Aunty Amarya" Murmushi jiddah ta kirkira ta karaso ita ma cikin parlon, har ranta taji dadin ganinsu, Ahmad ya xauna yace "Ya gidan Jiddah?" A hankali tace "Lfya lau, ina yini?" Yace "Fine Alhmdlh, dama an kawo mai gadi gidan ne?" Kallonsa kawai Jiddah ke yi kafin tace "Nima ban sani ba ai" Tausayinta Ahmad ya ji, can yace "Toh baxa a kawo mana ruwa ba?" Tashi Jiddah tayi tana murmushi a kunyace ta wuce kitchen ta kawo masu har da lemo, tun jiddah na kin sakin jiki, har daga karshe ta sake gaba daya, Ahmad ya dinga mamaki ganin ashe tana da baki, ga zakin murya kamar zaabiya, sosai Maimoom taji tana son Jiddah, har abinci sai da ta kawo masu, ana kiran azahar Ahmad yace mata xasu wuce don yau ma xai koma Abuja, lkci daya mood dinta ya canxa, Maimoon sai taji tausayinta, makullin gidan Ahmad ya mika mata yace "Su Maimoon xasu dinga xuwa taya ki hira a kai kai idan captain din baya gari so kar ki damu kinji" kasa basa amsa tayi don har hawaye ya kawo idonta, dariya ta basa, yyi kasa da murya yace "Amma fa kar ki sanar masa xuwan mu kinji? Wataran idan naxo tafiya xanyi dake daga gidan gaba daya" Ta gyada masa kai, a haka suka tafi duk yanda ta so daurewa ta kasa sai da tayi kuka. Bayan la'asar wajajen karfe biyar ta gaji da xaman dakin da tsayuwar window ta fito, kallon hanyar da xai kai ta part din Abuturrab tayi, tun ranan da suka fito daga wajen bayan ya nuna mata takarda bata sake bin hanyan ba, tsaye tayi tana ta kallon direction din, can dai ta karasa tana tafiya a hankali har ta isa kofar parlonsa ta bude tana lekan ciki, komai na parlon fess ko alamar datti bata gani ba sai wani kamshi ma da take ji, shiga parlon tayi tana bin ko ina da kallo gabanta ya dinga faduwa, can ta karasa wani kofa da ta gani, bude kofar tayi a hankali tana lekan ciki, daki ne da wani babban katifa da bedsheet a kai, babu abinda bbu a babban dakin, karasawa tayi ciki tana kallon wani table da jirgi a kai, xaro ido tayi tana kallon karamin jirgin, dauka tayi da hannu biyu tana jujjuyawa ta kai idonta tana leka d'an windows din jirgin, hotonsa ta gani jikin bangon dakin da fararen kaya ya rike hula tsaye kusa da wani katon jirgi, a ranta tunani ta shiga yi kilan shi ya ta6a ganin jirgi tunda gashi yayi hoto kusa da jirgin, ita dai a sama kawai suke hangosa dan mitsili, kallon fuskarsa ta dinga yi, lkci daya gabanta ya fadi tana ganin kamar xai iya magana a hoton, a hankali ta juya, taga wani kofa ta karasa ta bude ta ga wani makeken bandaki da abu kamar katon glass a ciki har tana iya hango ciki, kwata kwata bandakin ba irin nata bane, ga shi da girma sosai, ko ina a bushe yake sai kamshi bandakin yake, a hankali ta rufo kofar sannan ta bude wani kofar da ta gani daga can end, xaro ido tayi ganin view din, karamin balcony ne, ta dinga bin gidan da kallo daga kasa wanda ke shimfide da carpet grass ga wasu flowers a gefe, sosai wajen ya mata kyau ba kadan ba, ta kalli wani babban gidan dake opposite dinta suka yi ido hudu da wani dake xaune shi ma a balcony, laptop ne gabansa da drink, shi dai kallonta kawai yake, ta Sunkuyar da kanta da sauri ta juya ta koma ciki ta kulle kofar, da sauri da sauri ta koma dakinta. Daren ranan bayan isha Abuturrab na Abuja a gidansa sbda weather bai bari sun koma kano ba, Aneesah ce xaune kusa da shi a dakinsa, yace "Kince kina da lectures da safe, why not sleep now?" Ta hade rai tace "Toh ae it's not a crime idan nayi bouncing lectures din ko?" Ya gyada mata kai yace "Haka ne...." Lamo tayi ta lumshe ido kusa da shi, ya ci gaba da abinda yake, bayan few minutes ta bude ido tana kallonsa tace "In tambayeka mana captain" Yace "Ina jin ki" tace "This days kamar u are not longer eager being with me, why?" ya buda ido sosai yace "Why do u say so?" Ta marairaice tace "Haka naga alama, or do u have anything in mind?" Murmushi yyi yace "Yaushe rabon mu hadu? It's almost 10 days now" ya ja hancinta yace "And ke kin fiye ma mutum jan aji ne" Rungumesa tayi cike da shagwaba tace "Wallahi ba haka bane, ae kai din ne sai ka xo Abuja kake neman mutum" ya cire hulan kanta yace "Ohh really??" Dariya tayi tace "Aa wasa nake my captain ni kadai...." yyi murmushi yace "In few days time su Abbanmu xa su je gidanku in sha Allah" ta wara ido tace "Da gaske my captain?" Yace "In sha Allah" Rungumesa tayi tace "I can't wait Babynah" ya d'an hade rai yace "Baby kuma?" Dariya tayi sosai tace "Au.. to yi hakuri na manta baka son sunan, amma fa kada wataran ka xo kayi ta rokana in kiraka da Baby" yace "Sai kace wani jariri" Dariya kawai take tana kallonsa don tun ba yau ba tasan bai son irin wannan soyayyan da yawanci yake kiransa da na yarinta, ta daura kanta saman shoulder dinsa tana jin wani sabon sonsa na fixagarta... Karfe daya saura few minutes Abuturrab ya fito bedroom dinsa bayan yayi wanka ya shirya cikin jallabiya, xaunawa yyi parlor yyi dialing number ya kai kunne, sae da ya katse ba a dauka ba sannan ya kalli agogo, ajiye wayar yyi ya kwanta saman doguwar kujera ya lumshe ido... Throughout week din nan Jiddah bata ji kadaici sosai ba don ranan laraba ma sai da Maimoon ta xo gidan, A ranan kuma Abuturrab yyi niyyar dawowa amma cikin ikon Allah sai bai samu dawowan ba, ranan alhamis Maimoon ta kara xuwa tare da Ramlah da abinci wanda Umma ta basu su kawo ma Jiddar, sosai Jiddah ta sake da su don ba kadan suke debe mata kewa ba, Ramlah ta dinga mamaki kamar yanda Ahmad yyi ganin ashe dai Jiddah na magana haka, ga dariya kamar me, xuwan su ya sa har ta samu confidence din fita suka xaga cikin gidan gaba daya tare da su, a nan ne ma tasan da mai gadi da matarsa a gidan, sai bayan magrib Umma ta aika driver ya je ya daukosu, Jiddah ranta fess ta ci sauran abincin da suka rage sannan tayi wanka tayi isha ta shirya ta kwanta, nan da nan bacci ya dauketa. Karfe tara saura Abuturrab dake xaune hotel room dinsa a kano yyi dialing number nata, har ya gama ring bata daga ba, da mamaki ya dinga kallon wayar, ya sake kira nan ma no answer, sake kira yyi ya sake ringing ya gama ba a daga ba, da yamma ma ya kira sau biyu no answer, a lkcn kuma Jiddah na can compound tare da su Ramlah, ajiye wayar yyi, can ya mike ya shirya within few minutes ya dau makullin motarsa da jakar laptop dinsa ya fita dakin, abinda bai ta6a yi ba xai yi ranan, wato driving to kaduna at night, dama da asuba yyi niyyar komawa kaduna sbda throughout gobe ba shi da duty, amma yanxu yyi deciding din tafiya kawai, sai kusan sha biyu da wani abu Abuturrab ya shiga gida yyi parking mai gadi ya taho da sauri yyi masa sannu da xuwa, amsawa yyi ya wuce ciki, makulli ya ciro ya bude kofar dake a kulle, Jiddah bata mance warning din Ahmad na cewar duk wanda ya xo kar ta mance kulle gidan da makulli bayan ya tafi ba sannan ta boye makullin, bin parlon ya dinga yi da kallo, ya kashe wutan dake a kunne ya wuce sama, kofar dakinta ya bude, kwance ya ganta tana bacci cikin nutsuwa, karasawa cikin dakin yyi still looking at her da wani expression can ya juya ya fice daga dakin ya tafi bangarensa. Washegari da safe bayan Jiddah tayi wanka ta shirya ta fito daga dakinta, cak ta tsaya jin kamar tana jin murya a can daya part din, to ko tv ne a kunne, ko ma ita ce ta ta6a abu da ya kunna tvn ranan da ta shiga dakin bata sani ba, gabanta na faduwa ta fara tafiya xuwa can din a hankali, har ta isa sannan ta bude kofa cikin nutsuwa tana lekan parlon, babu wani tv dake a kunne ta dinga bin parlon da kallo, sai taji ba tv bane karatun qur'ani ne, har xata juya ta d'an yi jim kamar me shakkar shiga ciki, can dai ta karasa ciki tana kallon kofar bedroom din da ba a rufe ba gaba daya, tunani ta dinga yi ko ita ta bar kofar haka jiya, a hankali ta kutsa kai ciki, wani kara tayi a tsorace ganin mutum kwance with short and singlet yana bacci, ta juya da sauri ashe ta mayar da kofar ta ci karo da kofar, wani ihun ta kuma yi ta dafe forehead dinta.... Don Allah no Reader should come and ask me of complete document na Jiddatul Khair plss, naga dai ba tsohon book bane da xaku dinga cewa sae an baku document xaku biya, snn shi page guda guda da ku ke karantawa ae ba kyauta bane shi ma, to don hka ko wacce ta ji da bashin dari biyat din mutane😏 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Bude ido Abuturrab yyi ya tashi xaune yana kallonta da mamaki, ta mike tsaye hannunta a goshinta, ko ina na jikinta rawa yake, duk ta daburce, xata bude kofar cikin tsawa yace "Me ya kawo ki nan??" Kin juyowa tayi hannunta na rawa ta bude kofar xata fita, wani tsawan ya kuma yi mata yace "Kar ki kuskura ki tsallaka bakin kofar nan" fashewa tayi da kuka amma taki juyowa kuma bata fita dakin ba, ya sauka daga saman gadon ya dau jallabiyansa ya saka sannnan ya nufeta, tana jin alamar ya sauka gadon ta juyo da sauri, ganinsa tayi tsaye gabanta, fuska daure yace "Me ya kawo ki bangarena?" Cikin rawan murya ta durkusa tace "Wllh kara naji shine na xo in ga meye, ban san ka dawo ba Allah" Ya rungume hannunsa yace "Wato har nan kike shigowa kenan idan bana nan kenan?" Ta fashe da matsanancin kuka tana girgixa kai tace "Aa bana shigowa, ni ba shigowa nake ba wllh" Yace "Toh ina ruwanki da koma me kika ji da xaki shigo min daki?" Hawayen dake makale idonta ya sakko ta girgixa masa kai kawai bata ce komai ba, yace "Toh tafi ki dauko abun shara, ki share tun daga cikin dakin har parlor sannan ki goge, ki wanke bandakin...." Ta sunkuyar da kanta don har ta ji hankalinta ya kwanta xatonta har marinta sai yyi yau, kofar balcony din dakin ya nufa ya bude yana nuna mata yace "Har nan xaki share kiyi mopping" Gyada masa kai kawai tayi, ya dau wayarsa har ya nufi kofa ya tsaya, ya juyo yana kallonta yace "Kar ki ga na kyaleki yau, billah idan kika sake shigo min bangarena ko da wasa xaki sha mamaki" Kai kawai ta gyada masa a sanyaye, ya juya ya fita, sai da ya fita parlon gaba daya sannan ta juya a hankali ta fita ita ma, downstairs ta sauka ta gansa xaune parlor ya kunna TV, ta wuce kitchen ya bi ta da kallo, abun sharan ta dauko da mopping bucket tare da mop with duster sannan ta wuce sama, aikin ta shiga yi babu ganda, har xanin gadon sai da ta sake shimfidawa, bayan ta gama da bedroom din ta tafi balcony, kallon inda taga mutumin ranan tayi duk da babu kowa wajen sai kujera amma sai take ganin kamar shi a wajen, ta fi minti biyu tsaye tana ta kallon wajen kafin ta fara share balcony din ta yi mopping ta dawo dakin ta kulle kofa, parlor ta tafi nan ma ta share ko ina ta goge har kayan kallon, tana gamawa ta koma bedroom din ta bude kofar da take tunani bandaki ne, kallon bracelet din hannunta me kyau tayi wanda yau ya kai kwana uku da ta saka shi, ta tafi gaban mirror dinsa ta cire sannan ta ajiye tana kallon turarrukan da ke gaban madubin, kwalabensu ne ya burgeta sosai, they look so unique, ta dau daya daga ciki ta bude ta kai hanci, rufe ido tayi sannan ta bude, da wannan kamshin ta sansa, babu kuma abinda ya fado mata sai lkcn da yake xuwa can wajenta a Hayin rigasa, ta dau murfin xata rufe turaren ya subuce daga hannunta duk kokarin ganin ta kama turaren kan ya kai kasa hakan ya faskara don tuni yayi landing kan tiles sbda irin faduwan da yayi kuma lkci daya ya tarwatse, a tsorace ta ja baya ta dafe kirjinta da ya hau bugawa, lkci daya ta fara yarfe hannu murya can kasa tace "Na shiga uku" hankali tashe take kallon turaren, ta ma rasa abun yi, can ta nufi kofa sai a sannan ta fashe da kuka ta fita part din, downstairs ta sauka ta makale jikin bango tana kallonsa gabanta na faduwa, jin footstep kuma bai ji ta karaso cikin parlon ba ya sa ya juya, sunkuyar da kanta tayi, ya mike yana kallonta ganin hawaye a idonta, satan kallonsa tayi ganin kallon da yake mata ta fashe masa da kuka tace "Don Allah kayi hakuri" kasa daina kallonta yyi, can yace "Me kika min a sama?" Ta kara rushe masa da kuka tace "Don Allah kayi hakuri nace" Ya wani hade rai yace "Me kika yi nace?" Kin cewa komai tayi, ya nufeta, da gudu ta bar wajen ta wuce sama, ya bi bayanta, tuni ta shige dakinta ta rufe kofan da karfi, part dinsa ya nufa tun bai shiga parlon ba ya soma jin kamshin turarensa, ya shiga parlon sannan ya bude kofar dakin, tsaye yayi bakin kofa ya rungume hannunsa yana kallon tsadadden turaren nasa a kasa, Jiddah dai sai zare ido take tana jiran jin ya shigo dakin amma bai shigo ba har sha daya na safe, sai a sannan ta fara jin yunwan da ya dameta, lamo tayi kan gado kamar xata yi kuka tana tsoron fita, tana nan a haka har kusan sha biyu, mikewa tayi daga karshe ta nufi kofarta ta bude a hankali, cikin sanda ta sauka downstairs bayan ta tabbatar baya kasa sannan ta wuce kitchen, indomie ta dauka ta fara dafawa a kitchen din, ko kadan bata yrda tayi making noise da xai sa a san tana kitchen din ba, yanda taga Ramlah ta dafa masu indomie jiya take yi, with ingredients, tana duba indomie da har ya dahu kamar ance ta juya ta gansa tsaye bakin kofa, sake murfin tukunyar tayi a rikice tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" end din kitchen din ta tafi ta tsaya tana kallonsa a tsorace kamar xata yi kuka, ya karasa gun gas din ya kashe na indomien, da kuma na kwai dake tafasa, tana ganin haka xata fita kitchen din da gudu, ya tare hanyar, hade hannunta tayi waje daya ta marairaice tace "Don Allah kayi hakuri" yana mata wani kallo yace "Laifi nawa kenan kika yi yau a gidan nan?" Ta hadiye abu da kyar tace "Biyu" yace "Wanne da wanne?" Tayi narai narai da ido ta ki cewa komai, ya hade rai yace "Ina jin ki" Cikin rawar murya tace "Na fasa maka turare" yace "Ehen, sai me?" Tace "Na ji kamar radio na magana shine naje sashinka ka kamani" Ya gyada kai yace "Good, kinsan nawa turaren nan da kika fasa min?" Ta bude ido tana kallonsa amma bata ce komai ba, yace "Toh ki sani cewar tara ki nake, turaren nan kuma sai kin biyani duk yanda za ki yi ba ruwana" a hankali tace "Toh ae ni bani da kudi" yace "Ehh nemosu xa kiyi duk inda xa ki nemo su" ta sauke idonta kasa, kallonta yake daga sama har kasa, ya sauke idonsa kan fingers dinta yaga babu farce alamar tana cirewa a kai kai, ya kalli fararen toes dinta, kallon fuskarta yyi yaga har sannan kasa take kallo, yace "Cire hular ki" sae a sannan ta daga kai ta kallesa amma taki cirewa, ya hade rai yace "Magana nake maki" a hankali ta xame hular, ya dinga kallon bakin gashin nata wanda sak na Fulani, amma duk ya takure waje daya duk da da ribbon ta dauresa a tsakiya ya sauka kasan wuyarta, tun gyaran gashin da Umma tayi mata har ranan bata ta6a gashin ba, ya yamutsa fuska yace "Meye wannan din?" Ta kallesa bata ce komai ba, ya mata tsawa yace "Ba tambayar ki nake ba" Cikin sanyin murya tace "Gashina ne" Yace "Ke kaxamar wace gari ce, gashin ki ne kika bari haka kamar na mahaukaciya?" Ita dai bata ce komai ba, ya koma baya yana sake kare ma gashin kallo da mamaki, satan kallonsa tayi ya mata wani shegen kallo yace "Sae na tsokale idonki kika sake kallona, kina mace da ke dubi ynda gashin ki ya koma kamar gashin jikin tinkiya?? What nonsense" Lkci daya hawaye ya kawo idonta, strictly yace "Ki gama cin abincin kiyi sllh ki jirani a parlor" Bata ce komai ba ya juya ya fice daga kitchen din, Jiddah bata wani ci abincin ba sae hawaye, daga karshe ta mayar kitchen ta rufe taje sama ta wanke bakinta ta dau gogaggen hijab dinta ta saka ta dawo parlor ta xauna fuskarta babu walwala, sae da ya dawo sallahn Juma'ah sannan ya dau makullin motarsa, ya isa bakin kofar fita sannan ya kalleta yace "In xo in dauko ki ne" mikewa tayi a sanyaye ta bi bayansa, gaban motar ta xauna don bata mance abinda yace mata ba last time da ta xauna a baya, wani saloon ya kai ta, yana xaune mota ya jira har aka gama sannan daya daga workers din ta fito ta sanar masa an gama ko xa ayi mata lalle, yace "Aa, nawa ne kudin gyaran gashin naku?" Ta fada masa ya ciro kudin ya mika mata tayi masa godiya ta koma ciki, ba a dau lkci ba sai ga Jiddah ta fito daga saloon din, walking slowly ta iso gun motar har sannan fuskarta babu walwala, ta bude gaban motar ta shiga, ta rufe bata ce komai ba, kallonta kawai yake da mamaki, gani yake kamar da kyar ta iya rabuwa da halin gidadanci, ya daga kafada don yasan yana magana xata fara hawaye abinda bai shirya gani ba kenan, ya tada motarsa ya bar saloon din, suna tsaye traffic ganin yanda take kallon me tallan Apple a bakin glass din motar yace "Xa ki ci ne?" Sauke idonta tayi bata ce komai, yace "Ba magana nake maki ba?" Ta girgixa masa kai fuskarta a tamke tace "Baxan ci ba" hade rai yyi yace "Keee" Juyawa tayi ta kallesa tace "Nace A'a" Wani mugun kallo ya dinga mata ta dauke kanta, har suka isa gida bata sake kallon inda yake ba, yana gama parking ta sauka amma tana tsoron ta fara tafiya yyi mata masifa, Matar Mai gadi ce tsakar gidan daga kofarsu ganin Jiddah tace "Sannunku da dawowa Hajiya, Ina wuni...., duk yau shiru baki fito ba" gaban jiddah ya fadi sosai, Abuturrab ya dinga kallonta, Jiddah ta yi murmushin karfin hali tana kallon matar tace "Ina yini" daga haka ta fara tafiya da sauri, bin bayanta Abuturrab yyi, sai da ya shiga parlor ganin har ta isa stairs xata wuce sama yace "Dawo nan" juyowa tayi sannan ta dawo gabanta na faduwa, yace "Ta ina kike fita har take ce maki yau baki fito ba?" Ta xaro ido tace "Ai kofar a rufe kake barinsa, ni bana fita ko ina, ban ta6a ganinta ba ni sai yau" kallonta kawai yake ta Sunkuyar da kanta, ya xauna saman kujera, ita dai bata yadda ta sake kallonsa ba, yace "Ina gyaran gashin da aka maki?" Cire Hijab din jikinta tayi sannan ta sauke hular tana kallonsa, da mamaki yace "Daga nan xan gani" A hankali ta duka kasa ta matsa kusa da kujeran da yake xaune ta juya masa kan nata, kallon bakin gashin dake ta sheki yake, yace "Ta haka xan ga gyaran an daure gashin?" Ta juya ta kallesa sannan ta xame ribbon din gashin ya sauka kasa, bayan few seconds jin bai ce komai ba ta juya ta kallesa suka hada ido, hade rai yyi yace "Tashi ki tafi" Tashi tayi ta mayar da hulan sannan ta wuce sama dakinta. Mikewa yayi ya dau makulli ya fita don xuwa can gida ya gaida su Ummi, Tana jin an bude gate ta mike ta isa bakin window ta tsaya tana lekan compound din har ya fita da mota, turo baki tayi ta koma bakin gado ta xauna, can ta kalli wrist dinta sai kuma ta mike ta fita dakin ta tafi can bangarensa da sauri, a hankali ta bude kofar parlon ta shiga ta karasa bedroom da sauri ta isa gaban madubin tana duba bracelet dinta bata gani ba, bin dakin ta shiga yi da kallo bata ga alamarsa, juyawa tayi ta fita ta koma dakinta ta kulle kofa ta kwanta. Da daddare Abuturrab na bedroom dinsa yana operating laptop wayarsa ya fara ring, dauka yyi ganin me kiransa ya katse ya kirata, daga daya bangaren tace "Hi ya Abuu, Grandma want to vid call with u, na kira naga baka online" Yace "Ohk, how about zoom?" Tace "Aa ta WhatsApp dai" katse wayar yyi ya bude datansa ya hau online sannan ya kirata vid call din, Hajja ta hakikance gaban screen da katon eye glass dinta, yyi dariya yace "Ina wuni Hajja" Tace "Aa ba ruwana, meye kuma ina wuni, kai baka kiran mutane sai dai a kiraka kawai don kana matukin jirgin sama, baka da wani bambanci fa da me jan motar haya wllh, naga kamar wani jin kanka kake, ga Saleem kullum sai ya kira Farida ya ga fuskata, haka ma Bashir, ko daxu sai da Bashir ya kira muka ga fuskar juna, to kawai don bana kasar sai kayi watsi da ni, sai kace ba ni nayi wahala da kai ba, ko uwarka ce tace ka fita harkata, don dai har yau bamu san xuciyar matar nan ba" Abuturrab na shafa kansa yana murmushi yace "Ya gidan Hajja" Tace "To lafiya lau, ai naji Baban farida xai taho Nigeria ni dai nace tare xa mu taho don na gaji, babu wani abinci a nan banda gurasar alkama, to ina dalili duk na kanjale na xata wajen arxiki ne ashe ba haka ba, basu da komai sai alkama da madara" Abuturrab yace "Yaushe xa ku taho kenan?" Tace "Aa ni dai kawai ji nayi xai taho, amma ban san yaushe ba" Yace "Toh Allah ya kai mu" Tace "Kana nan kana tukin jirgin har yanxu dai ko? Don duk na sanar ma abokan arxiki da nayi a kasar nan cewar jikana tukin jirgin sama yake, bbu kamarsa duk Nigeria" Abuturrab yyi murmushi kawai, tace "Aa ba batun murmushi ba, ko sun koreka a aikin ne nake nan nake ta tsuga karya?" Yace "Ke fata kike a koreni" kiran Aneesah ne ya shigo wayar, hkn yasa vid call din yyi still, ya daga kiran, daga daya bangaren cike da fara'a Aneesah tace "Guess what My captain?" Ya jawo pillow ya kwanta ya lumshe ido cikin calm voice dinsa yace "I am not a good guesser u know...." Hansai ce xaune kan takalmanta da kawarta Zulai da ita ma ta xauna kan takalman nata a karkashin bishiyar wani tsakar gida, Mata ne sun fi talatin a d'an tsakar gidan, ko wacce da hijabinta yarkace yarkace, wasu da goyo wasu da ciki, Hansai tace "Anya Zulai xa mu samu ganin mutumin nan yau kuwa, ni d'an cinikin awaran yau ma nake ji, don wllh Bibalo ba yi xata yi ba ta gwammace in ma kwantai ne awaran yyi, nan gaba fa sai na koma xan fara tuya, ga layi kamar baxa a xo kanmu ba, to ko wacce da matsalarta a kugunta" Zulai ta gyara xama tace "Shi sa nace maki mu fito da sassafe Hansai, amma kika tsaya dafa awara, mutumin nan aiki yake kamar yankan wuka shi sa ake masa layi wllh, idan ba da asuba mutum ya shigo ba sai ya kai magariba ma bai gansa ba, don ma mutumin baya tashi sallah kenan" Hansai tace "Toh ko dai mu je mu dawo goben da asuba Zulai? kinga fa uban layin yaushe aka xo kanmu" Zulai tace "Kin ji ki, mu kashe kudin mota kusan dubu daya kice mu tafi mu dawo Hansai??" Hansai tace "To ni ya xance? Wllh kwantai awarata xata yi yau, Allah ma yasa ta yanyanka min in dai bibalo ce, kinga idan ya so gobe sai in sake xaran dubu daya cikin kudin awaran mu taho" Zulai ta mike tace "Toh shhkn, mu tafi" Mikewa Hansai tayi tana sa6a bak'in gyalenta da duk ya takure suka fito waje tana cewa "Ni dai fatana Allah ya sa na xo gun karshen wahalata" Zulai tace "Ahaf ai fada ma 6ata baki ne wllh, in dai kika saki kudi rass xai maki aiki bbu algus, kina xaune rana tsaka xaki ga Jiddah har gida kamar an korota, wnn ai karamin aiki ne a wajensa, shi fa mutumin nan har haukata mutane ance yana yi" Hansai ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Ae ban san amfanin shegiyar yarinyar ba sai da ta tafi, ashe ita ce rufin asirina ban sani ba, gaskiya idan Allah ya dawo min da ita auren ma wllh baxata yi ba har ta mutu, tun bayan bacewarta har yau banyi cinikin awara da yafi na dubu biyu ba, shi ma da kyar, snn xan ce ma malamin ya sa mata bak'in jini yanda bbu wanda ma xai yi sha'awan aurenta a bar min a bata kawai" Zulai tace "Da dai ya fi wllh, kinga bbu ma saurayin balle yace xai aureta" A haka suka isa bakin titi Hansai tace "Allah dai ya kai mu goben, in sha Allahu komai ya xo min karshe, wahalata ta kare" Abuturrab na tsaye balcony misalin karfe takwas na safe wayarsa kare a kunnensa yana sauraran wani abokinsa, sai da ya jira abokin ya kai aya snn yace "I thought xa a samu mata ne, in dai ba a samu matan ba kawai a bari, i will think of another alternative" Daga daya bangaren abokin nasa yace "Amma wa kake nema ma lesson teacher din?" Ya xauna saman kujeran dake balcony din yace "Wata daughter na ne" Abokin nasa me suna Farouq yace "Ohk in dai an samu matan i will let u know Capt, kasan maxan ne sun fi juriyan koyarwan" Abuturrab yace "Eh haka ne, nagode da kulawa" Daga haka suka yi sallama, ya koma parlor ya xauna, daukan wayarsa da yyi haske yyi, ya dinga kallon screen din ganin El-Basheer ke kiransa, it's been a while da suka yi magana, duk da shine baya daukan kiran nasa, can dae ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren El-Basheer yace "Sai aka yi yaya da baka daga kirana?" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera yace "How are you doing?" El-Basheer yace "Saboda baka da bayanin da xaka min kan auren da kayi ma kanka ne yasa baka picking call dina??" Abuturrab ya gyara xama yace "Babu xancen wannan auren ne yanxu, shi sa ma na samu kwarin gwiwan daga kiran ka" El-Basheer yace "Ohh really? amma few days ago mun yi magana da Ahmad kuma yace min kana gidan ka da matarka...." Abuturrab ya daure fuska yace "Matar da ya aura min?" El-Basheer yace "But wait.... On a serious note Captain don kaje ka yi ma kanka aure babu shawara da kowa shine kake ignoring mutane, why are u avoiding good frnds? mu baxa mu hanaka xama da matarka ba ae no matter who she is" Abuturrab yace "Look Bashir, am serious babu xancen wannan auren yanxu, kasan ni bana karya, i don't have any god-damn wife now.... amma this is just between i nd u don 'yan gida basu sani ba har ynxu" El-Basheer yace "Ban gane ba, sakinta kayi?" Abuturrab yace "Ba sa'ar aurena bace ita ae, kawai tsautsayi ne da kaddara ya fada min" El-Basheer yace "Then why are u still hiding it from people at home in har da gasken ka saketa?" Abuturrab yace "Bcos we are staying under same rood with her har ynxu, and Abba won't take it likely if he finds out na saketa, i think we should change topic now dude...." El-Basheer yace "Anyway... Ina kaduna, turo min address din gidan naka, i will be leaving in two days time in sha Allah" Abuturrab yace "Really? Yaushe ka shigo, kuma me ka xo yi" El-Basheer yace "Forward to me ur address now" Abuturrab ya d'an yi shiru, sae kuma yace "Ohk" daga haka ya katse wayar..... Ya d'an yi jimm, bayan kusan 5 minutes kawai ya tura masa Address din sannan ya mike ya wuce sama, dakin Jiddah ya bude ya ganta tana faman shafa man gashi a dogon gashinta da ya cika ko ina na kanta, atamfa ce jikinta, ta daga kai tana kallonsa, fuskarsa bbu yabo bbu fallasa shi ma yake kallonta, a hankali tace "Ina kwana" yace "Idan da abinda xa ki yi a kasa ki sauka ynxu kiyi, xuwa anjima bana son ganin ki a kasa" Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya bar bakin kofar. Mikewa tayi bayan tayi parking gashin ta saka hula ta sauka parlon, xaune ta gansa parlon yana rike da remote, ta sunkuyar da kanta ta wuce kitchen, dankali ta shiga ferewa ta soya da kwai, sannan ta fito kitchen din rike da plate din Irish da egg din, ya bi ta da ido ganin xata wuce sama yace "Ina shayin?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Koma" Ba musu ta juya ta koma kitchen din ta sa ruwan xafi sannan ta hada shayin a cup ta kara fitowa kitchen din, still yana kallonta yace "Wani ruwan kike sha gidan nan?" Tana kallonsa tace "A bandaki nake sha, ko a pampon kitchen" Bude baki yyi yana kallonta with shock, can ya mike yace "Ruwan bandaki?" Sosai gabanta ya fadi ta fara komawa baya, ya lura da hakan gudun kar ta saki ruwan shayin hannunta tunda ya san ba setin kirki gareta ba, calmly yace "Je ki ajiye abun hannunki ki dawo" A sanyaye ta wuce sama bayan ta ajiye plate da cup din ta mike ta fito a sanyaye, lkci daya hawaye ya kawo idonta, tsaye ta gansa har sannan yana jiranta, ta makale jikin stairs bayan ta sauko cikin rawan murya tace "Gani" Juyawa yyi yana kallonta, ta sunkuyar da kanta da sauri, daga sama har kasa yake kallonta, riga da skirt na atamfa da ya kamata, babu abinda kayan ya boye na surarta, ya rungume hannunsa yace "Daga yau kada ki sake sa atamfa a gidana" Ta d'an kallesa, sae kuma ta kara sunkuyar da kanta, yace "Idan baki son Abayan da nake siyo maki kiyi yawo ba kaya kawai" Ita dai bata dago ba balle tace komai, yace "Sannan kika ce ruwan bandaki kike sha?" Ta marairaice ta girgixa masa kai, strictly yace "What??" Tace "Sae cikin dare ne nake shan na bandaki, amma da safe da rana da yamma na pampon kitchen nake sha" Gani tayi ya nufota ta juya da sauri xata koma sama yace "Allah idan kika motsa daga nan xan maki abinda ban ta6a maki ba, wato xan gaura maki mari" Kuka ta fara yi, tana hawa stairs din da daddaya da daddaya cikin rawan murya tace "Don Allah kayi hakuri" Yana isa ta fasa kara, ta durkushe wajen tace "Kayi hakuri don Allah" Bai karasa kusa da ita ba yace "Shi ruwan fridge din na waye?" Ta boye fuskarta tace "Naka ne" yace "Ni nace maki nawa ne?" Ta girgixa masa kai, yace "Toh daga yau kika sake shan ruwan pampo a gidan nan Allah sae na mareki" Ta gyada masa kai da sauri, yace "Tashi ki bar nan" mikewa tayi da sauri ta haura sama, sae a snn ta juya tana kallonsa a downstairs, yana tsaye yanda ta bar sa, da sauri ta shige dakinta. Bayan azahar El-Basheer ya iso gidan, Abuturrab ya fita ya shigo da shi, Abuturrab ya sakala hannu a kafadar cousin din nasa yana murmushi yace "The prince himself" El-Basheer na murmushi yace "It's been long Captain...." sosai suke shige da Abuturrab sai dai ya fi Abuturrab din haske, don shi ya fi shige da larabawa wanda hakan ke nuna kilan shi din ruwa biyu ne.... El-Basheer na bin gidan da kallo bayan sun shigo yace "Everything seems perfect, sai dai unfortunately ba Aneesah ta fara shigowa gidan ba...." Abuturrab ya shafa sajensa kmr baxai ce komai ba, sae kuma yace "Kwanan nan xata shigo gidan in sha Allah, bikin Ahmad saura few weeks so, bayan bikinsa sai inyi ma su Abba magana...." El-Basheer ya shiga bin parlon da kallo yace "But wait.... Where is.... I mean the wife u married?" Abuturrab ya hade rai yace "Wacce wife din?" El-Basheer yace "Warce muka ji labarin ka aura ma kanka mana..." Abuturrab yace "Pls hakan na bata min rai wllh, Nace maka she isn't my wife any longer" El-Basheer yace "Yes haka kace, but why not ka sanar ma kowa bbu auren??" Taku suka ji a stairs, Abuturrab ya saci kallon Stairs din da sauri, El-Basheer dai bai juya ba sae kallon Abuturrab yake yana jiran amsan sa Jiddah ta sakko walking slowly ta shigo parlon da ganin kasan a d'an tsorace take, Kallon Abuturrab dake kallonta tayi ganin irin kallon da yake mata ta d'an tsaya ta ki karasowa, El-Basheer ya juya ya kalli inda Abuturrab ke kallo, lkci daya Abuturrab ya mike, ta marairaice tana kallonsa tace "Kai ne kace in daina shan ruwan bandaki, wllh kishi nake ji" Fuska daure yace "Juya ki koma" Juyawa tayi da sauri ta koma sama, Sai a sannan ya koma ya xauna yana kallon El-Basheer da ya bi ta da kallo..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Abuturrab ya dau throw pillow dake gefensa ya jefa ma El-Basheer da ya bi Jiddah da ido, sae a sannan El-Basheer ya dauke idonsa, sai kuma ya daga kafada as if counting his words yace "Ita ce.... Ex-wife din taka?" Abuturrab na kallonsa da wani expression yace "Does that warrant u to stare at her that way??" El-Basheer yyi shiru yana danna wayarsa kamar baxai ce masa komai ba, sai kuma ya kallesa yace "Naga kamar ganinta ya fi jin ta ne, ita ce yar hayin rigasar?" Abuturrab ya masa wani kallo ya dau remote yana canxa channel, El-Basheer yace "Ko dai a gidanka ne ta samu transformation din nan, she's got a beautiful shape" Abuturrab ya mike, sounding fed up yace "Stop this plss El-Basheer... U r sounding lousy" El-Basheer yana shafa gashinsa yace "Lousy? Ohk sorry about that" Abuturrab ya dinga kallonsa da wani expression that is expressing how really angry he is, ya koma ya xauna yana canje canjen channel, El-Basheer ya bi parlor din da kallo yace "I need something cold to take now, haka kake treating visitors?" Mikewa Abuturrab yyi ya wuce kitchen, El-Basheer ya bi sa da kallo, fridge ya bude ya dau bottle water daya sannan ya fito, sama ya wuce yana cewa "In dai ni xan kawo maka ruwa xaka dade baka sha ba" El-Basheer ya bi sa da kallo yana d'an murmushi, can ya girgixa kai, bude kofar dakin Jiddah Abuturrab yayi ya shiga.... xaune ya ganta ta takure waje daya, tana ganinsa ta gyara xamanta tayi narai narai da ido tana kallonsa, ya ajiye ruwan gaban mirror ya juyo fuska a tamke yace "Me nace maki daxu?" Shiru tayi, yace "Ba ce maki nayi kar ki fito ba all through?" Hawaye ya cika idonta tace "Ruwa ai naje in dauka, ba ce min kayi in daina shan na bandaki ba" Yace "Me ya hanaki dauka daxu da kika sakko" shiru tayi bata ce komai ba, yace "Xo ki dauka" mikewa tayi ta tafi gun madubin ta dau goran ruwa, yana kallonta yace "Sannan ba nace kada ki sake sa irin kayan nan a gidan nan ba?" Ta kallesa tace "Ai daxu ka gaya min, ina ce daga yau kace.." Bai kuma cewa komai ba ta koma inda take ta bude ruwan, sai da ta sha ruwan sannan ya juya ya fita dakin, tsaye ya ga El-Basheer a parlor hannunsa rike da kwalin lemon chivita yana sha, Abuturrab ya xauna yace "What will u be taking for lunch?" Xaunawa El-Basheer yayi yace "Naaah... I'm full, i just need rest" Abuturrab yace "Okay mu je sama" Mikewa yayi ya fara tafiya sama, El-Basheer ya mike ya bi bayansa rike da lemonsa, Abuturrab ya kai sa part dinsa, xaunawa El-Basheer yayi gefen gado cikin bedroom din bayan ya rufe lemon hannunsa ya ajiye yace "Tsarin gidan yayi sosai, the Architecture is really good" yana fadin haka ya kwanta, Abuturrab dai na tsaye gaban madubi yana kallonsa ta madubin, can dai yace "Xan je in dawo yanxu!!!" El-Basheer ya dago yace "Ina xa ka?" Yace "To get lunch" daga haka ya nufi kofa ya fita, yana isa kofar Jiddah ya bude, ya d'an hade rai yace "Dauko Jilbab dinki, ki sameni waje" Daga haka ya wuce, yana cikin mota Jiddah ta fito da Hijab har kasa, sai da ta shiga gaban motar sannan yayi horn, mai gadi ya hau bude gate din, jan motar yayi suka fita gidan, wani babban eatry ya tafi, ya siya ma shi da El-Basheer fried rice and chicken, Jiddah dae na xaune kan kujeran da ya nuna mata cikin eatry din, sai bin mutanen wajen take da kallo, baka ta6a cewa tare suke da Abuturrab don bai ko sake kallon inda take ba, wani mutumi ne ta ga ya ja daya daga kujeran table din da take ya xauna, ya daga face cap dinsa yana kallonta, ta saci kallon Abuturrab da ke xaune wani table can yana jiran order din da yayi, ta sake kallon mutumin, ya sakar mata murmushinsa me kyau, ta sunkuyar da kanta da sauri, yace "Hello, how are u doing, are u waiting for ur order?" Ta saci kallon Abuturrab taga kallon direction dinsu yake ko kiftawa babu, sosai gabanta ya fadi, cikin rawan murya tace "Yayana na nan fa" Mutumin ya bi eatry din da kallo, kawai gani yayi Abuturrab ya nufosu, ita dai gabanta sai faduwa yake, Abuturrab na isowa yana kallon mutumin babu yabo babu fallasa yace "Didn't she tell u she is married?" Mutumin ya mike yace "Ooh i am sorry plss" Abuturrab bai tankasa ba ya ja wani kujeran ya xauna facing her directly, mutumin ya kara basa hakuri, nan ma yaki amsawa har mutumin ya bar wajen, Jiddah ta saci kallonsa suka hada ido, ya jefa mata wani kallo yace "Ko tausayin rayuwarki baki ji har xaki fara kula maxa ko?" A hankali tace "Ni bani na kirasa ba kawai xuwa yayi" Yace "Toh bari kiji har sai kin gama jami'a kin fara aiki, kafin ki kalli ko wani namiji balle har ki kulasa" Ta gyada masa kai kawai, ya ci gaba da danna wayarsa har aka kawo masa order da yyi a takeaway, without looking at her yace "Me xa ki ci?" ta sunkuyar da kanta tace "Ko meye" tsaki yyi ya mike ya bar wajen, jollof rice yayi mata order da kazar ita ma sannan suka bar eatry din, tana rike da ledan nata ta wuce dakinta bayan sun isa gida, Abuturrab na shiga bedroom dinsa ya tadda El-Basheer a kwance yanda ya bar sa idonsa lumshe, parlonsa ya koma ya xauna. Bayan la'asar Abuturrab ya sauko downstairs ya samu El-Basheer dake xaune yana jiransa, El-Basheer yace "Plss idan baxa kaje ba ni in tafi mana, i have many places to go yau din nan, i will be leaving probably tomorrow in sha Allah" Abuturrab ya mika masa wayar hannunsa yace "Aneesah..." amsar wayar El-Basheer yyi ya kai kunne, Abuturrab ya ajiye makullin motarsa sannan ya koma sama, El-Basheer ya amsa gaisuwar Aneesah yace "Ya kwana biyu?" Aneesah tace "Alhmdlh, he is just telling me kuna tare yanxu" El-Basheer ya d'an yi murmushi yace "Yea daxu na shigo kaduna and am at his resident now" tace "Oh ohk, ya su Ummi?" Yace "Ban je ba" Aneesah tace "Ayya, to ya garin?" El-Basheer yace "Cool, i have a question for you Aneesah, nasan baxa ki boye min ba" kafin ta ce komai yace "Tell me.... is Aliyu saying the truth na cewar ya saki yarinyar nan??" Aneesah ta yi shiru da fari, can kuma cike da confusion tace "Yarinya? Wacce yarinyar? Kuma sakin me?" Shiru El-Basheer yyi, can yace "Ohk then, i will pick a call right away...." Daga haka ya katse wayar ganin from all indication she knows nothing about what he is saying now, sake kira tayi ya ajiye wayar gefensa ya jingina da kujera, Abuturrab na tsaye dakin Jiddah dake rakube jikin gado, yana kallonta strictly yake cewa "In har muka shigo gidan nan kika wani sakko wai xaki dau wani abu xaki sha mamaki na, duk abinda xa kiyi kiyi ki gama yanxu kafin mu dawo" ta gyada masa kai kawai, kamar wanda ya tuna abu ya juya da sauri yana kallon kofa, lkci daya ya fice daga dakin ya sauka downstairs yana kallon El-Basheer da manyan idanuwansa yace "Hope... Hope you didn't say anything apart from greeting to Aneesah???" El-Basheer yace "Of course baka ce min haka ba, na tambayeta ko gaskiya ne ka saki yarinyar nan kamar yanda ka fada, and from d way she sounds, bata san komai kan maganar ba ma" Abuturrab ya xaro ido yace "Ohh my God... Me yasa xaka yi mata wannan maganan El-Basheer?? We are still hiding it from her" Mikewa El-Basheer yyi ya dau makullin motar Abuturrab yace "Ni kace min bata sani bane, ga ta nan tana ta kira, pick and find what to say to her" daga haka ya nufi kofa ya fita, Abuturrab ya bi sa da kallo xuciyarsa na tafarfasa. Daukar wayarsa yyi yaga calls din Aneesah har biyar yayi silencing wayar ya bi bayan El-Basheer.... Bangaren Aunty suka fara shiga suka gaisheta bayan sun isa gidan, Aunty na kallon El-Basheer tace "Har ka iya xuwa wai gidansa El-Basheer, ni fa na tattare lamarin Abuturrab na watsar a gefe, i see no reason da xai dinga boye boyen cewar ya saki yarinyar nan, ko meye fa'idan xama gida daya da ita bayan ya saketa, who is he deceiving?? To wllh I've made up my mind cewar Abbansa na dawowa sati me xuwa xan sanar masa komai, wannan ae iskanci ne, to ko minti biyar ba ayi da muka gama waya da mahaifiyar Aneesah ba, labari ya je masu, kana tunanin xaka iya ci gaba da boye masu ne dama?? Wllh yanxu haka duk hankalina a tashe yake, nayi kokarin fahimtar da su ba auren amma ya faskara...." Kallonta kawai Abuturrab yake yi, shi na Aneesan ma bai damesa ba kamar na Abba da tace xata sanar ma ya saki Jiddah kuma yana xaune tare da ita, gaba daya yaji hankalinsa yyi mugun tashi, Waje ya nema ya xauna jin har kansa ya fara juya masa, El-Basheer yace "Ni banga abun boye boye a nan ba, let this be known to everyone that she is no longer ur wife, kana xaune gida daya da macen da ba muharramarka ba, who does that??" Abuturrab ya kalli Aunty da ta ci gaba da abinda take bbu fara'a fuskarta, yyi kasa da murya yace "Amma Aunty kinsan Abba won't be happy idan yaji na saketa, he will be highly disappointed at me, kuma ni sbda bana son bacin ranki ya sa na saketa wllh, idan kika gaya ma Abba cewar nayi hakan yanxu he won't take it likely with me, i am just confuse Aunty" Aunty ta juyo a fusace tace "Ni kuma dole in sanar masa duk abinda xae faru ya faru ba, are u this happy being with the girl da yasa ka daina dawowa weekend gidan nan sae dai ka sauka gidanka ka karashi weekend dinka ka wuce, haka xaman naka da ita yayi dadi duk da ba matarka bace ashe?? To kuwa xaka sha mamakina kuwa wllh" Ya girgixa kai yace "Aunty ni weekend din ma gaba daya na daina dawowa fa, Jiya ne kawai na dawo sbda El-Basheer yace min yana hanya" Aunty tace "Wato ita kadae ke yanda ta so a katon gidan? Ka sakar mata babban gida haka ta ci karenta ba babbaka, to baxai yiwu ba ne wllh" Shiru yyi bai ce komai ba, Aunty tace "Don kuwa da ta ci gaba da xaman gidan nan naka gwara ka dawo da ita nan, dama mai aiki xata tafi garinsu jibi, kaga ba wani xai ce ta bar nan gidan ba wataran..." Kallonta kawai Abuturrab ke yi gabansa na bugawa, tayi masa tsawa tace "Kallon ne amsan ka? Ko baxa kayi abinda nace bane??" Ya girgixa kai yace "Aunty can din ma ina assuring dinki ba sae wani yace ta tafi ba xata tafi, wllh ita kadai ce bbu kowa" Aunty ta kara masa wani tsawa tace "Nace ka dawo da ita gidan nan, ko ban isa ba??" Ya sunkuyar da kansa lkci daya jikinsa yyi sanyi, can ya kalleta cikin sanyi yace "Toh" Sannan ya mike ya nufi kofa ta bi sa da harara tana huci, El-Basheer ya d'an yi murmushi yace "But how can a normal human being do what Abuturrab did?" Cike da bacin rai Aunty tace "Atoh... Isn't this irritating Bash?? Wllh da lamarin nan nake kwana nake tashi a raina, ya ce ya saketa quite alright he did that, na sani, to kuma xaman me suke tare idan anyi magana yace Abbansa, ance masa da Abban nasa ya san ya saketa xae barsa ya ci gaba da xama gida daya da ita, ga yarinyar ido a bude, to xaman iskanci yake son fara yi da ita ko me, don dai shi ma ba saiti garesa ba kuma ba jin magana yake ba, ka sani, na sani, shi yasa bai dauki xaman da yake under same roof with her wani abu ba" El-Basheer ya mike yace "Allah ya kyauta" daga haka ya fita. Ko bangaren Ummi Abuturrab bai shiga ba ya fice daga gidan ya shiga motarsa ya jinginar da kansa da kujera yana jiran El-Basheer, dalilin da yasa bai son xuwa gidan kenan idan ya dawo weekend, ganin har bayan minti sha biyar El-Basheer bai fito ba Abuturrab yyi dialing numbersa, El-Basheer na dagawa, a fusace yace "Inyi tafiyata ne?" El-Basheer yyi murmushi ya katse wayar, kallon wayar Abuturrab ya dinga yi, sai ga text ya shigo masa, bude content din yyi, "C'mon wani irin gaisuwa kake son inyi ma Ummi, gaisuwan minti goma? Tunda kai kaki shigowa gaisheta ni baxan iya ba" Abuturrab ya mayar masa reply yace "Ka sameni a gida then" daga haka ya ajiye wayar ya tada motarsa ya bar anguwar. Yana parking ya shiga parlor ya xauna kujera ya jinginar da kansa ya lumshe ido yana jin ransa ba dadi, text ne ya shigo wayarsa ya bude ido a hankali ganin Aneesah ce tayi text din ya bude content din, "Abinda ka min was the least i expected from you Aliyu, ban yi xaton haka ko a mafarki ba, amma ka sani ka cuceni, ka ci amanata, ka yaudareni, ka ruguza min rayuwa, i gave u all my trust but u ended up betraying me, why Aliyu, did i deserve this harsh treatment from you?" Ko gama karanta text din bai yi ba yayi mata reply kamar haka "Since you never expect this from me... Then u consider me... Aure kuma sai idan kece kika ce baxa kiyi da ni ba, as for me you will be my first and last wife in sha Allah.... i will call u in 5 hours time in sha Allah" daga haka ya tura mata text din ya ajiye wayar ya mike ya wuce sama. Har bayan Magrib El-Basheer bai shigo gidan ba, hakan ya sa Abuturrab yyi dialing number sa, yana fara ring El-Basheer ya daga yace "Gobe xan shigo before leaving, Ummi tace i should spend the night here" Abuturrab yace "Ohk" daga haka ya katse wayar. Mikewa yyi ya wuce sama ya bude kofar dakin Jiddah, tun da ya dawo ko motsinta bai ji ba, tana xaune gaban mirror tana ma gashinta kitson kalaba, ganinsa ta dau hulanta ta saka, yana tsaye bakin kofa yace "Meye hakan kike yi?" Tace "Aa ina kitson gashin ne, yana karyewa idan ban yi kitso ba" Yace "Sai anyi kitson ne baxai karye ba?" Ta gyada masa kai, yace "Toh kwance wannan abinda kika yi, tunda a garinku ne aka ce maki xai karye idan ba ayi kitso ba, a tsefe xaki bar gashin, haka nake so" Ta kallesa da sauri, that was when he realized what he just said, lkci daya ya hade rai yace "Ko kina ganin kitso a gashin su Ramlah, mu a nan ba a kitso" Cikin sanyin murya tace "Toh" ta fara tsife dogon gashin nata da ta kitsa, har ta gama tsefe daya bata ji ya tafi ba, hakan yasa ta leko sa ta cikin gashinta da ya rufe mata fuskarta gaba daya, suna hada ido ya juya ya fita dakin. Ana kiran isha ta gama parking din dogon gashin nata ta kitse jelan sannan ta sa hularta. Karfe tara saura wayar da Abuturrab ya bata ya fara ring a gaban madubi, karasawa tayi ta dauka tana kallon number jikin screen din sannan tayi picking ta kai kunne, muryarsa taji yace "Ina jiranki a parlor" Daga haka ya katse wayar, ajiye wayar tayi ta sa Hijab dinta ta fita, shi kadae ne xaune parlon ta durkusa jikin kujera a hankali tace "Gani" Yace "Me kika ci?" Ta sunkuyar da kanta tace "Taliya na dafa" ya nuna mata ledan dake gefensa yace "dauka" mikewa tayi ta isa kusa da shi ta duka ta dau ledan, ya rike numfashinsa sbda wani kamshi na daban da ya doki hancinsa, ganin kwalin lemo a cikin ledan ta cire xata ajiye, ya saki breath dinsa ya hade rai yace "Har da shi xa ki tafi" Innocently tace "Ban iya sha ba" Yace "Haka xa ki je ki koyi sha yau, tunda ke yar kauye ce" Bata ce komai ba ta mayar da kwalin cikin ledan sannan ta mike ta nufi stairs, bin ta yyi da kallo tana isa stairs ta juyo suka hada ido, da sauri ya dauke idonsa, tace "Nagode" sannan ta wuce sama, jinginar da kansa yayi a hankali da kujera yana jin damuwa iri iri a ransa, gasasshiyar kaza ce da yaji Jiddah ta bude a dakinta, sai kamshi kazan yake, ta kalli kwalin hollandia din sannan ta bude ta d'an sha kadan, ji tayi yayi mata dadi a baki sbda gardinsa, ta lumshe ido ta kara sha sannan ta ajiye ta fara cin naman a hankali, lkci daya rayuwar da tayi a gidansu ya fado mata, tura kazan tayi tuna Babarsu da tayi. Abuturrab na kwance wajajen sha daya a parlor, waya na kare kunnensa, he felt relieved bayan yayi convincing Aneesah a kan kaddara ce ya sa shi auren jiddah sannan kuma bashi da aurenta a kansa yanxu, daga daya bangaren cikin sanyin murya tace "Amma why is she still at ur resident My captain??" Yace "Ina kike son in kai ta yanxu?" Tace "Ni ko gidanmu ma ka kawota su Mummy baxa su ce Aa ba wllh, ni nasan karyar da xan masu, ka barta ta dawo gidanmu plss" Bai san lkcn da yyi wani murmushi ba, a hankali yace "Koh?" Ta marairaice tace "Sure dear" yace "I will think about that, xuwa nan da short period of time" tace "Do so fast plss Captain" daga kai yyi jin footstep a stairs, lkci daya yace "I call you in some minutes time" bai jira cewarta ba ya katse wayar, yayi kasa da idonsa kamar me bacci, A hankali Jiddah ke tafiya duk xatonta bacci yake hannunta rike da ledan kazan da ko yanka uku bata ci ba, to bata saba da shi ba shi yasa bata iya ci sosai ba, drink din ne ma ta d'an sha ba laifi, kitchen ta tafi ta ajiye ledan kazan a fridge ta ajiye lemon ma sannan ta fito, a hankali take tafiyar ta nufi stairs ya bi ta da kallo, nighty ne jikinta wanda ya wuce kneels dinta da hularta a kanta, sai da ta isa stairs ta juyo ta kallesa suka hada ido, sosai ta tsorata, yyi saurin mikewa xaune pretending to be awake at that moment yace "Me kike yi a nan" ta nuna masa kitchen tace "Na kai abu na ajiye" yace "Je ki dauko abinda kika ajiye" Tayi narai narai da ido ta ki motsawa daga inda take, ya hade rai yace "Baki ji abinda nace ba?" Da gudu ta wuce sama, ya mike tsaye da mamaki yana bin ta da kallo, har ta shige dakinta. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Washegari da safe Abuturrab ya sauko downstairs wajajen karfe takwas, jin motsi a kitchen ya fasa shiga kitchen din ya xauna parlor, bayan kusan minti ashirin Jiddah ta fito, tana ganinsa ta yi kasa da kanta kamar munafuka, ta nufi jikin kujera ta durkusa, a hankali tace "Ina kwana?" hararanta yake, taki yarda ta hada ido da shi ta mike tayi wucewarta sama, sae a sannan ya tashi ya wuce kitchen din, wanke wanke ya ga tayi ta goge ko ina na kitchen din, fridge ya bude ya dau apple uku ya dau karamin plate ya daura a kai sannan ya fita ya koma ya xauna yana cin apple din yana danna wayar sa, danna bell aka yi, ya kalli kofar da mamaki, can ya mike ya nufi kofar ya bude, ido hudu yayi da Aunty a tsaye ta hade girar sama da ta kasa, gabansa ya fadi sosai, ya kalli El-Basheer da ya xauna saman kujeran dake balcony din ya daura kafa daya kan daya, bangajesa Aunty tayi ta shiga parlon, ya bi ta da ido sannan ya kalli El-Basheer fuska daure, mikewa El-Basheer yyi yace "She only said in rakata anguwa, and i never knew nan xata xo" Wani kallo Abuturrab yyi masa ya juya ya koma cikin parlon, tsaye ya tadda Aunty fuskar nan nata babu alamar wasa, yyi kasa da kai da ladabi yace "Ina kwana Aunty?" tace "Ban kwana ba Aliyu, ina yarinyar take?" Yyi kasa da murya yace "Aunty dama ai anjima kika ce in kai ta can gidan ko" Cikin tsawa tace "Ta fito yanxu mu wuce, na hutassheka ba sai ka kai ta ba" a hankali yace "Toh" Daga haka ya fara wucewa sama, ta bi sa da harara tana girgixa kafa, sai da ya haura sama ya d'an juyo ya kalleta ganin bata ganinsa, ya nufi dakin Jiddah da sauri, Tana gyaran gado ya shigo, ta mike tana kallonsa, ya hade rai yace "Mu je" Tana kallonsa tace "Ina?" Fixgo hannunta yyi ta xaro ido tana kallonsa har suka fita dakin, ganin bangarensa ya nufa taki ci gaba da tafiyar tace "Me xanyi..." wani kallo ya jefa mata, hakan yasa ta ci gaba da tafiyar, parlonsa ya kai ta, ya bude kofar balcony yana kallonta yace "Shiga" da mamaki tace "Saboda me" shigar da ita balcony din yyi yana kallonta da kyau yace "Idan kuma so kike Auntyna ta tafi dake sai ki 6ara baki kiyi kuka har ta ji ki" Daga haka ya kulle kofar, ya sa makullin a aljihunsa, ya fita parlon a stairs ya hadu da Aunty, tace "Ta kasa sakkowa ne har yanxu xaka shanya ni a parlor" With confusion yace "Aunty I don't know, na duba dakin da take ban ganta ba, amma jiya Maimoon ta xo, ban san ko...." Wani tsawa tayi masa tace "Ni xaka raina ma wayo Aliyu?? Xuwa kayi ka boyeta?" Ya marairaice yace "Boyeta kuma Aunty, a ina xan boyeta ki shiga duk inda xaki shiga ki duba, ni fa jiya sai kusan sha biyu na dawo gidan nan, i don't know ko sun tafi tare da Maimoon, and tunda gari ya waye ban fito ba sai ynxu da ku ka xo" Bangajesa tayi ta nufi saman, dakin Jiddah ta fara budewa, hankalinta yyi mugun tashi ganin dakin kamar na amarya ga gaban mirror taff da kaya masu tsada, ta bude press, nan ma taga uban kaya, shi dai yana tsaye yana kallonta, ta juya tana kallonsa... Da sauri yace "Ko biyar dina babu a nan Aunty, Umma ce da Abba da uncles dina duk suka yi wannan siyayyan, ki tambayi Ummi ma" har bathroom sai da ta bude bata ga Jiddah ba, Juyawa tayi ta fita ta shiga sauran dakunan nan ma bata ga alamarta ba, fita tayi ta tafi bangarensa, iya dubanta bata ga Jiddah ba, kofar Balcony din ta murda, Abuturrab dake tsaye bakin kofa duk yana kallonta, yyi kasa da murya yace "I can't find the key to that place, balcony ne ai kin sani" Da ido ya bi ta har ta fita parlonsa, snn ya bi bayanta, Jiddah dai na tsaye balcony din, lkci lkci take satan kallon mutumin dake xaune a daya building din, da ta saci kallonsa kuma sai su hada ido, daga karshe ta canxa position dinta, sai bayan minti talatin Aunty ta bar gidan bayan ta ta66atar da gaske Jiddah bata nan, don ta duba ko ina, Ba tare ta koma da El-Basheer ba bayan ta amshi makullin mota tayi wucewarta, Ko kallon El-Basheer Abuturrab bai yi ba ya shige parlor, mikewa El-Basheer yyi ya bi bayansa, Abuturrab ya xauna saman kujera, El-Basheer ya xauna yana facing dinsa yace "Now tell me d truth, Ina yarinyar take?" Abuturrab yace "You encouraged Aunty to my house right?" El-Basheer yace "Not at all, bata ma ce min nan xata xo ba, sannan me yasa baxa ka bari ta koma gidan naku ba tunda ba matarka bace, or ka kaita bauchi" Abuturrab yace "Ohkk, saboda duk banyi niyya ba" El-Basheer ya shafa kansa sannan ya mike yace "Ohk then, anjima xan koma Bauchi in sha Allah" Abuturrab yace "Allah ya tsare" Kofa El-Basheer ya nufa, Abuturrab ya bi sa da kallon gefen ido har ya fita sannan ya tashi ya kulle kofar parlon da makulli ya wuce sama xuwa part dinsa, ya ciro makullin a aljihunsa ya bude kofar, daga kai tayi suka hada ido, ganin taki motsawa yace "Baxa ki fito ba" bata ce komai ba ta bi ta gefensa ta shigo parlon ya kulle kofar..... Karfe biyu saura Jiddah ta sauko parlor sbda yunwan da taji take ji, tun bayan tafiyar su Aunty Abuturrab ya sa ma gidan makulli ya koma parlon bangarensa, wayarsa dake saman center table ne ta ji yana vibrate, kallon wayar ta dinga yi sannan ta karasa ta duka ta dauka tana kallon screen din, Cikin few seconds tayi kokarin hade rubutun screen din wayar, "Blossom" katsewa kiran yyi aka sake kira, kamar ance ta juya suka yi ido hudu da shi a tsaye ya rungume hannu yana kallonta, daburcewa tayi xata mayar da wayar ta ajiye masa nan bakin center table din ya fado kasa, ta mike a tsorace tace "Dama kiran ka ake" karasowa yyi ya dau wayar fuskarsa daure yana duba screen din, juyawa tayi da sauri xata bar wajen yace "Tsaya nan..." Tsayawa tayi amma ta ki kallonsa, Sternly yace "Baki da hankali ne?? Ba na hanaki ma shigowa parlon nan idan ina nan ba? Ko don kinga ina kyale ki??" Tayi narai narai da ido tace "Kitchen xanje sai naji wayar na kara" Tsawa yayi mata yace "Ina ruwanki da wayar? Ko ke kika ajiye min a nan?" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, on a serious note without bothering ko ta gane turancin nasa ko bata gane ba yace "Naga kina neman fara wuce boundaries din ki a gidan nan, to bari kiji, daga yau, i mean daga yanxu da kike tsaye nan kada ki sake shigo min parlor idan ina gidan nan, idan kin tashi da asuba kafin in fito da safe dama ki girka duk abinda xaki girka na safe da rana ki kai dakin ki, karfe biyar na yamma ina sama, sai kiyi amfani da wannan opportunity din ki sakko ki dafa abinda xa ki ci da daddare, kafin shidda ki tabbatar kina dakin ki.... Am i clear?" Ita dai kanta na kasa, ya mata wani tsawa yace "Baki ji na ne?" Ta dago kanta hawaye cike idonta tace "Toh" Yace "Get out.. Tafi ki ban waje" Juyawa tayi a hankali ta wuce sama, ya xauna yana sake kallon wayar tasa da screen ya tsage. Abuturrab bai yi mamakim k'in daga kiransa da El-Basheer yyi ba, don ya kirasa ya fi sau biyu yaki dauka, Da yammacin ranan Abuturrab na operating laptop dinsa a parlor aka danna bell, wani faduwa gabansa yyi ya mike yana kallon kofar, bayan few seconds ya isa kofar yace "Who is there?" Muryar Umma yaji tace "Ni ce" Ya d'an buda ido da mamaki sai kuma ya bude kofar, lkci daya kuma yyi pretending as if he wasn't even surprise yana murmushi ya bata hanya, yana shafa kansa yace "Welcome Umma, sannu da xuwa" Ta shigo parlon tace "Unexpected visit... Ban ce xan xo ba ko?" Yace "Ai ba sai kin ce min ba Umma, ya hanya?" Ta xauna saman kujera tace "Alhmdlh, ina jiddar?" Ya d'an kalli sama sannan yace "Tana sama" daga haka ya wuce sama, calmly ya bude kofar dakinta, xaune ya ganta can karshen gado ta takure waje daya, tana ganinsa ta sauke kafarta ba tare da ta yarda ta sake kallonsa ba, kallon idanuwanta da suka yi ja yyi, kana ganinta kasan kuka tayi sosai, ya hade rai yace "Wani abu aka maki da kika xauna kike kuka?" Ta girgixa masa kai kawai, ya dinga mata wani kallo kafin yace "Tashi ki wuce bandaki ki wanke fuskarki ynxu" sauka tayi daga kan gadon ta shiga bathroom tayi yanda yace, yana tsaye dakin har ta fito yace "Dauka Hijab din ki" Ba musu ta dau hijab din ta saka, yana son mata warning ko da umma xata yi mata wani tambaya ta bata positive answers but ya fasa sanin cewar baxa ma ta ce da umman komai ba, kofa ya nuna mata alamar ta fita, ta fita dakin ya bi bayanta, wuce ta yayi, ya riga ta sauka downstairs, Yana kallon Umma da murmushi fuskarsa bayan Jiddah ta sakko parlon yace "Daxu take kuka umma wai in kai ta wajen ki, but yau xa mu wuce kano and ina wani aikin shi yasa ban kai ta ba" Umma dai bata ce masa komai ba sai kallon Jiddah da ta nufo ta tana murmushi a sanyaye tayi, dukawa tayi kusa da ita a hankali tace "Umma sannu da xuwa" Umma na kallonta tace "Me ya sami idonki?" Abuturrab yace "Kuka tayi, wai in kai ta can gida wajen ku, nace ba yau ba" Still Umma bata kallesa ba, Jiddah dai kanta na kasa tana wasa da fingers dinta, Umma tace "Toh je ki dauko abinda xaki dauka mu wuce yanxu" Abuturrab ya bude ido da sauri yace "Umma ta fara karatu fa" Daga kasa Umma ta kallesa har sama sannan tace "Is that so?" Ya sunkuyar da kansa yace "Eh Umma, tare xa mu koma kano da ita" Lkci daya hawaye ya kawo idon Jiddah tana kallonsa, Umma tace "Toh shkkn, Allah ya taimaka, dama anguwan na shigo shine nace bari in karaso mu gaisa, i will take my leave now, tunda na same ku lafiya Alhmdlh" Yace "Umma da wuri haka, ki bari after magrib...." Ta katse sa tace "Ohk da magariban xa ku dau hanyan kanon kenan?" Shiru yayi bai ce komai ba, ta mike tana kallon Jiddah tace "Toh xan koma jiddah" Kasa dago kai Jiddah tayi, Abuturrab yace "Toh mun gode Umma, Allah ya kara girma" Jiddah ta share idonta a hankali tace "Sai anjima Umma" Duk da tausayinta da Umma ta ji sosai amma sai bata wani nuna ba ta nufi kofa tace "In dai xan xo ki dinga kuka gwara kar in sake xuwa, kusan sati biyu ai ya kamata ki sake haka ko..." Jiddah ta bi ta da kallo hawaye na sauka idonta, wani kallo Abuturrab yyi mata sannan ya bi bayan Umma, Umma bata wani sauraresa ba har ta hau motar ta ta wuce, ya shafa kansa ya bi motar da kallo, juyawa yayi ya koma cikin compound din, bai tadda Jiddah a parlon ba, hakan ya sa ya wuce sama ya bude kofar dakinta ya shiga yaga bata ciki, shesshekar kukanta ya ji a bandaki, ya karasa kofar ya murda yaji ta kulle da makulli, ya hade rai yana knocking kofar yace "Ohh har kuka kika samu damar yi kenan, toh bude kofar kar ki bari in bude da kaina" Kin bude kofar tayi ta kara rushewa da kuka kamar an aikota, bude baki yyi da mamaki, duk yanda yayi Jiddah ta bude kofar kin budewa tayi, har dai ya dawo kwantar da murya amma kamar yana dada tunxurata, banda kuka babu abinda take, kallon agogo dake nuna shiddah da few minutes yayi ya xauna gefen gado yayi wani sigh, a ranan ya ke son komawa kano but he just can't go like that.... spare key din bandakin ne ya fado masa ya mike da sauri ya fita xuwa bangarensa, sai bayan da ya dauko ya koma dakin ya fara addu'an Allah yasa ta cire makullin daga jikin kofar, yana sa makullin kuwa ya ki budewa alamar makulli na jiki, rungume hannunsa yayi yace "Baxa ki bude kofar ba malama, kin san kina bata min lkci kano xan wuce?" Bai ji alamar xata bude kofar ba, but kukan nata da ya daina ji yasa yaji hankalinsa ya tashi bayan ya tuna da vow din da tayi kwanki wai xata kashe kanta, ya ga fa kamar ba seti gareta ba, ya kwantar da murya yace "Jeeddarh..." Nan ma bata amsa ba, rasa abinda xai yi yyi, a haka har aka kira magrib, hankalinsa ba a kwance ba ya tafi yyi alwala a parlor sannan ya wuce masallaci, ana idar da sllh da ya shigo gida dakinta ya kara shiga, har lkcn tana cikin bandakin, jingina yayi da kofar a hankali yace "Jeeddarh" bata tanka sa ba, hakan yasa yace "Ohk to ki gaya min me kike so, ni kuma xan maki" Jiddah dake durkushe jikin kofar ita ma, ta daga kai a hankali jin abinda yace, ya kara kwantar da murya yace "Kin ji?" Tana goge idonta tace "Gidanmu nake son in koma" Buda ido yyi da mamaki jin abinda tace, yace "Wani gidan naku?" Tace "In da ka gan ni mana" Rungume hannunsa yyi, bai san lkcn da yayi murmushi ba yace "Can hayin rigasa?" Tace "Ehh" yace "Kin tabbatar?" Hawaye ya silalo idonta tace "Ehh" Yace "Tohh shkkn bude kofar, sai mu tafi" Tana goge idonta tace "Ni ban yarda ba" Yace "Kinga ina karya? Da gaske nake xan kai ki, ba dai har kin gaji da xaman gidan nan ba" Tace "Ehh, na gaji... Wajen Baabarmu xan koma" yace "Toh bude kofar, dare na yi" mikewa tayi a hankali ta bude kofar, ya koma gefe yana jiran ta fito, tana fitowa suka yi ido hudu da sauri ta sunkuyar da kanta, ta wani sha kunu, har hakan ya so bashi dariya, yace "Toh hada kayan na ki" Kallon jakan da Umma ta bata tayi sannan ta nufi gun jakar, yana kallonta ta fara hada kaya, har ta gama ta daga jakar sama, yace "Ina ma kika ce in kai ki?" Tace "Gidanmu nace" yace "Toh tafi parlor da jakar ki jirani" Jan trolley din ta fara yi ta nufi kofa ya bi ta da ido har ta fita sannan shi ma ya fita ya tafi bangarensa, Jiddah na parlor ta xauna kasa tana jiransa, banda wasa da yatsunta babu abinda take har ya sakko rike da makullin motarsa, ba tare da ya kalleta ba yace "Mu je" mikewa tayi tana jan trolley din ta bi bayansa, bakin motarsa ta tsaya ganin ya bude Booth ta saka trolley din a ciki, sannan ta tafi ta bude gaban motar ta shiga, ya tada motar suka bar gidan. Tun jiddah na kalle kallen hanya ko xata ga sun shigo titin anguwar tasu har ta fara ganin daji babu alaman gidaje, driving kawai yake da speed amma kuma da nutsuwa, marairaicewa tayi ganin kamar sun fita gari tace "Ina xa mu je?" Ko tanka ta bai yi ba hakan yasa bata sake ce masa komai ba, sai hawaye, duk da baccin da ta dinga ji har suka shigo garin kano wajajen karfe sha daya bata yi baccin ba, hotel din da ya ke sauka ya tafi yayi lodging yayi ordering abinci, bin sa kawai take yana tafiya har suka isa dakin da aka basa, tana shiga dakin ta jingina da bango ya kulle kofar ta dinga bin dakin da kallo, ya ajiye makullin motarsa da wayoyinsa gefen gado ya shiga bandaki ya dauro alwala ya fito, ita dai tana ta tsaye, ya shimfida darduma yayi sllhn isha, bayan ya idar da sllh aka yi knocking kofar, mikewa yayi ya isa kofar ya bude, ya amshi abincin da aka kawo sannan ya kulle kofar, shayi ya sha, sai pepper soup din hanta bai bude takeaway din shinkafar ba ya mike ya dau wayarsa yayi dialing number Aneesah don tun yana hanya take ta kiransa, fita yyi dakin ya kulle daga waje, Jiddah ta bi sa da kallo, xaunawa kasa tayi hawaye na taruwa idonta bayan kusan minti sha biyar ta mike ta shiga bandakin ta dauro alwala ta fito tayi magrib da isha, kwanciya tayi kan darduman nan da nan bacci ya dauketa. Karfe sha biyu da mintuna Abuturrab ya shigo dakin abincin ya fara dubawa ko ta ci ya ga bata ci ba, ya xauna gefen gado ya sa hannu ya buga gefen kafarta bude ido tayi ganinsa ta mike xaune da sauri, babu yabo bbu fallasa yace "Dauki abincin ki ci" Tace "Ni na koshi" wani kallo ya mata, ta jawo abincin ta bude ta fara turawa, bai takurata sai ta ci da yawa ba, bayan ta rufe sauran yace "Tafi ki wanke bakin ki kiyi wanka" Bata iya ta ce masa komai ba amma ji tayi kamar ta fashe da kuka, ta mike ta cire Hijab din jikinta ta linke ta ajiye ta bude jakarta ta ciro sabulu da sponge, toothpaste da toothbrush, xata wuce bandakin yace "Tawul din fa?" Dawowa tayi a hankali ta kara bude jakar ta dau towel dinta ta wuce bandakin, ta kusa minti biyar tsaye bayan ta gama wankan ta rasa yanda xata fito daure da towel, gashi bata shigo da hijab ba, gajiya tayi da tsayuwa daga karshe ta bude kofar a hankali tana lekan dakin, bata gansa a dakin ba, ta fito da sauri, ta fiddo kayan da xata sa da turarruka da mai, tana rufe jakar ya shigo dakin, kasa dago kanta tayi ya rufe kofar, bata yarda ta kallesa ba ta mike ta dau kayan nata ta shiga bandaki, sai da ta gama sakawa sannan ta fito ta mayar da turare da cream din cikin jaka ta tafi kan darduma ta xauna, yana xaune can gefen gado ya kalleta yace "Tashi ki kwanta" sunkuyar da kanta tayi, sai kuma ta mike ta tafi can karshen gadon ta kwanta, ba a dau lkci ba kuma bacci ya dauketa, karfe daya nayi ya kashe laptop dinsa ya ajiye sannan ya dau pillow ya ajiye a kasa ya kwanta. Da asuba ana idar da sllh Abuturrab yyi wanka ya shirya, tun ana sllh Jiddah ta tashi amma bata juya ba balle ya san idonta biyu, tana jinsa yana shiryawa har ya gama, kallonta yayi ya buga gadon yace "Ke baki sallan asuba ne dama?" Mikewa xaune tayi ba tare da ta yarda ta kallesa ba ta wuce bandaki, kwance ta gansa da ta fito idonsa a lumshe ta tada sllh bayan ta idar ta kwanta kan darduma, karfe bakwai da few minutes Abuturrab ya tashi, tashinta yyi ta mike xaune da sauri, yace "Anjima idan anyi knocking ki bude kofa ki karbi abinda aka kawo, apart from that ban ce ko bakin kofar ki je ba, kin ji me nace maki??" A hankali tace "Toh" Sai da ya fara kunna TV dake dakin ya kai tashar hausa sannan ya dau jakarsa ya nufi kofa ta bi sa da kallo har xai fita ya juyo, da sauri ta dauke idonta daga kallonsa, yace "Saura ki bude kofar a haka baki sa hijab ba idan aka kwankwasa" bai jira cewarta ba ya fita dakin ya kulle kofar, mikewa tayi ta hau saman gado ta ci gaba da baccinta. Karfe takwas taji an kwankwasa kofa, mikewa tayi har ta nufi kofar haka ta dawo da sauri ta dau hijab da ta daura kan riga da wandon jikinta na bacci, sannan ta nufi kofar ta bude, abinci aka kawo mata ta amsa tare da godiya ta juya ta koma cikin dakin, sai da tayi wanka ta shirya sannan ta yi breakfast din da aka kawo mata. Throughout ranan haka ta yini ita kadai dakin sai dai tayi kallo idan ta gaji tayi bacci, tana farkawa ta ci gaba da kallon, abincin lunch da aka kawo mata ma sai kusan la'asar ta ci, karfe biyar da rabi tana tsaye bakin window taji an bude kofar, da sauri ta juyo, shigowa dakin yyi, ya ajiye ledan hannunsa,duk da wayar da ta gani kare a kunnensa hakan bai hanata ce masa Ina yini ba, ya xauna gefen gado ya ci gaba da wayarsa, bayan ya gama ya tashi ya fita ta bi sa da kallo, sannan ta kalli ledan da ya ajiye. Sai bayan magrib ya shigo tana xaune saman darduma ta bi sa da kallo har ya xauna ya bude ledan da ya shigo da shi ya fara cin naman tsiren dake ciki, dauke idonta tayi bayan few minutes tace "Kace min gidanmu xaka kai ni, baka kaini ba shine xaka kawo ni nan, ni wllh ka maidani wajen Babarmu" Bai tanka ta ba, hakan bai hanata maimaita abinda ta fada ba, ya juya ya kalleta yace "In maida ke wajen Baabarku?" Tayi shiru bata ce komai ba, mikewa yayi ya koma gefen gadon ya xauna yana facing dinta yace "Tambayarki nake?" Ta sunkuyar da kanta tace "Ehh kai kaini wajenta" Yace "Ohkk... amma bari in tambaye ki" Ta dago idanuwanta ta kallesa yace "Kina tunanin xamana da ke ba burden da damuwa bane a gareni?? Ina nufin baki san cewar rayuwar ki tare da ni nauyi babba na daura ma kai na ba da rashin kwanciyar hankali? Do you think ko matata ba iyakar abinda xan mata nake maki ba? What's so important about staying under same roof with you? Kina tunanin ni ajin ki ne da nake kula ki nake kula al'amuranki? Toh bari ki ji, ni din nan da kike gani ba ajin ki bane, ina taimakon ki ne saboda Allah ba don komai ba, gidan naku da kike cewa in mayar da ke an gaya maki baxan iya daukan ki in maida ke ba duk abinda xai faru dake ya faru? Toh bari ki ji, sau da yawa tausayi kan canxa mutum, banda haka bani da abinda xan yi dake a waje daya, and i mean it, ni ba ajinki bane" Yana fadin haka ya mike ya fice daga dakin, ta bi sa da ido kafin ta sunkuyar da kanta. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Har karfe daya da wani abu na dare Jiddah bata yi bacci ba, abu bai ta6a tsaya mata rai irin abubuwan da Abuturrab ya gaya mata ba, gashi har sannan ko digon hawaye bata yi ba, amma abun ya ki barin xuciyarta, da yake a kasan darduma ta kwanta kuma bai bi ta kanta ba yyi kwanciyarsa saman gado, ta mike xaune a hankali ta daura kanta bisa gwiwanta, sai a sannan hawaye ya shiga sauka idonta, gaba daya taji da ma ta hakura da aurenta da Iliya, taji ta gwammace gwara ta koma gidansu komin abinda xae faru, taji gwara ta gudu kawai, daga kai tayi hawaye na sauka idonta ta kallesa, duk da wutan dakin a kashe yake, tana ganinsa kwance saman gado. Da safe bayan ya gama shirinsa haka ya fita ba tare da yace mata komai ba, tun bayan da ta gaishesa bata ma san ko ya amsa ba har ya fita bata kalli inda yake ba ita ma, sae dai bata ga ya dau jakar laptop dinsa ba. Bayan fitarsa da minti kusan talatin ta mike ta dau Hijab dinta ta saka ta bude kofar dakin ta fita, a reception din hotel din ta gansa xaune da shayi a kan table din gabansa idonsa a kan screen din wayarsa, sosai gabanta ya fadi tayi still a inda take, dago kai yyi suka hada ido, tana ganin haka ta nufi kofar fita da sauri, da ido ya fara bin ta da mamaki, lkci daya kuma ya mike ya bi bayanta, fita tayi compound din hotel din, ya fara kalle kalle sbda baya son attention, luckily babu mutane haraban hotel din, hakan ya kara masa kwarin gwiwan bin ta ya fixgota ta fashe masa da kuka tace "Ni ka kyaleni in yi wucewata, wllh baxan xauna a nan ba wajen Baabarmu xan koma" Bai saurareta ba ya ciro makullin motarsa a aljihu ya ja ta xuwa parking space da motarsa yake ya bude back seat, turata ciki yyi ya kulle motar, sannan ya jingina jikin motar ya rungume hannunsa yana imagining... assuming baya xaune downstairs tafiyar xata yi da gaske, Jiddah ta dinga rusa kuka cikin motar, ya fi minti 7 a tsaye kafin ya bude motar ya shiga ya kulle, can gefe ta koma tana shessheka taki kallonsa, yana kallonta fuskarsa a daure yace "Ina xa ki tafi kika ce?" Cikin rawar murya tace "Gidanmu mana" Yace "Auren xa ki je a maki da mashayin saurayin naki?" Tace "Ehh" da mamaki yake kallonta, tace "Ni kawai ka mayar da ni, na yarda xan auresa din" Dauke kansa yayi bai ce komai ba, bayan few seconds ya kalleta yace "Toh ba kaduna muke ba yanxu, nan kano ne, ki jira idan mun koma kaduna sai in mayar da ke gidan naku da kaina ba sai kin tafi ke kadai ba, kin ji?" idonta ta fara gogewa tace "Yaushe xa mu koma kadunan?" Yace "Aiki nake yi a nan, sai ranan alhamis" Wani hawayen ya taru idonta, yana kallonta yace "Kin ji abinda nace?" Hawayen ya xubo mata tace "Har sai alhamis kuma?" Yace "Jibi ne alhamis din ai" Ta sunkuyar da kanta tana goge hawayenta, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawa babu, a hankali tace "Toh" Bai kuma cewa komai ba, ya juya ya bude motar ya sauka yana dubanta yace "Sauko" Ba musu ta sauko daga motar tana wani kumbure kumbure, yana kallonta yace "Wani man kike shafawa?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Wanda ka siya min mana" Bai ce komai ba, bayan few seconds yace "Toh kar ki kara shafawa" ta kallesa yace "Mu tafi ciki" Ba musu ta fara tafiya ya bi bayanta, ba komai ya sa ya tambayeta ba sai ganin yanda ta kara haske, which he don't like, ko kadan baya son idan mace ta doso waje ayi noticing dinta, haske kuma na daya daga abinda yake sa ayi noticing mace a waje, ita kam Allah ya hore mata wannan, juyawa tayi ta kallesa suka hada ido ta ci gaba da tafiya yana biye da ita, har suka shiga reception din sannan taji yace "Tafi ki shirya ina jiranki, minti ashirin na baki" Bata ce komai ba ta wuce sama ya bi ta da kallon gefen ido, kallon agogon wrist dinsa dake nuna karfe takwas da rabi yayi, he will be piloting around 10:30, shi kuma bai son xama daki tare da ita shi ya sa ya sakko ya xauna reception din. Karfe tara dai dai Jiddah ta sakko, tun da ya kalleta sau daya ya dauke kansa... Abaya ce baki a jikinta, i need not to say yanda kayan ya haskata, sai karamin jaka da takalmin kafarta same color, ta iso table din da yake xaune, lkci daya kamshin turaren da ta saka ya baxa wajen, ya fi minti biyu bai ce komai ba, can dai ya kalleta yace "Baki xo da Hijab bane?" Ta girgixa masa kai kawai, Bai kuma ce mata komai ba, ta xauna d'an nesa da shi, sai a snn yace "Me xaki ci?" Tayi shiru bata ce komai ba, chips and egg ya sa aka kawo mata sai shayi, ya sa ta tafi sama tayi breakfast din, ta mike ta wuce, ya bi ta da kallo, lkci lkci yake duba agogon hannunsa dake nuna after 9, tashi yyi ya wuce sama, ya tarar ta gama, jakarsa ya dauka yace "Kina bata min lkci Malama" Tashi tayi ta bi sa suka fita ya kulle dakin, tana biye da shi har suka iso gun motarsa, ya ajiye jakar a back seat ya shiga maxaunin driver ya tada motar, xagawa tayi a hankali ta bude front seat din ta shiga ta xauna, warming din motar yayi suka fita haraban hotel din ya dau hanyar Airport. Abuturrab ya samu discount wajen yankar mata ticket din Business class, wanda hakan yasa take cikin boarding group na farko, duk wanda ya ga jiddah a lkcn xai xata ba farkon boarding din plane dinta bane, she is so calm, but deep inside her she is so so Afraid, bata ta6a tunanin haka jirgi yake da girma ba, snn bata ta6a mafarkin xata ga jirgi ido da ido ba balle har ta shiga wataran, kuma tunda ta shiga jirgin ta xauna idonta ke kasa, sai ka lura da ita sosai xaka gane a tsorace take, daya daga flight crew member ce ta nufota tana murmushi da ladabi tace "Ina kwana Hajiya..." Jiddah ta daga kai ta kalleta a hankali tace "Ina kwana" Cabin crew din na murmushi ta xauna kujeran gefenta tana kallonta ta buda mata ido sannan ta shiga fastening Seat belt dinta, wanda da alama Abuturrab ne ya sa ta gwada mata yanda zata saka seat belt din, Jiddah dai kallonta kawai take har ta gama sakawa, Flight crew din tace "Toh saka naki haka" Ba musu jiddah tayi yanda taga tayi, matar tayi murmushi ta yi unfasten din nata ta mike tace "Toh ki cire, sai jirgi xai tashi xa ki saka, Allah ya sauke mu lafiya" Jiddah ta cire, matar ta kuma sakar mata murmushi ta juya ta wuce, jiddah ta bi ta da kallo don kayan jikinta yayi mata kyau sosai ba kadan ba, ba su fi ashirin a Business class din ba, kowa kuma harkan gabansa yake, tunda wani mutumi ya xauna gefenta ta xama so uncomfortable, ga kamshinsa da ya cika wajen, shi dai bai kalleta ba sai operating din wayarsa da yake yi attentively, bayan minti ashirin duk passengers din sauran class din suka gama boarding plane din, Nan aka fara announcing ayi fastening Seat belt, ganin kowa na saka nasa ita ma ta fara kokarin saka nata, amma sai ta kasa sakawa sai fama da belt din take, sai a sannan mutumin dake gefenta ya kalleta ta gefen ido, ganin ta rasa yanda xata saka, ya kai hannunsa ya saka mata, bata iya ta kallesa ba kuma bata ce komai ba, a haka jirgin ya fara tafiya, dukar da kanta da yaga tayi na kusan minti 5 yasa ya sake kallonta yace "Are you okay?" Da sauri ta dago, dai dai nan jirgin ya daga, ta rufe bakinta hankalinta a tashe tace "Amai nake ji wllh" da mamaki yake kallonta yace "Amai?? Ohk hold it for a while" Ita dai hannunta na bakinta tana gyada masa kai, he gets she might be prone to motion sickness... ya jira har sai da jirgin ya tafi can sararin samaniya suka kai cruising altitude, duk da seat belt sign that is still on... hakan bai hana shi cire nasa seat belt din ba sannan ya cire mata nata, And he led her to the lavatory, wata cabin crew ta nufosu tana kallonsa tace "Is she alright?" Yace "Sure she will be" yana tsaye har jiddah ta fito daga lavatory din tana sauke numfashi, banda jiri babu abinda take gani, ga kanta dake juya mata, yace "How are you feeling now?" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yace "Toh mu je" Tafiya ta fara yi ya bi bayanta, har xuwa wajen seat din nasu, ta xauna sannan shi ma ya xauna, kamar ya lura she is so uncomfortable from d clouds she is seeing via the porthole that she is sitting beside, rufe wajen yyi yana kallonta, hakan da yayi ya taimaketa sosai kuwa, bayan some minutes da take off dinsu aka kawo masu snacks with drinks, kallonta yayi suka hada ido, bayan an ajiye masu ya dau nasa ya fara ci, ganin bata ci komai ba har ya gama cin abinda xai ci ya kalleta yace "Ain't you eating?" Tayi shiru bata ce komai ba, bai kuma yi mata magana ba, har ta fara bacci, seeing how uncomfortable she is sleeping yasa ya bata access to his shoulder, a haka kuma ta dinga bacci har aka fadi nan da mintuna nawa xa su shiga lagos, shi ya saka mata seat belt din nata bayan an bada umarnin yin hakan, dalilin da yasa ta tashi daga baccin da take kenan, jiddah bata san lkcn da ta rikesa ba ta rufe fuskarta a jikinsa da xa su yi landing, Cikin kuka take gaya masa amai take ji, ya dago kanta yace "Hold it for a while..." ya bude porthole din da ya rufe yana nuna mata, juyawa tayi ganinsu a kasa jirgin na gudu ta ji hankalinta ya d'an kwanta, amma har lkcn xuciyarta bai daina bugawa ba, shi dai kallonta kawai yake, can ta kallesa, d'an murmushi yyi yace "Ya sunanki?" Ta sauke idonta tace "Jiddah" yace "Jiddah!!" Ta gyada masa kai, yace "Wannan ne farkon hawanki jirgi Jiddah?" Ta gyada masa kai, bai san lokacin da yyi murmushi ba yace "I see, to mun kawo lafiya, hope ur next flight won't be as frightening as this?" Ita dai bata ce komai ba, yace "Ke kadai kika xo lagos?" Ta girgixa masa kai tace "Aa ni da yayana" yace "Wow, yana ina?" Ta buda masa hannu alamar bata sani ba, yace "Ba tare ku ka shigo jirgin ba?" Tace "Toh ni ban sake ganinsa ba" yana waige waigen business class din yace "Ohk, sunana Yousuf.... Yousuf Umar" yana fadin haka ya ciro wayarsa yace "Sa min digit dinki so i can say hi some other time Jiddah" Tayi shiru tana kallon wayar tasa me kyau kirar samsung, can tace "Ni ae bani da waya" da mamaki yace "Baki da waya?" Ta gyada masa kai yace "Ban yrda ba" tace "Wllh, wanda yayana ya bani yana gida" ganin how she is speaking innocently yasa ya yrda, ya ciro Complimentary card dinsa ya mika mata yace "Toh ki min alkawarin xa ki kirani ga number na nan" ta dinga kallon katin dake dauke da number sa kafin tace "Alkawari fa kace" yace "Eh Jiddah" jan fingers dinta ta fara yi bata ce komai ba ya bude jakarta ya sa mata katin dai dai nan kuma jirgin ya tsaya cak, yace "Hakan na nufin kin dau alkawarin" Ta xaro ido tace "Kamar yaya" yace "A yarenmu yanda kika yi da fingers dinki yana nufin kin dau alkawarin" Ta xaro ido tana kallonsa, ya sakar mata murmushi, Cabin crew din da ta gwada mata yanda xata saka seat belt dinta daxu ce ta iso inda take tana murmushi tace "Captain Aliyu yace in taho da ke Hajiya" Jiddah ta kalli Yousuf Cabin crew din ta basu waje ta koma can ta tsaya tana jiran Jiddah, Yousuf yace "yayanki ne yayi tukin jirgin kenan?" Da mamaki take kallonsa tace "Tukin jirgi fa kace? Aa baxai iya ba" yana murmushi yace "Toh tashi ki je... ina jiran kiranki" shi ya rigata mikewa ya dau briefcase dinsa ya fara tafiya ta bi sa da ido snn ta mike ta nufi cabin crew din da tayi mata jagora har Cockpit inda Abuturrab yake xaune tare da Co-pilot dinsa wani black American suna secure Cockpit checklist, da mamaki Abuturrab ke kallon Crew din don ce mata yayi tayi leading dinta outside d plane, hannu black American din da ya kafe jiddah da ido ya mika mata yana murmushi yace "Hello...." Kallon Abuturrab Jiddah tayi, lkci daya taga ya mata wani shegen kallo, amma calmly yace "Juya ki tafi ki jirani ina xuwa..." Juyawa tayi da sauri ta bar wajen, Yana ma American din murmushi yace "We don't do that captain, and she doesn't even understand English" Pilot din na kallonsa yace "Ohh, is she ur sister?" Abuturrab yace "My friend's wife...." Jiddah na sauka jirgin ta dinga kalle kalle ganin jiragai da yawa, mamaki ta dinga yi wai yau ita ce ta hau jirgi, Crew din daxu ce ta sakko suka bar wajen tare, sai bayan kusan minti ashirin Abuturrab suka sauko daga jirgin da Co-pilot dinsa. Kallonsa Jiddah ta dinga yi ganin ya kuma canxa kaya, daxu da fararen kaya ta gansa kamar uniform da hula a cikin jirgi, yana isa inda take ba tare da ya kalleta ba ya wuceta, ta bi sa da kallo, juyawa yyi ganin bata taso ba yace "Ko in daga ki ne?" Mikewa tayi a hankali ta bi bayansa, hotel din da ya ke sauka a lagos not too far from Murtala Muhammad Airport ya nufa tare da ita cikin taxi, Tana biye da shi bayan sun sauka taxi din sun shiga hotel din, bin sa take kamar xata shige jikinsa ganin mata kusan tsirara suna yawo hankali kwance, garin kallon wata da ta gani da wando iya cinya ta kusa fadawa kansa, ya juyo yana kallonta, kamar xata yi kuka tace "Ina ne nan ka kawo ni?" Ci gaba yyi da tafiyarsa ta bi bayansa, har ya amshi makullin daki a reception tana makale da, shi dai bai sake ce mata komai ba suka shiga dakin da ya amsa, bayan ya kulle kofar kamar xata yi kuka tace "Su basa jin kunya ne?" Juyawa yayi ya kalleta pretending not to know what she is talking about yace "Su wa?" Ta sunkuyar da kanta, yace "Tambayarki nake su wa?" Still ta ki cewa komai, ya ajiye wayoyinsa yace "Ke me ya aike ki kallonsu?" Bai jira cewarta ba ya fita dakin ta bi sa da kallo, a hankali ta karasa ta xauna gefen gado tana bin katon dakin da kallo, ya ma fi wanda suke ciki a kano kyau sosai, Ba a dau lkci ba ya dawo dakin, fried rice with chicken, jollof rice with beef and plantain, sai pepper soup da ruwa with drinks.... abubuwan da ya bude kenan tsakar dakin ya xauna kan carpet yana nannade hannun shirt din jikinsa, ita dai kallonsa kawai take, sai da ya fara cin fried rice din sannan ya daga kai ya kalleta yace "Idan xa ki ci ki sakko" A hankali ta girgixa masa kai, ya hade rai yace "Sakko...." Bata sake cewa komai ba ta mike ta dawo ta xauna daya side din carpet din, abincinsa kawai yake ci, ganin haka ta dau spoon dake nannade cikin tissue ta saka cikin jollof rice din ta fara ci, ya gama cin abinda xai ci ya mike ya shiga bandaki ya wanke bakinsa sannan ya fito ya kwanta, ta d'an saci kallonsa ta dau sauran naman kazan da ya rage ta daura kan abincinta, hada ido suka yi lkci daya ta daburce ya mike xaune yace "Maida shi, ai nace baxa ki sake cin kaza ba" Da sauri ta mayar da kaxan kan abincin da ya rage, ya koma ya kwanta, bayan ta gama cin abincin ta gyara wajen ta hade takeaways din cikin leda, ruwan da drink ta ajiye su gefe daya, sannan ta mike tana kallonsa taga idonsa a rufe, can gefen gadon ta tafi ta xauna a kasa. Karfe biyu saura Abuturrab ya koma Airport tare da Jiddah, don he will be piloting to Abuja, hankalinta ya tashi ganin jirgi xa su kara shiga tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Don Allah mu hau mota, wllh bana son jirgin nan" Lkci daya hawaye ya kawo idonta, yace "Baki so saboda me?" Tana goge idonta tace "Amai nake yi, kuma ina ganin jiri, don Allah kar mu shiga tsoro nake ji" Yace "Daxu kin yi amai kenan?" Ta gyada masa kai yace "A ina kika yi aman?" Tace "Wani mutumi ne da ya xauna kusa da ni ya kai ni bandaki" Abuturrab ya juya da sauri yana kallonta yace "Ya kai ki bandaki??" Ta gyada masa kai, maimaitawa ya sake yi, ta kuma gyada masa kai, yace "Sai aka yi yaya?" Tace "Ya jirani nayi aman sannan muka dawo, da jirgin xai sauko kasa ma shine ya kamani wllh tsoro nake ji" Sake baki yayi yana kallonta yace "Ya kamaki a ina?" Tayi shiru bata ce komai ba, ya rungume hannunsa yace "Ya mutumin yake???" Tace "Yana jin hausa, kuma dogo ne kaman ka, sannan yace min sunansa Yousuf" Ya xare glass din idonsa yana kallonta, can yace "Ohk har hira ku ka yi kenan" Tace "Aa bamu yi hira ba" Bai kuma ce mata komai ba ya ci gaba da tafiya ta bi bayansa gabanta na faduwa, ticket din da Abuturrab ya yankar mata sai da ya tabbatar the person next to her is a female, exactly abinda tayi daxu daga kano xuwa Lagos shi tayi daga Lagos xuwa Abuja, Bayan jirgin ya sauka Abuja ta fita tana kare ma jirgin kallo tana fatan babu abinda xai kaddara mata sake shiga jirgi, har suka isa gidan Abuturrab wajajen la'asar jikinta a sanyaye yake, duk yana lura da ita bai ce komai ba, xaunawa tayi kan kujeran parlon tana bin parlon da kallo, yana kallonta yace "Yanxun ma kinyi aman a jirgi kenan?" Ta gyada masa kai kamar xata yi kuka, hararanta yyi ya wuce bedroom dinsa don yin alwala ya wuce masallaci dake layin, Har ya dawo tana nan yanda ya barta yace "Bakya sallah ne?" Mikewa tayi tace "Ban san inda xanyi alwala ba" Ya nuna mata dakin dake parlon, ta nufi dakin, ya bi ta da kallo sannan ya wuce dakinsa. Bayan ta idar ta fito parlor ta xauna tana sake kare ma parlon kallo, a haka bacci ya dauketa bayan ta jinginar da kanta jikin kujeran da take xaune, wajen karfe biyar da rabi aka kwankwasa kofar parlon, hakan ne ya farkar da ita, jin an kara kwankwasawa ta mike ta nufi kofar ta murda key din ta bude kofar, komawa baya tayi tana kallon warce ke tsaye bakin kofar kamar yanda take kallonta ita ma, dai dai nan Abuturrab ya shigo parlon, Jiddah ta juya tana Kallonsa.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Abuturrab yace "But you didn't tell me kina xuwa Aneesah" Aneesah tayi wani murmushi tace "How will i tell you ina xuwa Aliyu, dama dalilin da yasa kake walakanta ni kwana biyu kenan, dama wata ka samu? Dama wannan ce dalili" Daga sama har kasa take kare ma Jiddah kallo tana murmushin takaici tace "Ki bar murna kin samu pilot har yana kawo ki gidansa saboda tsagwaron so, nima haka ya dinga min, but...." Abuturrab ya katse ta yace "Come off it pls Aneesah, what's all this? I thought i explain better to you her position, she is the lady...." Aneesah ta sake kallon Jiddah da sauri, Jiddah dai banda kallonta ita ma babu abinda take, A hankali Aneesah tace "Which lady Aliyu?" Yayi kasa da muryar yace "Ba ke kika ce in kawota ta xauna gidanku ba" Sosai gaban Aneesah ya fadi don bata ta6a tunanin Jiddah ce wnn yarinya da Abuturrab ke fadi mata ba, ta dinga kallon Jiddah xuciyarta na bugawa, ta ma rasa abinda xata ce masa, Abuturrab yace "Tunda kin xo yanxu sai ku tafi tare, dama anjima nake son kai ta gidan naku, hopefully nasan Mumy ta yarda ta xauna with ur family..." Aneesah ta hadiye abu da kyar, har sannan ta kasa daina kallon Jiddah da tayi mata wani kwarjini, a xuciyarta ta shiga kokwanton anya ita ce me awaran da Aunty ta ce, or is Aliyu playing her?? Abuturrab ya juya ya kalli Jiddah bbu yabo bbu fallasa yace "Dauko mayafinki" Shiru tayi tana kallonsa, a d'an tsawace yace "Baki ji na ne?" Ta koma baya tace "Toh ina xanje idan na dauko?" Yace "Ban sani ba, wuce ki dauko" Juyawa tayi ta koma can tsakiyar parlon ta tsaya kamar xata yi kuka tace "Allah ni babu inda xanje, ba gidan Baabarmu nace ka maida ni ba, nasan ita wacece da xan bi ta" Daga maganarta Aneesah ta kara tabbatarwa ita ce me awaran, Abuturrab ya saki baki yana kallon Jiddah, Aneesah ta hade rai tace "Toh nan din gidan ubanki ne da baxa ki bari ba?" Jiddah ta kalleta, a hankali tace "Ubana fa kika ce?" Aneesah da xuciyarta ya dau tafarfasa tace "Shi din..." Lkci daya Jiddah ta fashe da kuka tace "Ba dai ubana dake kabari ba wllh sai dai naki" Aneesah ta saki jakar hannunta tace "Kika xagi ubana?" Jiddah ta goge idonta tace "Ehh an xaga, me nawa uban ya maki da kika xagesa ke?" Aneesah tayi kanta a mugun fusace, fixgota Abuturrab yyi yace "Hey are u okay, what are u trying to do?" Fixge hannunta tayi kamar wata zakanya ta nufeta, cikin tsawa Abuturrab yace "Don't try that Aneesah, u will definitely see the other side if me by touching her" Tuni Jiddah ta tsorata ta bar wajen da gudu ta yi hanyar kitchen hakan bai hana Aneesah bin ta ba, shakota Aneesah tayi tace "Uban wa kika xaga?" Tuni Abuturrab ya nufesu, Jiddah ta kwala kara ta gatsa mata cixo a hannu, Aneesah bata yi wata wata ba wajen sauke mata lafiyayyen mari a fuska sannan ta wuntsular da ita a kasa tana cewa "Don kaza kaxanki ubana sa'an kaf danginki ne aka ce maki?" wani ihu Jiddah ta fasa tana cewa wayyo bayanta, wayyo kafarta, Kamar daga sama Aneesah taji saukan tagwayen mari wanda sai da yasa taga duhu na few seconds, ya fixgota fiercely yace "How dare you? You bitch" with shock Aneesah ke kallonsa, ya nufi kofa ya wuntsular da ita waje kamar yanda ta ma Jiddah yyi banging kofar, Banda rusa kuka babu abinda Jiddah dake yashe a kasa take tana kiran Baabarmu, Bude kofar Aneesah tayi tana daga tsaye bakin kofa hawaye kaca kaca a fuskarta tace "You called me a bitch Aliyu?? Ni ka walakanta ka sauke yatsunka fuskata a kan wannan yar talakawan bagidajiya jaka? Ni ka ci ma mutunci haka in her present? U threw me out of ur house a kan yar talakawa me tallan awara?" Jiddah ta goge idonta ta mike cike da tsiwa tace "Idan ana tafiya lahira da arxiki sae ki daura naku a kai ki tafi da shi in ga, kuma Allah ya isana, ban yafe maki ba, axxaluma...." Fixgo hannunta Abuturrab yyi ya nufi daki, cikin kuka tana son kwace hannunta take cewa "Ni ka kyaleni, me na mata xata mareni...." Turata yyi cikin dakin ya sa makulli, sai a snn ya daga kai ya kalli Aneesah, ji yyi gaba da gwiwansa ya sace, ya nufeta, tana ganin haka tayi wani murmushi tace "Watch out for it Aliyu, xaka san ba a ta6a mu a xauna lafiya, daga yau ka kafa daka sanin abinda ka min a rayuwarka..." Daga haka ta dau jakarta xata fita parlon hawaye na sauka idonta, ya rikota yyi kasa da murya yace "But Aneesah...." Ko rufe baki bai yi ba ta sauke masa mari sau biyu, hakan bai sa ya saketa ba ta dinga dukansa a kirjinsa, ya rungumeta gamm yace "I'm sorry Aneesah" kuka kawai take, shi kam duk jikinsa yyi sanyi, cikin rawar murya tace "A kan wannan bagidajiyar xaka mareni and throw me out of ur house Aliyu??" Ya kwantar da ita kirjinsa yace "U are misperceiving me Aneesah..." Turasa tayi da karfi ta nufi kofa tana kuka ta fita, dafe kansa yyi ya xauna saman kujera yana furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, daukar wayarsa yyi ya shiga dialing number Ahmad, har ya katse bai dauka ba, yana ta xaune parlon har kusan magrib sannan ya mike da kyar, bedroom din da Jiddah ke ciki ya nufa ya bude kofar, kwance ya ganta a kasa, ya karasa ciki yana kallonta ya duka, bacci take, ya kai hannu goshinta, bude ido tayi, ya daure fuska ya mike, ta tashi xaune tana mitsika ido, yace "Kin san warce kika xaga daxu?" Ta kallesa tace "Toh ai nima bata san wacece ni ba" ya duka yana kallonta da kyau yace "Gaya min ke wacece?" Ta turo baki ta taki cewa komai, kallon fuskarta da shatin mari ya kwanta kawai yake, can ya mike jin xa a tada sllh ya fita dakin. Abuturrab na dawowa masallaci ya ga kiran Ahmad a wayarsa, ya xauna sannan ya kuma dialing number sa ya kai kunne, daga daya bangaren Ahmad ya daga yace "Ya kwana biyu?" Abuturrab ya shafa kansa ya mike ya koma dakinsa, a hankali yace "Alhmdlh, how is work?" Ahmad yace "Alhmdlh, baka yi piloting xuwa Abuja bane yau" Abuturrab yace "Ina Abuja" Ahmad yace "Alright, ya na ji ka so calm dude?" Abuturrab bai ce masa komai ba, Ahmad yace "Xan shigo after isha" Abuturrab yayi kasa da murya yace "Ka taho da paracetamol or any pain reliever" Ahmad yace "Ko har Aneesar ta je ne?" Abuturrab ya katse wayar, ya ajiye yana tunanin where he is going to start from, sure yasan yana son Aneesah sosai baya son komai da xai bata mata rai, But why did all this happen, why did things turn out this way.... Shafa kansa kawai yayi knowing the only way out now shine ya tura gidansu in few days time, wayarsa ya sake dauka har xai yi dialing numberta ya fasa. Abuturrab na xaune parlor bayan ya dawo isha yana jiran xuwan Ahmad, karfe takwas da few minutes Ahmad ya danna bell, ya mike ya bude masa kofa, Ahmad ya shigo parlon, xaunawa yayi saman kujera yace "After leaving me all my self with my wedding preparation, still u have d gut not to ask how everything is going.... right?" Abuturrab yace "Ohk ka fara shirye shirye ne?? Sure juma'ahn sama ne koh? I'm sorry na manta wllh, what are u up to now? Kasan ba haduwa muke yanxu a kadunan ba kamar da" Ahmad yyi dariya yace "Ya xa mu hadu kuwa, tunda ga ka ga amaryar ka Jiddah" Abuturrab ya tsura masa ido, can yace "Is there anything i will gain idan na maka karya Ahmad?? But don Allah ka gaya min me yasa kake ganin har ynxu matata ce ita?" Ahmad yace "Toh gashi nan ba sai na fada ba, da fa duk na shigo kd sai mun hadu, infact kai ma kake xuwa gidanmu ynxu kuwa kana gidanka, idan ba wanda yyi sabon aure ba, giyan auren na dibarsa waye ke yin haka??" Abuturrab yace "Ka dai jira xanyi auren kwanan nan sae kaji dadin fadin duk abinda ke ranka, amma yanxu kam i am a bachelor just as u, sae sabon title da na samar ma kaina na xama Uba, i am more like a father or guardian now" Ahmad yyi murmushi yace "Toh ka bani ita inyi ta biyu da ita Captain" Abuturrab ya kallesa, kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Are you for real?" Ahmad yace "I'm serious wllh in dai Umma xata yrda i will" Abuturrab yace "Ohk, but.... How are we going to open up all this to our parent? Kasan dai ynxu banda Aunty da kai, sai ita yarinyar babu wanda yasan babu auren nan" Ahmad yace "We will cross the bridge when we reach there, yanxu dai ka amince min kai?" Calmly Abuturrab yace "In da gaske kake na amince, nima burden xai sauka kaina, if not for her da banyi making mistake da nayi daxu ba" Ahmad yace "Wani mistake?" Abuturrab ya dau remote din TV yana canxa channel yace "Ba ruwan ka" Ahmad yyi murmushi yace "Everything is settled now tunda ka amince" Kafin karfe tara Jiddah tayi bacci bayan tayi wanka, Hijab din Aneesah dake gidan ya bata tayi sllh tun magrib. Abuturrab na xaune har sannan a parlor tare da Ahmad sae dai hankalin sa baya tare da Ahmad, bai yi tunanin Ahmad xai kai har 10 a gidan ba, Can dai Abuturrab yace "Wai kana kallon agogo kuwa?" Ahmad yace "Ohh ta kusa xuwa kenan, anyway ko baka fada ba dama yanxu xan wuce sai da safe" Daga haka ya mike ya nufi kofa Abuturrab ya bi sa da kallo, mikewa yyi ya bi bayansa yace "Ka ajiye ni eatry let me get something to eat" A tare suka fita gidan, sai kusan karfe goma da rabi Abuturrab ya dawo, yana shigowa parlor ya kulle gidan sannan ya wuce dakin da Jiddah take, tayi nisa baccinta, Ya ajiye ledan abincin ya nufi gadon, buga gadon yayi ko motsawa bata yi ba, yayi hakan ya kai sau uku ganin bata tashi ba ya dau bottle water ya bude, sai kuma ya fasa xuba mata ruwan ya ajiye sannan ya kai hannu kafarta yana tashinta, bude ido tayi a hankali, yace "Tashi ki ci abinci" Ta girgixa masa kai tace "Na koshi" Yace "C'mon tashi nace" Mikewa xaune tayi da kyar tana kallonsa da idanuwan bacci tace "Na koshi" Ya hade rai yace "Sakko nace" Xamowa tayi ta sauka kasa tana lullumshe ido, ya bude mata tuwo da veg soup din, ta tashi tana rurrufe ido yace "Ina xa ki?" Tace "Xan wanke hannu" Bai ce komai ba ta tafi ta wanke hannun ta dawo, tun da ta fito yake kallonta, Kana ganin yanda Hijab din yayi a jikinta xaka kasan bata saka komai ba a ciki, dama kuma hijab din har kasa yake ja mata, xaunawa tayi ta jiginar da kanta jikin gadon ta lumshe ido, buga gadon yayi ta bude ido da sauri ta kalli abincin gabanta sannan ta kai hannu ta fara ci a hankali, juyawa yayi ya fita dakin.... Washegari da safe Abuturrab ya fita yayi mata shopping din few clothes, karfe goma kuma ya nufi airport tare da ita, babu abinda ya sanyaya masa jiki sai yanda kiran Aunty ya dinga shigowa wayarsa babu kakkautawa, shi kuma yaki dagawa, Jiddah na ganin inda suka xo hankalinta ya tashi, marairaice masa tayi tace "Ni fa bana son hawan jirgin wllh" Yana kallonta yace "Sai me xa ki hau?" Tace "Motar" Wani kallo yayi mata yace "Sai ki hau motar inda kika gansa ai" Lkci daya hawaye ya kawo idonta bata kuma ce masa komai ba, tun bata kai ga shiga jirgin ba taji kanta ya fara juya mata, Tana rike da wayansa da ya bata ta nemi kujera ta xauna a business class, sai waige waigen inda xata gansa ta mika masa wayar take, to ina shi yake xama ne a cikin jirgin, tunawa tayi a inda ta gansa jiya bayan jirgi ya sauka, and she assumed a wajen yake xama shi, jin taku a gefenta Jiddah ta juya, buda ido tayi sosai ganin wanda suka shiga jirgi tare da shi a rana na farko, seat dinsa ya nufa ya ajiye karamin jakar hannunsa a sama sannan ya xauna, da sauri ta dauke kanta gabanta na faduwa, wata mata ce ta xauna kusa da ita tayi mata sannu, murmushi kawai Jiddah ta mata tana juya wayar Abuturrab dake hannunta, bayan wani lkci jirgin ya tashi, suna keta hazo ta cire seat belt dinta da sauri ta mike bayan ta ajiye wayar Abuturrab, hanyar lavatory ta nufa sai a sannan Yousuf ya ganta ya bi ta da kallon mamaki, ba a dau lkci ba ta fito, matar dake kusa da ita tace "Did u feel nauseous?" Jidderh tayi mata murmushin karfin hali ta xauna, Ta d'an saci kallon Side din da Yousuf yake suka hada ido, sunkuyar da kanta tayi, throughout the short journey to kano bacci tayi a jirgin, snacks da aka kawo mata ma bata ci ba, Matar dake gefenta tayi tapping dinta tace "Ki saka seat belt dinki" Bude ido Jiddah tayi ta fara saka seat belt din, runtse ido tayi da jirgin ya fara sauka bayan ya samu izinin yin hakan, matar da ta lura she is very uncomfortable ta riketa, tace "It's just for a few seconds, sorry dear" Jiddah bata ce mata komai ba har jirgin ya sauka, rufe bakinta tayi kar ma tayi ihu, matar na Kallonta tana murmushi tace "it's all over" A hankali Jiddah ta cire seat belt din, bayan da jirgin ya tsaya ta mike ta dau hand bag dinta ta fara fita kamar yanda ta ga sauran nayi, da kallon mamaki matar ta bi ta, tana mamakin to ko kurma ce dai, Yousuf ya mike ya dau jakarsa ya bi bayanta da sauri, a hankali take sauka daga matakalan jirgin iska me sanyi na kadawa a filin airport din, tana sauka kasa kamar ance ta juya taga Yousuf yana saukowa shi ma, murmushi ya sakar mata har ya iso inda take yace "Jiddahh" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, mika mata hannunsa yayi yace "Bani wayar taki in sa maki number na tunda Allah ya sa kin taho da shi yau" Ta buda ido sosai tace "Ba wayata bane, na yayana ne" Da mamaki yake kallonta yace "Yayanki? Yana ina?" Ta kalli cikin jirgin tace "Kaman yana ciki, ni dai ban gansa ba" Yace "Ina ku ke xuwa tare da shi ko da yaushe a jirgi?" Tace "Nima dai ban sani ba" Yace "Baki sani ba kamar ya?" Tace "Allah ban sani ba ne" Yayi shiru yana kallonta walking slowly together with her, can yace "Me ku ka je yi a Lagos?" Ta kallesa da sauri tace "Lagos?" Yace "Ehh" Tace "Nan ne Lagos din don Allah?" He couldn't help it but left his mouth agape yana kallonta with surprise, ta dauke kanta tana ci gaba da tafiya yace "Wait Jiddah, are you kidding me, or you just don't want to give me an answer" Bata ce komai ba, calmly yace "I am talking Jiddah..." Tsayawa tayi tana kallonsa tace "Ni fa ba wani turanci nake ji ba" Sake baki ya kuma yi yana kallonta, bai san lkcn da yace karya kike.... Tace "Wllh ba karya nake maka ba" Sincerely ta fadi hakan, ya shafa kansa yana sake kallonta daga sama har kasa yana naxarin abinda tace wai bata jin turanci, but how?? tsadadden abaya ce jikinta blue da ya mugun haskata, ko kwalli babu a idonta, wanda kuma bai kalli lips dinta da kyau ba, sai yayi assuming pink lip gloss ta saka coz after being pinkish har sheki lips din nata yake, ga manyan idanuwanta farare tasss kamar madara, hancinta kuwa have the perfect shape a nose should have snn ga tsayi, ya d'an mata murmushi yace "Na yarda Jiddah, yanxu ina xa ki?" Tace "Nima ban sani ba yayana nake jira, kilan yana saman jirgin har yanxu" Yace "Yayanki... iyayenku daya da shi?" Shiru tayi can kasan ranta kuma tana tunanin abinda xata fada masa, yace "Ki gaya min gaskiya Jiddah" Ta kallesa still bata ce komai ba, yace "Ina sauraranki" ta kwantar da kai tace "Me yasa kake son sani?" Yace "I just..." Shiru yayi kamar wanda ya tuna abu, sai kuma yace "Kawai ina son sani ne" Tace "Ba iyayenmu daya ba amma yayana ne" A hankali yace "Ko dai saurayin ki Jiddah" Ta wani xaro ido, sai kuma ta kyalkyale da dariya tace "Saurayi na? Saurayina fa kace? Aa ni ba saurayina bane shi wllh, saurayina sunansa Umar amma mun rabu yanxu" Yace "Umar?" Tace "Ehh, shi wannan kawai yayana ne" Wayar hannunta ya amsa da sauri tace "Nace maka nasa ne wayar" Bude screen din yayi don wayar a bude yake, ya dinga kallon hulan pilot dake jikin screen din wayar, karban wayar tayi hannunsa, xuwa lkcn bbu kowa haraban parking din jirgin sai ma'aikatan airport, Yousuf ya daga kai yana kallon Abuturrab dake saukowa daga jirgin yana kallonsu babu ko kiftawa, har sannan pilot uniform ne a jikinsa, Jiddah ta daga kai ganinsa ta kalli Yousuf tace "Shine yayan nawa" Yousuf ya d'an yi murmushi yace "Shine matukin jirgin... i guess right" Juyawa Jiddah tayi da sauri tana kallon Abuturrab, Yousuf ya karasa gunsa ya basa hannu suka gaisa yana murmushi yace "I guess you did the landing..." Abuturrab na kallonsa ya d'an yi murmushin gefen baki kamar wanda aka tilasta ma yace "Yea, i did" Yousuf yace "Nice landing...." Abuturrab yace "It's a pleasure flying you" Yousuf ya masa murmushi sannan ya juya ya bar wajen, yana isa inda Jiddah take yace "Ina jiran kiranki kamar yanda kika yi alkawari ranan" Yana fadin haka ya wuce, Jiddah ta kalli Abuturrab da ya hade girar sama da ta kasa yana kallonta.... A motarsa suke tafiya xuwa hotel din da suka sauka a kano, har sannan babu abinda yace mata, sai dai fuskarsa bbu ko digon annuri, har suka isa hotel din, kulle dakin hotel din yyi after going in together with her, yana kallonta fuskarsa a tamke yace "Waye wannan mutumin da na ganku tare?" Tace "Wai da gaske kai ne kake tukin jirgin in ji sa? Ni dai nace masa ba kai bane ae baxa ka iya ba" fixgota yyi, tayi wani kara xata durkusa ya dagota yace "Tambayar ki nake waye shi??" Kamar xata yi kuka tace "Toh ba q jirgin muke haduwa ba" ganin taki tsayawa cikin tsawa yace "Baxa ki tsaya ba" Kin tashi tayi tace "Toh don Allah ka sakeni" kallonta kawai yake yi, can ya saketa, xamewa tayi ta xauna kasa, yace "Waje daya ku ka xauna da mutumin?" Tace "Aa, kawai da na sauka jirgin shine ya bi ni yana min magana" Shiru yayi yana kallonta ita dai bata yarda ta kallesa ba, can ya juya ya bude kofar dakin ya fita. Bayan la'asar suka bar kano xuwa kaduna a motarsa, Jiddah na kallonsa after the 20 mins silence tace "Meyasa muke ta shiga jirgi bayan ga mota, kyauta ake tafiya a jirgin ne?" Ya mata wani kallo yace "Kyauta? Tsoronki ake xaki shiga jirgi kyauta?" Tace "Toh Iyah ta ta6a ce min kudin jirgi yana da tsada kusan miliyan ne" Ya d'an kalleta yace "Haba??" Ta wara ido tace "Wllh, kasan ta ta6a xuwa makka sau daya, yaranta ne suka biya mata, toh ni na xata masu kudi ne kawai ke hawan jirgi" D'an murmushin da bai shirya ba yyi yace "Ni ba me kudi bane kenan?" Ta d'an xaro ido tana kallonsa tace "Aa bance haka ba, amma wannan motar taka ce?" Bai ce komai ba, a hankali tace "Kayi shiru..." Yace "Aa na Abbana ne" Tace "Toh gidan fa?" Yace "Wani gida?" Tace "Wanda muke ciki?" Yace "Shi ma na Abbana ne" Tace "Kenan shi ne ya biya kudin jirgin da muka shiga?" Yace "Ehh" Tayi shiru tana kallonsa, ta gefen ido ya kalleta, ta sauke idonta, bayan few seconds tace "Abbana ya ta6a ce min watarana xan shiga jirgi, amma Makka yace xanje" Ya kalleta yace "Haba" Ta gyada masa kai, tace "Kuma gashi na shiga amma ban je makkan ba" Yace "Toh idan kina da kudi ki kawo in biya maki Umrah ki je" Ta buda ido tace "Kudi?? A ina xan ga kudi ni ba sana'a nake ba" Yace "Ohk kina son kiyi sana'a ne? Ko awaran xaki siyar a bakin layin gidanmu?" Dariya ta fara yi, ya dinga kallonta don bai ta6a ganin dariyarta ba, tayi me isarta sannan tace "Idan kace inyi sai inyi in dai xa a siya" Da mamaki ya d'an kalleta kafin ya maida dubansa kan titi yace "Xa kiyi kenan idan nace kiyi" Tace "Ehh, sai in yi har da wainar flawa da dankali" Yace "Toh bari mu je a samar maki waje a bakin titin ko?" murmushi ya ga tayi tace "Toh" Ji yayi kamar ya fixgota ya rankwasheta, tace "Toh amma kudin xa su taru har in je makkan kuwa?" Yace "Wannan ke xan tambaya ai, babarku ta tara kudin ya isheta har taje makka?" Shiru tayi tana kallonsa, can tace "Toh ai abinci muke ci da kudin sana'ar, wannan kuma baxan siya abinci da kudin ba tunda akwai abinci a gida koh" Shafa millionaires belt dinsa yyi still wondering if yarinyar nan xata ta6a wayewa, though ya ma yi mamakin yanda har ta fara iya dressing ko don kayan da ya siya mata sunyi correlating da mahadinsu ne, sannan bai ga tana irin kwalliyan nan na masu talla ba, a ja gira a shafa barbada kumatu, a shafa gazal, babu wanda xai kalleta yace she is local or even an illiterate sai ya ji xancen dake fita daga bakinta, mamaki ma yayi yanda ta bude baki take creating conversation da kanta yau, muryarta yaji tana cewa "Idan kudin ya taru da yawa kai ma sai in biya maka tunda ka taimakeni koh?" Ya d'an kalleta da sauri sannan yace "Haba?" Tace "Ehh, ko kuma in biya ma Umma" Murmushin gefen baki yayi yace "Ashe na taimake ki?" Tayi shiru tana kallonsa, sai kuma ta gyada masa kai a hankali, Bai kuma cewa komai ba, kuma bai kalleta ba, jin tayi shiru bayan kusan minti goma sha biyar, breaking the silence yace "Bayan awaran da dankali babu wani sana'ar da xa ki yi?" Ya d'an kalleta da yaji bata amsa masa ba, bacci yaga tana yi, xuwa lkcn sun fara fita outskirt din garin kano, ya kai hannu a hankali ya kwantar mata da kujeran motar, snn ya kara Ac din motar, har suka shigo garin kaduna bayan magrib bacci take, amma ta farka yyi sau biyar a hanya, mai gadi na bude masa gate yayi parking a parking space, ya sauka motar yana stretching kansa, coz he is very tired bayan tukin jirgi ga na mota, jingina yayi da motar ya rungume hannunsa, har ya mance rabonsa da workout, tun sanda burden din Jiddah ya hau kansa, xagawa yyi ya bude side dinta ya bubbuga motar slowly, a hankali ta bude ido ta fara kalle kallen inda suke, yace "Sakko" sauka ta fara yi daga motar ya koma gefe tana fitowa ya kulle motarsa. Bayan sun shiga gidan xata wuce dakinta yace "Ki tabbatar kinyi sallah" Wanka jiddah tayi sannan ta dauro alwala bayan ta idar da sllh ta saka kayan baccinta ta kwanta. Karfe tara ya shigo dakin da abinci, tunda ya kalleta sau daya ya dauke kai, kawai ya ajiye ledan ya fita. Washegari da ya kasance ranan juma'ah Jiddah na idar da sallan asuba ta sauko kasa ta hada shayi ta dumama abincin da ya kawo mata jiya da daddare ta wanke tukunyar da ta bata ta koma dakinta, duk kafin ya shigo gidan daga masallaci, don sai ya gama azkar dinsa yake shigowa gida, bata mance warning din da yayi mata ba, ganin har karfe sha biyu Abuturrab dake xaune parlor bai ga ta sakko ba, lkci lkci kuma ya ke kallon sama, daga karshe ya mike ya haura stairs din sannan ya bude kofar dakinta, bacci ya sameta tana yi, yayi knocking kofar da karfi wanda hakan ya farkar da ita ta mike xaune da sauri, ya wani daure fuska yace "Baki da hankali har yanxu bacci kike?" Tace "Aa nayi wanka na gyara dakin" Ganin hararan da yake mata ta dauke kanta, yace "Ohk kin fi so ki kwanta daki kullum in fita in siyo maki abinci in kawo maki anjima kice ai bani da kudi?" Buda baki tayi tana kallonsa tace "Ni yaushe nace baka da kudi?" Ya rungume hannunsa yace "Jiya a mota" Tace "Aa ni fa kudin jirgi nace baka da shi tunda ya kai miliyan daya, kuma kace min Abbanka ne ya biya ai ko??" Yace "Ehh abincin da kike ci ma ai duk shi yake siyowa in kawo maki ko" Tayi shiru tana kallonsa, can tace "Toh me yasa baka son kayi sana'a, kaga Umar yana fita kasuwa kullum, don kawunsa na da shaguna uku a kasuwan bacci..." Kallonta yake ko kiftawa baya yi, tace "Kai ma xa ka iya ce a neman maka waje a kasuwa tunda Abba na da kudi ae" Ya shafa fine beard dinsa yace "Haka ne kuma, amma ya aka yi kika san bana sana'an komai" Ta sakko da kafafuwanta daga saman gadon tace "Naga to ko da yaushe kana gida, idan baka son ka xauna a gidan kuma sai ka tafi kano, to ko sana'a kake xuwa yi a kanon?" Ya girgixa kai da sauri yace "Can ma kawai xama nake a gida, ai ba a bani sana'an da xan yi ba" Tayi shiru, sai kuma ta kallesa tace "Amma lkcn da kake xuwa hayin rigasa a ina kake samo wannan kudin da kake bani in ba Babarmu?" Yace "Abbana ke bani" Tace "Toh, shkkn" Yace "Yanxu kasuwan xan fara xuwa nima kenan" Tace "Eh ka gaya ma Abbanka ya bude maka shago" Yace "Sai ni dake mu dinga xama a ciki ko?" Kallonsa tayi ta fashe da dariya sosai dimples dinta na lotsawa, ya dinga kallonta, second time da yake ganin dariyarta kenan, tayi me isarta tace "Dama mata na xuwa kasuwa?" Ya rungume hannunsa yana kallon large eyeballs dinta yace "Tunda xa su iya xaman gefen titi su siyar da awara da dankali me xai hana??" *Toh Chamo dai tace banyi addu'ar Allah yayi min katangan rodi with some set of readers ba, duk da dai ra'ayinsu suke 6a6atu a kai nd they are entitled to der opinion, but oh God do not allow me to be seeing der comments so that i can write happily till end without mind spoilage Ameeeeenn* 🫣 to those of u reading my book for free know that u owe me dari biyar kacal ehe... 😚 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Jiddah ta langwabar da kanta tace "Ai ban sani ba, in dai mata na xuwa sai mu dinga tafiya tare" That wasn't were Abuturrab wanted the conversation to end, but because of how cautious he was with time sbda sllhn juma'ah, ya kalleta kawai yace "Kafin in dawo masallaci ki tabbatar kin sake wanka kin shirya cikin atamfa, sannan ki karya..." Sae kuma ya hade rai, Ta sauke idonta kasa tace "Ni na karya da asuba ai" Daga sama har kasa ya kalleta sannan ya juya ya fita ta bi sa da kallo.... Ko da ya dawo juma'ah har ta shirya kamar yanda yace mata, Hijab ya sa ta daura kan atamfar, bayan ta sauko ta tsaya tana kallonsa, sau daya ya kalleta ya dauke kai yace "Fita ki jirani a waje" Ba musu ta nufi kofa ta fita daga parlon, sae a sannan ya tashi ya kashe appliances din gidan ya dau makullin motarsa da hulansa ya fita, the ride was silent har suka iso gidansu, gaba daya he was absentminded, yau da safe ma kiran Aunty ne ya tashe sa, har sannan kuma ya ki daukan kiranta, then is he even suppose to go home now? bai yi parking a kofar gidansu ba in case of necessity, ya juya yana kallon Jiddah yace "Ki jirani" Bai jira tace komai ba ya bude motar ya sauka.... Da murmushi Abuturrab ya amsa gaisuwan mai gadinsu ya shiga cikin gidan, sosai ya ji hankalinsa ya kwanta da kanninsa suka ce Aunty ta fita, Yana kallon Ramlah yace "Ina ta tafi?" Ramlah tace "She left for Abuja this morning" Shiru yyi yana kallonta, can ya nufi parlon Umminsa, ganin bata parlon ya fito, ganin ya nufi kofar fita Ramlah tace "Ummi na bedroom fa" Bai tanka ta ba har ya fita, tare ya dawo cikin gidan da Jiddah, murmushi kawai tayi ma su Ramlah da suka gaisheta, ta bi bayansa xuwa parlon Mahaifiyarsa, kafin yace mata komai ta xauna a kasa, ya karasa cikin bedroom din Ummi da sallama, gaisheta yayi da ladabi, ya shafa kansa yace "Ummi xa ku gaisa da ita a parlor" Ummi tace "Ohkk" Mikewa yayi ya fito parlon, ya xauna kan kujera, ba a dau lkci ba Ummi ta fito, jiddah ta sunkuyar da kanta ta gaisheta, Ummi ta amsa da murmushi fuskarta tace "Ya ku ke?" jiddahh tace "Lafiya lau" Ummi tace "To madallah, sannun ku da xuwa" Ummi dake kallonta kasa kasa ta ga ta canxa mata sosai, haskenta na ainahi ya fito ga wani glowing da take yi, Shi dai Abuturrab danna wayarsa kawai yake, jin Umminsa bata kuma cewa komai ba ya daga kai ya kalleta yace "Ummi wai Aunty ta tafi Abuja?" Ba tare da ta kallesa ba "Ai na xata xaka fi kowa sani tunda kun fi kusa" Ya sunkuyar da kansa yace "Aa bamu yi magana ba" Ummi tace "Ayyo" yace "Yaushe tace xata dawo?" Ummi tace "Baka da lambarta ne?" bai kuma cewa komai ba kuma bai dago ba, Jiddah dai sai kallon Ummi take, Bayan few seconds Abuturrab ya dago yace "An kawo lefen Ramlah ne?" Ummi tace "Bakwa magana da Ahmad din ne?" Yace "Shekaranjiya mun hadu a Abuja da na sauke jirgi a airport din can" Da sauri Jiddah ta kallesa, suka hada ido ya hade girar sama da ta kasa yana kallonta, turo baki tayi, Ummi dai tv kawai take kallo, Ya dauke kai yace "Amma yace min xai shigo kadunan yau, kilan xanje daukosa a tashan jirgi anjima" Ummi tace "Allah ya kawosa lafiya" yace "Ameen" Ummi tace "Idan kaga xaka iya sai ka bar ta nan har bayan bikin, tunda ranan talata xa su fara shagalgulansu" Abuturrab ya d'an yi shiru, can ya daga kai ya kalli Ummi yaga kallonsa take, suna hada ido tace "Ranan bikin sae ka kawota" Da sauri yace "Aa Ummi gobe xan kawota tunda bata xo da kaya ba" Ummi tace "Aa a bari ranan bikin dai" Yace "Uhn xan kawota goben in sha Allah" Ummi tace "Baxa ka siya mata ankon bikin ba?" Ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Nawa ne?" Ummi tace "Kala uku ne, daya na family, sai general one da xa a saka ranan yini, sai kuma na dinner, although naji yan matan sun fidda wani da xa su saka ranan talata" Yace "Nawa ne duka" Ummi ta hada masa kudin gaba daya tace "Gaba daya 40k ne" Yace "A dinke xa a siyo kayan?" Ummi tace "Ehh, da yake kayan dama a kyauta aka samosu daga kasuwa, iyakar kudin dinkin ne dubu arba'in" Abuturrab ya bude ido ya fara dariya yace "Ummi tambaya fa kawai nayi" A takaice tace "Nima amsa na baka" Ya shafa kansa yana murmushi bai ce komai ba" Ummi na kallon Jiddah tace "Su Ramlah na can daki kije ki samesu tunda naga baki son magana" Tayi murmushin karfin hali ta mike ta nufi kofa, Abuturrab ya mike yace "Ai bata san dakin ba, i will back Ummi" Da ido kawai Ummi ta bisa da kallon mamaki har suka fita. Dakinsu Ramlah ya kai ta, Ramlah na xaune da Siyama sai wata kawarta da Aisha step sis dinta, tana ganin Jiddah ta mike tana welcoming dinta da fara'a, bai amsa gaisuwan yan dakin ba banda na kawar Ramlah da bai sani ba, sannan ya juya ya fita ya koma bangaren Umminsa.... Karfe hudu saura yace da Ummi xai je dauko Ahmad a train station, Ummi tace "Toh Allah ya tsare" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga parlon, dakin su Ramlah ya nufa, Jiddah na xaune tana ma Siyama tsifa, su Ramlah suna ta labari a dakin ganinsa duk suka yi shiru, yana kallon Siyama yace "Ke tsifan sai an maki??" Tayi dariya tace "Ita tace ta xata min Yaya" Yana kallon Jiddah yace "Kinci abincin ko baki ci ba?" Ramlah tace "Yanxu muka gama cin abincin fa yaya" Wani kallo ya jefa mata yace "Nayi da ke?" Bata kuma cewa komai ba, yana kallon Jiddah fuska daure yace "Tambayar ki nake" Tace "Mun ci" juyawa yayi ya fita, Sai da Ramlah ta tabbatar ya tafi don har sai da taje ta d'an bude kofar taga babu kowa wajen sannan ta dawo tana kallon jiddah da murmushi tace "Yaya yana ji dake kamar yanda yake ji da profession dinsa..." Jiddah dai bata ce komai ba ta ci gaba da tsifar da take.... Bayan kusan awa daya da tafiyar Abuturrab Aunty ta dawo gidan, alamar dai ita ma train din ta biyo daga Abuja ta dawo, tun da ta kyallara ido taga Jiddah taji kamar taga mugun abu a gidan, ko gaisuwar Jiddah bata amsa ba, bata sake shiga damuwa ba sai ganin wani haske da kyan da Jiddah tayi alamar kwanciyar hankali, ita Abuturrab xai raina ma wayo?? Ta kusa minti ashirin xaune gefen gado a dakinta, ta saka wannan ta kunce wnn, ita Abuturrab ke son kunyatawa gun aminiyarta? Takanas ta shirya yau ta tafi Abuja ba mahaifiyar Aneesah hakuri bayan sun sanar mata abinda Abuturrab din yyi ma Aneesah a airport kamar yanda Aneesan ta gaya ma uwarta... Wani murmushi Aunty tayi tana gyada kai. Jiddah na ta xaune parlorn Ummi ita kadai don su Ramlah da yan matan gidan sun fita xuwa gun tailor, Ummi kuma ta hanata bin su tace mijinta bai sani ba, Jiddah na ta juya furucin Ummi a kanta, wai mijinta, ai ba mijinta bane Aliyu, tunanin hakan kawai sai taji jikinta yayi sanyi sosai, Ummi ce ta fito daga dakintaz ganinta xaune ita kadai tace "Ki shiga kitchen kiga ko aunty na ciki ki tambayeta abinda xa ki kama mata Jiddah" Jiddah ta kalli Ummi a hankali tace "Toh" Mikewa tayi ta fita bangaren Ummi, tayi hanyar kitchen din, jikin kofa ta tsaya tana lekan kitchen din don ita har taji tana tsoron matar nan da ake ce ma Aunty, ganin Auntyn a ciki, cikin sanyin murya tace "Aunty me xan kama maki wai?" Juyawa Aunty dake yankan cabbage tayi tana mata wani irin kallo tace "Me xa ki kama min?" Jiddah ta gyada mata kai gabanta na faduwa, Aunty ta ajiye wukan hannunta ta kunduma mata xagi tace "Ke a wa xaki kama min aiki?? Yanda kika samu wajen xaman yin iskanci gidan Aliyu kin xata nan ma haka ne, toh bari kiji... Wllh ki saka a ranki cewar xamanki ya xo karshe a gidan Aliyu, sai dai ya dinga bin ki can kauyen naku yana iskancin da yake dake, yau xai san ni mahaukaciya ce wllh" Jiddah dai kallonta kawai take a ranta tana kara nanata kalmar da ta jefa mata wai iskanci, tana nufin iskanci suke yi da Aliyun kenan? Muryar Aunty ya sake dawowa da ita, ciki tsawa tace "Baxa ki fita ki bar min kitchen ba mayya...." Cikin sanyin murya Jiddah tace "Ni ba iskanci muke yi ba wllh...." Aunty ta fixgi roban cabbage din gaba daya ta watsa mata ranta bace ta kunduma mata xagi tace "Kina shige da karuwar xaki ce min ba iskanci ku ke ba, dama mace da namiji na xama gida daya tare babu aure? Fita ki ban waje kada in fasa maki ido algunguma" Jiddah da ta rufe idonta da hannunta taji kuka ya taho mata ta juya da sauri ta bar kitchen din jikinta duk cabbage da suka makale, dai dai nan Abuturrab ya shigo parlon, durkusawa tayi nan parlor ta fara kuka kamar an aikota, kallon hanyar kitchen din yayi yaji muryar Aunty tana cewa "Sai yanxu na ke sake yarda cewar da gangan yayi komai da ya faru, har sabida ke xai walakanta min Aneesah, to in dai nice wllh xai sha mamaki, ba mu xai kawo ma gayyar tsiya family ba..." Karasawa yayi gun Jiddah ya dagota, kuka kawai take ya kakkabe jikinta ya kama hannunta suka fita parlon, nan balcony ta saka takalminta sannan suka fita compound xuwa gun motarsa, har suka bar layin kuka take kamar xata shide, ya hade rai yace "Ya isheki haka nan, me yasa baki tsaya kitchen din kin mata kukan sosai ba?" Bata ce komai ba ta hade kanta da gwiwa tana shessheka, har suka isa gida hawaye na xuba idonta, bayan yyi parking yana kallonta yace "Baki ji ki daina kukan ba?" Ta dago kai cikin rawan murya tace "Ce min tayi wai muna yin iskanci fa" Ya dinga kallonta kafin yace "Da wa ku ke yin iskancin" Cikin kuka tace "Wai kai" Dauke kai yayi da farko, can ya juyo yace "Ai ban san wani irin iskanci take nufi ba" Tana hawaye tace "Tace iskanci muke yi da kai a gida" Ya buda ido sosai yace "Toh fa, ni iskancin da na sani shine ace mutum bashi da kirki ko baya jin maganan mutane..." Da sauri Jiddah tace "Ba shi bane" Yana kallonta yace "Toh wanne ne?" Cikin rawar murya tace "Kilan ta xata kana ta6a ni" kallonta ya dinga yi, can ya kai hannunsa ya kamo nata yana caressing dinsa gently yace "Haka take tunani?" Da sauri Jiddah ta janye hannunta ta saida kukan tana kallonsa, ya daga kafada yace "Don an kama hannun mutum shine iskanci?" Ta girgixa kai tace "Tayi tunanin muna kwana a daki daya" Yace "A kano ba a daki daya muka kwana ba? Sai ace wannan iskanci ne" wasu hawayen suka sauko mata tace "Aa ba haka ba" Yace "Toh ya ne?" Tana goge idonta tace "Tana tunanin muna kwana waje daya" Yace "Toh me ake yi idan an kwana waje daya da ake kiransa da iskanci" Kin cewa komai tayi, ya bude motar ya sauka, ya nufi cikin gidan, bude motar tayi ita ma ta bi bayansa tana goge idonta, Tun da ta shiga dakinta bata fito ba har bayan isha, ita iskancin da Aunty tace take yi ne ya tsaya mata har da ce mata karuwa, wanka kawai tayi tasa rigar baccinta ta shige cikin duvet da ta tuna sai taji hawaye ya taho mata. Karfe tara ya bude kofar dakinta, duk da tana ji bata motsa ba, ya isa inda take ya bude bargon, suka hada ido hawaye ya gani idonta, yace "Ohk kukan kike yi har yanxu kenan" ta gyada masa kai wasu hawayen na taruwa idonta, yace "Saboda ance kina iskanci kike kuka har yanxu" ta mike xaune ta hade kanta da gwiwa tace "Toh ni ae ban ta6a iskanci da kowa ba" yana kallonta yace "Toh ae gwara kawai kiyi ki san kinyi ko?" ta dago kanta da sauri tana kallonsa, ya rungume hannunsa shi ma yana kallonta, tace "Inyi iskanci fa kace" yace "Ehh, ko hakan xai sa abun ya daina damunki, kinga kinsan kinyi kenan ko an fada baxai maki ciwo ba" Ta wani ja gefe daya ta hade rai tace "Allah ya kiyaye ni ba yar iska bace" Dariya ta basa, amma bai yi ba, yace "Amma ko jiya kin kama hannuna ai" da sauri ta juyo a tsorace tace "Ni??" Yace "Ehh" ta hade rai ta hararesa tace "Ni ban ta6a haka ba wllh" karasawa yayi daya side din da take yace "Ni kike harara haka?" Saukowa tayi da sauri ganin ynda ya hade rai tace "Ni ban harareka ba wllh" Ya fixgo hannunta tana ganin haka ta rufe fuskarta a jikinsa tace "Don Allah kayi hakuri ni ban harare ka ba" daga sama har kasa yake kallonta, ya d'an rufe ido sae kuma ya rungumeta tightly to himself yace "Yanxu me ake kiran wannan?" Kwace kanta take son yi amma ta kasa yana jin ynda xuciyarta ke bugawa kamar yanda nasa ma ke bugawa, lkci daya kuma ya saketa, ta juya da sauri ta bar wajen, a mugun tsorace ta juyo tana kallonsa, ba tare da ya kalleta ba yace "Kinga maganar Aunty ya fito, don haka idan tace kina iskanci kada ki sake damun kanki tunda gashi har rungumeni kika yi ynxu, ko bayan wannan akwai wani abu da ake kira iskanci?" Juya masa baya tayi xuciyarta na bugawa sosai, daga sama har kasa ya dinga kallonta, riga ne da wando red color na bacci a jikinta rigar ce kadai barrier din skin dinta, dauke idonsa yyi ya nufi kofa ba tare da ya kalleta ba yace "Ki sakko kasa ki dau abincin ki, kuma kar ki yrda in dawo baki sakko ba" daga haka ya fita, ta bi sa da kallo har sannan xuciyarta na bugawa, bayan kusa minti goma sbda tsoron kada ya dawo kamar yanda yace, ta dau Hijab dinta a sanyaye ta saka har kasa sannan ta sauka, kanta a kasa ta shigo parlon, ta durkusa jikin kujera taki kallonsa a hankali tace "Ni ba yunwa nake ji ba, naci abinci a can gidan" Yace "Koh?" Bata ce komai ba, kuma bata dago kanta ba, ganin ya mike ita ma ta mike da sauri tana kallonsa, da alamar ta tsorata da shi, dariya ta basa amma ya fuske yace "Ohk, da ni mijinki ne haka xaki dinga yi idan na ta6a ki??" Ta kasa ce masa komai, yace "Ki bani amsa" Ba tare da ta kallesa ba tace "Toh ai kai ba mijina bane" Kallonta kawai yake yi, can yace "Toh amma mijin na ki baxa ki dinga yi masa haka ba ko" A takaice tace "Nima ban sani ba" yace "Dauki abincin ki" tace "Na koshi" yace "To tafi" juyawa tayi ta wuce sama, ya bi ta da kallo, xaunawa yyi ya jinginar da kansa jikin kujera, daga karshe ya dau wayarsa ya kashe wutan parlon ya wuce sama xuwa bangarensa ya kwanta, Aneesah ya shiga kira, sai da ya kusa katsewa ta daga amma bata ce komai ba, yyi lumshe ido yyi kasa da murya yace "I know i did what is uncalled for, but... I hope u aren't among d set of pple that believe ban saketa ba ko?" Tace "How will i believe you Aliyu bayan abinda ka min a kanta jiya?" Ya kwantar da murya yace "What if na auroki kika shigo gidan kika gani ma idonki cewar ba matata bace?" Tace "Then i will believe u 100%" Yace "Ranan juma'ah daurin auren Ahmad, kafin uncles dinmu su koma xa a kawo gaisuwa da kudin saka ranan gidanku ranan lahadi in sha Allah" Kamar xata yi kuka tace "Are you for real Aliyu?" Yace "Sure" Farin cikin da Aneesah tayi a lkcn baya misaltuwa, lkci daya duk ta mance abinda Aliyu yayi mata jiya, amidst d joy yace "I am missing you seriously, vid call?" Tace "Sure, amma kar ka wani kashe wuta" yace "I have to" bai jira cewarta ba ya katse wayar ya kashe switch din dake kusa da gado sannan ya shiga kiranta vid call.... Washegari Abuturrab na dawowa masallaci ko azkar bai tsaya yayi ba ya dawo gida a stairs suka kusa cin karo da Jiddah xata sauka kitchen, da sauri ta juya masa baya don bata sa hijab ba, bata yi xaton shigowarsa a lkcn ba, ta koma sama da sauri ta shiga dakinta, bangarensa ya nufa ya shiga daki ya kashe wuta ya kwanta. Kiran Ummi ne ya tashesa wajen karfe takwas da rabi, ya jawo wayar a hankali ya daga coz she's been calling him since yesterday har ma da Aunty, ya kai kunne hade da sallama, Ummi tace "Don walakanci Jiya ka dawo ka tafi da Jiddah babu sallama??" Ya mike xaune da sauri yace "Ummi yau xan kawota dama, bak'i nayi a gida..." ummi tace "Good!!!Abbanka na nemanka, kuma ka taho tare da Jiddar, ba jiran ka xai yi ba, karfe goma xai fita yace" Daga haka ta katse wayar, sosai ya ji gabansa ya fadi, Abba calling him for what? Kallon agogo ya sake yi sannan ya ajiye wayar ya lumshe idonsa yana jin xuciyarsa na bugawa, bayan minti goma ya mike ya shiga bathroom. Tara da minti goma ya fito daga bangarensa cikin kananun kaya, ya tsaya bakin kofar jiddah for some seconds kafin ya bude kofar a hankali, gyaran daki ya sameta tana yi, ta sunkuyar da kai, ganin ta shirya yace "Dauko hijab din ki" Daga haka ya juya ya fita, karasa gyaran dakin tayi sannan ta sa hijab din ta fito. Throughout the ride hankalinsa baya jikinsa, sai da yaga sun kusa gidan ya kalleta rasa abinda xae ce mata yyi har suka shiga gidan, parlon Abba ya nufa direct tana biye da shi a baya, yana sallama aka yi masa izinin shigowa, shi ya fara shiga sannan ta shiga, Aunty na xaune parlon tare da Ummi da Umma, kamar dai xuwansu ake jira, ya ji gabansa ya fadi sosai, xaunawa yyi kasa, jiddah ta xauna side dinsa a hankali, ita ta fara gaishesu cikin sanyin murya sannan shi ma ya gaishesu, Abba gaisuwanta kawai ya amsa, yana kallon Abuturrab babu yabo babu fallasa yace "For how long have u divorced her Aliyu??" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Abuturrab ya buda ido sosai yana kallon Abbansa gabansa na faduwa yace "Divorce kuma Abba?? Why will i do so bayan kayi instructing dina kar inyi haka? Ni ban saketa ba Abba ga ta ka tambayeta, idan na saketa ae baxa mu xauna tare ba.. " Ba Aunty da ta bude baki tana kallonsa ba, har Jiddah kallonsa take da mamaki, Ummi dai wani direction din daban take kallo, Umma kam duk jikinta a sanyaye yake jin batun nan da ya tasheta da sassafe, Abba kansa ya kasa cewa komai, Aunty ta saki salati tace "Yaushe ka fara karya Abuturrab? Yaushe ka dawo makaryaci? Bakina da naka kace min ka saki yarinyar nan tun ranan da ku ka tare shine xaka karyata ni yanxu a nan?" Ya girgixa kai a hankali yace "Ban karyata ki ba Aunty, kawai na gaya maki haka ne saboda hankalinki ya kwanta tunda naga baki son auren, amma ni ban saketa ba, bana son abinda xai sa ki dinga damun kanki shi yasa na fada maki haka" Bude baki tayi tana kallonsa, yayi kasa da murya yace "Abba ga ta nan ku tambayeta ni ban saketa ba, I'm saying nothing but the truth" Jiddah ta sunkuyar da kanta daga kallon da take masa duk jikinta yayi sanyi, Abba kam ya ma rasa abun cewa, Can Ummi na kallon Jiddah tace "Jiddah" dago kai Jiddah tayi ta kalleta, Ummi tace "Ki fada min gaskiya Jiddah, Aliyu mijinki ne a yanxu ko ba mijin ki bane?" Gabanta ya dinga faduwa taji hawaye ya kawo idonta, Abuturrab ya gyara xamansa shi ma gabansa na faduwa sai dai bai kalleta ba, a hankali tace "Mijina ne Ummi" Aunty taji kamar ta rusa ihu a wajen lkci daya idonta yayi jajir, Abuturrab ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciyar relieve, Abba yace "Shkkn, Allah ya rufa asiri, u can leave now Aliyu" Abuturrab ya mike ba tare da ya kallesu ba yayi masu sallama, ita ma ta tashi ta sallamesu sannan ta bi bayansa tana goge hawayen idonta, Umma ta bi su da kallo xuciyarta na kokwanton amsan da Jiddah ta ba yar uwarta, this isn't joking matter, she needs to investigate deep into this issue... Aunty ma ta bi su da wani kallo sai kawai ta saki kuka kamar warce aka sanar ma sakon mutuwa, ita Abuturrab xai yaudara, ita xai karyata, ita xai watsa ma kasa a ido, ita xai kunyata gaban kowa?? Ko minti daya Abuturrab bai kara a a gidan nasu ba ya wuce da Jiddah, bai ce mata komai ba ita ma haka har suka iso gida bayan ya siyo masu abinci a hanya, parking yyi a compound dinsa, sai da ya sauka sannan ita ma ta sauka motar, ya mika mata ledan abincinta yana kallonta, kin amsa tayi hakan yasa yyi wucewarsa ciki da ledan ya bar ta tsaye a wajen, xaunawa yyi kan kujera a parlor ya jinginar da kansa da kujeran ya sauke ajiyar xuciya feeling relieved, sai bayan kusan minti sha biyar ta shigo parlon, xata wuce sama yace "Xo nan" Ta ki tsayawa har ta wuce, ya bude baki yana bin ta da kallo. Through out ranan jiddah na daki shi kuma yana downstairs, bai bi ta kanta ba har after isha, bayan ya dawo mosque ya dai ga alamar tayi making tea a kitchen, yana haurawa sama ya tsaya kofar dakinta sai kuma ya bude slowly, xaune ya ganta idonta yyi ja, ya kulle kofar dakin yana kallonta, yace "An maki wani abu ne kike ma mutane kuka tun safe?" Ta ki kallonsa, a d'an tsawace yace "Ba magana nake maki ba?" Ta juya masa baya, rungume hannu yyi yana kallonta, can yace "Kuka kike saboda kina tunanin kinyi musu karya?" Ta juyo tana kallonsa cikin rawan murya tace "Ehh mana, me yasa xa ka masu karya??" Yace "Ohh da na masu sai nace ke ma kiyi masu??" Kallonsa ta dinga yi ko kiftawa babu, ya karasa ya tsaya gabanta yana kallonta da kyau yace "Ni ai ban aike ki kiyi masu karya ba... sannan akwai wani abu na musamman da ke sa mutane su yarda cewar mata da mijinta ne ke rayuwa a cikin gida? akwai wani abun da xanyi da xai tabbatar da cewar ni da ke mata da miji ne? Ko bana ciyar da ke yanda miji ke ciyar da matarsa ne? Ban baki sutura ba? ban baki wajen kwana ba? ban baki kariya ba? Ina ce duk wannan shine abinda miji ke ma matarsa? Ko akwai wani abu daban da ban sani ba ki sanar da ni nima in maki don xaman namu yayi kama da na mata da miji a daina xargin mu..." ta dauke kanta tace "Idan mun yaudari mutane ai Allah shi yasan gaskiya, kuma ai kai ma kasan ni ba matarka bace nima kuma nasan kai ba mijina bane" Kallonta kawai yake yace "Toh meye shaidan hakan?" Tace "Ai kai ma kasani, meyasa baxa ka fada masu gaskiya ba, sannan ni ka bani takardan in ajiye wajena tunda baka aikeni inyi karya ba" durkusawa yyi yana kallonta yace "Haba?" Tace "Ehh" yace "Toh ko dai in fara maki abinda masu aure ke yi, kilan hakan xai sa ki fara rage tunanin ai ni ba mijin ki bane, infact mancewa ma xaki yi cewar babu aure tsakaninmu, takarda kuma da kika ce... Mu je in baki ki ajiye wajen ki" mikewa yayi still yana kallonta, ta k'i tashi, ya hade rai yace "Mu je ki amsa nace" mikewa tayi a hankali, ya nufi kofa ta bi bayansa xuwa bangarensa, suna isa ta tsaya bakin kofar babban parlon, ganin bata shigo ba yace "A bakin kofa xan baki takardan?" Shigowa parlon tayi taga ya nufi bedroom dinsa yana isa ya tsaya bakin kofa ganin bata karaso ba yace "Shigowa xa kiyi ai malama" daga haka ya shiga cikin dakin, a hankali ta bi bayansa tana shiga ya kulle kofar, ta makale jikin bango tana kallonsa, sanyi sosai ne a dakin sbda Ac dake aiki, ya nufi gaban mirrow ya dau diary dinsa ya bude sai ga takarda well folded ya ciro a ciki yana kallonta ya mika mata yace "Gashi" Ta sauke kanta kasa kamar baxata je ba sai kuma ta karasa ta sa hannu xata amshi takardan ya fixgota, kara tayi a tsorace ta fara kokarin kwace kanta, yace "Saboda ina tsoronki xan baki? And.. ina ruwanki da rashin auren dake tsakaninmu, ci kika rasa ko sha??" Gaba daya a tsorace take, kamar xata yi kuka tace "Kayi hakuri don Allah...." Yace "Baxan yi ba" a hankali ta daga kai ta kallesa, saketa yyi ya tafi gaban madubi ya ajiye takardan sannan yace "Idan kin isa ki dauka ki fita" Yana fadin haka ya nufi kofa ya bude ya fita ta bi sa da kallo har ya kulle kofar, a hankali ta isa gaban madubin ta dau takardan ta warware tana dubawa, takardan ne kuwa, in accord to the content of d paper, he is no longer her husband, duba diary din tayi taga ba a ciki ya falli takardan da yayi rubutun ba, wajen mirror din ta dinga dubawa nan taga takardan da ya cira a ciki, ita ma ta cira sannan ta mayar da sauri ta ajiye, linkewa tayi yanda ya linke na rubutun ta ajiye gaban madubin sannnan ta dau wanda rubutu ke jiki tana tunanin inda xata boye, kana ganinta kasan a tsorace take, hularta ta saka hannu ciki taji gashinta is very oily, ta sake ciran wani sabon takardan ta nannade na rubutun a ciki sannan ta tusa a cikin hulan ta koma inda take tsaye ta tsaya, bayan kusan minti goma sai ga shi ya shigo, sunkuyar da kanta tayi cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri baxan sake cewa ka bani ba kuma" Bai ko kalleta ba, ya ajiye sauran bottle water din hannunsa, sannan yace "Aa ki dauka dai, gashi can gaban madubin" Ta girgixa masa kai kawai, gun takardan ya nufa gabanta ya dinga faduwa tana kallonsa ko kiftawa babu, ya dauka, bata jira taga me xai yi ba har ta juya xata fita da gudu taji yace "Gashi ki tafi da shi" Juyowa tayi tana xare ido taga yana mika mata takardan, kallonta kawai yake, yace "Amsa nace" Ta karasa a hankali ta sa hannu xata amsa ya murda kunnenta yace "Tahowa kika yi xa ki amsa kenan" Bata fuska tayi bata dai ce komai ba, lkci daya taga yana bude takardan da gudu ta nufi kofa ta fice daga dakin ya bi ta da kallo ganin babu komai a jikin takardan, mamaki ne ya cikasa ya sake juya bayan takardan that is plain, Bude baki yayi with so much surprise, bai san lkcn da yayi murmushi ba ya rungume hannunsa, so tana da irin wannan wayon ashe, bai bi ta ba sabida yasan xa ma ta dawo ne, ya tafi gefen gado ya xauna, Jiddah ta jingina da kofar parlonsa ta xame kasa tana yarfe hannu, gaba daya a tsorace take, sai jiran fitowarsa take anytime amma har sannan bai fito ba, bin babban parlon ta dinga yi da kallo kamar xata hango makullin kofar, har bayan minti talatin bata gansa ya fito ba, gajiya tayi da xama a bakin kofar, ta mike a hankali tana leka kofar dakin nasa, can dai ta karasa bakin kofar ta leka ciki don kofar ba a kulle yake gaba daya ba, kwance ta gansa waya kare kunnensa, ta juya da sauri ta koma inda take xaune kamar xata yi kuka, har sha biyu saura Jiddah na xaune gefen kofar, bacci ne ya fara damunta, mikewa tayi ta tafi kan kujera ta kwanta nan da nan bacci ya dauketa, can cikin dare taji ana lalubata, ta mike a tsorace ganin duhu a parlon tace "Wayyo Allah na" Muryarsa taji yace "Ina takardan yake" Jikinta ma rawa tace "Yana cikin hulana" Xata cire hulan ya rigata cirewa ya ga takardan a kanta ya dauka sannan ya saketa ya koma dakinsa ya kulle kofar, har lkcn gabanta faduwa yake ta mike xaune tana bin parlon da kallo don ko alamar haske babu, a hankali ta mike tana neman hanya har ta isa kofa ta murda taji a kulle har sannan, jingina tayi da kofar kamar xata yi kuka, can ta juya ta koma saman kujeran ta kwanta, nan da nan bacci ya sake dauketa, kiran sallan asuba ne ya farkar da Jiddah, ta tattaba lallausan abinda taji a jikinta, kofar daki aka bude da sauri ta rufe idonta don hasken dakin ya hasko parlon, tana ji ya bude kofar parlon ya fita, lkci daya kamshin turarensa ya gauraye parlon, sai bayan kusan minti biyar ta cire duvet din jikinta ta mike a hankali jin xa a tada sallah, ajiye duvet din tayi kan kujeran ta nufi kofa ta bude ta fita xuwa dakinta. Karfe takwas saura Jiddah ta farka daga baccin da ta koma bayan tayi sallan asuba, mikewa tayi ta shiga bandaki sai da tayi wanka ta wanke baki sannan ta wanke bandakin ta fito, tana gama shiryawa ta hau gyaran dakin, bude kofa aka yi ta juya da sauri, calmly yace "Ki sameni kasa" daga haka ya rufe kofar, ta gama abinda take sannan ta sauka kasa, yana xaune parlor yana kallo, agogon wrist dinsa ya kalla yace "Na baki minti talatin ki je ki dafa abinda xa ki ci...." tsayawa tayi tana kallonsa, ganin bata motsa ba ya daga kai ya kalleta, da sauri ta juya ta wuce kitchen din ya bi ta da kallo, indomie ta dafa ta ci a kitchen din ta wanke plate sannan ta fito, ya kalleta ya nuna mata karamin travelling bag dinsa da ya sauko da shi parlor yace "Ki je ki hada kayanki kala biyu da duk abinda xa ki bukata, kar ki bata min lkci, ki saka Jilbab idan xa ki sakko" A hankali tace "Ina za mu je kuma, amma ba jirgi xa mu hau ba ko??" ganin irin kallon da yake mata ta dau travelling bag din ta juya ta wuce sama, kayan nata ta hada sannan ta sauko kasa a sanyaye, Hijab ne har kasa jikinta, ya mike ya nufi kofa ta bi bayansa rike da jakar. Parking Abuturrab yayi kofar gidansu Ahmad, Jiddah ta juya ta kallesa ganin inda suka xo, wani farin ciki taji a ranta, bude motar yayi ya sauka, ita ma ta sauka ta bude back seat ta dau jakar kayanta, ai da ta san nan xa su xo da ta debi kaya da yawa, ganin ya nufi gate din gidan ta bi bayansa da sauri, gaba daya farin cikinta ya kasa boyuwa, sai kallon kofar Maman Abdallah take har suka shiga main parlor din gidan, Umma ta fito daga dakinta ganinsu tace "Aa daga ina haka kuma" Yayi kasa da kai yace "Daga gida Umma" nan ya gaisheta, ta amsa tana kallon Jiddah tace "Sannu da xuwa Jiddah..." Gaisheta Jiddah ma tayi tana mayar mata da murmushin, Umma ta amsa tana tambayarta ya gida, Jiddah tace "Lafiya lau" Umma tace "To kun ma karya kuwa wannan sammako haka?" Abuturrab yace "Eh mun karya, i brought her ahead of the wedding...." Umma da taji dadi har ranta don wnn shine right time da xata fahimci gaskiyan abinda Aunty ke fada tace "To maa sha Allah, that's very good" Yace "Kudin ankon kuma wa xa a tura ma?" Umma tace "Anko kuma?" Yace "Ummi ce tayi maganan ankon ran Friday" Umma tace "Kyale Ummi, ae ta riga ta mata, har dinki an bada" Yace "Toh Allah ya saka" mikewa yayi yace "Sai anjima Umma, xan wuce kano da yamma in sha Allah, ranan alhamis xan dawo" Umma tace "Toh Allah ya tsare, shi ma Ahmad din ranan laraba xai shigo..." Abuturrab yace "Ehh mun yi waya da safe, haka yace min" Ya d'an kalli Jiddah sannan ya nufi kofa yana ma Umma sallama, Umma tace "Toh baxa kiyi masa rakiya ba Jiddah?" D'an murmushi kawai tayi ta sunkuyar da kanta, Umma tace "Tashi ki je" a hankali ta mike ta nufi kofa ta fita, cike da kasaita yake tafiyar, ta bi sa da kallo, bin bayansa tayi har suka fita gidan, ya bude driver seat xai shiga sai kuma ya tsaya yana kallonta don makalewa tayi jikin gate, suna hada ido ta sauke nata idon, yace "Kina son wani abun ne" Ta d'an turo baki tace "Umma ce tace in raka ka" ya shafa kansa yace "Idan Umma tace ki shirya ku je can gidan kice mata baki jin dadi baxa ki iya xuwa ba" Tana kallonsa tace "Toh ka tayani gaya mata mana" ya daga kafada yace "Toh ki tafi ni ba ruwana" Daga haka ya bude motarsa ya shiga ya tada yayi reverse, a hankali ta juya ta koma cikin gidan, daren ranan Maman Abdallah na parlon Umma tare da mai aikin gidan suna ta hira, duk sbda Jiddah ta shigo kuma, sai kusan karfe goma maman Abdallah ta bar parlon, duk yan matan gidan na can gidansu Abuturrab, mikewa Jiddah tayi a hankali tayi ma mai aikin sai da safe ta wuce dakin da Umma ta sa ta ajiye jakarta, tuni Umma ta tafi ta kwanta tana tunanin where to start from coz ko kadan bata yarda da Jiddah da Abuturrab ba, Jiddah tayi wanka ta sauya kayan jikinta xuwa na bacci sannan ta kwanta. Washegari monday Jiddah ta taya Huraira mai aiki girkin breakfast, sosai ta sake a gidan ba kamar gidan su Abuturrab ba duk da Seeyama bata nan, Karfe sha daya na safe ta raka Umma kasuwa da driver, basu dawo gida ba sai kusan azahar, Jiddah na sallah ta kwanta don sun ci abinci a restaurant, da yammacin ranan Seeyama da Aisha da Safiyya suka xo gidan amsar ma Aunty sako wajen Umma, Seeyama tayi murnan ganin Jiddah a gidan, Umma tace "Sai ki shirya ki bi su Jiddah, idan na je anjima da daddare sai mu dawo tare" Shiru Jiddah tayi ta kasa ce mata komai, Seeyama tace "Ki tashi sister Jiddah Aunty na jiranmu" Mikewa Jiddah tayi a ssnyaye ta saka Hijab dinta, Driver Umma ta sa ya mayar da su can gidan saboda Jiddah, tun da suka sauka motar gaban jiddah ke faduwa ta dai bi bayan Seeyama rike da handbag dinta har suka shiga parlor, dai daikun baki ne da suka xo biki a parlon, Jiddah ta sunkuyar da kanta ta nufi bangaren Ummi, tana shiga parlon taga mata biyu a xaune, Xaunawa kasa tayi ta gaishesu, duk suka amsa, ba a dau lkci ba Ummi ta fito daga daki, ganinta tace "Daga ina haka, ina Aliyun?" Jiddah ta gaisheta sannan tace "Tare muka xo da su Seeyama" Ummi tace "Ohk toh ki shiga can ciki" mikewa Jiddah tayi ta wuce bedroom din Ummi, Hajiya Murja kawar Ummi tace "Kaddai ita ce matar Aliyun?" Ba tare da Ummi ta kalleta ba tace "Ehh ita ce" Hajiya Salaha tace "Allah sarki, ashe yarinya ce ma, toh Allah ya basu xaman lafiya, ga ta dai kamar ba sa wa ba hanawa" Ummi ta d'an yi murmushi kawai, Seeyama ce ta shigo parlon tace "Ummi Aunty Jiddah ta shigo nan" Ummi tace "Tana ciki" Seeyama ta shiga sai ga ta sun fito tare da Jiddah suka fita parlon, sosai gabanta ke faduwa tana tsoron kar ta hadu da Aunty har suka shiga dakinsu Ramlah, Ramlah na ganin Jiddah ta washe baki tace "Aunty Jiddah sannu da xuwa" Jiddah ta xauna tana murmushi tace "Ya gida" Ramlah tace "Lafiya lau, yaya fa?" Jiddah tace "Ya tafi kano" Seeyama tace "Shi sa ya kai ki gidan Umma?" Kai kawai Jiddah ta gyada mata. Suna nan xaune har aka kira magrib, bude kofar dakin aka yi Aunty ta leko tana cewa "Wai baxa ku fito kuje ku yi wanke wanken can ba dake bakin pampo gashi har anyi magariba, ko waye xai maku? Ai sai ku hakura xuwa gobe ku sakankance tunda nasan yan kauye masu wanke wanken xa su iso" Jiddah dake kan darduma ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa, tsit Aunty tayi ganin Jiddah kan darduma, can tace "Ko da yake tun safe ai ku ke ta aiki, ke ya kike da suna??" Jiddah ta kalleta, Aunty tace "Ehh da ke nake kike kallona haka, tashi ki fita ga wanke wanke can bakin pampo kije ki wanke" Mikewa tayi da sauri, Seeyama ta mike tace "Ta barshi kawai xa mu yi aunty" Aunty ta jefa mata wani kallo tace "Toh ita xa ta yi, ku kuma xan aikeku yanxu tare da driver xa ku je min siyayya a supermarket" Jiddah ta nufi kofa ta bi gefen Aunty da ta bi ta da wani kallon tsana ta fita, kitchen Jiddah ta nufa ganin kofar kitchen din a bude ta fita taga uban kayan wanke wanke a bakin pampo ga omo da soso, ruwa ta tara ta fara wanke wanken, ba a dau lkci ba sai ga Aunty ta shigo kitchen din ta dinga fitar da plates wankanku tana ajiye su kan marasu wanki, ita dai Jiddah bata ce komai ba, har tukwanen sai da ta fitar da su sannan ta dau soson waya ta jefa mata tace ki tabbatar kin bi bayan tukwanen nan kin wanke su fess, xuwa gobe kuma xan san yanda xanyi da ke, daga haka ta juya ta koma ciki, Jiddah dai ta ci gaba da wanke wanken da take a sanyaye. Ba ita ta bar bakin pampon nan ba sai kusan karfe tara da rabi, duk ta gaji ga uban yunwan da take ji, bbu kowa parlon sai yara dake ta wasa, iyayensu kuma na can sama, Jiddah ta rakube jikin kujera tana jin kanta na mata ciwo, har ta mance rabon da tayi irin wannan aikin, tun bayan rabuwanta da Hansai, Aunty ce ta shigo parlon da sauri tana sanye da Hijab, har ta nufi kitchen sai kuma taga Jiddar a rakube a parlor, tana kallonta tace "Yauwa mu je ki rakani xan amso sako yanxu" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Mîkyããj_Sããdy Beauty Soap* *Hy my beautiful people ina gaisuwa🙋🏻‍♀️ku karka'de kunnuwanku da kyau ku ji💃🏻ina mai sanar muku da cewa akwai gara6asa me kyau ta musamman ga wanda suka saba sayen sabulunmu da ma wanda zasu fara saya🥰, akwai ragin kaso 20% bisa dari 100% ga wanda suka saba saye, sannan akwai ragin 10% bisa ga masu sha'awar fara saye🥰, akwai farashi mai sauki ga 'yan sari, me yapi wannan dadi kam🤔ki sayi guda 4 kanana a baki kyautar daya, ki sayi guda uku manya a baki kyautar karami daya, ki sayi bucket biyu a baki kyautar babban rubber daya😍 kema da kike da burin saya ku'dinki bai kai ba😰to ga naki, ki kawo customers uku ki karbi naki kyautar Sabulun😍😍* *Kawata 'yar 'kwalisa me kike jira,ita mace fa kullum cikim yin ado da 'kãwa take😍 ya kamata ki yunkuro wajen ganin kin rabu da wannan kurajen da tabo tabon fuskan nan haka🥺, kinga kema sai a saka ki a layin masu 'kwalisa da bajakolin ado💃🏻😍uwar gida a daure ayi gyaran jiki, sbd karbar goron a wajen me gida🥰,, ina amaren bayan sallah ku pito ku sayi naku Sabulun kuje kuyi ta wanaka hmmm 😍kamshi kawai zaku yi tayi kaca kaca😍😍, laushin fata Baja baja😃😂😂a yunkuro azo a karbi kayan gyaran jiki tare da sabulun gyaran fata a wurin _Mîkyããj_Sããdy_🥰* *Duk wanda suka gwada Sabulun mu sun san babu 'karanta a ciki🥰in dai fannin gyaran jiki ne to sabulunmu shine amsarku,, shi ke mai da fata ta zama babu Pimples, Acne, Spot, Stretch Mark, da Duk wata matsala da ta shafi fata,, akwai lightening, nd glowing😍* _*In kina son jikinki yai su6ul da shi, fata tai santsi da sul6i, ki yi haske me aji, 'kamshi kaca kaca ko ta Ina, ki ta fresh abunki hankali kwance ki zama Wankan madara yauqin zuma😍💃🏻Anty madam😃To ki mallaki 3d (Extra Whitening Soap, Ko da kudinki sai da rabonki hajiyata)💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻*_ *Akwai hadin:* *Mai da tsohuwa yarinya* *Uwargida ta koma amarya* *Amarya ta koma tamkar 'yanmata* *'Yan mata su koma 'yan dagwai²* _Ga masu bu'kata sai su tuntu6emu ta kafar sadarwa kamar haka;_ _Call/WhatsApp:08061570778_ _IG@mik_yaaj_saady_ Mikewa Jiddah tayi tsaye tana kallonta, Aunty da har ta nufi kofa ta juyo ganin Jiddah bata biyota ba ta hade rai tace "Ba magana nake maki ba" Jiddah tace "Ban saka hijabi ba" Aunty tace "Nan nan ne ba nisa muje baxa ki rasa mayafi a tsakar gida ba" Jiddah bata ce komai ba ta nufeta, Umma ce ta shigo parlon da sallama, Aunty ta koma gefe tana yake tace "Sannu da xuwa Hajiya Ramlah" suka gaisa Umma tace "fita xa ki yi halan" Aunty tace "Ehh wllh sako xan amso nan bakin titi, da har nace mu je da Jiddan tace min Hijabinta na sama" Umma ta kalli Jiddah tace "Toh ki tafi saman ki dauko hijabin naki" Aunty tace "Aa bari kawai inje ae nan bakin titi ne" bata jira cewar Umma ba ta fice daga parlon tana jin wani mugun takaici, Umma ta kalli Jiddah tace "Kin ci abinci kuwa?" Jiddah ta girgixa masa kai, Umma tace "Toh saboda me, ke ba sai ki je ki diba ba, Ummi na sama ne?" Jiddah ta gyada mata kai, Umma tace "Mu je" Jiddah ta bi bayanta suka wuce sama, Bangaren Ummi suka shiga, bayan Umma ta gaisa da yayarta tace "Yaya wai bata ci abinci ba" Ummi ta kalli Jiddah tace "Ae nayi tunanin tana tare da su Ramlah ne, kuma an kai masu abinci tun daxu, taje can dakinsu ta diba" Umma ta kalli Jiddah tace "Ki je ki deba abincin a can" Juyawa Jiddah tayi ta fita, Umma na kallon yayarta tace "Naga kamar baki saki jiki da ita har yanxu ba yaya" Ummi tace "Aa ko daya, baki ganin ita ma ba maganar take ba" Umma tayi murmushi tace "Ae kam ni muna hira da ita" Ummi tace "Did u know what is baffling me Ramlah?" Umma ta girgixa kai tana kallonta, Ummi tace "Yanda Aliyu ya mayar da mu shashashai ya maida mu wasu 'yan yara, kinsan da gangan yaje yyi ma kansa aure da yarinyar nan?" Ummi tace "Me yasa kika ce haka yaya" Ummi tayi wani murmushi tace "Ai ni na haifesa ba shi ya haifeni ba, bai kuma isa yyi deceiving dina ba, he intentionally did what he did, abubuwan da nagani game da shi da yarinyar bai yi kama da abun da mutum yyi ba da son ransa ba, kinsan satinsa nawa rabonsa da gidan nan yanxu?" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Nima ae ya daina xuwa min yaya..." Ummi tace "Toh yayi kyau... Xai gane bashi da wayo" Umma tace "Amma duk da haka akwai ayar tambaya fa a kan xaman da suke, don duk inda kika ji kishin kishin din magana da akwai kamshin gaskiya, ina jiran Ahmad ne yanxu inji matsayin auren nasu" Ummi tace "Ni ma dai nayi shiru ne kawai, amma ban aminta da xaman nan ba" Umma tace "Toh kin ga, don dama da bakinsa yyi ta cewa xae rabu da ita, na dinga hanasa tare da Abbansa to wa ya sani ko watsar da xancenmu yyi" Ummi tace "Ni kuma haka kawai naji ina son rabuwan nasu Ramlah" Umma dai tayi shiru bata ce komai ba, can ta sauke ajiyar xuciya tace "Allah dai yyi mana me kyau, kuma bana tunanin ya sa ta a karatu har yanxu, and she doesn't look happy always...." Ummi tace "Sannan ina ma son xanyi magana dake tun kwanaki, kinga lamarin rayuwar Aliyu? dama ina son in cire idanuwana da komai na a kai, sai yaje ya kara rike warce yake ganin ta fini daraja da hannu bibbiyu, ita yake ga xai iya komai na sirrinsa, ita yake ga xai fi ji da yarda da maganarta, to suje su karata, ni gaisuwan da yake min duk sanda yaga dama ma ce masa xanyi na yafe masa ya daina" Umma tace "Wannan ba magana bane yaya, tun farko ke kika xuba ido aka janye maki shi, Ahmad ya sha kawo min wannan same complain din, idan baki manta ba akwai wani lkci da na maki magana a kan hakan kika ce min ai ba komai duk daya ne, wnn mata ni ban ta6a ganin makira irinta ba..." Ummi ta girgixa kai tace "Aa ba ruwanta, ai shi ba yaro bane ya kuma mallaki hankalin kansa, he knows what is right from wrong, kawai dai hakan yake ga yafi masa alkhairi, sai yaje ya karata, amma ina dab da yi masa wankin babban bargo a gidan nan" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Ki dai yi hakuri yaya, Allah xai ganar da shi, wankin babban bargo kuma sai dai ki hada har Kishiyarki don munafuka ce" Bayan kusan minti talatin Umma ta gama abinda ya kawota, sallama tayi da yayarta har ta nufi kofa tace "Toh in tafi da Jiddar ne don can ya kai ta" Ummi tace "Aa wannan kuma ban sani ba" Umma tace "Naji xa su fita saloon gobe, kawai su tafi tare ita ma tayi gyaran gashin idan ya so ko driver sae ya maido min ita goben" daga haka tayi ma yayarta sallama ta fita dakin. Kwana dayan da Jiddah tayi gidansu Abuturrab ta fadi ma yan garinsu gashi gidan ya cika da mutane yan biki, Aunty tayi mugun saka ta gaba tun da garin Allah ya waye, ko wani aiki da aike ita ake sa wa, da ta xauna xata tasota gashi abincin kirki ma bata samu ta ci ba, da rana yan matan amarya duk suka yi shirin tafiya saloon, dama kafin Ummi ta lura da Jiddah balle har tace mata ta bi su, aunty ta hada kayan wanke wanke a bakin pampo ta turata taje tayi, yawanci duk masu girki ranan sun xata ma mai aikin gidan ce Jiddah, ko mai aikin gidan bata yi aikin da Jiddah tayi ba tunda gari ya waye, cikin ruwan sanyi Aunty ke gallaza mata, duk tunanin Ummi kuma har da Jiddah aka tafi saloon don tun bayan da suka gaisa da safe bata ganta ba, a gajiye Jiddah ta fito daga kitchen wajen karfe hudu ga wani yunwa da take ji, wata tsohuwa ce ta mika mata purse tace "Yan mata ki kai min daki wajen Hajiya Hauwa ta adana min, kada a yasheni a gidan biki, dubu daya da dari biyar ce a ciki" Jiddah ta amsa tace "Toh" lkci daya Jiddah ta gane warce take nufi wato Ummi, bangaren Ummi ta nufa ta bude kofar parlon da sallama, Ummi da frnds dinta Uku ne a parlon sai wasu yan uwa guda uku, Jiddah ta gaishesu gaba daya, Ummi dai sai kallonta take da mamaki, Jiddah ta sunkuyar da kanta ta duka gefenta tana mika mata jakar tace "Ummi wai ajiya aka ce a kawo maki" Ummi ta amshi purse din tace "In ji waye?" Jiddah tace "Ai ban santa ba" Ummi tace "Dama baki je saloon din ba ke" Jiddah ta gyada mata kai kawai, Ummi tayi shiru tana son nuna ma yan uwan mai gidanta da kawayenta cewar ita ce matar Aliyu amma ta kasa, can dai tana kallon jiddah tace "Toh gobe sai a kai ki ke" a hankali Jiddah tace "Toh" daga haka ta mike, dai dai nan Abuturrab ya fito daga bedroom din Ummi, sosai gaban Jiddah ya fadi bayan sun hada ido, amma kuma sai taji dadin ganinsa ba kadan ba, duk yan parlon suka juya suna kallonsa, Ummi ma kallonsa tayi don tun daxu take fama da shi ya fito ya gaisa da yan uwan Abbansa su uku sun iso daga Damaturu amma ya ki fitowa wai ya gaji, gwara frnds dinta a parlon ya samesu da ya shigo, Hajiya Zuwaira ta rike ha6a tace "Dama Aliyu na ciki?" Ummi ta kirkiri murmushi tace "Eh bacci yake, saukansa daga kano kenan ko awa biyu ba ayi ba" Tuni Jiddah ta fita daga parlon, gaishesu Abuturrab yayi yana yake ya nufi kofa ya fita parlon Ummi ta bi sa da kallon mamaki har ya kulle kofar, har Jiddah tayi nisa yace "Keee" tsayawa tayi ta juya tana kallonsa, ya karasa inda take yana kallonta daga sama har kasa, gaba daya ta wani susuce, yace "Yaushe kika xo gidan nan" Ta sunkuyar da kanta tace "Umma ce tace mu taho..." ya kara kallonta daga sama har kasa sannan ya sa hannu ya ciro makulli a aljihunsa yace "Dakin dake ta can bangaren inda babu mutane, ki je can ki jirani" Tana kallon makullin tace "Bude kofar xan yi?" Ya hade rai yace "Aa kullewa xa kiyi, bakya jin hausa ne?" Juyawa tayi ta bar wajen don ta gane dakin da yake nufi babu wanda ke xuwa ta wajen, bata yarda ta kalli kowa ba har ta nufi bangaren ta sa makullin ta bude dakin sannan ta shiga, babban daki ne sosai babu abinda babu a ciki, sai dai abubuwan ciki ba masu hayaniya bane, sannan ba a wani cika kaya a dakin ba, xaunawa tayi kasa ta jinginar da kanta kan babban katifar dakin don gaba daya ta gaji, Bayan kusan minti sha biyar taji an bude kofar dakin ta daga kai da sauri, Shine ya shigo dakin, ya kulle kofa yana kallonta yace "Baki cin abinci ne?" Ta girgixa kai tace "Aiki nake yi shi yasa ban ci ba" Yace "Wani aiki?" Tace "Nayi wanke wanke da safe na share duk tsakar gidan, sannan na taya masu girki wanke naman kaza, wani wanke wanken ya taru na kara wankewa, kuma naje siyo ledan kwasan tuwo sau uku wajen da nisa sosai almajiri ne ya rakani, da na dawo kuma wani wanke wanken ya taru na sake yi, sannan na share tsakar gidan da aka bata...." Katseta yayi yace "Duk wa yake sa ki?" Ta sunkuyar da kai tace "Aunty" Bai ce komai ba, bayan kusan minti biyar yace "Tashi ki shiga bandaki ki hada ruwa kiyi wanka" Mikewa tayi ta nufi bandakin she looks so tired and worn out, ya juya ya fita ya sa ma dakin makulli ya cire ya tafi da shi, a parlor ya tadda Aunty na welcoming din bak'in da suka shigo da mugun fara'arta, ido hudu yayi da mahaifiyar Aneesah, Ya sauke kansa kasa sannan ya karasa cikin parlon ya gaisheta da ladabi bata ko kalli inda yake ba balle tayi kamar ta ji, Aneesah ce ta shigo parlon da jakar kayanta, Aunty ta rungumeta tace "Sannunku da xuwa manyan baki, ya hanya?" Aneesah na murmushi tace "Alhmdlh Aunty don ma dai jirgi muka biyo ai da sauki wahalan" Kofa Abuturrab ya nufa don ko hada ido bai son yi da Aunty, Babu yabo bbu fallasa yaji tace "Aliyu get them something meaningful to eat, kasan sha'anin abincin biki, ba lallai yayi suiting taste bud dinsu ba" Toh kawai Abuturrab yace ya fice daga parlon. Parking Abuturrab yayi bakin gate dai dai lkcn da driver ya sauke su Seeyama bakin gate din, duk suka nufi motarsa, bai amsa gaisuwar da suke masa ba, ya dau leda biyu na abinci yace "Ku kai ma Aunty" Seeyama ta amsa sannan suka wuce ciki, bayan few minutes ya bude motar ya sauka ya shiga cikin gidan rike da leda daya, direct part dinsa ya nufa, ya ciro makulli ya bude kofar ya shiga sannan ya kulle, Jiddah na kwance kan carpet idonta kulle, karasawa yayi yaga bacci take, ya buga katifar kusa da ita, firgit ta mike xaune, ya ajiye ledan hannunsa ya hade rai yace "Baki ce ma Ummi baki ci abinci bane duk yau?" Ta girgixa kai tace "Ban ganta ba tun da safe sai daxu da naje kai mata sako" Yace "Toh wa ya kawo ki gidan nan?" Tace "Nace maka Umma tace in taho tare da su seeyama" ajiye ledan hannunsa yyi ya mike ya koma can karshen katifar ya xauna ya fiddo wayarsa dake vibrate a tunaninsa Ahmad ne don yana restaurant ma ya kirasa, amma sai ya ga akasin haka don Aneesah ce ke kiransa, silencing wayar yyi, Jiddah ta bude abincin da ya ajiye mata ta fara ci. Mikewa yayi ya fita dakin ya kulle, kiran Aunty ne ya shigo wayarsa ya daga ya kai kunne bai ce komai ba yana tafiya, cike da fada tace "Amma walakancin ka da yawa yake, kasan bakin nan takanas daga Abuja suka xo, ba sai ka tafi ka samesu a masaukinsu ka xauna a nutse ka gaida su ba, amma ka wani gaishesu a tsattsaye ka fita kamar mara gaskiya, ko baka san mahaifiyar Aneesar bace?" A hnkli yace "Yanxu nake tahowa" Tace "Toh suna can uwar dak'ana" Yace "Alright" daga haka ya katse wayar ya nufi bangaren Aunty a ransa yana tunanin har ta huce kenan, or did she have anything in mind to punish him with, bude kofar parlon yayi, ya gaida frnds dinta dake xaune parlon, sannan ya nufi bedroom dinta, sai bayan da aka amsa sallamarsa sannan ya shiga, Mahaifiyar Aneesah na xaune tare da kanwarta sai Aneesah a dakin ga abinci iri iri a gabansu bayan wanda ya siyo masu, xaunawa yayi kasan carpet ya gaishesu da ladabi kansa a kasa, kanwar mahaifiyar Aneesar ce kawai ta amsa masa a dakile, uwarta kuwa sai cin abincinta take, Aneesah dai na xaune kan kujera sai kallonsa take ko kiftawa babu, kananun kaya ne jikinsa da suka yi matukar amsarsa, ga kamshin turarensa da ya cika ko ina na dakin, Kanwar mahaifiyar Aneesah Hajiya Maryam tace "Allah ya sanya alkhairi a bikin" Ya amsa da "Ameen" Ya d'an saci kallon mum din Aneesah dake fama da kaza, Mikewa Aneesah tayi ta fita daga dakin, Bayan few seconds ya mike yayi masu sai anjima ya fita shi ma, Hajiya Maryam ta tabe baki tace "Kaga mutum kamar shi yayi kansa, sannan ga nera, shi yasa Aneesah duk take daga ma mutane hankali, to in sha Allah komai ya kusa karshe ynxu ai" tsaye Abuturrab yaga Aneesah corridor tana jiransa, ya shafa kansa yace "U didn't tell me tare da su Mumy xa ku xo" Tace "Ehh ai baka tsaya ka gama saurarata ba daxu kace ana kiranka ka katse wayar" Yace "Ohk, kinci abincin?" Tace "Bayan leda biyu ka siyo me xan ci a ciki?" yace "Ehh ai banga Hajiya ba i only saw u and mum" Ta tabe baki tana gyara siririn gyalenta, ya rungume hannunsa yace "Toh yanxu ya xa ayi?" Tace "Xuwa xa mu yi ka siya min abincin" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Toh ki jirani wajen motar xan dauko makulli a dakina" Tace "Ohkk" daga haka ta fara tafiya, ya bi ta da kallo sannan ya sauka xuwa dakinsa, makulli ya sa ya bude kofar xai shiga yaji muryar Aunty tana kiransa alamar tana biye da shi a baya, da farko niyyar kulle dakin yyi da makullin amma sanin xata yi suspecting abu sai ya fasa ya shiga dakin kawai bayan ya amsa kiran nata, Jiddah na tsaye bakin window ya nuna mata alamar ta shige bandaki, ai da gudu ta shige ciki ita ma jin muryarta, ta kulle har da sa makulli hakan ya kusa basa dariya, dai dai nan Aunty ta shigo dakin, ya xauna gefen gado yana shafa kansa yace "Ya gajiyan aiki Aunty?" Maimakon ta amsa sai ta sa makulli dakin ta shigo, shi dai kallonta kawai yake, ta kalli ledan abincin tace "Wannan fa?" Yace "Ni na siyo na ci" Kujera ta ja ta xauna tace "Abuturrab!!" Ya daga manyan idanuwansa ya kalleta, sake kiransa tayi murya can kasa yace "Na'am...." Tace "Dama Abuturrab ra'ayinka ne xuwa hayi kayi aure ban sani ba? Dama haka ka mayar dani gantalalliya ban sani ba" Ya girgixa kai yace "Wllh ba ra'ayina bane Aunty" tace "To son yarinyar ka fara all of a sudden? Da ka toxarta ni gaban ubanka?" Ya girgixa kai yace "Ko daya wllh Aunty" tace "Toh kawai xubar min da mutunci da walakanta ni gaban iyayenka ka so yi??" ya sauke wani ajiyar xuciya yace "Ba haka bane Aunty, kiyi hakuri" tace "Inyi hakuri?? Dama shirga ni kayi baka saketa ba Aliyu??" Da kyar yace "I'm finding it hard to confide in u anymore aunty..." Tace "Why??" Yace "U did what i never expected, kema kin san na kowa me sauki ne kan na Abba, how will u expect him to take it cewar na saketa da gaske? Wllh he can even disown me, kin fa san waye Abba, kin fi kowa saninsa, amma kika yi exposing dina wajensa" Da karfi tace "Karya kake, wllh baka saketa ba ni xaka mayarda sha sha sha yanxu? Are u stupid?" Yayi kasa da murya yace "Xa kiyi kaffara Aunty, nace maki ba aure tsakaninmu da yarinyar nan amma kuma bai kai har ki je ki gaya ma Abba ba, i trust u shi yasa na sanar maki" Shiru tayi tana kallonsa tana huci tace "Toh dadin xama kake ji da ita ne da kaki rabuwa da ita har yanxu???" Yace "Ko daya, idan na rabu da ita bata da wajen xuwa Aunty, Aunty da xa ki kwantar da hankalinki ki xuba min ido xaki ga me xai faru in sha Allah, i have plans wallahi, ba haka nan kawai na ajiyeta gidana ba, the house isn't meant for her..." tace "Which nonsense plan Aliyu, dubi fa yanda yarinya tayi wani kyau ta kara uban haske fatarta lui lui kamar a latsa jini ya fito, a haka ne xan amince da kai baxan sa shakku a raina ba? Dubi fa yanda tayi fresh alamar bata da wani damuwa ta samu gida kawai, sbda ita ko weekend ka daina dawowa gidan nan sai dai ka sauka can kayi yanda kaga dama da ita, don wllh ban yarda baka harkanka da ita ba" Kallon Aunty ya dinga yi ba ko kiftawa, sannan yace "Inyi harka da ita fa fa kika ce Aunty" Tace "Toh eh mana, kana xaune da budurwa irin wannan a gida baxa kayi yanda kaga dama ba?" ya girgixa kai yace "Ba yanda kike tunani bane aunty, amma dai yanxu ya kike son ayi?" Aunty tace "Kawai ka dawo da ita gidan nan gaba daya da xama, she will be very useful wllh" Kallonta kawai yake yi, tace "Ko baka ji abinda nace ba?" Yayi murmushi yace "Na ji" tace "Wato baxa ka yi ba kenan??? Wato wllh ban ma yrda cewar babu abinda ke shiga tsakaninka da yarinyar nan ba da ya sa kaki rabuwa da ita har ynxu duk da ba auren" Ya girgixa kai yace "No plss, Wllh babu wani abu Aunty ai kinsan ba haka nake ba" Tace "Toh ka maidota gidan nan nace idan na isa da kai, tunda already tana nan kawai kayanta xaka debo gaba daya ka maido su nan" Ya shafa kansa yace "Toh Aunty amma sai mun yi magana da Ummi ko...." Wani kallo ta jefa masa tace "Sai kun yi magana da Ummi? Ni ban isa da kai ba kenan da xaka yi involving Ummi??" Yace "Kin isa" tace "Toh ba sai ka sanar mata komai ba, kawai taga ta dawo nan din, idan tace don me, sai kace ita kadai ce a gida kuma aiki ya maka yawa" Yace "Ohkk" mikewa tayi tace "Xan koma wajen bak'ina, bayan bikin xa muyi magana a tsanake" Daga haka ta bude kofa ta fita ya bi ta da kallo, mikewa yayi ya karasa ya kulle kofar dakin sannnan ya dawo ya bubbuga kofar bandaki, bude kofar Jiddah tayi ta fito tana kumbure kumbure tace "Don Allah kar ka dawo dani gidan nan kayi hakuri" sai kuma ta sakar masa da kuka, dariya abun ya basa, ya dake yace "Gidan namu kike kuka kar in dawo da ke??" Tace "Don Allah kayi hakuri" yace "Dole ma ki xauna nan din ki samu saiti sosai" Durkushewa tayi gabansa ta hade hannayenta tana kara rushewa da kuka tace "Aa don girman Allah kayi hakuri" Xaunawa yayi gefen gado yace "Kin fi son xama tare da ni kenan, duk da kince ni ba muharraminki bane?" Ta gyada masa kai a hankali tana share idonta, ya kauda kai yana murmushi, tuna Aneesah dake jiransa bakin mota yyi, da sauri ya tashi ya dau makullin motarsa ya fita ya kulle dakin ta bi sa da kallo. Har Aneesah xata shigo parlor suka hadu bakin kofa, sai da ya fara surveying wajen yaga ba mutane ya riko hannunta yace "C'mon dear, am sorry Aunty ce ta bata min lkci wllh" hararansa kawai take, yayi murmushi ya ja hancinta sannan yace "Mu je" duk abinda tace xata ci ya siya mata a eatry din da suka je sannan suka dawo gida, ta tafi bangaren Aunty shi kuma ya tafi dakinsa, bude kofar yayi ya tadda jiddah yanda ya barta, ya kulle kofar ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya sauya kayan jikinsa xuwa pajamas sannan ya kwanta.... Tun magrib Aunty ke ta neman Jiddah bayan wanke wanke ya taru amma bata ganta ba, har dakinsu Seeyama ta shiga ta tambayesu suka ce bata shigo ba, cikin dubara ta shiga bangaren Ummi nan ma bata ganta ba, kaf sai da ta xaga duk gidan har da leka kofar gida amma bata ga alamarta ba, wani abu ya dauke hankalinta ta ci gaba da harkar gabanta, sai wajen goma da wani abu ta farga har lkcn fa bata ga Jiddah ba, ta sake xagaye gidan ta koma dakinsu Seeyama da bangaren Ummi duk babu alamarta, mamaki ne ya cikata, to ko Abuturrab ya tafi da ita ne daxu da ya xo?? Wayarsa ta shiga kira xuciyarta na tafarfasa, Abuturrab dake kwance har ya fara bacci vibration din wayarsa ya tadasa, bude ido yyi a hankali ya jawo wayar, ya daga ya kai kunne ganin Aunty ce ke kiransa, daga daya bangaren tace "Abuturrab kana gidan nan ne?" Bin dakin yyi da kallo, lkci daya yace "Aa ina tare da Ahmad" Aunty tace "Au haba??" Yace "Ehh a nan xan kwana, da wani abu ne?" Ta girgixa kai tace "Aa tunda baka nan sai da safe kawai" Daga haka ta katse wayar tayi wani murmushi, dama so take ta ta66atar da cewar ba shi ya dauketa ba, addu'a ta shiga yi a ranta na cewar Allah yasa karawa gaba jiddah tayi kawai... Abuturrab ya kalli kasan carpet din dakin ya ga jiddah kwance ta gaji da kukan bacci ya dauketa, har ya koma ya kwanta ya mike ya bude press dinsa ya fiddo da xanin gado ya rufa mata sannan ya kwanta saman gado ya kashe wutan dakin. Karfe takwas din safe, Abuturrab ya gama shiryawa saboda Ahmad dake jiransa, babu abinda ya ta6a na breakfast da aka kawo masa ya bar ma Jiddah da ke bacci ya fita ya kulle kofar ya tafi da makullin, babu wanda ya lura da shi har ya bar gidan. Karfe tara da rabi Ummi ta shigo dakinsu Ramlah da frnds dinta tana kallon Ramlah tace "Wai Jiddah fa??" Ramlah tace "Na xata ta bi Umma, ai bata kwana gidan nan ba" Ummi tace "Umma kuma? Umma ta xo gidan nan ne jiya?" Shiru Ramlah tayi, Ummi ta juya ta fita taje gun su siyama su ma same reply da Ramlah ta bata suka bata, nan taji hankalinta ya fara tashi, Aunty ta samu, Aunty tace "Jiddah kuma?? Ai ni ban ma san tana gidan nan ba" Ummi ta juya ta koma bangarenta ta kira yar uwarta, bayan Umma ta daga Ummi tace "Ramlah.... Jidderh ta koma gidanki ne??" daga daya bangaren Umma tace "Jiddah?? Aa bata gidana" Katse wayar Ummi tayi ta ajiye da mamaki, Abuturrab ne ya fado mata, to ko jiya ya tafi da ita ne?? Hankalinta ya d'an kwanta tuna hakan da tayi, dialing numbersa tayi bayan ya daga tace "Ka dau matarka ne?" Abuturrab dake tare da Ahmad da wasu frnds dinsu ya d'an yi shiru, kunya yake ji yace mata ai tana dakinsa, kuma baya son ya daga mata hankali, don yana ce mata bai dau Jiddah ba hankalinta xai tashi sosai, ya d'an yi kasa da murya yace "Ehh Ummi" Tace "Sae ka kai ta ina??" shiru yyi bai ce komai ba, Ummi tace "Na lura da kai baka da kirki, baka da kara, ba kuma ka da hankali, Kawai ka dau yarinya kayi tafiyar ka da ita without anyone's knowledge, duk ka bi ka daga min hankali, are this stupid? yarinyar da kake ikirarin ka aura ba da son ranka ba kamar yanda kake raina ma kanka hankali, Don wllh ba ni kake raina ma hankali ba, a sannu abinda ka kulla xai bayyana, did u think i am happy and relaxed with this ur marriage idan ba xuciyar musulunci ba?? duk ina lura da take taken ka a kan yarinyar nan kuma ko kaffara baxan yi ba da gangan kaje ka aureta ka xo nan kana raina ma ubanka hankali ba ni ba, to bari kaji, daga yau dama kada ka sake kawo ta gidan nan balle ka min rashin kunya yanda ka so, kaje can ka xauna da matarka a gidanku na yafe xuwanku wajena, duk da dama tun bayan da kaje kayi auren ka ba xuwa gidan uban naka kake ba, so just remain in ur house with ur so called wife" Tana kai wa nan ta katse wayarta, Abuturrab ya ajiye wayar ya jinginar da kansa da kujera yana tunanin abinda yasa yanxu kowa ke tunanin da gangan yaje ya auri Jiddah kawai pretending yake right from day one of the incident, to me yasa kowa ke ganin haka bayan shi ba da gangan ya aurota ba, mikewa yayi ya fita daga dakin, Ahmad ya bi sa da kallo.... Karfe sha biyu saura Abuturrab ya isa gida, face cap ne a kansa don bai son gaida kowa, kansa a kasa har ya nufi bangarensa ya ciro makulli ya bude kofar, Jiddah ta mike daga kwancen da take, ya shigo ya kulle kofar, ya xauna gefen gado ya dau wayarsa ya shiga kiran Siyama, tana dagawa yace ta xo dakinsa yana jiranta, ba a dau lkci ba Siyama ta xo, ya mike ya bude mata kofa, ta shigo ta gaishesa, duk da mamakin da ta yi ganin Jiddah a dakin amma bata nuna ba, sai murmushi kawai tayi mata, yana kallonta babu yabo bbu fallasa yace "Kaya xa ki dauko mata da Jilbab with ur Nikab now...." Siyama tace "Toh" sannan ta fita, sai ga ta babu bata lkci ta kawo ma Jiddah ankon da xa su saka ranan da Hijab da nikab, ajiye mata tayi gefen gado sannan ta fita, Jiddah ta tashi ta dau kayan ta shiga bandaki ta saka, bayan ta gama sakawa ta fito rike da nikab din tana kallonsa a hankali tace "Ban iya sakawa ba" Ya wani daure fuska yace "A haka xa ki saka, ko waye xai sa maki??" Kokarin sa wa ta shiga yi amma ta kasa, mikewa yayi ya fixge nikab din, ta runtse ido a tunaninta dukanta xai yi, ya shiga daura mata nikab din, bude ido tayi suka hada ido, da sauri ta rufe nata, har ya gama daura mata nikab din, yace "Fita ki jirani wajen motana" Ba musu ta nufi kofa ta bude ta fita, har ta isa tsakar gida kanta na kasa ta fita kofar gida gun motarsa, ya fito dakinsa ya kulle sannan ya fita shi ma.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Mîkyããj_Sããdy Beauty Soap* *Hy my beautiful people ina gaisuwa🙋🏻‍♀️ku karka'de kunnuwanku da kyau ku ji💃🏻ina mai sanar muku da cewa akwai gara6asa me kyau ta musamman ga wanda suka saba sayen sabulunmu da ma wanda zasu fara saya🥰, akwai ragin kaso 20% bisa dari 100% ga wanda suka saba saye, sannan akwai ragin 10% bisa ga masu sha'awar fara saye🥰, akwai farashi mai sauki ga 'yan sari, me yapi wannan dadi kam🤔ki sayi guda 4 kanana a baki kyautar daya, ki sayi guda uku manya a baki kyautar karami daya, ki sayi bucket biyu a baki kyautar babban rubber daya😍 kema da kike da burin saya ku'dinki bai kai ba😰to ga naki, ki kawo customers uku ki karbi naki kyautar Sabulun😍😍* *Kawata 'yar 'kwalisa me kike jira,ita mace fa kullum cikim yin ado da 'kãwa take😍 ya kamata ki yunkuro wajen ganin kin rabu da wannan kurajen da tabo tabon fuskan nan haka🥺, kinga kema sai a saka ki a layin masu 'kwalisa da bajakolin ado💃🏻😍uwar gida a daure ayi gyaran jiki, sbd karbar goron a wajen me gida🥰,, ina amaren bayan sallah ku pito ku sayi naku Sabulun kuje kuyi ta wanaka hmmm 😍kamshi kawai zaku yi tayi kaca kaca😍😍, laushin fata Baja baja😃😂😂a yunkuro azo a karbi kayan gyaran jiki tare da sabulun gyaran fata a wurin _Mîkyããj_Sããdy_🥰* *Duk wanda suka gwada Sabulun mu sun san babu 'karanta a ciki🥰in dai fannin gyaran jiki ne to sabulunmu shine amsarku,, shi ke mai da fata ta zama babu Pimples, Acne, Spot, Stretch Mark, da Duk wata matsala da ta shafi fata,, akwai lightening, nd glowing😍* _*In kina son jikinki yai su6ul da shi, fata tai santsi da sul6i, ki yi haske me aji, 'kamshi kaca kaca ko ta Ina, ki ta fresh abunki hankali kwance ki zama Wankan madara yauqin zuma😍💃🏻Anty madam😃To ki mallaki 3d (Extra Whitening Soap, Ko da kudinki sai da rabonki hajiyata)💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻*_ *Akwai hadin:* *Mai da tsohuwa yarinya* *Uwargida ta koma amarya* *Amarya ta koma tamkar 'yanmata* *'Yan mata su koma 'yan dagwai²* _Ga masu bu'kata sai su tuntu6emu ta kafar sadarwa kamar haka;_ _Call/WhatsApp:08061570778_ _IG@mik_yaaj_saady_ Aunty ce ta shigo parlon Ummi duk da mutane da ke parlon ta ra6a xuwa cikin daki, Ummi na ciki tana bada sako, Aunty ta ja gefe ta jira har ta gama bada sakon sannan tace "Jiya kaina ya dau xafi kika xo kina tambayar Jiddah, to kin dai ganta ko?" Ummi tace "Mijinta ne ya dauketa" Still Aunty tayi tana kallon Ummi, trying to assimilate tace "Abuturrab din?" Ummi tace "Eh" Juyawa Aunty tayi ta fita daga dakin xuciyarta na tafarfasa, lallai Abuturrab ya gama rainata... Through out ranan da ya kasance mothers eve Jiddah na gida ita kadai, kuma ko a jikinta, sai yanxu ta gane xaman gidan da take ita kadai ma gata ne ashe, xamanta 24/7 a gida babban Rahama ne gareta, tun da Abuturrab ya ajiyeta ya tabbatar ta shiga ciki ya tafi bata sake ganinsa ba. Karfe shiddah saura na yamma bayan sun dawo daga babban event center din da suka yi booking against tomorrow's dinner, su biyar ne a motar, wani abokinsu Umar ne ke driving motar, Abuturrab na kallon Umar kafin su isa hanyar da xai kai sa gidansa yace "Umar ka samu waje ka ajiye ni a restaurant din gaba..." Ahmad ya kallesa da sauri, kamar baxai ce komai ba, sai kuma yace "Me xaka yi a restaurant bayan abincin da muka ci yanxu?" Abuturrab ya gyara xamansa babu yabo babu fallasa yace "Eh xan amshi abinci in wuce gida" Ahmad yace "Me xaka je kayi a gida?" Abuturrab yace "Kamar ya me xanyi a gida? Naga it's almost magrib yanxu ko kana nufin saboda gobe daurin aurenka sai in bar gidana in kwana a wajenka?" Murmushi Ahmad yyi yace "Kai dai ka fadi gaskiya, dama Ummi ta shaida min abinda kayi masu, kawai dai baka son ka bar matarka ta kwana ita daya a gidan, shine xaka amsar mata abinci yanxu ka wuce gida" Abuturrab ya d'an yi shiru idonsa a kan titi yana sake comprehending abinda Ahmad ke ce masa, Umar yace "Ni kuwa yau sai naje gidan Captain naga matar nan tasa mun gaisa" Najeeb ma yace "Same with me... matar da har yau ba wanda ya santa" Da sauri Abuturrab yace "To ai tana gidan biki, sai dai idan can xa mu je" Dariya Ahmad yayi yace "Tana gida bata wani gidan biki, mu je kawai Umar ai nasan gidan" Lkci daya mood din Abuturrab ya canxa amma ya kasa cewa komai, Ahmad na nuna ma Umar hanyar gidan har suka isa, horn Umar yayi mai gadi ya bude gate din bayan ya hango Abuturrab da ya sha kunu cikin motar, Umar na parking Ahmad ya fara sauka, sannan Abuturrab, sauran frnds din nasu uku ma duk suka sauka, tafiya kawai Abuturrab ke yi xuwa entrance din gidan, Ahmad na leading din frnds din nasu yana cewa "Wannan ai ba adalci bane ba a sanar maku biki ba kuma a ki kawo ku gidan amarya" Har wani nishadi yake suna dariya da frnds din suna biye da Abuturrab, Abuturrab na shiga parlon ya dinga bin ko ina da kallo, kamshin girki ne ke tashi a parlon wanda ko ina fess alamar har goge goge tayi bayan dawowarta, kitchen ya nufa ya ganta tsaye kusa da gas, ga miya tana yi a gas din, daga sama har kasa yake kallonta, wanda riga da skirt ne na atamfa jikinta amma ba ankon da ta saka da safe ba, har xai juya ya fita sai kuma ya sake juyawa yana kallonta babu yabo babu fallasa yace "Dama kar ki kuskura ki fito daga kitchen din nan" Bai jira cewarta ba ya fita parlor, su Ahmad na xaxxaune parlon har da kunna TV, Najeeb yace "Duk girkin amarya ne ya cika gidan nan haka, ashe yau xa mu kwashi girki" Ahmad ya hadiye dariyar da ke damunsa ganin fuskar Abuturrab, Abuturrab dai bai ce komai ba ya wuce sama, sai gashi ya sauko rike da folded hijab dinta ya wuce kitchen, mika mata yayi yace "Ki fito ki gaishesu, kuna gaisawa kuma ki wuce sama har su tafi kada ki kuskura ki sakko, saura kuma idan kin xo gaishesu ki xube kasa kamar kina neman gafara" amsan Hijab din tayi tace "Toh" ya juya ya fita, bayan ta saka hijab din ta bi bayansa, kanta a kasa har ta karaso cikin parlon, gaba dayansu kallonta suke, ta tsaya nan bayan kujera, sai kuma ta kasa gaishesu a tsaye don bata saba ba, xagayowa tayi ta xauna saman lallausan carpet din ta gaishesu ba tare da ta kalli kowa a cikinsu ba, amsawa suka yi gaba daya Umar yace "Yau Allah yayi xa mu ga amaryar captain, ashe shi yasan me yasa bai ta6a gayyatomu mu ganta ba" Ita dai kanta na kasa, Abuturrab sai danna wayarsa yake bai ce masa komai ba, Ahmad yace "Toh a kawo mana ruwa matar captain" Kallonsa tayi jin muryarsa, ta d'an yi murmushi sannan ta mike ta nufi kitchen, tray ta dauka ta daura ruwan gora uku da glasses hudu sannan ta fito ta ajiye nan tsakiyar parlon, daga kai Abuturrab yyi ya kalleta ganin tayi abun hankali, he was thinking a hannu xata rike goran ruwan ta kawo, Najeeb yace "Toh ni kuma girkin amarya xan ci" Sosai gaban Abuturrab ya fadi, don ko shi bai ta6a cin abinda jiddah ta girka ba, har Ahmad sai da ya ji faduwar gaba, can dai yace "Bayan wanda muka ci yanxu?" Umar yace "Wanda muka ci daban, wannan kuma na amarya ne" Jiddah dai tayi shiru, Najeeb yace "Ko baxa a bamu ba amarya?" Mikewa tayi tana murmushi ta nufi kitchen, Abuturrab ya kalli Najeeb yace "Yanxu fa ka ci abinci bawan Allah, sannan gwangwani daya ta dafa... ba daga kitchen din na fito ba yanxu, ai bata san xa ku xo ba" Dariya Najeeb yyi yace "Sai ta tsam mana a gwangwani dayan, duk wannan kamshin mu tafi bamu ci abincin amarya ba" Ahmad dai bai sake cewa komai ba, Abuturrab ya d'an saci kallon hanyar kitchen din, bai san lkcn da ya mike ya bi bayanta ba, plate ta dauka ta xuba shinkafar, tana tunanin ko a kai xata sa miyan, amma gidan umma taga waje daban ake sa miya idan an xuba ma baki abinci, hakan yasa ta dau wani bowl din me xurfi ta xuba miyan, tunda ta xo gidan bata ta6a girki da nama ba sai ranan, duk da ba wani girki ma take yi ba tun xuwanta, ganin Abuturrab ya shigo kitchen din ya kulle kofa ta juya da sauri tana kallonsa tace "a saman shinkafar xan xuba miyar?" Ya watsa mata wani kallo yace "Ko kuma a sama kaina ba, ke har wani girki kika iya xaki wani xo ki xuba masu abinci maimakon kice babu kare, ni kike son ki kunyata gabansu?? Ko ruwan shayi ma baki bari ya tafasa ballantana ki iya girki me dadi" Kallonsa kawai take ko kiftawa babu, ya nufi tray din da ta daura shinkafa da miyar, ya dau spoon ya debi miyar kadan ya sa a gefen shinkafar ya juya, sannan ya debi shinkafar ya kai baki, ita dai kallonsa kawai take gabanta na faduwa, ya fi second biyar trying to figure out the taste of the food, sai ya ji girkin kamar na gidan Umma, ko don sbda spices din da tayi amfani da ne, wanda umma ta bada a kawo mata, sake dibar shinkafar yyi ya kai baki, da gefen idonsa ya bi kitchen din trying to be sure ba Umma bace ta aiko mata da abincin, bai ga warmer ko wani abu da xai nuna kawo abincin aka yi ba, ya sake diban shinkafar ya kai baki, rungume hannunta tayi tace "Toh xaka cinye abincin ba a kai masu ba ai" cire spoon din yyi a baki da sauri, ya jefa mata wani kallo, ta koma baya ta turo baki, yace "Wa yayi girkin nan?" Bai san lkcn da yayi tambayar ba, sai yaji tambayar made him sound stupid, daukar tray din yyi ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, Najeeb ya sauke ajiyar xuciya yace "Ai har mun cire rai nace su tashi mu tafi kawai" Ahmad couldn't hold it any longer, banda dariya babu abinda yake, Abuturrab ya ajiye masu abincin nan middle of carpet yace "Ae nace maku d'an kadan ta dafa, gashi nan tunda yunwa ku ke ji" Najeeb ne ya fara sauka sannan Umar, shi dai khaleel murmushi kawai yake, Ahmad ya mike ya isa gun abincin ya ci spoon daya gabansa na faduwa, exactly tunanin da Abuturrab yyi shi ma shi yyi, kamar daga gidansu aka kawo mata abincin, komawa yayi ya xauna yana murmushi yace "Nima na ci abincin amarya" Najeeb yace "Kafin ka ci na taka amaryar kenan" Umar yace "Wllh u are missing Khaleel kaji dadin abincin nan kuwa" Tasowa Khaleel yyi shima ya ci spoon daya, sosai suka dinga yabon girkin, shi dai Abuturrab na xaune yana kallonsu, sai da suka cinye abincin duk da ba yunwa suke ji ba, sannan duk suka fita xuwa masallaci, Ahmad ne last din fita, kafin ya fita ya nufi Abuturrab yyi kasa da murya yace "Amma daga gidanmu aka kawo abincin nan ko?" Abuturrab yace "What did u mean?" Ahmad yace "Ba Jiddah bace ta girka" Abuturrab yace "Haka ta ce maka??" Juyawa Ahmad yyi ya bi bayansu Umar, Abuturrab ya mike ya dau tray din abincin ya wuce kitchen, har sannan jiddah na tsaye ta jingina da bango, ya ajiye tray din yana kallonta yace "Wa ya aiko maki da abincin nan?" Ta kallesa, a hankali tace "Abincin ya fi karfin ace ni na dafa ko??" Naxarin maganarta ya shiga yi, ta tattara plates da xata wanke a sink sannan ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Sake kallon pot din miyan yayi ya karasa ya bude sannan ya bude na shinkafar, rufewa yayi ya juya ya fita daga kitchen din xuwa masallaci. Ko da suka dawo mosque sun so Abuturrab ya kira jiddah suyi sallama da ita yace ai sallah take, haka nan ko wannensu ya basa kudi ya bata ladan girki, gefen kujera ya ajiye yace "Ta gode" sannan yayi masu rakiya har bakin mota yana kallon Ahmad yace "Xan shigo da safe in sha Allah" Ahmad ya hararesa yace "Kar ma ka shigo mana" a haka suka wuce a mota, Abuturrab ya juya ya koma cikin gidan, dubu sha biyar ne kudin da ya kirga, bayan kusan minti ashirin ya mike ya wuce sama ya bude kofar dakinta, xaune ya ganta kan darduma, ya nufi gaban mirror dinta ya ajiye kudin yana kallonta ta madubin yace "Gashi nan sun baki, dubu sha biyar, amma ban mance turarena da kika fasa ranan ba" juyawa yyi yana kallonta da kyau yace "Kinsan nawa turaren da kika fasa?" Kallonsa kawai take, yace "Dubu arbain da bakwai kika fasa ranan, don haka xaki ajiye wannan dubu sha biyar din har ki samo dubu 32 ki cika min kudin turarena" Yana fadin haka ya bar kudin gaban madubi ya nufi kofa ta bi sa da kallo, can tace "Toh ka tafi da kudin" Ya juyo yace "Sai kin cika" daga haka ya fita dakin. Karfe tara jiddah na wanke wanke a kitchen ya shigo, bin kitchen din ya shiga yi da kallo, ita dai tunda ta kallesa sau daya ta ci gaba da wanke wankenta, kettle din dafa ruwa ya dauko ya bude fridge ya fiddo goran ruwa daya ya xuba a kettle din sannan ya jona, satan kallonta yayi ganin hankalinta na kan wanke wanken da take, ya kai hannu a hankali ya bude murfin tukunyar shinkafar dake kan gas har lkcn, dai dai nan ta juya yayi saurin sakin murfin tukunyar, dauke kanta tayi ta ci gaba da abinda take, ya sosa kansa, sai kuma ya hade rai yace "Shi kuma sauran shinkafar wa kika bar ma??" Ta kallesa tace "Kai mana" ya kauda kai bayan few seconds yace "Na fara wasa da ke ko??" Bata ce komai ba ta dauraye hannunta bayan ta gama wanke wanken ta dau plate ta nufi gun tukunyar ta debi shinkafar duk da ta ci, ta ajiye pot din gun wanke wanke, ta bude miyar ta sa d'an dai dai da nama yanka uku sannan ta rufe sauran miyan ta dau wani plate me xurfi ta rufe shinkafar da shi ta dau spoon ta nufi kofa ya bi ta da kallon gefen ido har ta fita, shafa kansa yyi yana tunanin wani eatry xai kira yyi ordering abinci da daddaren nan a kawo masa, shayi ya hada bayan ruwan ya tafasa sannan ya fita kitchen din, yana haurawa sama ya kalli kofar dakinta sannan ya wuce bangarensa, bude kofar parlon yayi ya shiga sannan ya kulle, still yyi yana kallon plate din dake ajiye kan center table, ya karasa ya ajiye shayin hannunsa sannan ya bude plate din yana kallon abincin, ajiye murfin yyi ya mike, can ya kalli kofa, sai kuma ya xauna, kamar me contemplating sai kuma ya dau spoon din ya fara cin abincin. Washegari karfe takwas da yan mintuna Abuturrab ya bar gidan xuwa gidansu Ahmad, Umma bata amsa gaisuwar da yake mata ba, ya shafa kansa ya wuce dakin Ahmad, Ahmad na ganinsa ya mike yace "Let's talk" Kama hannunsa yyi ya fita suka tafi bangaren Abbansa, Abuturrab dai kallonsa kawai yake, Ahmad ya kulle kofar parlon yace "Me yasa ka dauke jiddah daga gidan su Ummi jiya?" Abuturrab ya hade rai yace "Gani nayi she isn't comfortable, sannan Aunty duk ta bi ta takurata duk ba wanda yace komai, shkkn saboda ba matata bace ita sai in xuba ido a cuceta?" Ahmad yace "Har Ummi ma cutarta take kenan?" Abuturrab ya shafa kansa ya xauna yace "Ni bance haka ba, wllh da kaga yanda na ganta shekaranjiya ko kai baxa ka bada shawaran in bar ta ba, ita Ummi bak'i sun mata yawa, babu abinda xata yi noticing, and Aunty sai aikenta take tana fita titi, what for?? I hate it when someone is being maltreated kai ma ka sani" Ahmad yace "Hmm, ka gano wani abu kuwa Abuturrab?" Abuturrab na kallonsa yace "Me kenan?" Ahmad yace "You are starting to develop feelings for Jiddah, na lura da hakan tun ba yanxu ba, wannan ya wuce tausayi da kwatar mata 'yan ci, gashi kayi gaggawar rabuwa da ita, don babu aure tsakaninka da ita believe it or not, ko da kuwa baka saketa ba shelan da ka dinga yi kana sanar ma kowa cewar ka saketa, ta saku babu wani kwaskwarima... Babu wani aure tsakaninku ynxu Captain, sannan kar ka manta babu idda a kanta..." Katse sa Abuturrab yyi yace "Nigerians have a very very poor thinking mentality, me yasa baxa ku yi koyi da wasu kasashen da suka fi ku wayewa ba, Shikenan ba dama mutum ya nuna rashin jin dadin abun da ake yi ma mace sai ace yana sonta? Ohk fine... Yanxu in xuba ido ayi ta cutarta kenan tunda ba sonta nake ba, ina ce ita ma mutum ce kamar kai, kamar ni, kamar kowa ma? To don me baxan kwatar mata right dinta ba, ko ka mance akan kwato mata right din nata yasa har naje na aureta? Sannan still a kan kwatar mata right din nata ne yasa na datse auren dake tsakaninmu, and duk wannan wa'axin da kake min ni na ta6a bude baki nace maka da aure tsakaninmu ne?? Ko kuma idan ma da auren gaya maka aka ce xanyi" Ahmad yyi murmushi yace "You are just confusing and disorganizing ur self, shi lamarin da ya shafi addini babu wayo a ciki dai, anyway Ummi is jet angry at you, gwara ko koma yanxu ka dau jiddah ka kai ta can gidan tunda dinner xa ayi yau, daga wajen dinner din sai ka wuce da ita gida, gobe Saturday ka kawota yini tunda baxa ka iya barinta a gidan ba, amma kasan me? Kawai ina ji a jikina xamanku tare da ita ya kusa xuwa karshe" Da ido Abuturrab ya bi Ahmad har ya fita. Motoci biyu ne lafiyayyu suka yi parking kofar gida, El-Basheer ya juya yana kallon warce ke xaune bayan mota ta sha glass yace "Toh ai sai ki sauka mun iso" Da mamaki tace "In sauka fa kace, a kan titin xan sauka d'an nan, motoci sun daina shiga get din gidan ne xan sauka a bakin titi" Yace "Toh ai babu wajen parking a ciki, ke baki ga mutane bane...." Tace "Toh ina ruwana da mutane, har yanxu dama Najeriyan bata canxa ba, mu ba haka ake yi a Masar ba wllh, idan ana biki ko wani shagali wllh dai daikun mutane ake gayyata da daddare, sai a tarfa ma kowa yar gurasar alkama a gefen faranti, a daura kofin madara a gefe, idan da yar cinyar kaza a saka a gefe shi ma, Allah ba a taro irin haka kamar ana yunwa, shi Kabirun yasan haka mutane xa su cika gidan xai bada mota a kawoni nan salon in gantale? wllh mu bamu saba haka a Masar ba, a gaskiya idan baxai yiwu ba a juyar dani kawai a mayar dani Bauchi, daga baya kada Usman ya kullaceni sai in dawo inyi Allah ya sanya alkhairi, amma wllh baxan sauka bakin titi ba duk k'ura ta kare min abinda babu a Masar, ko shi Usman din bai san ina hanya ba ai Aliyu ya sani tunda na sanar masa ta waya.... Aa gaskiya ba dole Allah ya sanya alkhairi juya mu koma kawai... Mu ba haka ake a Masar ba, komai bisa tsari ake yin sa" Kashe motar El-Basheer yyi yace "Kinga Hajja idan xaki sauka ki sauka ni xan tafi gun daurin aure ne, ga ki ga gate kice baxa ki sauka ba" Bude baki tayi tana kallonsa, can tace "Aa toh gaskiya Najeriya ba wajen xuwa bane, tunda nake a masar ba a ta6a min rashin da'a irin wannan ba, sun san girma da mutuncin tsoho..." Tana kai wa nan ta ciro wayarta fuska tsuke ta mika masa tace "Kira min Kabirun, ai shi na haifa ba kai ba" Bude motar El-Basheer yyi ya sauka yayi wucewarsa cikin gidan, ta bi sa da kallo baki bude, sai kuma ta sauko ita ma ta bi bayansa. Jiddah ce xaune bedroom din Umma kanta a kasa tana wasa da gefen hijab dinta, Umma tace "Jiddahh" dago kai tayi a hankali tana kallon Umma, Umma tace "Ina sauraronki, idan kika min karya kuma kar ki manta Allah na kallonki, kuma nasan kinsan makomar makaryaci" Lkci daya hawaye ya kawo idonta, Umma tace "Ina jin ki" Those nulls reading my book for free and still commenting nonsense should know that i owe dem 500.... subhanallah!!! It's their gut for me wllh. In ma ku biya in ma kar ku biya babu pardon tsakanin mu. My diehard fans kuma we move.... 💖 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Jiddah ta goge idonta still ta ki cewa komai, Umma tace "Baxa ki min magana ba Jiddah?" A hankali Jiddah tace "Umma yace min babu aure tsakanina da shi" Umma tace "Kamar ya babu aure a tsakanin ku?" Jiddah ta gyada kai tace "Eh haka yace, wai shi ba mijina bane" Umma tace "A ina yace hakan?" Jiddah tace "A can gidansa, ya rubuta ne a takarda ya bani" Umma ta dinga kallonta kafin tace "Ina takardan?" Cikin sanyin murya tace "Ya ki bani" Umma tace "Amma ya nuna maki?" Jiddah tace "Ehh" Umma tace "Cewa yayi ya sakeki a takardan?" Nan ma tace "Ehh haka yace, shi ba mijina bane" Umma ta gyada kai bata kuma ce mata komai ba, bayan kusan minti goma ta mike ta fita dakin rike da wayarta, wani dakin daban ta shiga tayi dialing number wata aminiyarta tana dagawa tace "Hajiya karfe nawa xa ki taho?" Hajiya Rukayya tace "Ina hanya yanxu haka" Umma tace "Babu kowa gidanki?" Hajiya Rukayya tace "Toh na bar su dai suna ta shirin tafiya dinner da wani abu ne?" Umma tace "Toh shhkn tunda ba kowa, dama wata yar uwarmu ce aka kawo biki to bata son hayaniya, kinga nan din ma akwai taro shine da nake son ta xauna gidanki har bayan biki" Hajiya Rukayya tace "Ohh Allah sarki, to amma Badiya mai aikina na nan ai, ba sai su xauna tare ba" Umma tace "Yauwa toh, xan sa driver ya kai ta can din kawai, sai ki kira ki sanar mata bakuwa na xuwa" Hajiya Rukayya tace "Toh ba damuwa" Umma ta koma dakin da Jiddah ke ciki tace "Kaya kala nawa kika taho da?" jiddah tace "Na yau ne da gobe kawai" Umma tace "Ohk, xaku fita da driver xai kai ki gidan kawata yanxu, tunda naga ke ba son taro kike ba ai" Jiddah ta d'an yi shiru, sai kuma a hankali tace "Umma ai yace xai dawo anjima ya daukeni" Umma tace "Ehh kafin ya dawo din, sai yaje can gidan ka ya daukeki, ki tafi da jakar kayanki kawai" Jiddah tace "Toh" Bayan mota Umma ta sa ta shiga ta ajiye mata jakarta a gefenta, sannan driver ya bar gidan bayan ta sanar masa inda xai kai ta, tafiyar kusan minti ashirin da wani abu suka yi suka isa gidan Hajiya Rukayya, Drivern yayi ma mai gadi maganan cewar yayi leading dinta har entrance din gidan, tana shiga cikin compound din mai gadin ya nuna mata direction da xata bi, ta makale jikin kofar ta kwankwasa a hankali, ta fi minti biyar tsaye sannan aka bude kofa, wata mata ce ta bude kofar ganinta tace "Ke ce bakuwar da Hajiya ta sanar kina xuwa?" Jiddah ta gyada mata kai kawai, Badiya ta amshi jakar hannunta tace "Toh sannu da xuwa, Bismillah" Bin bayanta Jiddah tayi, ta xauna parlor, Badiya ta shiga dakin yan matan Hajiya Rukayya ta ajiye mata jakarta. Karfe biyar saura Abuturrab ya isa gidan Umma, ya fi minti biyar cikin mota sanin da mutane gidan shi kuma ba iya shiga xai yi ba, daga karshe kawai Maman Abdallah da ya gani a compound ya aika ta kira masa Jiddah, ba a dau lkci ba sai ga ta, tace "Wllh yallabai Umma tace suna can gidansu amarya" Da mamaki ya dinga kallonta, can yace "Toh nagode" Tada motar yayi ya bar layin ya dau hanyar gidansu, bayan yayi parking a waje ya dau waya ya kira Siyama tana dagawa yace "Ki ce Jiddah ta fito" Tace "Yaya mu muna wajen make up fa, kuma har muka bar gidan bamu ga ta xo ba" ya d'an yi shiru, kafin ya katse wayar. Tunanin wanda xai kira ya dinga yi a ciki amma ya ga ba kowa kuma don ko hauka yake ya san baxai kira Ummi ba, d'an tsaki yyi ya tada motarsa ya bar wajen. Tun da Abuturrab suka isa wajen da ake dinner tare da Ahmad da sauran abokansu yake xuba ido yaga inda xai hango Jiddah a wajen amma bai ga alama ba, hakan bai wani damesa ba don dama xuwa dinner din ne baya son ta xo ya kaita can gidan Umma, tun sanda Aneesah ta kyallara ido ta gansa take masa zarya a wajen, barin yanda taga yayi wani kyau cikin fararen shaddan da duk abokan Ahmad suka saka, ita a dole sai ta ankarar da jama'a cewar saurayinta ne, Ko mayafi bata daura kan damammen doguwar rigar jikinta ba shi dai sai bin ta yake da kallo, wani abokin Ahmad dake side din Ahmad din Abuturrab ke ta kallo yana son tuna inda ya ta6a ganinsa, he looks familiar amma dai bai ce masa komai ba, karfe goma saura Aneesah ta xo ta samesa tana yauki tace "My captain wai xaka xo ka maida su Mummy gida yanxu" Ya d'an kalleta yace "Toh ai bani na taho da motata ba, ban ma san inda yake yanxu ba, nima abun hawa na samu ya kawo ni nan" Tace "Haba Captain, ko wajen daya daga abokanku baxa ka amshi mota ka maida su gida ba...." Ko rufe baki bata yi ba sai ga aunty ita ma ta sha wani ubansun lace tana goge xufan goshinta da handkicin hannunta tace "Aliyu ka tashi ka maida su Hajiya Safiyya gida" Bai ce mata komai ba, tace "Ko baka ji na ne?" Yace "Toh bari in nemi wanda makullin motata ke wajensa" Juyawa tayi ta bar wajen, ya kalli Aneesah da ta hade rai tana kallonsa, d'an murmushi yyi yace "Kema dai kinsan wasa nake, dole in nemo mota ko na waye in maida su" Yana fadin haka yayi patting shoulder din Umar dake side dinsa yace "Bani makullin motarka pls" Umar ya mika masa sannan ya mike yace "Kice su fito" Daga haka ya nufi hanyar fita daga hall din.... Karfe daya Abuturrab ya koma gidansa bayan sun maida duk bak'in da suka je dinner masaukinsu, ya fi minti goma xaune a parlornsa thinking of where Jiddah might be, daxu da ya maida Mum din Aneesah har gida ya shiga bai ga alamar tana nan ba, shi kuma ya kasa tambayar Ummi, akwai wasu bakin da still ya mayar can gidan Umma, can ma ya shiga bai ganta ba, bayan kuma ya tambayi Maimoon tace ai tana gidan Umma, mikewa yayi daga karshe ya wuce sama xuwa dakinsa don ya gaji sosai. Da asuba kiran sallah ya farkar da jiddah, ta mike xaune daga kan gadon da take tana kallon yarinyar dake kwance saman gado gefenta, tun xuwanta gidan jiya banda ita da Badiya bbu kowa a gidan har tayi bacci wajajen karfe goma saura, bandaki ta tafi ta dauro alwala ta fito sannan ta tada yarinyar da baxata wuceta ba, yarinyar ta mike xaune, ita kuma ta shimfida darduma ta fara sllh.... Karfe tara saura yarinyar da tayi wanka ta shirya cikin atamfa ta kalli Jiddah tana murmushi tace "Ya sunanki?" Jiddah tace "Jiddah" Yarinyar tace "Ni sunana Amina, mu je parlor mu gaida su Mama sun fito" Jiddah ta saka Hijab dinta ta bi bayan yarinyar suka fita parlor, yan mata biyu ne xaune parlon sai Hajiya Rukayya, wanda Jiddah na ganinta ta gane mahaifiyarsu ce don sun yi kama, Jiddah bata yarda ta xauna kan kujera ba ta gaida matar, ta amsa da fara'a tana tambayarta ta tashi lafiya, Jiddah ta sunkuyar da kanta, sauran yan matan ma sai kallon Jiddah suke, Wani ne ya shigo parlon daga waje waya kare kunnensa, ganin mahaifiyarsa a parlon ya katse wayar ya zauna yace "Ina kwana" Tace "Lafiya lau... Jiya kuma sai kayi wucewarka ka bar mu a event center" Yace "Mama ciwon kai wajen ke sa min, it's been long da na tsaya waje that's so noisy haka" Hajiya Rukayya tace "Toh Allah ya kyauta" Tun da ya shigo Jiddah ke kallonsa kamar taga wani mugun abu, Ganin xai kalli direction din da take ta dauke kanta da sauri gabanta na faduwa, Yace "Mama bakuwa ku ka yi?" Hajiya Rukayya tace "Ehh, ga breakfast dinka can a dining" Yace "Ohk" sannan ya mike ya tafi dining din, Mikewa Amina tayi ta tafi dauko ma ita da Jiddah breakfast don taga alamar yayyinta duk sun yi, kuma da ba don Jiddar ba tare xata je ta xauna su yi breakfast din da yayanta, gaba daya Jiddah ta kasa sakin jiki a parlon, lkci lkci take satan kallon hanyar dinning din, daga karshe dai ta mike xata wuce daki, Hajiya Rukayya tace "A daki xaki yi kumallon?" Ta d'an yi murmushi ta gyada kai ta wuce daki da sauri, dole dakin Amina ta kai masu Breakfast din. A ranan bayan an sauko juma'ah aka daura auren Ramlah da Ahmad... Abuturrab na tsaye daga bakin kofa a bedroom din Umma bayan sun gaisa yace "Tana gidan nan ne Umma?" Umma ta kallesa tace "Wa?" Jin bai ce komai ba tace "Wai Jiddah?" Yace "Eh" Tace "Ba a jima ba suka tafi can gidanku da Maman Abdallah" Bai kuma cewa komai ba, tace "Hajja kuka tace tun da ta xo baka je ka gaisheta ba" Yace "Ai ban je can gidan ba Umma, anjima da daddare xan shiga in gaisheta" Tace "Yauwa gwara kaje din da daddare dama ya fi, an kai maku abincin kuwa?" Yace "Ehh an kai" daga haka ya juya ya fita. Da yamma su Amina duk suka tafi gidan yinin Biki, Hajiya Rukayya kuma tun karfe goma dama ta bar gidan, gidan ya rage daga Jiddah sai Badiya, tana kitchen tare da Badiya tana tayata girkin dinner, wayar Badiya dake parlor ya fara ring, Badiya tace "Dauko min wayar Jiddah..." juyawa tayi ta fita xuwa parlor, dai dai nan kuma aka bude kofar parlon suka hada ido, sanye yake da farar shadda idonsa sanye da glasses, sosai gabanta ya fadi, ta sunkuyar da kanta tana kalle kallen inda xata ga wayar Badiya, kasa karasowa cikin parlon yyi, sbda rudewa ta ma rasa inda wayar yake ta juya xata koma kitchen din taji yace "Jiddah" juyowa tayi suka sake hada ido, tayi murmushin karfin hali tace "Ina yini?" Ya karaso cikin parlon yana ci gaba da kallonta da mamaki, bata jira me xai ce ba ta juya da sauri ta koma kitchen din. Har Hajiya Rukayya ta dawo wajajen magrib Jiddah bata sake yarda sun hadu da Yousuf ba, can daki ta shige taki fitowa through out, Hajiya Rukayya na shigowa gidan ta kira Yousuf a waya don baya nan, yana shigowa tace "Don Allah bakuwar nan xaka ajiye min gidansu Ahmad yanxu, Hajiya Ramlah tace ka kaita" Yousuf yace "Ohkk" Har mota su Amina suka raka Jiddah, shi da Yousuf na xaune cikin motar tasa, Jikin Jiddah yyi sanyi ganin shi xai maidata, hannu kawai ta daga ma kanninsa har suka fita compound, sai da suka d'an yi nisa taji yace "Dama ke yar uwar Ahmad ce?" Kai ta gyada masa kawai, ya d'an kalleta yyi murmushi yace "Har yanxu sai kice min baki da waya ko?" Ta gyada masa kai, yace "What if na baki tawa wayar?" Ta xaro ido tace "Sai in ce wa ya bani?" Yace "Ni" ta girgixa kai tace "Aa bana so" yace "Jiddahh" ta d'an kallesa suka hada ido, yace "Kin san wani abu?" Ta girgixa masa kai, yace "Tun da muka hadu dake a jirgi kullum nake addu'an Allah ya sa in sake arba da ke, sae gashi kin xo har cikin gidanmu, kinsan me yasa hakan ya faru?" Nan ma ta girgixa masa kai, yace "It is because i have good intention toward u..." Jiddah dai tayi shiru kamar ta gane me yace. And the rest of the ride was silent, yayi parking dai dai kofar gidansu Ahmad ya juya yana kallonta, yace "Tunda baxa ki amshi wayata ba, xan kiraki ta wayar Maimoon" Ita dai bata ce komai ba, ta bude motar ta sauka, ta bude baya ta dau jakan kayanta, Yousuf na kallonta yace "Sai na kira" Tace "Toh" sannan ta nufi gate, shi kuma yayi reverse.... Dama Umma Jiddah kawai take jira don har ta saka Hijab dinta tana parlor a xaune, Jiddah na shigowa kuwa ta saka driver ya kai su can gidansu Abuturrab, har sannan da akwai sauran yan biki a gidan duk da tun wajen shidda saura aka kai amarya, direct parlon Abban Abuturrab Umma ta nufa tare da Jiddah suka shiga da sallama, Abban Abuturrab da brothers dinsa ne a parlon sai Hajja dake xaune kan carpet, bayan ta xauna suka gaggaisa, ta gaida Hajja ma, Hajja tace "Ni dai tun jiya nake ta kallon ki Ramlah, ya aka yi kika amince kika narka uban kiba haka, to ai ba kyau, mu a masar da tuni an kai ki asibiti duk hankali a tashe, mu ba ma haka a can" Umma dai bata ce mata komai ba, Can ta kalli Jiddah da ta sunkuyar da kanta tun bayan gaida su Abba tace "Ita kuma wannan sadaka yallar fa?" Nan ma babu wanda ya ce mata komai, Abba ya dau waya ya kira Ummi ya sanar mata Umma ta iso, su xo tare da Aunty, Hajja tace "Ai masar tayi wallahi, ba ruwanmu da abinda bai shafemu ba, kowa ta kansa yake, shi yasa xuwa jibi nake son idan Allah ya kai mu in koma, nafi wayo a can..." Ummi ce ta shigo parlon tare da Aunty, tunda Jiddah taga Aunty gabanta ke faduwa, Brother din Abba dake gefensa yace "Ka kira Aliyun ne?" Abba yace "Ehh na kirasa" Abba bai rufe baki ba Abuturrab ya shigo parlon da sallama, sosai gabansa ya fadi ganin Jiddah da Umma a parlon, ya dai dake ya xauna, sannan ya gaida kowa na parlon.... Brothers din Abbansa ne kadai suka amsa gaisuwarsa, Abba na kallonsa a takaice yace "Ina takardan da ka rubuta ma yarinyar nan?" Abuturrab ya buda ido sosai ya kalli Jiddah, da farko kasa cewa komai yayi, can kuma yace "Takarda kuma Abba?" Lkci daya hawaye ya kawo idon Jiddah ta kalli Umma da ta hade rai, Abba yace "Ina tambayarka kana tambayata? Are u stupid?" Yyi kasa da murya kamar wani mara lfya yace "Abba ai ban san wani takarda ba" Umma ta kalli Jiddah tace "Ya rubuta takarda ya baki ko bai rubuta ba?" Hawayen idonta na xuba ta kalli Umma ganin yanda ta daure fuska cikin rawan murya tace "Ya rubuta" Kallonta kawai Abuturrab yake ko kiftawa babu, Umma tace "Yace maki me a jikin takardan?" Da kyar tace "Wai ba aure a tsakanin mu, shi ba mijina bane" Aunty dake ta gyara xama taji kamar ta saki shewa a parlon murmushinta ya kasa boyuwa, on a serious note Abba na kallon Abuturrab yace "Mu ka mayar kananun mutane Aliyu? Ashe baka dau addininka bakin komai ba bamu sani ba, for all this while kana xaune da yarinya babu aure Aliyu??" Da kyar Abuturrab yace "Abba wllh wllh ba saki na rubuta a takardan ba..." Hajja dai ta hangame baki tana bin kowa da kallo a parlon, Caraf Aunty ta amshe tace "Toh ai aikin banxa kenan, tunda duk ka bi ka sanar ka saketa aure kuma ai ya lalace, ko ka mance addininka ne? Ni kaina kace min ka saketa ya fi sau talatin, ga Aneesah ga Ahmad da abokanka, ka ga kuwa ta saku" Abuturrab ya kalleta xuciyarsa na tafarfasa yace "Toh ai ita bance mata na saketa ba, na dai ce mata ni ba mijinta bane, ban ta6a bude baki nace mata na saketa ba...." Mikewa Abba yayi ya tafi daki sai gashi ya fito.... Abuturrab ya dinga kallonsa xuciyarsa na bugawa. I just have to update today not to keep pple waiting, but I'm not feeling well.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Abba ya ajiye masa takarda da biro din hannunsa ya koma ya xauna yace "Tunda kana kokwanton auren da ake ce maka babu tsakaninku upon sanarwa da ka dinga yi ka saketa, to ni yanxu na umarce ka da ka kara wanda baxa kayi kokwanto ba a ranka" Kallonsa kawai Abuturrab ke yi kamar bai gane me yake nufi ba, Abba ya daka masa tsawa yace "C'mon my frnd ina sauraronka" Ya sauke idonsa a hankali yace "Toh ai Abba ni bance baxan xauna da ita ba, ban ta6a maku musun xama da ita ba, tuni na riga da na hakura...." Da karfi Aunty tace "Wllh karya kake munafuki... har ce min kayi kawai sbda Abbanka kake xaune da ita bayan ka saketa don kar ya samu labari yayi fushi da kai, kuma mu baxa mu xuba maka ido kuna xaman haram da yarinya ba, banda ma dai ni da na damu da lamarinka, ina ce ranan da na gano irin xaman da ku ke na xo na sanar gwaleni Abbanka yayi, to Alhmdlh ai yanxu tunda Hajiya Ramlah ce ta xo da batun da kanta" a kufule Hajja tace "Waye wannan dallah... Ya xa ki cika ma mutane kunne haka, ita uwar yaro ma ta ja bakinta tayi gumm kamar sabuwar kurma sae ke xaki dinga daga jijiyoyin wuya kina hak'i uwa dai kin hada wani abu da Aliyun, iyakarki fa matar ubansa, waye bai san auren cin amana ku ka yi da Usman din ba, daga dai ke da uwarki kuna fama da bakar talauci kuna tuyan masa da miyar taushe a daya daga gidajen hayana dake Tudun wada, shi kuma Usman na aikesa yaje ya fatattaki wani kato da yaki biyana haya kusan sati uku da karewar kudinsa, shkkn fa mata kika makale ma d'a na har da kullo masa yar wainar shinkafa a leda, to mu muka san abinda aka barbada a kai sai ga Usman ya birkice shi xai kara aure bayan ko shekara biyu da auren wannan Bafillatanar Hauwan bai yi ba, a takaice dai wllh tsallake maganata yayi ya aureki don na hanasa yaki ji ya bada toka a ido xai xageni, to ba dole in yafe masa ba tunda kowa dai yasan ku 'yan Benue ne, Mu dai babu abinda muka sani da ya wuce wannan, to yaushe ma xa a ga haka a Masar? Aa wllh basa haka...." Alhaji Umar yayi kasa da murya yace "Hajja ai ina ga ba wannan xancen muke yi a nan ba, duk ba shine ya kawo mu nan ba" a fusace Hajja tace "Toh don ba xancen ake ba sae in yarda ta gigita min jik'a, ni dai har gobe ina danasanin basu gidan hayata, daki daya ma fa suka kama suke rayuwa a ciki, kafin ma in basu dakin cewa suka yi gidan da suka baro watsi aka yi da kayansu bakin titi a unguwar mu'axu, gashi suka dinga ban wahala da kyar suke biyan kudin hayan a lkcn ma wllh.. to ni duk na wannan ba don Allah ma bai ce ayi tone tone ba, wanda kuma ya rufa ma d'an uwansa asiri Allah ma xai rufa masa asiri, amma ai an cuci Usman, to kuma ni ance min Aliyu ya auri yar hayi lkcn ina Masar, tsoro ya kamani na fita hayyacina na gigice da naji wannan xance sbda ni nasan ina ne hayi, kuma ni nasan mutanen cikinta, to sae gashi kabiru yace min ae suna xaune lafiya lau da matarsa, hakan yasa na saki raina duk da ban samu xuwa bikin ba, toh ynxu abinda ban gane ba wannan yar farar dake xaune ce yar hayin koko?" Umma tace "Ita ce" Hajja tace "Ikon Allah... toh kai Usman ya kake son kashe masu aure kamar kai ka halicci auren?" Alhaji Umar yace "Hajja babu wannan auren fa yanxu musulinci, don ya riga da ya saketa da bakinsa, sannan kuma ya saketa a rubuce, ni ba mijinki bane ae dai dai yake da na sake ki...." Hajja ta rike ha6a tace "Naga jaraba, a gabanka aka yi sakin kake wnn ciccijewan ko kawai karere, Sannan kana min gatsal gatsal idan shafa'atu ce xaka mata haka yau?" Abba yace "Don Allah Hajjaju kiyi shiru muyi abinda ya kawo mu nan, baki san komai a kan maganar nan da ake a nan ba, yaushe rabonki da kasar??" Hajja ta rungume hannu hade da ta6e baki tace "Nayi shiru, amma mu a masar wa xai yi haka? Wllh ba a haka, ayi aure kuma a dawo ana cewa ya mutu bai mutu ba" Ta gefen ido Abuturrab ya kalli Jiddah da ta kasa dago kanta, Aunty dai ta wani sha kunu a parlon tun bayan xancen Hajja a kanta, ita dai Ummi kallonsu kawai take ba um ba um um, a fusace Abba yace "U are wasting our time Aliyu, saki me hujja nake so kayi ynxu tunda duk wanda kayi a baya baka aminta da su ba..." Ya dago kansa yana kallon Abbansa yace "Abba ni nasan na aureta sannan ina xaune tare da ita saboda inyi biyayya gareka, bayan hakan babu wani abu kuma...." Abba ya katse sa yace "Toh an dauke maka wannan biyayyan, write d divorce now, sai ka tashi ka tafi Allah ya baka ladan taimako, ae kayi me wuyan tunda ka rabota da tsananin da take ciki" Abuturrab bai kuma cewa komai ba, bayan few seconds yace "Yanxu sakin xan rubuta mata?" Abba yace "Ehh, baxa ka mayar da mu kananun yara ba mu xuba maka ido, har yau mun rasa gane xaman me ku ke da yarinya" Abuturrab ya sunkuyar da kansa ya fara rubutu a takardan, d'aga kai Jiddah tayi tana kallonsa, ya gama rubutun ya mike da ladabi ya mika ma Abba, Abba ya amsa yana duba content din takardan, Abba yace "Good, Allah ya maka albarka, ya baka ladan taimako, daga yanxu kuma babu ruwanka da duk wani harka da ya shafeta, xa mu yi mata komai in sha Allah, kai ma kuma kayi iya naka kokarin don ta dalilinka duk muka santa, Allah ya maka albarka...." Abuturrab ya amsa da "Ameen" Sannan ya juya ya fita daga parlon jiddah ta bi sa da kallo, Abba ya nuna ma brothers dinsa biyu takardan, Alhaji Umar yace "To maa sha Allah, kaga yanxu babu wanda xai ci gaba da kokwanton xaman da suke, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi, shi kuma Allah ya saka masa ya basa ladan taimakonsa, ku kuma Allah ya baku ikon riketa da gaskiya" Aunty da taji jikinta na wani tsumma don farin ciki gaba daya ta mance abinda Hajja tayi mata sae jiran takardan take ya xo garesu, ai ko ana miko mata bayan ta karanta tayi wani murmushi ta mika ma Umma, Umma ma ta mika ma Ummi bayan ta karanta, Hajja tace "Amma na tsorata da lamarin Aliyu, Kunga da yana sonta da gaske ai kuka xai sakar mana a nan yace shi baxai saketa ba, amma almurin kamar jira yake gashi ya cike takarda da rubutu, aa gaskiya ba sonta yake ba, ku duba fa babu wani gardaman a xo a gani ya rubuta takardan, Lahh wanne mutum a masar, to amma ai shkkn sae a bani ita mu tafi Bauchi don kwana biyar xanyi a can kafin in koma Masar, idan ma kunga xaku iya biya mata jirgi kawai sai mu tafi tare, ai d'a na kowa ne bawa sai mai shi..." Umma ta kalleta da sauri tace "Hajja karatu xa a sata ai" Wani kallo Hajja ta watsa mata tace "Shi kuma masar din duk jahilae ne ba a karatu.... Banda neman magana ina ruwanki Ramlah, ni fa da d'a na nake kika tsomo baki, ko Ahmad ne ya tsintota a hayi?" Ta gefen ido Ummi ke kallon Hajja, Abba yace "Dama haka ake tafiya Masar din Hajja, ina laifin ma kice idan kin tafi a turo ta?" Hajja tace "Kai ba ruwana ni ku rabu dani, xa a Wani min caaa, dangin uwa ko na uba, meye hadina da ita banda Aliyu da ya aurota a gantale ya saketa kuma a gantale, kuma ma wasa nake, haka kawai inje in daura masu nauyi nima da ya ake bani yar gurasar da ake ban balle na tafi da wata?" Mikewa tayi tace "Banda Najeriya ina ake aure a gantale ayi saki a gantale, Hauwa taho ki bani sakon da na baki" Tana kai wa nan ta fita, Ummi ta mike ta bi bayanta, Aunty ta bi ta da harara, Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Alhaji xan tafi da Jiddah ta koma gidana ta fara karatu" Caraf Aunty ta amshe tace "Me xai hana tayi a nan din, ga dai sa'aninta su Aisha" Abba yace "Da nan din da can ai duk daya ne, Allah dai ya bata ilimi mai amfani" Ko kadan Aunty bata ji dadin haka da Abba yace ba, Umma tace "Toh nagode Alhaji, Allah ya tayani riko" Duk suka amsa mata da "Ameen" amma banda Aunty da ranta ya baci, can dai tace "Amma ai xata dinga xuwa nan din ko" Umma tace "Aa me xai hana kuwa" Umma na fadin haka ta mike tana kallon Jiddah tace "Mu je Jiddah" Jiddah ta mike a hankali ta bi bayanta, Aunty ta bi ta da kallon tsana, shi kam Abba tausayinta kawai yake ji, banda rashin gata ya xa ayi hakan ya faru gareta ma. Bangaren Ummi Umma ta kai ta, Ummi na xaune parlonta da Hajja dake mata magana kasa kasa, amma ganin Umma sai tayi shiru, Umma tace "Toh yaya mun tafi sai da safe" Ummi tace "Baxa ku yi isha ba?" Umma tace "Eh to bari inyi" Daga haka ta karasa bedroom din yayarta, Jiddaj dai na rakube jikin kujera, Ummi ta kalleta tace "Kije kiyi sallan ke ma" Mikewa Jiddah tayi ta fita, Hajja ta tabe baki tace "Toh ai gwara ma da aka kashe wannan auren don ai Aliyu d'an usuli ne, ita kuma bamu san yaya ba" Ummi tace "Ai babu wanda bashi da usuli Hajja" Hajja tace "Aa Hafsat dai bata da shi, an rasa gane ko kwatakwali ce har yau, duk da tace uwarta yar Benue ce" Ummi dai bata ce komai ba, Hajja tace "Shi yasa gashi duk ta amshe gida tayi bake bake, komai sai inji Usman yace Hafsa, to wacece kuma Hafsa, dama Hadiza ta bani labarin irin xaman da ku ke yarda ce kawai ban yi ba, gashi duk ta rufe maki baki ta amshe gida, wa ya sani ko ma har da ya yanki? Tunda na xo naga take takenta komai sai ace sai ita, to a kan me?" Ummi tace "Aa Hajja kowa ai da matsayinsa a gidan" Hajja tace "Toh kunga lalacewa ko? Wani matsayi matar da ta kwace maki miji ta karfi, me yasa kike abu sakwa sakwa kamar warce aka ce ma je ki kya gani Hauwa, komai fa na bikin nan naga sai dai ace Hafsat to wacece kuma Hafsat, gashi ana maganan tabargaxan da yaro yayi mata tayi bake bake a kan xancen kamar d'an ta, to ni tunda na xo ma ba sau daya Salem ya shigo gaisheni ba, duk sun tsotsa a nono wllh, dubi fa Aisha kamar yar karuwai Allah na tuba, to ba dai komai tunda duk jikokina ne, amma idan xaki tashi tsaye ki amshi gidanki ki tashi" Fitowar Umma yasa Hajja tayi shiru, Umma tace "Toh sai da safe Hajja, yaya sai mun yi waya" Hajja tace "Toh Allah ya ba yara xaman lafiya ya kauda fitina amma ki dai je asibiti kiga kibar ta mecece kika narka haka kinji" Umma bata tankata ba har ta fita, Hajja tace "Toh sai da safe" Sai da Jiddah ta sake shigowa tayi ma Ummi da Hajja sai da safe sannan suka bar gidan tare da Umma, har driver ya maida su gida Jiddah bata cewa komai, duk tayi sanyi sosai, ta rasa ko farin ciki take ko bakin ciki, Wajen karfe tara Umma ta xaunar da ita a dakinsu Maimoon tace "Kina ji na Jiddah?" Jiddah ta daga kai ta kalleta, Umma tace "Kin dai ga yanda abubuwa suka kasance, ni nasan Abuturrab bai da niyyar cutar dake a ransa, kuma har abada ina son ki daukesa da girma da mutunci don ya maki abinda ba kowa xai iya maki ba a rayuwa, duk abinda xaki xama a rayuwa nan gaba Allah ne ya tabbatar da hakan amma Abuturrab ne sanadi, ina son kuma ki maida hankalinki kiyi karatunki, kin san wacece ke kinsan daga inda kika fito" Hawaye ne ya shiga xarya idon Jiddah tana kallon Umma, Umma tace "Ni kuma ina fatan Allah ya bani ikon yi maki duk abinda ya kamata a rayuwarki Jiddah" Cikin rawar murya tace "Toh Umma baxan sake ganinsa ba kenan?" Da mamaki Umma tace "Don me baxa ki gansa ba, in dai Allah ya kawosa gidan nan ai xaki gansa, sannan xaki dinga yawan xuwa gida Ummi, idan baku hadu a nan ba xaku hadu a can, balle ma nace tsakaninki da shi kawai girmamawa ki daukesa kawai a matsayin babban wan ki, nasan shi ma a matsayin kanwarsa xai daukeki" Jiddah ta share hawayen idonta a hankali tace "Toh Umma nagode" Umma ta sakar mata murmushi, har ranta taji tana son Jiddah tana kuma son inganta rayuwarta, Umma tace "Gobe da safe sai mu je can gidan a kwaso duk wani abu naki" Jiddah ta gyada mata kai kawai, Umma ta mike tace "Toh sai da safe" Daga haka ta nufi kofa Jiddah ta bi ta da kallo wasu hawayen na kawowa idonta, Umma na fita Maimoon ta shigo dakin. Washegari misalin karfe Goma Umma ta kira Abuturrab, miss calls tayi masa kusan uku kafin ya daga, bata amsa gaisuwan da yake mata ba tace "Kana gidanka ne?" Yace "Ina nan" Umma tace "Ohk i am coming now" Bai ce komai ba ta katse wayar, tare driver ya kai su gidan Abuturrab da Jiddah da Maimoon da safiyya, mai gadi ya bude masu gate driver ya shiga da motar cikin compound, Umma ta sauka motar sannan su Jiddah, Hijab ne har kasa jikinta, suka bi bayan Umma xuwa entrance din parlon, a bude suka tarda parlon, yana kwance saman doguwar kujera da jallabiya, suna hada ido Jiddah tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na bugawa da karfi, sanye yake da jallabiya ya mike xaune a hankali yace "Ina kwana Umma?" Tace "Lafiya lau, ya gajiyan jiya?" Yace "Alhmdlh" Maimoon ta gaishesa ya amsa, Jiddah ma tace "Ina kwana?" Sai dai taki yarda ta kallesa, bai amsa ba ita dai ta xauna kasa kusa da kujeran da Umma ta xauna, Umma tace "Jiddah xata debi kayanta na nan ne" Ba tare da ya kalli Umma ba yace "Ohk" Umma ta mike tana kallon Jiddah tace "Mu je" Mikewa Jiddah tayi ta nufi stairs Umma na biye da ita Maimoon ma ta bi bayansu, da ido Abuturrab ya bi su har suka haura sama, Kaf sai da Umma ta kwashe duk abubuwan Jiddah dake dakin, Maimoon ce ke kai wa booth din mota, Ita dai Jiddah na tsaye jikin kofa sai kallonta take, ta rasa dalilin da yasa taji tana son tayi kuka, Umma ta mika mata babban ledan da ta hada duk abubuwan gaban madubi a ciki tace "Ki kai wannan" Jiddah ta karasa ta amsa ta nufi kofa ta fita, a stairs suka hadu da Maimoon, Maimoon tace "Kawo in kai toh" Jiddah ta kirkiri murmushi tace "Xan kai" Maimoon ta shiga dakin ita kuma fita, satan kallon parlon ta dinga yi taga baya nan, ta fita balcony, sosai gabanta ya fadi da ta gansa a xaune kan kujera yana danna wayarsa. Xata sauka stairs din balcony din taji yace "Toh ni dake wa yyi lose?" Ta juya tana kallonsa don bata gane me yace ba, yayi wani murmushi ya mike, speaking calmly yace "Kema kinsan wllh idan ba kaddara ba babu abinda xai hadani dake a rayuwa balle har in aureki bisa kuskure, aurenki da ni babban kuskure ne wanda nayi sbda in taimaki rayuwarki.. banda haka ai ni nafi karfin ki, komai da ya faru ya faru ne sbda haka Allah ubangiji ya tsara, duk da fin ki komai da nayi haka na hakura na xauna same roof dake sbda biyayya da kuma xuciyar musulinci, amma wai har ke xaki je ki sanar ma iyayena na sakeki? Toh yanxu da na maki sakin me hujja akwai wani abu da xai ragu a rayuwata ko kuma wani asara xan yi?" Ita dai kallonsa kawai take ko kiftawa babu, yayi wani murmushin kuma yace "Toh na maki duk abinda na maki saboda Allah ba don ki nuna kin san ni wataran ba, kai ni ko a hanya kika gan ni kar ki ta6a nuna kin ma san ni don kunya hakan xai bani, kiyi wucewarki inyi wucewata, na kuma fi kowa farin ciki da murnan xuwa karshen wannan al'amarin, i am now free like every other...." Jiddah dai kallonsa kawai take bbu ko kiftawa, ganin ya koma ya xauna cikin sanyin murya tace "Toh nagode" Daga haka ta juya ta kai ledan mota... Tare suka fito gidan da Umma bayan duk an kai komai mota, Har sannan yana xaune balcony, Umma tace "Toh sai anjima, yaushe xaka koma aikin" Yace "Anjima in sha Allah" Tace "Toh Allah ya tsare" Daga haka ta nufi mota, Maimoon tace "Sai anjima yaya" Yace "Ohk" Sai da Jiddah ta sauka balcony ta d'an kallesa tace "Sai anjima...." *Rumor Creators how market? A masar dai ba a haka idan xaku gyara ku gyara, ku kuma masu karanta na bati da kuka fi kowa xakalkalewa a xo a biya bashi dai ko xa a samu nutsuwa, my fans dat wished me speed recovery ina godiya Allah ya saka da alkhairi sbda ku nace let me manage and give this little update na karfin hali, nagode sosai, snn abinda ke ci mun tuwo a kwarya shine yanda masu karantawa a free suka fi kowa bada hakuri, wllh duk sun cika min inbox, don Allah bakwa jin kunya ne, baka biya abu ba ka dage sai an ci gaba, tsaf ina da saved number din duk wanda yayi subscription din littafin nan ku ji in gaya maku* 🙄 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Mîkyããj_Sããdy Beauty Soap* *Hy my beautiful people ina gaisuwa🙋🏻‍♀️ku karka'de kunnuwanku da kyau ku ji💃🏻ina mai sanar muku da cewa akwai gara6asa me kyau ta musamman ga wanda suka saba sayen sabulunmu da ma wanda zasu fara saya🥰, akwai ragin kaso 20% bisa dari 100% ga wanda suka saba saye, sannan akwai ragin 10% bisa ga masu sha'awar fara saye🥰, akwai farashi mai sauki ga 'yan sari, me yapi wannan dadi kam🤔ki sayi guda 4 kanana a baki kyautar daya, ki sayi guda uku manya a baki kyautar karami daya, ki sayi bucket biyu a baki kyautar babban rubber daya😍 kema da kike da burin saya ku'dinki bai kai ba😰to ga naki, ki kawo customers uku ki karbi naki kyautar Sabulun😍😍* *Kawata 'yar 'kwalisa me kike jira,ita mace fa kullum cikim yin ado da 'kãwa take😍 ya kamata ki yunkuro wajen ganin kin rabu da wannan kurajen da tabo tabon fuskan nan haka🥺, kinga kema sai a saka ki a layin masu 'kwalisa da bajakolin ado💃🏻😍uwar gida a daure ayi gyaran jiki, sbd karbar goron a wajen me gida🥰,, ina amaren bayan sallah ku pito ku sayi naku Sabulun kuje kuyi ta wanaka hmmm 😍kamshi kawai zaku yi tayi kaca kaca😍😍, laushin fata Baja baja😃😂😂a yunkuro azo a karbi kayan gyaran jiki tare da sabulun gyaran fata a wurin _Mîkyããj_Sããdy_🥰* *Duk wanda suka gwada Sabulun mu sun san babu 'karanta a ciki🥰in dai fannin gyaran jiki ne to sabulunmu shine amsarku,, shi ke mai da fata ta zama babu Pimples, Acne, Spot, Stretch Mark, da Duk wata matsala da ta shafi fata,, akwai lightening, nd glowing😍* _*In kina son jikinki yai su6ul da shi, fata tai santsi da sul6i, ki yi haske me aji, 'kamshi kaca kaca ko ta Ina, ki ta fresh abunki hankali kwance ki zama Wankan madara yauqin zuma😍💃🏻Anty madam😃To ki mallaki 3d (Extra Whitening Soap, Ko da kudinki sai da rabonki hajiyata)💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻*_ *Akwai hadin:* *Mai da tsohuwa yarinya* *Uwargida ta koma amarya* *Amarya ta koma tamkar 'yanmata* *'Yan mata su koma 'yan dagwai²* _Ga masu bu'kata sai su tuntu6emu ta kafar sadarwa kamar haka;_ _Call/WhatsApp:08061570778_ _IG@mik_yaaj_saady_ Bayan sati biyu Jiddah na xaune dinning area ita kadai bayan magrib, Hijab ne har kasa jikinta, Huraira kuma na kitchen tana wanke wanke, gaba daya hankalinta na kan takardan gabanta taji an danna bell, mikewa tayi ta nufi kofar ta bude, ta koma baya tana kallonsa tace "Ina yini" Da murmushi yace "Lafiya lau Jiddah" ta juya ta koma parlon ya karaso ya xauna, tace "Ya Aunty Ramlah?" Yace "Tana gaisheku, Umma na daki ne?" Tace "Ehh" yace "Tou xauna mana" d'an murmushi tayi ta xauna edge din kujera yace "Kin fara karatu koh?" Tace "Eh" yace "Amma ki fada min gaskiya, kina ganewa?" Ta gyada masa kai, yace "Aa bude baki ki min magana" Sunkuyar da kai tayi har sannan tana murmushi tace "Ina ganewa" Yace "Toh wani rana da wani rana ku ke karatun?" Tace "Ranan litinin xuwa juma'ah" Yace "Asabar da lahadi fa?" Tace "Islamiyya muke xuwa tare da su Maimuna" Yace "Toh me da me ake koya maki litinin xuwa Juma'ahn?" Tace "Karfe tara na safiya take xuwa mu yi boko xuwa karfe biyu, sai kuma Islamiyya karfe uku xuwa shidda" Yace "Duk ita ke maki bokon da Islamiyya?" Ta girgixa kai tace "Aa wata ce daban take xuwa karfe uku" Yace "Maa sha Allah, kawo takardun naki in ga" Mikewa tayi ta nufi dining ya bi ta da kallo ta dauko jakar da duk litattafanta ke ciki ta dau har da na kan dining table sannan ta kai masa, ya amsa yana dubu abubuwan da suka yi na sati biyu, ita dai tana xaune tana wasa da fingers dinta, ya daga kai ya kalleta yace "Anya ke da kanki kike aikin nan da malama ke baki?" Tayi murmushi tace "Ni ce nake yi ka tambayi Maimuna" Yace "Maa sha Allah, ki dinga maida hankali haka kinji?" Tace "Toh" Ya dau wayarsa dake ring, ta jira har ya gama wayar ya ajiye sannan tace "Aliyu fa?" Daga kai yayi ya kalleta, ta sauke idonta yace "Waye Aliyu?" Jin bata ce komai ba yace "Ohh captain wai?" Still bata ce komai ba, yace "Yana kano, mun yi sati biyu bamu hadu ba, kuma bana jin ya xo weekend" Tace "Toh" Umma ce ta shigo parlon ganin Ahmad tace "Yaushe ka shigo?" Yace "Not too long" Ta karaso ta xauna yace "Ina yini Umma" Tace "Lafiya lau, yau ma baka xo da Ramlan ba?" Yace "Ehh na barta da su Aisha ne sun je can gidan" Umma tace "Ohk" kallon Jiddah tayi tace "Har kin gama karatun?" Tace "Aa ina kan yi" Tana fadin haka ta mike ta isa gun Ahmad ta kwashi duk takardunta ta wuce daki, Ahmad yace "Cewa nayi ta kawo in ga performance dinta and naga she is really trying" Umma tace "Gaskiya kam, she isn't dull kawai dai karatun ne bata samu ba, amma in sha Allah nan da few months a yanda naga take da hazaka she might catch up with her mate, tana da kwakwalwa kam maa sha Allah" Ahmad yace "Toh Allah ya sa hakan, sai ayi enrolling dinta jss3 ko?" Umma tace "Ehh" Ya shafa kansa yace "Umma daxu Yousuf ya kirani..." Umma tace "Ya aka yi?" Ahmad ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Wai a kan Jiddah..." Murmushi Umma tayi tace "Ni dai nasan ba haka nan yake xuwa gidan nan frequently ba da dalili, toh maa sha Allah..." Ahmad yace "But Umma ai bata bukatar wannan yanxu, she need to concentrate fully on her studies" Umma tace "Toh ai sai ka jira in gama magana ko... ni baxan hanasa alaka da ita ba, sai dai shigo da batun soyayya gareta yanxu isn't necessary, he should wait a little...." Ahmad dai bai ce komai ba. Aunty ce xaune gefen gadonta waya kare kunnenta tayi shiru fuskar nan nata a daure, can ta mike tace "Haka yace maki?" Daga daya bangaren Aneesah tace "Wlh Aunty" Aunty tace "Toh kyaleni da d'an iskan, nasan maganinsa...." Aneesah tace "Ni fa wllh Aunty yau kusan wata daya kenan na ma kasa gane kan relationship din nan namu" Aunty tace "Daina kiranki yayi?" Tace "Toh ai dama tun farko ba kira yake ba sai in ni na kira ya bi miss call, yanxu kuma ko na kira din ma sai sanda ya ga dama yake kira, sai yace aiki yayi yawa..." Aunty tayi shiru tana sauraronta, sai kuma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Amma kuna dai maganan still koh?" Tace "Aa muna magana, kawai sabon miskilanci da jiji da kai ya karo... Sai yayi ta cewa shi baya son damuwa, shi baya jin dadi, shi he want to sort somethings bothering him, shi yana son break, shi he wants to be alone for sometimes, haka dai wllh... Kamar baya son magana da ni" Aunty dake ta jin ta, tace "Amma ya siya maki abinda nace kice ya siya maki ko bai siya ba?" Tace "Aa ya tura min kudin har da kari ma" Aunty tace "Toh shkkn, xan kiraki xuwa anjima, ki kwantar da hankalinki" Tana kai wa nan ta katse wayar tayi dialing number Abuturrab, sai da ya kusa yankewa ya daga, yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Wani laifin muka maka Aliyu yau kusan sati uku babu kai babu labarin ka?" Yace "Aa aiki ne yayi yawa yanxu..." tace "An sake employing dinka a wani airline din ne bayan wanda kake aiki?" D'an murmushi kawai yyi bai bata amsa ba, tace "Atoh gwara ai in ji, kuma ai kana shigowa kadunan, xuwa gida ne kawai baka yi" yace "Aa bana shigowa, amma xan shigo friday din nan in sha Allah" Tace "Toh ina saurarenka" Daga haka ta katse wayar. Hijab Jiddah ta dauka xata saka bayan ta gama shiryawa Maimoon ta hade rai tace "Meye hka kuma, ba ga mayafi na ajiye maki ba" Jiddah ta xaro ido tace "To ae an hanani" Maimoon tace "Wa ya hanaki?" Ta sake xaro ido sae kuma tace "Tou bari in sa" daukan mayafin tayi ta yafa, Maimoon ta washe baki tace "Waoww kinga yanda kika yi kyau kuwa" Murmushi kawai Jiddah tayi, suka fita xuwa dakin Umma, Umma tace "Kuna kai sakon ku dawo, ba sai na gaya maku kuna da Islamiyya karfe biyu ba" Maimoon ta marairaice tace "Yau dai kawai Umma, Sis Ramlah fa na can gidan" Umma tace "Toh ku bani xan ba Driver ya kai idan ya dawo" Maimoon ta xaro ido tace "Aa wllh ynxu xa mu dawo Umma" Kudin mota ta basu suka fita gidan, Jiddah na rike da ledan sakon da Umma ta bada su kai ma Hajja, karfe sha daya da rabi suka isa gidan, Maimoon tayi sallama bakin kofa tayi knocking sannan ta tura, Jiddah ta bi bayanta, babu kowa a parlon suka nufi part din Ummi, Ummi ta fito daga bedroom dinta jin sallama, ganinsu tace "Aa sannunku da xuwa" duk suka xauna suka gaisheta ta amsa da fara'a tace "Ku kadai?" Maimoon tace "Eh Umma ce ta aiko mu gun Hajja" Ummi tace "Ohk, ya karatu Jiddah" Jiddah ta kalleta ta d'an yi murmushi tace "Alhamdulillah" Ummi tace "Toh maa sha Allah, Allah ya taimaka" Maimoon tace "Ramlah ta koma ne Ummi?" Ummi tace "Aa tana ciki tana bacci" Maimoon tace "Toh bari mu kai ma Hajja mu dawo" Ummi tace "Ohk" mikewa tayi jiddah ma ta tashi suka fita daga parlon, dakin da Hajja ke sauka idan tana garin Maimoon ta nufa Jiddah na biye da ita, Maimoon tayi sallama bakin kofar sannan ta bude, Hajja ta daga kai tana amsa sallaman, karasawa ciki Maimoon tayi ta duka tace "Ina kwana Hajja" bata jira ta amsa ba ta kalli Abuturrab dake xaune dakin yana kallonsu daga sama har kasa ta cikin glass din idonsa, ta sunkuyar da kanta tace "Ina kwana yaya?" Yace "Me yasa baki ajiye mayafin a gida kin fito haka ba?" Maimoon ta hau gyara mayafin jikinta tana murmushi, Jiddah dai kanta na kasa ta durkusa ita ma ta gaida Hajja, sannan ta d'an kallesa taga wayarsa yake dannawa tace "Ina kwana" Ya kara wayar a kunne ya mike ya nufi kofa, Hajja ta saki baki tana kallonsa har ya fita, can ta kalli Jiddah tace "Ji ruba66e, toh ke idan ba dai neman wajen xama kike ba meye na gaishesa bayan iyayensa sun sa ya sakeki babu ko dar ya cike takarda ya mika maki, ai babu abinda kika hada da shi kuma yanxu, toh ga dai shi ya gwaleki, tun jiya fa na samu labarin dawowar almurin amma kun ga sai yanxu ya shigo gaidani yana shan kamshi ya wani sha uban gilashi kamar sabon makaho, Aa bak'in halinsa ya fi karfinsa gaskiya, alhalin sbda shi nake xaune har yau a gidan nan ban koma masar ba, to Hafsah ta ce min sati me xuwa xa a kai kudi gidan yarinyar da yake so da aure amma in ja bakina inyi shiru tunda ba a gaya min ba tukun, shine yasa nake ta xaune nan Allah" Maimoon dai sai murmushi take, Hajja tace "Toh aiko ku Ramlan tayi?" Maimoon ta ajiye mata ledan kusa da ita tace "Ehh tace mu kawo maki wannan" Hajja ta leka cikin ledan tace "Ahh da kyau, baiwar Allah nace mata gobe xan tafi shine ta bada tsaraba a kawo min, to tafiya ai ta lalace tunda auren Aliyu ya tunkaro, yanxu shigowarsa nake tambayarsa shi ma ya tabbatar min da haka ne" Jiddah dai sai kallon Hajja take, Maimoon tace "Toh Allah ya kai mu lafiya" Hajja tace "Ameen, ita ma Ramlah gata can ta xo tun shekaranjiya, kilan mijin baya nan, amma da kyar idan ba ciki ne da ita ba, kai cikin ne ma wllh, sai wani salalo salalo take" Maimoon ta kalli wayarta dake ring ta mike tace "Xa mu koma Hajja, sbda muna da Islamiyya karfe biyu" Hajja tace "Toh ai shkkn, anjima xan sa Aliyu ya kawoni in mata godiya idan ya ga dama kenan, kabu kabu fa yake amma jin kansa yake kamar me wani sana'ar arxiki baya ganin kowa da gashi, ga d'an banxan girman kai, ba ga masu kabu kabun ba muna ganinsu a tashar mota, ga yan acaba suma ai duk kabu kabun ce, to kuma waye shi Allah na tuba" Su dai basu ce mata komai ba suka fita dakin, sai a snn Maimoon ta mika ma Jiddah wayar tace "Yousuf" Jiddah ta amsa ta daga sannan ta kai kunne, murya kasa kasa Maimoon tace "Don Allah kice ya xo ya daukemu basu da nisa sosai daga nan" Tana fadin haka ta wuce bangaren Ummi, Jiddah ta nufi parlor, cikin sanyin muryarta tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau, me Maimoon take rada maki?" Murmushi tayi ta xauna saman kujera tace "Aa babu komai, ya ciwon kan yayi sauki?" Yace "Alhmdlh, ya su Umma?" Tace "Umma tana gida" Yace "Ku kuna ina?" Tace "Umma ta aiko mu gidansu Aunty Ramlah" Yace "Ohk, yaushe xaku koma gida?" Tace "Karfe biyu xa mu tafi Islamiyya" Yace "Baxa ku dade ba kenan?" Tace "Eh" yace "Toh in xo in maidaku gida?" Ta d'an yi shiru, yace "Kin fa ce kin daina taurin kai" D'an murmushin tayi ta kwantar da kanta jikin kujera dai dai nan suka yi ido hudu da Abuturrab dake xaune dinning area din parlon da laptop gabansa, wani faduwa taji gabanta yayi, Yousuf yace "Kinyi shiru" Ta dago kanta tace "Toh sai ka xo" Yace "Good, in few minutes time xan iso yanxu in sha Allah" Cikin sanyin murya tace "Toh" Katse wayar yayi, ta dinga kallon screen din, can ta saci kallon Abuturrab taga laptop dinsa yake dannawa, ta mike ta wuce part din Ummi, ya bi ta da ido. Karfe daya saura Yousuf ya iso kofar gidansu Abuturrab, ganin xa a tada sallah ya sauka ya shiga masallacin kofar gidan, bayan an idar ya kira number Maimoon, Maimoon ta mika ma Jiddah, Jiddah na kai wa kunne yace "Ina waje ku fito" Jiddah tace "Toh" Katse wayar yayi, suka yi ma Ummi sallama a bedroom dinta sannan suka fita, gaban Maimoon ya fadi ganin Abuturrab da ya fito daga masallaci, amma taki yarda su hada ido, Jiddah kam bata ma gansa ba ta kalli Maimoon tace "Ke da kike son ya xo ya daukemu ai ke xaki yi jagora" Maimoon tace "Don Allah ke dai mu je" Jiddah ta fara tafiya Maimoon na biye da ita, ta bude front seat ta shiga, Maimoon ta shiga baya, sai a sannan Jiddah ta ga Abuturrab da ya tsaya yana kallonsu, Yousuf da ya gansa shi ma yace "Ba yayan nan naku bane wancan" Maimoon ta kirki murmushin karfin hali tace "Ehh, kaje gu gaisa ya Yousuf sai kace masa Umma ce tace ka xo ka daukemu" Ta madubi ya kalleta ta kara kirkiran murmushi, Jiddah dai taki yarda ta sake kallon wajen motar, Yousuf ya bude motar ya sauka ya nufi gun Abuturrab da ya kara waya a kunne roaming about the gate, hannu ya mika masa hade da sallama yana kallonsa, Abuturrab yyi stretching nasa hannun, nan suka gaisa sannan yousuf ya juya ya koma gun motarsa, yana shiga motar Maimoon da duk hankalinta ya tashi tace "Kace masa Umma ce tace ka xo ka daukemu?" Yousuf yace "He don't have any business with that" Maimoon bata kuma cewa komai ba, ya tada motarsa suka bar anguwar. Hansai ce xaune da aminiyarta Zulai gaban wani katon mutumi da babu riga jikinsa, Hansai duk ta baxa kunnuwa da idanuwa tana jiran jin abinda xai ce bayan ya gama dube dubensa, Mutumin ya kalleta da idanuwansa da aka lafta ma uban kwalli yana girgixa kai cikin katon muryarsa yace "Babu wani aure a kan yarinya, amma tana can cikin kwanciyar hankali da daula... Bata da wani matsala a rayuwa, ba abinda ta rasa..." Hansai ta sharce wani bakin xufa a goshinta tace "Toh Malam babu abinda xa ayi da xai sa hankalinta ya karkato ta dawo gida, idan ya so sai a maida min Bibalo can, wllh Malam ina fama da bakar talauci yanxu, jarin babu shi babu dalilinsa kamar dai kar ta bar wajen yarinyar, ga basussukan jama'a a kaina suna min tonon asiri har na fara tunanin in siyar da d'an gidan da muke ciki in biya bashi sai mu kama haya da sauran, in sake jan wani jari, to amma gidan fa duk ya ru6e, wa xai siya da mutunci" Mutumin wanda da alama ya gaji da surutunta yace "Ki fadi abinda kike so ayi a takaice" Hansai ta gyara xama tayi kasa da murya tace "Kaga Malam so nake kayi duk abinda xai dawo min da ita duk inda take, ta dawo wajena ni ban k'i ko karuwanci ma ta xo ta min ba mu samu na rufa ma kai asiri, nasan dai yanxu karya ne ace bata san maxa ba, dama gata da kyau ga farin jini wllh kasuwa xa mu yi sosai" Zulai sai gyada kai take, Mutumin yace "An gama, dubu hamsin kudin aikin ki" Zulai ta dafe kirji tace "Dubu ashirin fa Malam, ina nagansa? Bani da shi bani da dalilinsa wllh, ko dubi daya na kaina bana magani yanxu" Yace "Toh ku tashi ku tafi duk ranan da ku ka shirya ku dawo" Xata yi magana cikin tsawa yace "Ku fita nace sai kun shirya" Da sauri suka mike suka fita a d'an dakin, Hansai ta fashe da kuka tace "Yanxu ya xanyi Zulai, kema kinsan bani da ko dubu biyu na kaina wllh, duk na siyar da kayan dakina babu komai balle in dauka in siyar" Zulai tace "Daga karshe dai gidan nan kawai xaki siyar in dai bukata xai biya, in har Jiddah ta dawo ai sai kin kera wanda ya fi wannan a cikin gari, dama ba sai an 6ata ake gyarawa ba, kawai mu je a sa gida a kasuwa..." Hansai ta share idonta tace "Toh shkkn, in sha Allahu baxan ji kunya ba" Daren ranan Jiddah na karatu a dinning kamar yanda ta saba bayan magrib aka bude kofar parlon, Hajja ce ta shigo sakale da jakarta tace "Assalamu alaikum" Jiddah ta amsa sallaman tana mata sannu da xuwa, Hajja tace "Ina Ramlan take?" jiddah ta mike tace "Tana daki bari in mata magana" Hajja tace "Toh yi maxa wancan d'an daban sai ya iya tafiya ya kyaleni, kinsan dama da kyar ya kawoni sai da uban ya sa baki" Jiddah dai bata ce komai ba ta tafi dakin Umma, ba a dau lkci ba Umma ta fito sanye da Hijab da murmushi tace "Sannu da xuwa Hajja" Hajja tace "Yauwa Ramlah daxu naga abun arxiki shine nace bari dai in taso in xo da kaina inyi godiya, don mu a Masar haka ake, Allah yayi maki albarka ya kara arxiki sai dai tafiyar ma ta lalace don wannan yaro Aliyu gobe xa a kai kudin aurensa kuma ina nan har sai anyi komai idan Allah ya yrda" Umma tace "Allah sarki, ai da kinyi waya na xo kawai Hajja ba sai kin fito da daddaren nan ba" Hajja tace "Aa barni na xo, banda me sonka wa xai tuna da kai har ya baka tsaraba haka..." Tana kai wa nan ta mike tace "Toh ni dai bari in koma ni da wancan d'an kabu kabun ne muka xo kar ya tafi ya barni in rasa tudun dafawa" Umma tace "Tare da Aliyu ku ke?" Hajja tace "Ehh wllh, sai da ma ya xageni a hanya muna tahowa daga nace masa ba jirgi fa yake figa haka ba, ni dai bakina alaikum naki biye masa ya kunyata ni a kasar mutane" Umma tace "Amma yace wani abu, shine baxai shigo ya gaisheni ba??" Hajja tace "Ahaf ai wannan mutumi dai daga d'an iska sai shi, baya ganin kowa da gashi" Umma ta kira Huraira a daki tace "Tafi kice ma Abuturrab ina kiransa a waje" Tace "Toh" sannan ta fita, Hajja ta koma ta xauna tace "Gwara dai kiyi masa soso da sabulu sannan ki hadani da d'an arxiki ya maidani gida kar kasheni a hanya" Umma dai bata ce komai ba, Maimoon ta fito tare da Safiyya suka gaidata, Hajja tace "Allah maku albarka, ya baku ilimi me amfani" Jiddah dai tuni ta koma ta ci gaba da karatunta a dining, Ba a dau lkci ba Abuturrab ya shigo parlon kansa a kasa, Ya karaso ciki ya gaida Umma da ladabi tace "Saboda ka isa yasa ka xo gidan nan ka xauna mota baka shigo gaisheni ba?" Ya ki kallonta a ido, yana kame kame yace "Aa waya nake yi a motar dama xan shigo Umma" Hajja tace "Karya yake algungumi har cewa yayi minti biyar ya bani wllh, ni dai ki hadani da me hankali ya maidani gidan d'a na don Aliyu abun tsoro ne, babu uwar da na hada dashi balle ya cuceni, gashi uwar tayi ta xuba masa ido kamar tana tsoronsa bata fada masa gaskiya, ita kuma yar Benuen can tayi kane kane a kan lamarinsa, ai ni ina ganin iftila'i tunda ja sauka gidan Usman, abubuwa suke babu tsari kamar dai gantalallu" Abuturrab dai sai kallonta yake ta gefen ido, Umma tace "Toh ka kyauta, from henceforth i don't want to see ur legs in my house again, get out" Bai ce mata komai ba ya juya ya nufi kofa ya fita, Jiddah ta bi sa da kallo, Hajja ta ajiye jakanta ta cire mayafinta ta linke ta ajiye, ta gyara xama tace "Dama idan babu me mayar dani gida sai dai in kwana a nan kawai, baxan bi mutumin can ba abu ya lalace min" Maimoon ta fashe da dariya Hajja ta marairaice tace "Allah kuwa ke baki ga yanda ya wani fita kamar Zaki ba daga fadan gaskiya" Umma tace "Kiyi xamanki kawai a nan Hajja" Hajja tace "Toh a kai min kayana daki" Karfe tara da rabi Umma na dakinta tare da Jiddah dake gyara mata press din kayanta, Umma tayi dialing number yayarta, nan kuma ta sanar mata duk abinda Aliyu yayi mata daxu, Ummi tace "Kiyi hakuri Ramlah, Ni yayi ma ba ke ba, kinsan wannan xancen auren da ya kirkiro ma kansa da Hafsah kawai suke sabgarsu, ban san komai a kai ba, uban ne ma yace min gobe xa su kai kudi, wllh bai ce min komai ba shi har yanxu" Umma tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Yaya ina ta ce maki a tashi tsaye kince Aa ba komai, wllh wannan abu ba lafiya a ciki, ga dai abu kiri kiri fa" Ummi tace "Aa ki kyalesu kawai, shi ba yaro bane kuma sarai da hankalinsa, abinda kike tunani ba shi bane, shi dai ne ya xabar ma kansa haka, ai ba shi daya na haifa ba dai? Dama shi da namiji ai wasu kake haifa ma" Umma tace "Ki kyaleni da shi xan saita masa xama wllh" Sun jima sosai suna waya, Jiddah dai duk sai bata ji dadi a ranta ba, taji kuma a xuciyarta tana son yi ma Abuturrab magana, to amma a ina xata gansa?? Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Ranan asabar kamar yanda Ummi ta sanar ma Umma aka kai kudin auren Aneesah, on that same day kuma aka saka ranan bikin wata biyu, Umma na xaune parlor da yamma Hajja ta shigo parlon ta rike ha6a tace "Ramlah kinji wai an sa bikin Aliyu nan da wata biyu, yanxu Usman ya kirani yake sanar min, sun kai komai saura sadaki" Umma tace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Hajja tace "Atoh dai, mu iyakar abinda xa mu ce kenan, yaron da baya mutunta iyayensa...." Daga haka ta juya ta koma ciki, ita dai Umma bata ce komai ba. Abuturrab na xaune shi kadai a parlorn gidansa dake Abuja idonsa na kan screen din wayarsa da yake dannawa.... knocking din kofar parlon aka yi ya kalli hanyar kofar, amma bai yi wani yunkurin tashi ya bude ba, aka sake knocking duk a tunaninsa Aneesah ce, wayar hannunsa ya fara vibrate ya ga Ahmad, yyi ta kallon wayar kafin ya daga ya kai kunne, Ahmad yace "Are visitors not welcome any longer?" Abuturrab yace "Nace maka ina nan ne?" Ahmad yace "Su kuma takalman da ka bari bakin kofa fa?" Abuturrab bai ce komai ba ya katse wayar, bayan few seconds ya mike ya nufi kofar ya bude ya dawo cikin parlon, kallonsa kawai Ahmad yake don rabon da ya gansa an yi sati uku yanxu, ya kirasa severally baya responding, har ma ya daina kiransa, Ahmad ya karasa ya dau drugs da ya gani kan center table yana jujjuya su, lkci daya ya ajiyesu yace "Bai kamata ka dinga shan irin wa ennan magungunan saboda yanayin aikin ka, and why are u having sleepless night?" Abuturrab ya kallesa yace "Haka nace maka?" Ahmad yace "Aa haka dai drugs din yace min..." Abuturrab yace "Then you are mistaken, ka kara gaba can da karyar likitancin ka..." Murmushi Ahmad yyi yace "Toh Shikenan, amma da an canxa maka prescription din drugs din" Abuturrab yace "Wannan kuma likitan da ya fi ka yayi prescription din" Ahmad yace "Ohk then, kwana da yawa, i called severally baka responding ko nayi wani laifi ne" Abuturrab ya ki kallonsa, Ahmad yace "Shine dai yau sanin schedules dinka nace bari in karaso gidanka na nan inji laifin da nayi" Abuturrab yace "I just decided to live my life without hypocrite" Ahmad ya buda ido sosai yace "Hypocrite? Su waye hypocrite din?" Abuturrab yace "Decision dina kenan" Ahmad yace "Kai ne babban hypocrite ai tunda har kana tunanin anyi wronging dinka amma ka kasa bude baki kayi magana ka dau gaba da mutane, balle ni dai nasan i did nothing to you" Abuturrab ya jefa masa wani kallo yace "You did nothing to me?" Ahmad yace "Of course, ba abinda na maka" Abuturrab yace "That's ur cup of tea... To yanxu bayan munafurcin da ku ka je ku ka hada har aka sa na saki wancan yarinyar ko da akwai wani abu da ya ragu a rayuwata tun bayan wannan lkcn, akwai wani abu da nayi loosing?" Ahmad yace "Eh mana gashi har bacci kayi loosing, sbda duk wanda ke isasshen bacci babu abinda xai hadasa da wa en nan kwayoyin dake gabanka...." Kallonsa kawai Abuturrab ke yi babu ko kiftawa, Ahmad ya daga shoulder yace "And da bai dameka ba ko baka yi loosing komai ba babu abinda xai sa ka dinga isolating kanka daga cikin al'umma, but that's not my problem now, my major problem is that daga yanda na ganka nasan you are down for now may be they took u unexpected, don haka take a break from work, kada wataran muje mu ji labarin da ba shi kenan ba, shi Pilot banda nutsuwa da kwanciyar hankali ba a bukatar komai daga garesa, amma yanxu yanda kake a birkicen nan bai kamata ka dinga daga al'umma xuwa sararin samaniya ba, toh bayan wannan kuma ina son ka cire duk xargi a ranka, ka bar ganin ko da hadin bakina aka saka ka saki Jiddah, i know nothing about it... Kawai dai coincidentally nayi maka magana da kwana biyu sae kuma abinda ya faru ya faru, da ina da niyyar sanar ma kowa tun farkon auren xan sanar ae ba sai da aka dau lkci ba" Abuturrab yace "To ko kai ka fada ko ba kai ka fada ba ance maka abun damuna yyi ne? Banda ma wani burden da aka sauke min meye nayi loosing a lamarin nan, sae ma peace of mind da freedom da na samu, plss close this chapter, ba shi da wani amfani a gareni" Ahmad yace "Ok then, i heard su Abba sun xo gidansu Aneesah yau" Abuturrab yace "You heard right!!" Ahmad yace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Abuturrab bai tankasa ba ya mike ya shiga kitchen, Ahmad ya bi sa da kallo yana murmushi, Hmm is Abuturrab really sure he looses nothing living without Jiddah?" Har karfe sha biyu Ahmad na gidan kasancewar bashi da night duty, ya tashi ya shiga bedroom yyi kwanciyarsa ya bar Abuturrab yana operating laptop. Karfe uku da yan mintuna Ahmad ya fito parlor ganin Abuturrab bai shigo ba, bai gansa a parlon ba har sannan kuma wutan parlon na kunne ga laptop dinsa ka a kunne, kitchen ya karasa nan ma bai gansa ba, ya fito ya duba sauran dakunan duk baya ciki, ganin kofar parlon da ba ayi jamming ba ya karasa ya bude kofar, xaune ya gansa balcony with his phone, da mamaki Ahmad yace "What are you doing here by this time?" Abuturrab yace "Zafi nake ji" Da mamaki Ahmad yace "Xafi kuma ga Ac ga fanka? Are you okay?" Abuturrab yace "To iskan waje nake so ba na Ac ba" Ahmad ya fi minti biyu tsaye yana kallonsa, Abuturrab bai kuma kallon inda yake ba, Ahmad yace "Ka sha drugs din naka?" Abuturrab yace "Ae ba kai ka min prescribing ba balle ka tambayeni" Ahmad bai kuma ce masa komai ba don sae a sannan ya tuna cewar ya sha wajen karfe sha daya, juyawa yyi ya koma parlon ya xauna yana mamakin is Abuturrab okay?? Har kiran sallan farko Abuturrab na xaune balcony, Ahmad ya gaji da xama ya koma daki ya kwanta. Da asuba Ahmad ya fito da alwala parlon, dai dai sanda Abuturrab ma ya fito daga bathroom din parlon, shi dai Ahmad kallonsa kawai yake har ya fita don bai ga alamar ya kwanta ba, Abuturrab ya bi bayansa xuwa masallaci... Bayan an idar sun fito mosque din Ahmad na kallonsa yace "Karfe nawa xaka yi piloting yau?" Abuturrab yace "Karfe daya..." Ahmad yace "Okay..." Gidan ya shiga ya dau makullin motarsa ya fito ya ga Abuturrab xaune balcony yace "Xan dawo before 7" Da ido Abuturrab ya bi sa har ya wuce. Kamar yanda ya fada karfe bakwai ya dawo gidan, xaune ya tadda Abuturrab a parlor ya jinginar da kansa jikin kujera, Ahmad ya xauna ya ajiye ledan hannunsa yace "Good morning" Abuturrab yace "Afternoon duty ka koma yanxu" Ahmad na bude ledan da ya ajiye yace "I think u are suffering from lack of sleep" Abuturrab ya dinga kallonsa yace "Wa ye xaka yi ma allura? Ni nace maka bani da lafiya ne??" Ahmad ya kallesa yace "Aa baka ce min ba, but this will help" Abuturrab ya gyara xama yace "You are wasting ur time, gwara ma kar kayi wasting alluranka, idan kuma ka hada sae ka nemi wanda xaka yi ma" Ahmad bai tanka sa ba ya gama hada ruwan alluran, sannan yace "Kaga kar ka 6ata min lkci ka 6ata ma kanka lokaci Captain, how will a normal human being stay all through the night without sleeping, sannan anjima yaje ya daga jirgi with over 300 passengers or less??" Abuturrab yace "Wai kai nace maka banyi bacci bane, shkkn kuma mutum daga farkon dare har karshe sae yayi ta bacci?" Ahmad yace "Duk kwararren likita ya ganka yasan baka bacci bawan Allah, don haka idan xaka daina gardama ka daina...." Abuturrab yace "Ashe kai kwararren likita ne" Mikewa Ahmad yyi yace "You ur self will feel relieved after the injection...." It took anoda 15mins to convince Abuturrab sannan ya yarda Ahmad yyi masa alluran, in just less than 20mins ya kwanta nan kan doguwar kujera, Ahmad dake watching dinsa yace "Da dai ka tashi ka shiga ciki baccin xae fi maka ma'ana" Tashi Abuturrab yyi ya wuce bedroom dinsa, yyi rub da ciki saman gado.... Sae wajen takwas da minti goma Ahmad ya bar gidan bayan ya ga Abuturrab yayi bacci. Sha biyu da rabi na rana Ahmad ya dawo gidan ya tadda Abuturrab yana bacci har sannan, ya ajiye masa ledan takeaway din abincin da ya kawo masa, ya karasa yana kallonsa da kyau, lkci daya Abuturrab ya bude ido, ya dafe forehead dinsa yace "What's the time, our flight is..." Da sauri ya mike xaune yace "Karfe nawa?" Ahmad ya rungume hannu yace "This is after 12" Abuturrab ya xaro ido yace "What????" Tashi yyi daga kan gadon yaji wani jiri ya debesa ya koma, Ahmad yace "Look, don't deceive ur self nd ur Airline Captain, ka tura masu text yanxu cewar baka da lafiya" Abuturrab yace "Ni nace maka bani da...." Rike cikinsa yyi da sauri, yace "I feel like throwing up" Ahmad ya karasa ya bude masa bandakin, da kyar Abuturrab ya tashi ya shiga bathroom din. Karfe shidda suka iso train station na rigasa, Salem na cikin mota yana jiransu, Ahmad ya bude front seat ya shiga, Abuturrab ya xauna bayan motar ya jinginar da kansa da seat, Salem na kallonsa ta madubi yace "How are you feeling now?" Abuturrab yace "Alhmdlh" Salem ya gaisa da Ahmad sannan ya tada motar suka bar station din. Da magrib Aunty na tsaye kan Abuturrab dake kwance saman gadonsa with drip, tace "Ko wannan aikin naka ai ya isa yyi weighing dinka down, aiki babu hutu kullum mutum na sararin samaniya" Shi dai bai ce mata komai ba, tace "Toh Allah ya sauwake" daga haka ta juya ta nufi kofa ta fita, Aisha ce ta shigo dakin da cup din shayi ta ajiye masa tace "Ya jikin yaya?" Yace "Ummi fa?" Tace "Tana can daki" bai kuma cewa komai ba ta ajiye shayin ta fita. Umma ce xaune parlor tana kallon Ahmad da bai jima da shigowa gidsn ba, tace "Toh ya jikin nasa yanxu?" Ahmad yace "A'a da sauki nayi masa allurori kuma na sa masa drip" Umma tace "Ikon Allah, kuma yaya bata gaya min ba wllh, bari in kirata" Wayarta ta dauka ta shiga kiran yayarta, Bude kofar parlon aka yi Jiddah ta shigo da sallama rike da qur'ani da takardunta, Ahmad ya amsa, ta karasa parlon ta duka kasan carpet a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau Jiddah, har kun gama karatun?" Tace "Eh, ya Aunty Ramlah?" Yace "Tana can gida ai, baku je bane?" Tayi murmushi tace "Aa bamu je ba" Umma tayi ma Ummi sallama bayan ta daga wayar, suka gaisa sannan tace "Yaya ashe Aliyu bai ji dadi ba" Ummi tace "Ehh haka aka ce min" Umma ta kalli Ahmad tace "Wai dama ba can gida yake ba?" Ahmad yace "Can yake" Umma tace "Toh baki shiga kin dubasa bane Yaya?" Ummi tace "Aa masu dubasa dai nayi, ni yace min bashi da lafiya ne?" Umma tace "Aa yaya ai rashin lafiya daban ne, da kin shiga kin dubasa ai, nima ynxu Ahmad ke gaya min shi ya taho da shi daga Abuja ma" Ummi tace "Allah ya kara mana lafiya gaba daya" Umma ta d'an yi shiru sae kuma tace "Toh Ameen" sallama suka yi ta ajiye wayar, Umma ta kalli agogo dake nuna biyar da rabi sannan ta kalli Jiddah tace "Malamar ta tafi ne?" Jiddah tace "Ehh ta tafi" Wayar Umma ya fara ring ganin Ummi ke kiranta ta dau wayar ta mike ta wuce cikin daki, Ahmad na kallon Jiddah yace "Hope baki bukatar wani abu yanxu?" Ta girgixa kai tace "Aa ba komai" Yace "To ya karatun?" Tace "Alhmdlh" Yace "Kina dai ganewa sosai ae" Murmushi kawai tayi tace "Ina ganewa" yace "Toh ki dinga maida hankali sosai pls kin ji?" Ta gyada masa kai, a hankali tace "Ina son in tambayeka wani abu" yana kallonta attentively yace "Toh ina jin ki Jiddah" Ta sunkuyar da kanta tace "Don Allah xaka iya kai ni can gidanmu in ga Baabarmu?" Sake baki yayi yana kallonta, can yace "Me xa kiyi ma baabar taku?" Cikin sanyin murya tace "Ina son xuwa in gaisheta" Ahmad ya girgixa kai yace "ko xaki je ba yanxu ba tukun Jiddah...." Tayi kasa da murya tace "To akwai wata Iyah a layinmu, tana min kirki sosai, baxan iya xuwa gaisheta ba ita?" Da mamaki Ahmad ke kallonta, can dai yace "A layin baabar taku?" Ta sunkuyar da kanta, Murmushi kawai yayi ya rasa abinda xai ce mata... Umma ce ta shigo parlon, tana kallon Ahmad tace "Idan anyi magrib sai ka kai ni can gidan in duba Aliyun" Ahmad yace "Toh Allah ya kai mu" kitchen ta wuce, Jiddah na kallonsa tace "Bashi da lafiya ne?" Ahmad yace "Ehh amma da sauki" Tana kallonsa tace "Nima xan iya bin ku in gaishesa da jiki?" Ahmad yace "Sai yanda Umma tace" Bata kuma cewa komai ba, bayan few seconds ta kallesa taga kallonta yake, murmushi ya sakar mata, ta sunkuyar da kanta tana murmushin ita ma sannan ta mike tace "Xan kai kayan karatuna daki" Yace "Toh Jiddah" Tana fadin haka ta yi hanyar dakinsu. Da magrib kamar yanda Umma tace ta shirya don xuwa duba Abuturrab tare da Ahmad, Jiddah ta rasa ta yanda xata ce mata ita ma tana son xuwa ta dubasa, ganin Ahmad ya fita kafin Umma ya fito ta bi sa da sauri ta riskesa a waje tace "Yaya don Allah xaka tayani gaya ma Umma, ni ina jin tsoro" Ya wara ido yace "Aa nima ba ruwana sai dai ki gaya mata da kanki" Jikinta yayi sanyi, a hankali tace "Toh" sannan ta juya ta koma cikin gidan, Umma ta fito parlor da hijab da jakarta tana kallonsu Maimoon dake parlon tace "Kar dai ku bar ruwa ya cika yyi ta xubewa...." Maimoon tace "Umma ni ma xata da mu xa ku je mu duba yayan muma?" Umma tace "Ba cewa kika yi kina da Hadda ba" Maimoon tace "Toh shkkn sai kun dawo" Safiyya dai na xaune tana danna wayarta, Umma ta nufi kofa Jiddah ta bi ta da kallo, a hankali tace "Umma sai kun dawo" Umma tace "Yauwa, kema kiyi karatun ki duk da dai ba kallo kike ba na sani" Jiddah bata ce komai ba har Umma ta fita parlon... Umma na shiga mota Ahmad ya kalleta yace "Umma na xata da su xa mu je can gidan su duba Aliyun, daxu Mumy ta tambayeni nace xan taho da su...." Umma tace "Toh ai ni baka gaya min ba, kuma sai a bar Huraira ita kadai a gidan?" Ahmad yace "Toh shkkn" Xai tada motar Umma tace "Bari su fito din dai" Wayar Safiyya Umma fa kira, tana dagawa tace "Safiyya wai yayanku ku fito mu tafi tare" Tana fadin haka ta katse wayar, Tun da suka fito outside gate din Ahmad ke kallon Jiddah sai dai ba ga expression da yake expecting gani a fuskarta ba, ita da Maimoon suka shiga bayan motar sannna Ahmad ya kunna motar suka bar layin.... A kofa gida yayi parking, Safiyya ta sauka sannan jiddah ma ta sauka, su Umma ma suka sauka duk suka shiga gidan, Ummi ce xaune parlor tare da Hajja, Hajja na cewa "Tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin irin haka ba wllh sai a kanki..." Sai kuma tayi shiru tana amsa sallaman Umma, Umma tace "Sannu Hajja" Hajja tace "Yauwa sannu, sai kika ji Aliyu ba lafiya ko?" Umma tace "Eh wllh" Hajja tace "Toh mu ma haka muka ji, ashe wannan yaro Ahmad ne ya tafi ya dauko sa a Habuja rai a hannun Allah, ni dai dama nace wannan halin da ya tsiro ma kansa ba halinsa bane, ashe bashi da lafiya ne bawan Allah" Umma tace "Allah dai ya basa lafiya, yana dakinsa ne?" Hajja tace "Ehh yana can an kara masa ruwa, kai har makota babu wanda bai shigo dubasa ba amma uwarsa ta ki shiga ban san dalili ba" Umma dai bata ce komai ba ta yi hanyar dakin Abuturrab, yana xaune hannunsa rike da bowl din farfesun hanta, Aunty ma na xaune dakin tana cewa "Idan ka ci wllh xaka ji dadin bakinka, sannan kar kaji komai ni da kaina na maka sai da na tsaftace shi" Aunty tace "Aa sannu da xuwa Hajiya Ramlah" Umma tace "Yauwa sannu ya mai jiki?" Aunty tace "Aa yaji sauki wllh, ai da ma baku wahalar da kanku kun fito ba, jiki ai da sauki sosai" Umma na kallonta tace "Xuwa duba d'an nawa ne wahal da kai?" Aunty tace "Aa wai naga dare yayi ne ai..." Umma tace "To ba wahal da kai bane, d'a na ne halaq malaq" Aunty dai bata ce komai ba, Umma na kallonsa tace "How are you feeling now" Ya sunkuyar da kansa yace "Alhmdlh da sauki" Aunty tace "Nace maki ai da sauki" Umma ta kalleta tace "Naga shi ma yana da baki ai Hafsah" Aunty ta mike tace "Bari a kawo maka shayin Aliyu" daga haka ta fita, Maimoon da Safiyya ne suka shigo dakin da sallama, Umma da ta nemi waje ta xauna ta kallesu tace "Ina Jiddar?" Sai a sannan Abuturrab ya daga kai suka yi ido hudu da Jiddah da ta shigo dakin a lkcn, Maimoon da Safiyya suka xauna kasan carpet din dakin suna kallonsa suka yi masa ya jiki, yace "Alhmdlh" kusa da Umma Jiddah ta xauna a kasa tana kallonsa a hankali tace "Ya jiki?" Ayi min afuwa jiya ban dawo da wuri gida ba... Idan naga da sarari xanyi update later in sha Allah... Thanks for understanding. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Abuturrab bai ce komai ba ya ci gaba da shan pepper soup din hannunsa, Jiddah ta sunkuyar da kanta jin bai amsa ba, Umma tace "Amma you are getting much better now" Ya kalli Umma yace "Alhmdlh" Tace "Toh Allah ya kara afuwa..." Mikewa tayi tace "Allah ya sauwake" Ba tare da ya kalleta ba yace "Ameen" Kofa ta nufa Jiddah ta bi ta da kallo sannan ta juya ta kallesa suka hada ido, bata san sanda ta mike ba tana son fita dakin taji muryarsa a tsakiyar kanta, "Dauko min ruwan gora a kitchen" Kallonsa tayi don ta tabbatar da ita yake, ganin shi ma kallon nata yake tace "Toh" sannan ta juya ta fita dakin, Ya kalli su Maimoon da ke kallon tv dake aiki a dakin yace "Toh nagode" Kallonsa suka yi a tare da sauri, Maimoon ta wara ido tana kokarin mikewa tace "Allah ya sauwake Yaya" Yace "Ameen" Safiyya tace "Allah ya kara lafiya" a tare suka fita daga dakin suka kullo masa kofar, bayan few minutes Aunty ta shigo dakin rike da goran ruwa ta ajiye masa kan bedside drawer, ya dinga kallonta, can dai yace "Ke kika dauko da kanki?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ehh, na sa ta wanke kwanukan da aka 6ata a kitchen din" Bai ce komai ba, ta dau magungunansa ta shiga buda masa yace "Aunty...." Ta dakatar da shi tace "Ehh ka hadiyesu yanxu" Bai kuma ce mata komai ba, ta mika masa tulin drugs din, ya sa hannu ya amsa, ta dau goran ruwan ta bude shi ma ta mika masa ya amsa ya hadiye maganin, kallon bowl din hannunsa tayi ganin ba wani shan pepper soup din yake ba tace "Bani in tafi da shi gun wanke wanke, dama nasan baxa ka sha ba ai" Ya girgixa kai da sauri yace "Aa gashi nan ina sha" Tace "To Allah ya sa" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Ahmad ne ya shigo dakin yana dubansa yace "How are you feeling now?" Abuturrab yace "I'm good" Ahmad ya karasa dakin yace "Allah ya kara lafiya" Ba tare da ya kallesa ba yace "Ameen" Ahmad yace "Bari in je masallaci in dawo" Daga haka ya fita. Bayan fitarsa da few minutes Abuturrab ya cire drip din hannunsa ya mike ya dau bowl din pepper soup da Aunty ta kawo masa ya bude kofa ya fita, sau daya ya saci kallon mutanen dake xaune parlor ya wuce kitchen, muryar Aunty yaji tace "Ina kuma xa ka" Ya ki juyowa balle ya tsaya, ta mike ta bi bayansa Umma ta bi ta da wani irin kallo, yana shiga kitchen din ya rufe kofar, Jiddah dake tsaye tana wanke wanke ta juyo tana kallonsa, sae ga Aunty ta shigo, amshe bowl din tayi tace "To sae ka wani fito? ko a waya baxa ka kirani ba in shigo in dauka" kallonta kawai yake, ta ajiye bowl din a gefen Jiddah tace "Mu je" Bai ce komai ba ya juya ya nufi kofa Jiddah ta bi su da kallo, sae da ya fita sannan Aunty ta fita ita ma ta kulle kofar... Umma na kallon Abuturrab tace "Do u need anything" ya kalli direction din parlon ganin Ummi na parlon ita ma, ya karasa can, Aunty tace "Wai kawai mutum ya fige drip da aka saka masa yayi ta yawo cikin gida, ta ya xa a gane treatment din da ake" Abuturrab na karasowa parlon ya xauna yana kallon Ummi a hankali yace "Ina yini Ummi" Ummi tace "Lafiya qlau" Bai kuma cewa komai ba kamar yanda ita ma tayi shiru, Aunty tace "Don Allah ka taso mu tafi ka maida ruwan nan da ka cire" Umma ta mike tace "Wai ke Hafsah wannan shisshigin da neman wajen xama da kike duk na menene ban gane ba? Ina ruwanki da wani drip da aka sa masa, ko ke kika sa masa?" Aunty ta bude baki ta rike ha6a tace "Shisshigi kuma Hajiya Ramlah? Ban gane Shisshigi ba" Umma tace "Sai ki je ki xauna kiyi naxari ki gane da kyau, duk kin bi kinyi kane kane a kan abinda bai shafeki ba a gidan nan, ke kin isa ki hanasa xuwa ya gaida mahaifiyarsa, wacece ke...." Katseta Aunty tayi tace "Aa kinga ni baxan biye maki ba Ramlah dama kina da wani kuduri can da ban sani ba a kaina dake cikin ranki, banda haka ina ruwanki da issue din gidan nan, ita mahaifiyar tasa ai ta san da cewa ya dawo bashi da lafiya amma ko bin ta kansa ta yi, Aa gaskiya ni ba ruwana baxa ayi tashin hankali da ni ba" Hajja ce ta leko daga dakinta tace "Me ke faruwa ne nake jin hayaniya ga dai mara lafiya kwance shememe a gida?" Aunty ta kalli Hajja tace "Kawai dai daga Aliyu ba shi da lafiya ina tsaye kansa sai Hajiya Ramlah ta xo tana gatsa min magana, da yau ace bani da 'ya yan nan da nayi kwanan takaici a gidan nan..." Hajja ta fito tayi kasa da murya tace "Atoh ae da gaskiyarta Hafsah, kin bi kinyi bake bake kan d'an mutane kamar ke kika haifosa duniya, duk shekaruna a Masar ban ta6a ganin haka ba wllh, don cewa ma xa suyi kin masa wani mugun abun ne, su basa haka abinda ya shafesu kawai suke, da ran Hauwa fa ba mutuwa tayi ba Hafsah, to ina ruwanki da d'an mutane" Aunty tayi wani murmushi tace "Toh ai shkkn, su ma sai su ja sa jiki kamar yanda nake masa su ga ko baxai yi masu biyayyan da yake min ba, ai ko dabba ma yasan me kyautata masa" Bata jira cewarsu ba ta bar wajen, Hajja tace "Kaji mayya, wani jikin xa mu ja sa bayan mu dai bamu san abinda kika masa ba har yau, yin abubuwansa kawai yake irin na en benue fah, da a masar ne idan hukuma basu garkameki ba shegiya nake, don ai ba a san abinda kika masa ba yake makale da ke" Shi dai Abuturrab kansa na kasa, Umma tace "Xan ga yau ko ita ta haifesa, bari Ahmad ya shigo su tafi can gida ya ci gaba da treatment dinsa idan ta isa ta wanke kafa taje gidana taga tsiya" Abuturrab ya daga kai ya kalli Umma, Hajja tace "Shikenan bakinmu alekum, ni ma sai in tafi da kayana kala hudu duk mu tafi can idan ta isa ta bi mu, wllh sai na nuna mata ni yar banxa ce" su Maimoon dai sai dariya suke kasa kasa, Ita dai Ummi girgixa kafa kawai take, Hajja tace "Abinda duk mun san kan iskanci mu da muka xauna a Masar..." tana fadin haka ta shiga daki ta hau hada kayanta, Ahmad na shigowa kuma Umma ta sanar masa can gidan xa su tafi tare da Abuturrab, sosai Ahmad yayi mamakib musun da Abuturrab bai yi ba, shi da yafi kowa sanin halinsa tafiya ayi masa treatment a can gidan isn't something easy amma sai gashi yaga bai ce komai ba, Hajja dai tuni ta hada kayanta ta fito da yar jaka tace "Wannan dai sai dai muyi mota biyu idan ana son mu tafi cikin walwala" Ahmad yace "Har ke xa aje Hajja" Hajja ta kallesa kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Dadina da Masar wllh Yaro bai isa ya raina babba ba, wani ta6aran ai sai a Najeriya, wai ku ji fa wata tambaya da Ahmad ko wa yake ke min, to ina ruwanka fisabilillahi, gidanka ko gidan Hajiya Ramlah, tun fa da mahaifinku ya rasu ita ke ta fadi tashi na ganin shegun danginsa basu kwace katon gidan nan da ku ke ciki ba, mace me kamar maxa kenan fa Ramlah, duk sai da ta bi ta kwatar ma kanta yanci shi yasa ban ga laifin kibar da ta narka ba wllh, gidajensa biyu da motoci da ya bari duk bata amince an cuceta ba, kun ga inda ta fi Hauwa kenan, tunda ita gashi ma mijin ba mutuwa yayi ba amma er benue ta kwace gida da 'ya ya tana xaune sandandan, ba a san gawar fari ba amma yau ace Usman rai yayi hali ko tsinke da kyar Hauwa ta tsira da shi a gidan nan, balle dama tsawon rai garesa idan Allah ya amince, toh kuma yaro sai ka wani ce da ni xa aje sai kace xanje gidanka, shi sa tunda ku ka yi aurenku da Ramlah sau biyar naje gidan don kada in ja ma kaina raini" Tana kai wa nan ta kalli Umma tace "Wani motar xa mu shiga Ramlah" Umma ta mike tace "Ku je a na Ahmad, ni sai in ja motar Yaya tunda driver baya nan" Hajja tace "Aa gwara in shiga naki mu tafi a nutse, su kuma yaran su shiga motar Ahmad din" tana kai wa nan ta fita gun mota, Ahmad ya bi bayanta yana murmushi don xuwa ya bude mata motar sannan ya dawo duba Ramlah, Umma ta mike tana kallon Ummi tace "Xa mu tafi can gidan yaya" Ummi tace "Toh Allah ya sawwake" Umma tace "Ramlah fa?" Ummi tace "Tana daki tana bacci" Umma tace "Toh bari dai in dubata" daga haka ta wuce bangaren Ummi, Abuturrab ya mike ba tare da ya yarda ya kalleta ba yayi hanyar bangaren stepmom dinsa, da gefen ido Ummi ta bi sa da kallo. Jiddah ta fito kitchen bayan ta gama wanke tulin kwanukan da Aunty ta ajiye mata, Ummi na kallonta tace "Sannu da aiki" Jiddah tayi murmushi ta karaso parlon tace "Umma fa" Ummi tace "Ta shiga daki yanxu" Jiddah bata ce komai ba ta xauna kasa, Ummi tace "Xauna saman kujera mana" Murmushi kawai tayi ta ki tashi, bayan some minutes Umma ta fito daga bangaren Ummi, tana kallon Jiddah tace "Ki je ku gaisa da Ramlah tana tambayarki" Tace "Toh" sannan ta mike ta wuce part din Ummi, Ramlah na xaune saman kujera tayi murmushi ganin Jiddah tace "Sannu da xuwa" Jiddah ta mayar mata murmushin tace "Ya jikin?" Ramlah tace "Da sauki, ya su Maman Abdallah" Jiddah tace "Suna gida" Ramlah tace "Toh ki gaida min su" Jiddah tace "Xa su ji, to sae anjima" daga haka ta fita parlon. Umma ce ke magana da Ummi kasa kasa tana cewa "Allah bana jin dadin hakan yaya, da wnn shirun da kike kina fita harkansa gwara ae ki ci masa mutunci a fili har ita ta ji, gani take tsoronta fa ake, kuma tana lura da zamantakewarku da shi, shi yasa take samun daman yin duk abinda take yi, Sannan ina gaya maki abinda Aliyu yake Allah ba banxa ba" Ummi tace "Bari kiji, jira yake dama ki gama surutanki ki bar wajen ya tashi ya bi bayanta, kice wai bai san abinda yake ba, wllh tsabagen rainin wayo da walakanci ke damunsa, ba dai Hafsah ba gashi ga ta, sae ynxu abun nasu ke wuce misali, kinsan har kudi ya bata wai ta siya masa fili biyu for two months now, amma sae last week muna wata maganar ta gaya min, ni dai bance komai ba" Umma dai ta saki baki tana kallonta, can tace "Allah mai iko ni Ramlah" Umma tayi wani murmushi tace "Mu je dai xuwa kawai" Abuturrab na dakin Aunty tace "Toh kai baka da bakin budewa kace masu gidan ubanka kake son xama har Allah ya yaye maka ka koma bakin aikin ka?" Ya shafa kansa yace "Aunty ae xuwa gobe i will be very okay in sha Allah, da safe xan dawo gida" Aunty ta ja tsaki tace "Aikin banxa kawai wani ke tashi fadi a kanka banda ni, ita ta wani xo har gida nemana da fada, sai kace idan wani abun ya sameka ta ta6a tsayawa a kanka idan ba kinibibi da ya kawota ynxu ba" Yyi kasa da murya yace "Kiyi hakuri Aunty" tsaki ta kuma ja tace "Dai dai nake da ita wllh wllh, kuma xan nuna mata na fi ta iko da kai tunda auren ubanka nake kuma matsayin uwa nake a gareka" Ya shafa kansa ganin ba shiru xata yi ba, yace "Sai na dawo da safen Aunty" tace "Toh transfer din da kace xaka yi fa, gwara fa ayi ayi a hada abun nan, nan da nan xaka ga har lkcn yayi" Yace "Nawa kika ce?" Tace "Ko akwati ynxu ai yayi kusan dubu dari hudu da wani abu Aliyu" Abuturrab dake ta kallonta yace "Akwatin guda nawa?" Tace "Aa seti biyu xa ayi ai" Yace "Dubu dari hudu da wani abu?" Tace "Atoh don bance maka dubu dari biyar ba, ni na ma san sai na cika wllh, ai ba wai akwatin yaku bayi xa mu siya a xuba masu kaya a ciki ba" A hankali yace "Toh shkkn, idan na isa can gidan xan saka maki kudin ai ina da account dinki" Aunty tace "Toh shkkn, amma gobe dai kamar yanda ka fada ka dawo da safe" Yace "In sha Allah" daga haka yayi mata sai da safe ya fita... Parlor ya tadda su Umma da Ummi har sannan suna magana, Umma ta mike ganin ya fito tace "Yaya bari inje kar Hajja ta shigo yanxu tace ba haka ake a Masar ba" Ummi tayi dariya tace "Lallai kam, toh sai da safe" Umma tace "Allah ya tashe mu lfya" daga haka ta nufi kofa, Abuturrab ya karaso gun Ummi yace "Sai da safe Ummi" Tace "Allah ya kai mu" Kofa ya nufa ya fita parlon. Hajja da Jiddah suka shiga motar Ummi da Umma ke driving suka bar gidan, sun riga su Ahmad isa gida, Jiddah na kawo ma Hajja abinci Abuturrab ya shiga parlon, Ko kallon Hajja Abuturrab bai yi ba ya wuce dakin Ahmad, Hajja ta bi sa da kallo sannan ta ta6e baki tana kallon Umma tace "Idan kin lura komai nasa yanxu irin na Kishiyar uwar yake, wllh abun na damuna amma ni nasan me xanyi..." Umma dai bata ce komai ba, su Maimoon da Safiyya suka shigo parlon sannan Ahmad. Karfe sha daya saura Umma ta shiga dakin Ahmad, Ahmad na xaune yana danna laptop dinsa Abuturrab kuma yayi bacci, Umma tace "Toh drip din fa? Naga baka maida masa ba" Ahmad yace "Yace he is feeling much better, xan jira in ga har xuwa gobe" Umma tace "Toh Allah ya basa lafiya" Ya amsa da Ameen, sannan Umma ta fita dakin. Washegari da safe su Ramlah da Safiyya suka shirya suka tafi makaranta, Ahmad kuma ya tafi can gidansu Abuturrab duba Ramlah, Umma da Hajja na can daki, Jiddah na taya Huraira goge goge kafin malamarta ta karaso don karfe tara bai yi ba, Kamar ance ta daga kai taga Abuturrab ya fito parlon, Dauke kai tayi bayan sun hada ido tana ci gaba da goge gogenta tace "Ina kwana" Ya bi parlon da kallo bai ce komai ba, bata damu da hakan ba tace "Ya jiki?" Yace "Ki kawo min shayi yanxu" Yana fadin haka ya juya ya koma dakin Ahmad, ta bi sa da kallo sannan ta wuce kitchen, ta dauraye hannunta ta dau mug ta xuba ruwan flask a ciki ta yi making masa shayin, ta dauka ta fita kitchen din, ta fi minti daya tsaye kofar dakin Ahmad rike da cup din shayin, tana juyawa taga Ahmad yana tahowa, ya karaso kusa da ita yana murmushi yace "Shayi xaki kai masa..." Ta mika masa tace "Aa ce min yyi in kawo masa" Amsa Ahmad yyi yace "Malamarki ta xo tana balcony" Tace "Toh" sannan ta juya ta bar bakin kofar ta wuce dakinsu ta dau Hijab dinta ta saka ta dau takardunta ta fita, tunda Ahmad ya shigo Abuturrab ke kallonsa da cup din shayin, Ahmad ya ajiye masa shayin yace "Ya jikin?" Abuturrab yace "Shayin waye wannan ka kawo?" Ahmad yace "Jiddah ta bada a kawo maka" Abuturrab yace "Toh ni na riga na sha sai dai ka shanye" Tun da gari ya waye Aunty ke ta kiran Abuturrab, ta kirasa ya fi sau biyar daga karshe kawai ya dau account number dinta ya mata transfer din kudin da tace, ba a dau lkci ba ta turo masa message tace "Yauwa sun shigo, xan fita kasuwan yanxu" Ya dinga kallon message din kafin ya ajiye wayar, wajen karfe goma ya fita ya hado wani shayin da kansa sannan ya dawo ya sha, ya sha magungunan sa ya koma bacci.... Jiddah ta shigo parlor karfe biyu saura rike da takardunta, babu kowa a parlon, ta karasa dakin da Hajja take ta bude a hankali taga bacci take, dakin Umma ta wuce ita ma taga baccin take, sannan ta kai takardunta daki ta ajiye ta fito ta shiga kitchen, plates da taga anyi amfani da ta fara wankewa, ta gama kenan aka bude kofar kitchen din.... *I really appreciate the birthday wishes everyone, Allah ya bar xumunci, ku ma free Readers naga wishes dinku and i appreciate wholly but i am shock, don haka domin sauke maku bashi a kai xan maku bonanzan Jiddatul Khair yau, daga yau xuwa gobe da safe Jiddatul Khair will be 300 naira only* ☺️ To gashi dai na maku sauki sosai sosai sbda kauna🥰 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Jiddah ta juya tana Kallonsa, ya shigo ya kulle kofar, tana ajiye plates din a plate Rack tace "Ina yini?" A takaice yace "Ki daina gaisheni idan kin gan ni, bana so" tace "Toh" Ta dau plate daya ta bude warmer ta debi abinci still bata kallesa ba tace "Ya jikin" Yace "Ke yanxu a xatonki da tunaninki 'yancin kanki kika samu ko?" Sai a sannan ta juya ta kallesa suka hada ido, ya hade rai yace "Don kinga Maimoon na daukan mayafi karami ta saka ta fita titi kema sai kika fara saka mayafi karami, kin ma mance ke wacece koh" Shiru tayi bata ce komai ba ta kai hannu ta dau cokali, ya wani daure fuska yace "Kin saba saka mayafi daga can hayin rigasa ne, balle kuma gidana da kika xauna?? Kina tunanin ke da Maimoon daya ne?" Tace "To amma ai Umma ta gani bata ce komai, kaga da tace min in cire ai baxan sa ba" Yace "Toh daga yau ko nan da gate kada ki sake sa mayafi ki fita..." Da mamaki take kallonsa, can dai tace "Ko saboda me?" Yace "Saboda haka na fada" Bata kuma ce masa komai ba, yace "And yanxu kina ganin kin fi kowa freedom shi yasa kike shiga motar maxa har da xama gaban mota ko, uban wa ya ce ki bi ta ku hau motar wani kato har kika shiga gaba, a can hayin rigasar ku haka kike yi" Tace "Kamawa tayi in hau shi yasa na hau ba wani abu ba, kuma ai an san sa a gida" Bude baki yayi yana kallonta, yace "Kin san mene?" Ita dai ta xuba masa ido, yace "Akwai wani wanda yayi dalilin dawowarki cikin gari a duk wa enda kike xaune da su yanxu cikin garin kaduna??" Kallonsa kawai ita dai take, yace "Toh dama ai nine na fito da ke cikin gari, don haka yanxu sai in mayar da ke in da na dauko ki, duk me son sake fitowa dake cikin gari sai ya koma hayin rigasa ya dauko ki na musamman... Kin fahimce ni??" Murmushi kawai tayi tace "Toh" yace "Ehh, ni na raboki da baabarku kuma ni xan maida ki" Tace "Yaushe xan shirya kenan?" yace "Sai kin shirya ashe, dama kin xo da wani abun ne ban sani ba?" Tace "To shikenan" Ya jefa mata wani irin kallo ya fice daga kitchen din ta bi sa da ido, hawaye taji ya kawo idonta, ta rufe abincin ta fita ta koma daki ta kulle kofa ta kwanta saman gado tana iya kokarin ganin bata fashe da kukan dake cin ta ba... Har karfe uku Jiddah na kwance daki, Huraira ta xo ta kwankwasa kofar jin an sa makulli tana kiran sunanta, Jiddah ta mike da kyar ta isa gun kofar ta bude Huraira tace "Jiddah malamarki ta xo fa tun daxu..." Shiru tayi tana kallon idonta tace "Me ya faru Jiddah?" Ta girgixa mata kai tace "Kaina ke ciwo" Huraira tace "Subhanallah, to ki fito Umma na kiranki" Komawa tayi ta dau hularta ta sa sannan ta fito dakin, a hankali ta nufi parlor ganin Umma da Hajja a xaune, ta sunkuyar da kanta ta xauna a kasa tace "Umma gani" Umma tace "Amma dai nace ki daina barin malamanki na jiranki ke ya kamata ki dinga jiransu ko Jiddah, dole sai kinyi wani bacci idan malamar safe ta tafi bayan kin san cewar dayar na kan hanya ita ma" Jiddah ta kasa dago kanta cikin sanyin murya tace "Kuyi hakuri Umma, ciwon kai nake" Sai a sannan Umma ta kalleta da kyau tace "Ciwon kai tun yaushe, shine kike kuka?" Ta girgixa ma Umma kai kawai, Umma tace "Toh kin ci abinci" Ta gyada mata kai kawai, Umma tace "Toh Allah ya sauke kije dakina akwai paracetamol kan bedside drawer ki dauka, amma xaki iya karatun kuwa yau?" Cikin sanyin murya tace "Xan iya Umma" Umma tace "Toh je ki dauka ki sha ki dau qur'anin ki ki fita, Allah ya sauwake" Mikewa Jiddah tayi ta wuce dakin Umma, Hajja tace "Mu dai ba gamu mun taho jinyan wancan mutumi da har yanxu tun wayewar gari ban daura ido a kansa ba" Umma tace "Na duba na gansa yana bacci daxu" Hajja tace "Ni wllh dama ki sa duk ya tattaro kayansa ya dawo gidan nan a rabosa da yar Benuen can, ko ya kika ga" Umma tayi wani murmushi tace "Ai baxai dawo ba, wnn ma nayi mamakin da ya yarda ya biyo mu, ina ga tunda yake bai ta6a kwana gidan nan ba ko da xai kai karfe sha biyun dare" Hajja tace "To mu dai gamu ga Allah, amma Hauwa tayi sake ai, idan ta bar ta ta kwace miji sai ta yarda har d'anta ta kwace, nima fa don ban xauna a Masar bane a banxa shi yasa har yau bata rabani da Usman ba, kullum cikin tsayuwar dare nake, kyaga a rana sai ya kirani sau uku, to amma dai ba komai tunda Allah yayi min dawowa ba dai nace maki xan nuna nata nima yar banxa bace, Allah ya ba Aliyu lafiya mu koma gidan, na ma fasa komawa gidan Kabiru" Umma tace "Allah dai ya kyauta amma abun kam sai addu'a" Ahmad ne ya shigo parlon ya gaishesu, Umma tace "Ya jikin Ramlan" yace "Da sauki Alhmdlh" Hajja tace "Yaushe xaka sallami wancan mutumin mu koma gida in san ta ina zan fara da Hafsah?" Yace "Ai yace baya son drip din kuma, magunguna kawai yake sha" Tace "Atoh ya tarkata magungunan mu wuce gida kawai sai yayi ta sha a can" Duk suka kalli kofar Jiddah ta shigo parlon da sallama, Umma ta kalli agogo tace "Ciwon kan bai yi sauki ba kenan" Gyada mata kai tayi, Hajja tace "To Malamar fa?" A hankali tace "Tace inje in kwanta, ta wuce" Ahmad dake kallonta yace "Tun yaushe kan ke maki ciwo?" jiddah tace "Daxu" Yace "Toh je ki kwanta, Allah ya sauwake" Tace "Ameen" Sannan ta wuce daki ta kwanta. Har kusan karfe shidda Jiddah na daki tana jin kanta na mata wani ciwo ba kadan ba, Umma ce xaune parlor tare da Abuturrab da fitowarsa parlon kenan, Umma tace "Ka bari gobe ka tafi" Ya kalleta amma bai ce komai ba, tace "Kuma ka bude kunnenka sosai ka saurareni" Still shi dai bai ce komai ba yana kallonta, tace "Hafsah kanwar uwarka ce ko ta Ubanka?" Sunkuyar da kansa yayi, tace "Toh bari kaji Aliyu, wllh idan kana son ka dinga ganin dai dai a al'amuranka ka fita harkar matsiyaciyar nan ka kama uwarka..." Da mamaki yace "Me tayi kuma Umma?" Umma tace "Ni kake tambaya me tayi?" Yayi kasa da kai yace "Toh Umma naga dai lafiya suke xaune, kuma ita Aunty..." Umma tace "Tashi ka bani waje mara hankali kawai" Ya kalleta yace "Aa kiyi hakuri Umma" Cikin daga murya tace "Ka fini sanin lafiya suke xaune ko ba lafiya suke xaune bane?? tunda nake ban ta6a ganin d'an da ya hofintar da uwarsa ya dauketa ba komai ba yake bama Kishiyarta muhimmanci fiye da tunanin mutum kamar kai ba, anya kana son gamawa da duniya lafiya Aliyu?? Anya kana son ganin dai dai a rayuwar ka?? Uwa fa??" Kasa ce mata komai yayi yana ta kallonta da mamaki, to me Ummi tace ya mata?? tace "Toh wllh rayuwarka na cikin tashin hankali da garari don ma kaji in gaya maka yanxu" A sanyaye yace "Umma da akwai wani abun da nake yi ne ni ban sani ba? Ko da akwai wani abun da tace na mata ne" Tace "Kaje ka xauna kayi karatun ta nutsu bani xaka yi ma nonsense question din nan ba" Bai kuma cewa komai ba maganganunta na yi masa yawo a kai, shi a iya saninsa babu abinda yake ma Ummi yana mata biyayya yanda d'a ke ma uwa, to what is Umma talking about" Sake daga kai yayi yana kallonta yaga irin kallon da take masa tana girgixa kafa, ya shafa kansa a hankali bai ce komai ba, can kuma dai yace "Toh Shikenan xan je in bata hakuri, duk da ni dai ban san me nayi ba" Bai jira me Umma xata ce ba ya mike ya wuce dinning don tun daxu abincinsa ke can, Umma ta bi sa da kallo tana furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a ranta, lamarin Abuturrab anya lafiya kuwa?? Ahmad ne ya shigo parlon, Umma tace "Da wannan safa da marwan da kake a kan titi meyasa baxa ka dawo da Ramlah gidan nan ba Ahmad" Ya shafa kansa yace "Toh Umma" Umma tace "Kayi knocking ka shiga ka duba Jiddah don Allah" Yace "Alright" Abuturrab ya bi sa da kallo har ya wuce, sai da ya fara knocking Jiddah ta taso ta bude kofar ganinsa ta koma gefe kanta a kasa tace "Ina yini" ya dinga kallonta yace "Wai ciwon kan kike ma kuka Jiddah?" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yace "Kin ci abinci" Tace "Na ci" yace "Jikin ki da xafi?" a hankali tace "Nima ban sani ba" Toh bari in siyo maki magani yanxu in dawo" Yana fadin haka ya juya ya koma parlor, yana kallon Umma yace "Umma let me get her drugs, har yanxu bata jin dadi" Umma ta mike ta tafi daki wajen Jiddah, Ahmad ya karasa gun Abuturrab yace "Kayi bacci sosai ai ko?" Yace "Yau nake son xan koma gida" Ahmad yace "Ohk toh, bari in dawo xan siyo ma Jiddah magani she isn't feeling fine" Daga haka ya dau makullin motarsa ya fita. Bayan magrib Jiddah na xaune parlor bayan ta sha drugs din da Ahmad ya siyo mata, tana cin shinkafa da miya da Maimoon ta kawo mata, a hankali take cin abincin don baya ranta, gaba daya ji tayi xuciyarta babu dadi, Safiyya da Maimoon na haddansu a daki, Hajja da Umma kuma na daki, ita kadai ce xaune parlon sai Huraira dake wanke wanke a kitchen, tun da ya shigo parlon ta kallesa sau daya bata sake kallonsa ba, ya karaso tsakar parlon, ita dai taki yarda ta kallesa, looking at her directly yace "Don nace xan mayar da ke in da na dauko ki shine kika fara rashin lafiya, sabida baki da intention din sake komawa gidanku, ni ban ta6a ganin wanda ke gudun gidansu ba sai a kanki, ai xamanki a can xai fiye maki xama gidan mutane...." Ta daga kai ta kallesa tace "Toh sai ka mayar dani ai yanxu, ni bana tsoron komawa gida... Saboda nasan Allah na tare da ni, ko kaji nace maka baxan koma ba?" Yace "Toh sai ki tashi ki dauko hijab din naki yanxu" Mikewa tayi ta wuce daki, shi ma ya tafi dakin Ahmad ya dau makullin motarsa, Ahmad na kallonsa da mamaki yace "Ba Umma tace ka bari gobe ba" Ba tare da ya kallesa ba yace "Ehh ba nisa xanyi ba, i want to get something" Bai jira cewar Ahmad ba ya nufi kofa ya fita, Jiddah na daukan Hijab dinta dake linke Maimoon ta kai karshen ayan da take karantawa, tana kallonta tace "Ina xaki?" Jiddah taki kallonta balle taga hawayen dake makale idonta tace "Xan amso abu wajen Maman Abdallah ne" Daga haka ta fita dakin, yana tsaye bakin kofar parlor alamar ita yake jira, ta nufi kofar, muryar Hajja suka ji tana cewa "Ke ina kuma xaki da daddaren nan bayan nace ki min linke uwar rikon ki ta daure maki kugu wai baki da lafiya?" Jiddah ta kasa juyowa, Abuturrab na ganin Hajja ya fita parlon ya tsaya balcony, Ahmad ne ya shigo parlon shi ma yana kallon Jiddah yace "Where are you going to Jiddah?" Still bata juyo ba hawaye na sauka idonta tana gogewa da hannunta, ya karasa ya tsaya gabanta yana kallonta, buda ido yyi sosai ganin kuka take, yace "Me ya faru Jiddah" Hajja ma ta karaso tana kallonta tace "To ko dai tana da mutanen boye ne Ahmad?" Ahmad dai bai ce komai ba sai kallon Jiddah yake, Hajja tace "Aa ba ruwana bari in kira Ramlah kar abu ya lalace mana" Tana fadin haka ta tafi da sauri, Ahmad yayi kasa da murya yace "Gaya min me ya faru Jiddah, kuma ina xa ki?" Ta kasa cewa komai sai hawaye, Hajja ta dawo tare da Umma, Umma tace "Jiddah" Juyowa Jiddah tayi da jajayen idonta tana kallonta, Umma ta karasa kusa da ita tace "Me ya faru?? Kukan me kike, an maki wani abu ne" Shigowa parlon Abuturrab yyi xai wuce daki, Jiddah na kallonsa tana share idonta a hankali tace "Ce min yayi xai maidani inda ya dauko ni tunda shi ne ya kawoni dama ba wani ba" Gaba daya duk suka juya suna kallon Abuturrab da yaki kallonsu kuma yaki tsayawa, cikin tsawa Umma tace "Dakata a nan Aliyu" Ba musu ya tsaya amma bai juyo ba, Hajja ta marairaice tace "Wannan wani irin Bala'i ne Usman ya haifo Ramlah?" Umma ta kalli Jiddah fuska a daure tace "Gaya min abubuwan da ya fada maki" Cikin rawar murya Jiddah tace "Kawai haka nan yace, wai duk me son daukoni sai ya je ya dauko ni idan ya maidani hayi" Umma tace "Yanxu Hijabin da kika sa hayin xai kai ki?" Jiddah ta gyada mata kai, Hajja tace "Amma daga d'an iska sai Aliyun nan wllh, Muna ta tausayinsa ba shi da lafiya ashe dabanci xai xo yayi mana a nan ni Dijeee, anya kana son gamawa da duniya lafiya kuwa d'an nan, ashe haka kake Aliyu" Cikin dakewa Umma tace "Aliyu!!" sai a sannan ya juyo ya kalleta tace "Xan baka takarda kayi list din duk abinda ka kashe ma Jiddah tun daga lkcn da ka fara saninta har xuwa lkcn da ka rabu da ita, idan ma kudin sun fi karfina xan kai ma Abbanka ya bada su, sannan after that wallahil azeem ka sake kallon inda Jiddah take, i mean ka sake kallan min ita wllh sai ka sha mamakina a duniyar nan, xan maka tijara Aliyu, babu kai babu Jiddaha har abada, idan kuma kai ka cika d'an halaq ka dauketa ka mayar da ita hayin kaga, sannan maxa ka kama hanya ka koma gidanku kada ka sake xuwa min gida, idan kuwa kayi gigin xuwa sai nayi maka walakancin da baka ta6a xato ba" Hajja tayi mitsi mitsi da ido tace "Algungumi kawai, ana ta tausayinsa ba shi da lafiya ashe shi abinda xai kawosa nan gidan daban, to wllh har abada kai da wannan baiwar Allahn don ta ma fiye min kai sau dubu yanxu tunda bata ta6a xagina ba balle manyanta, kai kuwa idan aka ce xa a kirga adadin xagin da ka min ai sai da a tafi kotu don xuciya xai iya dibana inki yafe maka, to meye kuma xaka sa yar mutane a gaba bayan an raba ku, ko dai har yanxu sonta kake bamu da labari? Banda tsautsayi ma da ya fada mata me xata yi da d'an banxa irin ka?" Umma da taji xuciyarta na tafarfasa tace "Wato shi yasa dama babu musu ka yarda ka biyomu don ka ci mata xarafi da mutunci, to wllh kayi na farko kayi na karshe, Jiddah da kake gani tafi karfin walakancinka yanxu tunda ba kai ke ciyar da ita ba, wanda kayi a baya ma duk nace kayi list a biyaka" Hajja tace "Ko ni sai in dage gidana daya in siyar a biyaka wllh" Sai a snn ya kalli Hajja yace "Saboda nace maki don ke nayi da xaki biyani" Da karfi Hajja tace "Huuuuu ka dai ji kunya duk ka xubda ladanka, gantalalle kawai" Ta gefen ido ya kalli Jiddah dake share hawayen da yaki tsaya mata, shi dai Ahmad ya ma rasa abun cewa sai kallon Abuturrab yake da mamaki, kofa Abuturrab ya nufa ba tare da ya kallesu ba kamar xai tashi sama, Hajja ta dafe kirji tace "Mu ka xaga ka fita Aliyu?? Mu??" Ko kallonta bai yi ba har ya fice gaba daya, da karfi Hajja tace "Wawa kawai me xuciyar Hafsah, da kyar idan matar nan bata faki idon Hauwa kana jariri ta dura maka nononta ba, don babu halinta da ka xubar al-qur'an" Umma na kallon Jiddah tace "Daga yau ko gidan uban wa kika hadu da shi kika sake kallon inda yake balle ki gaishesa ko wata magana ta hadaki da shi sai na sa6a maki, babu ke babu shi har abada, a duk inda xa ku hadu kuwa...." Hajja tace "Dama kina ganinsa ki gudu kiyi ta kanki, ko kuma ki fasa ihu kawai idan wani taimakon ne a kai maki da gaggawa, ni ai nafi kowa sanin halinsa tunda a hannuna aka haifesa, sau nawa idan an bata masa rai yake take kaza ya kasheta har lahira a lkcn ma yana d'an mitsitsi.... Yanxu ai sai dai ya take d'an mutum" Jiddah dai kanta na kasa, Hajja tace "Kuma tun ban tafi Masar ba ya xama d'an daba fa, fada ne kawai banyi ba kar uban ya kullaceni nayi tafiyata bakina alekum, wa ya sani irin mugun abun da ake koya masu idan sun daga jirgi sama, shi sa har yau ban yarda na hau jirgin da yake ja ba wllh ko don yanda ya tsaneni ma ba sai ya sake jirgin da gangan duk mu hantsulo kasa ba" tana fadin haka ta nemi waje ta xauna tana fifita saboda xufan da ta hada don bala'i, Umma na kallon Jiddah tace "Dauka abincinki ki wuce daki" Jiddah ta karasa a hankali ta dau abincin ta wuce daki, Hajja tace "Ni wllh don baxa ku yarda bane amma da kun bani yarinyar nan kawai in tafi da ita" Umma tace "Sai dai taje maki hutu" daga haka ta bar parlon. Jiddah ta maida hankali sosai a karatunta babu wasa, wanda hakan yasa Umma ke kara jin sonta a rai domin kwazonta ya wuce misali, both Islamic da western din duk she's flowing well, kusan duk bayan kwana biyu Yousuf ke xuwa gidan da daddare, kuma duk idan ya xo ba wai wani hira suke da Jiddah ba iyaka ya sake guiding dinta a karatun nata shi ma, yawanci kuma turanci yake nace mata ta koya, kuma babu laifi she is really catching up, duk weekend Ahmad ke shigowa kaduna sbda duba Ramlah dake laulayi, shi ma kuma yana assisting din Jiddah a bangarori da dama na karatunta. Umma na parlor ranan wata asabar Jiddah ta fito rike da wayarta dake ring ta karaso ta mika mata, Umma ta amsa tana duba me kiran nata, Ganin Ummi ke kira ta daga, bayan sun gaisa Ummi tace "Toh sun gama hada lefensu wai sai ki xo ki gani gobe xa a tafi da shi" Umma tace "Kai ba lallai ba yaya, Allah ya sanya alkhairi kawai" Ummi tace "Aa da dai ki daure ki xo din Ramlah xai fi" Umma ta d'an yi shiru kafin tace "Allah da kawai kin bari su tafi da shi goben Yaya, ai ba sai na gani ba" Ummi tace "Toh ni kuma nace ki xo ki gani" Umma ta d'an yi shiru sai kuma tace "Toh shkkn, bari ruwan ya tsagaita xan sa driver ya kawo ni ko da yamma ne" Ummi tace "Allah ya kai mu" ajiye wayar tayi ta ci gaba da kallon da take a Tv. Da yamma kamar yanda Umma tace ta shirya wajen karfe biyar ta fito parlor tana kallonsu Maimoon da basu je Islamiyya ba sbda ruwan da aka yi, tace "Xa ku je can gidan ne ganin lefe?" Maimoon ta mike da sauri tace "Eh Umma dama ina tsoron gaya maki ne" Umma tace "Toh sai ku shirya ni ina ruwana kuma da xan hana ku" Maimoon da Safiyya suka mike gaba daya, ganin Jiddah bata motsa ba Umma tace "Ke baxa ki ba Jiddah?" jiddah ta girgixa kai tace "Aa xanyi assignment dina Umma" Umma tace "Ai ba dadewa xa muyi ba, tunda babu kowa gidan kawai ki shirya mu je yanxu xa mu dawo, idan muka tafi ma babu ke Hajja sai ta fassara mu tace ba a haka a Masar" Jiddah bata iya tace ma Umma komai ba, amma ba don ranta ya so ba ta mike ta wuce daki, Hijab ta saka suka fito parlon tare da su Maimoon...... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind Bridal kit:18k Beauty kit:11k Student package:7k Herbal whitening soap:3k Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝 Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166 Slowly Jiddah ke tafiya kamar bata son yi a compound dinsu Abuturrab, su Maimoon duk sun yi gaba tare da Umma, ita ce karshen shiga parlon, tsaye tayi bayan kujera ganin Abuturrab dake sakkowa cikin parlon waya kare a kunnensa, tayi bakin kokarin ganin bata kallesa ba, bayan ya shigo parlon ta xaga ta bayan kujera tayi wucewarta part din Ummi ya bi ta da kallo, Bayan Jiddah ta gaisa da Ummi, Ummi tace "Ki tafi dakin Hajja suna can" Mikewa tayi tace "Toh" sannan ta fita xuwa dakin Hajja, Umma na xaune su Maimoon na ta bude akwatunan da aka jera a dakin, Hajja tace "Yanda kika san wata yar gwal xa a auro, haka aka hada lefen har da na Allah ya isa..." Akwatuna biyar ne set biyu each da kit, Umma ta dinga kallon uban kayan da aka hada na lefen bayan su Maimoon na ta budewa, Hajja tace "Aa kar ki ji komai Ramlah ai nace duk xan dibar ma kanninsa abinda ya sauwaka a ciki, mu ba 6arayi bane da xa mu kai masu wannan ubansun kayan, ni kaina xan cire atamfa me tsada daya da jaka, takalmin ma baxai min ba sbda me tsini ne kar in je in karye shi sa baxan dauka ba, amma duk wa ennan yan matan xan cire masu duk abinda Allah yayi wllh" Umma tace "Aa Hajja ki bar masu kayansu kawai, Allah ya sanya alkhairi, ya bama yan baya haka" Hajja tace "Kaji wata magana irin ta 'yan kasar nan, wllh wllh babu shegen da xai yi haka a Masar, sannan me yasa baki bari Ahmad ya hada ma Ramlah irin wannan lefen ba? Ba shi ma yana da dukiyar ba na samu labari?? to shine ni xaki ce jikana ya dauka ya kai ma su gaba daya sbda sata yake yi a sararin samaniya? Aa wllh duk xan bi in rage ni ba gantalalla bace" Umma bata kuma ce mata komai ba, ita dai Jiddah na xaune ta rakube jikin kujera tana bin akwatunan da kayan ciki da kallo. Abuturrab ne tsaye parlon step mum dinsa da duk ta firgice masa, yayi kasa da murya yace "Toh ke ba dai kinsan duk abubuwan da kika xuba a ciki ba Aunty, komai kika ga yayi missing kar ki damu xan bada kudi ki siya wani ki saka" Aunty tace "Ni dai cewa nayi ka tafi ka xauna a dakin, idan aka ganka babu wanda xai ta6a komai cikin kayan, kafi kowa sanin Hajjan nan fa" Abuturrab ya girgixa kai yace "Aunty don girman Allah ki bari su yi ta daukan duk abinda suke so ni xan sake replacing, i just can't go to that room" Aunty ta wani hade rai tana kallonsa tace "Wato ban isa da kai ba Aliyu, ban isa in sa ka abu kayi ba??" Yace "Toh shkkn, bari in je" Daga haka ya juya ya fita parlon, sai da ta bisa ta tabbatar ya shiga dakin Hajja sannan ta koma parlonta, Ya d'an shafa kai bayan sun hada ido da Umma da ladabi yace "Ina yini" Banxa tayi masa, su Maimoon suka gaishe sa yace "Lafiya lau" Jiddah dai tunda ya shigo bata kalli inda yake ba idonta na kan akwatuna, Hajja dake ta fiddo kayan akwatunan tare da Safiyya ta mike tana kallonsa tace "Lafiya ka shigo kayi mana sandandan a kai Aliyu?" Yace "Takardan da na baki nake so in amsa yanxu" Hajja ta kalli Umma tace "Kinga jaraba ko, tun fa ban tafi Masar ba ya bani wasu shegun takardu da ban san isilinsu ba yanxu, shekaranjiya ya xo nace masa yayi hakuri ban san wani shirgin suka shigw ba amma har gidana xan sa aje a bude mu shiga mu bincika ko da rabon a gani, a haka muka rufe kess din da shi, to meye yanxu xai dawo ya tsaya min in basa takardu kamar wasu takardun jaraba, to gaskiya ban san isilinsu ba ka rabu da ni, ni bance ka dauko takarda ka bani ba" Daga haka ta ci gaba da abinda take, Umma ko kallon direction din Abuturrab bata yi ba banda daure fuska da tayi, Hajja ta dauki wani gyale me kyau ta jefa ma Maimoon tace "Gwada wannan" Umma ta girgixa kai tace "Hajja nace ki bari don Allah, wannan bai dace ba..." Hajja ta mike ta katseta tace "Kinga baiwar Allah tashi kiyi wucewarki in gama abinda nake, babu ruwanki da harkana, kin wani narka uban kiba kina bani oda kamar yar ki, nace ki tafi asibiti a dubaki kin ki, Da a Masar ne da tuni an kai asibiti wllh, to kuma ina ruwanki da abinda nake banda dai kawai kina kanwar uwar Aliyun uwa daya uba daya" Umma ta mike tace "Toh Allah ya sanya alkhairi na ga lefe sun yi kyau Maa sha Allah, Allah ya nuna na yan baya haka" Hajja tayi banxa da ita, Umma ta nufi kofa ta fita, Hajja tace "Banda kema cutar Aliyun xaki yi tunda ba ke kika haifesa ba kuma haushinsa kike ji kamar ki kashesa, wacece ita wannan yarinya da xa a kai ma lefe guda sha biyu komai na ciki kuma dozen dozen, ina kokarin ragewa kuma xaki kawo min raini, to wllh baxai sa6u ba, Dukiyar Aliyu ba banxa ba..." Rungume hannu Abuturrab yyi yana kallon Hajja, ta dau atamfa daya me tsada ta jefa ma Jiddah tace "Yayi maki kyau ko a canxa?" Jiddah ta bude ido sosai tana kallon Hajja, ta dau jaka ta jefa ma Maimoon ma, a takaice dai sai da ta ajiye ma Jiddah atamfa, mayafi, da jaka da takalmi da kayan kwalliya, su Maimoon ta basu kayan kwalliya da mayafai kawai duk don sbda haushin abinda Umma tayi mata, Jiddah dai gabanta sai faduwa yake tana kallon kayan gabanta, Hajja ta nemi waje ta xauna tana kallonsu Maimoon tace "Toh ku kulle masu kayansu, Allah ya sa albarka a abinda suka rage" Maimoon da Safiyya duk suka rufe akwatunan, Sai a sannan Abuturrab ya juya ya fita daga dakin, sai bayan da ya fita Hajja ta nemi ledoji duk ta sa ma kowa abinda ta basa a ciki, Jiddah dai duk jikinta yayi sanyi ta ma kasa ta6a ledan da Hajja ta ajiye mata a gabanta, Hajja tace "Ki tafi kice ma Zubaida take ko wa, kice mata baxata bani ruwan xafin bane in shiga makota in samo?" Jiddah ta kalleta don bata san ko da wa take ba, Hajja tace "Da ke nake, tunda barinsu kika yi da rufe akwatin kin xauna kamar sarauniya, banda dai Allah ya rufa maki asiri Usman ya rufa maki asiri ai da ke xa ayi ma kishiya yanxu, to kamar ya san da haka yasa aka sakeki" Mikewa Jiddah tayi ta nufi kofa ta fita, xaune ta tadda Abuturrab shi kadai a main parlor, duk da sun hada ido tayi wucewarta xuwa kitchen, bata tadda mai aikin a kitchen din ba, tayi ta tsayuwa daga karshe kuma ta fito, taki kallon inda Abuturrab yake ta wuce dakin Hajja, tana kallon Hajja tace "Hajja bata kitchen din" Hajja tace "Toh ta ci kanta, tafi da flask dina idan kin ga an daura ruwa ki juyo min ko bai yi xafi ba, tun daxu nake bin bakar matar ta ban ruwan xafi in sha shayi ta ki, Da a Masar ne wnn ruwan da aka tsuga yau ko wani gida kya ga butan tafasasshen shayi da kofuna kowa na ta sha" Jiddah bata ce komai ba ta dau flask din ta fita, har sannan Abuturrab na xaune parlon, tayi wucewarta kitchen, ta bude tukunyar da ta gani kan gas taga ruwa ne amma bai tafasa ba, ta dau cup kenan xata fara xuba ruwan cikin flask aka bude kofar kitchen din, sosai taji gabanta ya fadi wanda hakan yasa bata san lkcn da ta saki flask din hannunta ba, da sauri ya karasa ya amshi cup din ruwan xafin hannunta shi ma kar ta sake, iyakar rikicewa ta rikice a lkcn, cikin rawar murya tace "Ina yini" jin bai amsa ba ta durkusa ta dau flask din ta ga ya fashe, sae a sannan ta kallesa hankali tashe tayi narai narai da ido tace "Na shiga uku flask din ya fashe, me xan ce mata?" Yace "Ni kike tambaya?" Ta goge hawayen da ya kawo idonta, yace "Toh yanxu da kika hadani da Umma da Every of my family sae aka yi yaya?" Bata tsaya basa amsa ba tabi gefensa rike da flask din xata fita kitchen din ya jawota, kallon mamaki tayi masa yace "Ki bani amsata" Tace "Ni bani da amsan da xan baka" ya dinga kallonta, taki yarda ta kallesa, ya karbi flask din hannunta ya fita ta bi sa da ido, Hajja ta dinga kallon Abuturrab bayan ya shigo dakin, ya ajiye mata flask din gefenta yace "Ga flask dinki ya fashe sai ki fadi nawa kika siya a biyaki...." Da farko Hajja bude baki tayi tana kallonsa, sai kuma ta dauka da sauri ta jijjiga, lkci daya ta sake flask din ta mike sai kuma ta fashe da kuka tace "A Masar fa mijin Nafisa ya siya min flask din, waye yayi min wannan aika aikan??" Abuturrab yace "Ni ne, kuma shi yasa nace ki fadi nawa yake" Tace "Toh Allah ya isa wllh, don kaf dukiyarka baxasu siya min flask din ba tunda a Masar aka siye sa ba a kasar nan ba, sannan me ya kai flask dina hannunka bayan wancan matar na ba ta juyo min ruwan xafi?" Yace "In dai kin tambayi nawa aka siya sai ki gaya min" Daga haka ya juya ya fice daga dakin, ta fashe da kuka tace "Allah ka dai ga wannan xaluncin da aka min, a ina xa a samo flask irin wannan yanxu a kasar nan" Komawa gefe Jiddah tayi da sauri bayan Abuturrab ya fito don tana labe bakin kofar, ta bi sa sa kallo har ya wuce sannan ta shiga dakin gabanta na faduwa, a fusace Hajja tace "Ke garin yaya flask dina yaje hannun wancan mutumin da ya tsaneni?" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Dauka yayi Hajja" Hajja tace "Toh yaje shi, ni ba yafewa nayi ba, kuma bari Usman ya dawo tunda shi na haifa" Ita dai Jiddah bata ce komai ba. Bayan magrib Umma ta ajiye ma Ummi duk abinda Hajja ta ba su Jiddah da Maimoon na kayan lefe, Ummi tace "Ki bar masu kawai tunda ita ta basu" Umma tace "Aa maida masu da kayansu yaya, a ina aka ta6a haka" Ummi tace "Wai ba ni nace ki bar masu ba??" Umma tace "Toh Allah ya kyauta bari in je in ma Hajja sallama" Daga haka Umma ta fita bangarenta, a corridor suka hadu da Aunty xata sakko parlor, Aunty tace "Aa Hajiya Ramlah ashe kun shigo, mun wuni lafiya?" Umma tace "Alhmdlh" Aunty tace "Tun shekaranjiya nake ta ce ma Ummi ta kiraku an gama hada lefe wllh..." Umma tace "Ai kam kaya maa sha Allah, Allah ya sanya alkhairi" Aunty tace "Toh ai ni na xata kin xo kenan sai mun dawo daga kai lefen, kin san gobe ne xa a kai fa da safe" Umma tace "Aa sai kun dawo Hafsah, ni ba wani dadi nake ji ba, Allah ya kai ku lafiya ya dawo da ku lfya" Aunty tace "Ehh tun da ma da ni xa aje shkkn kawai, Allah ya kara lafiya..." Umma dai ta wuce dakin Hajja, Aunty kuma ta sauka parlor, Ummi na kallon Jiddah dake parlonta ita kadai, su Maimoon kuma na daki wajen Ramlah tace "Kwashi kayan ki kai mota Jiddah" Jiddah ta mike ta dau ledojin kayan da Hajja ta basu ta fita, Aunty dake xaune parlor da wata bakuwa da tayi, Abuturrab ma na parlorn don kudi ta kirasa xai tura ma bakuwar wai na zoben gwal guda biyu da xa a sa ma Aneesah a lefen, ta bi Jiddah da kallo tana kare ma ledojin hannunta kallo, shi ma Abuturrab kallonta yake, Jiddah ta gaisheta ta nufi kofa ta fita, mikewa Aunty tayi tace ma bakuwarta tana xuwa sannan ta fita da sauri, shi dai Abuturrab bai ce mata komai ba, a compound ta tsayar da Jiddah ta amshi ledojin hannunta tana duba abubuwan ciki, kwace dayan ledan tayi da karfi tace "Ubanki ne ya siya kayayyakin da aka baki ki kai mota??" Jiddah dai tayi shiru tana kallonta, Aunty tace "Baxa ki daina kallona cikin ido ba sai na tsole idanuwan?" Sunkuyar da kai Jiddah tayi, Aunty ta juya kamar xata tashi sama ta koma cikin gida, Abuturrab na kallon Aunty bayan ta xauna a parlor ta ajiye ledojin da ta amso a gefenta yace "Aunty da baki amsa ba ai ni nace xan siya duk abinda babu a ciki" Aunty tace "Rufe min baki, kai xaka gaya min abinda xanyi da wanda baxan yi ba, duk wanda bai rike girmansa ba xai ga rashin girma a gidan nan wllh, a kan me xa a debe ma yarinya kaya wannan ai karanta ne wllh, wannan abun kunya har ina kawai a bude lefen yarinya a yashe mata kaya??" Umma da ta shigo parlon tare da Ummi ta kalli Aunty amma bata ce mata komai ba suka fita parlon tare da Ummi Aunty tace "A gaida gida" a compound suka ga Jiddah a tsaye, Umma tace "Ina kayan? Kin kai mota?" A hankali Jiddah tace "Aunty ta karba" Juyawa Umma tayi ta koma parlon, Ummi ta bi ta da kallo sai kuma ta bi bayanta, Umma na kallon Aunty tace "Kayan da kika amsa xa ki bani Hafsah" Aunty tace "Wllh baxan bada ba Hajiya Ramlah, wannan ai ba girmanku bane daukan kayan yarinya, wannan ai karanta ne, ku idan aka ma 'ya yanku haka xa ku ji dadi??" Ummi ta kalli Abuturrab tace "Aliyu" ya daga kai ya kalleta, tace "So nake ka kwashe akwatunan nan gaba daya ka kai su gidan Ramlah da daddaren nan" Aunty tayi wani shewa tana tafe hannu tace "Gidan Ramlah? To ai naga ba Ramlah bace ta hada lefen, don haka xan ga me kwasan akwatuna ya fita da su gidan nan yau...." Shi dai Abuturrab kallon Ummi ya dinga yi ya kasa cewa komai, Hajja ta fito rike da fasasshen flask dinta tace "Me ke faruwa na ganku cirko cirko a tsaye?" Aunty na kallon bakuwarta tace "Xa a tura maki kudin na biyun ki tafi gida kawai Salaha" Daga haka ta bar parlon kamar xata tashi sama, Salahan ta mike ta fita parlon, Ummi na kallon Abuturrab strictly tace "Kaji abinda na gaya maka?" Yayi kasa da murya yace "Ummi duk bai kai haka ba, don Allah..." Wani tsawa tayi masa tace "I said take away the boxes to Ramlah's home" Hajja tace "Naga ikon Allah, na tambayi me ke faruwa an min shiru" Ummi tace "Cewa nayi ya kwashe akwatunan ya mayar gidan Ramlah daga can xa a kai su" Hajja tace "Atohh a kira mai gadi ya fitar da su xuwa motar mana me ake jira" Kallonta Abuturrab yyi fuska daure, Ummi tace "Ya fita ya kira mai gadin da kansa, idan ba haka ba wllh wllh baxa a kai kayan nan ba, kuma kudin da aka kai sai dai a yafe shi...." mikewa Abuturrab yyi yana kallonta, Ummi ta juya ta bar parlon Umma na biye da ita. Hajja ta nufi kofa don kirawo mai gadi tana cewa "Aa bai kai haka ba Hauwa ni da kaina sai in je in kira mai gadin a fito da akwatunan" Abuturrab ya koma ya xauna ya rike kansa ya rasa tunanin da xai yi, mikewa yayi ya nufi bangaren Aunty.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 07046881166 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare Waya Abuturrab ya tadda Aunty na yi a parlonta rai bace, ko ba a fada ba yasan da wanda take wayar, yana dai tsaye har ta gama ta jefar da wayar kan kujera tana huci, ya kwantar da murya yace "Aunty duk bai kai wannan extent din ba, pls i want u to calm down...." A fusace tace "Ya kai har ya wuce extent din da kake fada, kuma wllh xan ga uban da xai fitar da kayan nan a gidan ga yau, sun san da nuna ikon me ya hanasu wahalan hada lefen? Tun da na fara hada kayan nan kullum sai na fita kamar yar iska, kuma bani xan shigo gidan nan ba sai karfe takwas din dare, to a kan me ba a ce min Allah ya shi min albarka ba xa a dinga bata min rai ana sa ni a bakin duniya?? To wllh wllh Ramlatu ta fita harkata, ta fita idona in rufe idan kuwa ba haka ba xan kai kararta ba wani shege, ko kuma in kai ta gani ga ka ayi min iyaka da ita" Abuturrab dai kallonta kawai yake, wayarta ne ya fara ring ta dauka ta shige daki a fusace ta kulle kofar, Abuturrab ya shafa kansa sannan ya juya ya fita daga dakin, bangaren Umminsa ya shiga, ya kasa kallonta ya xauna saman kujera cikin sanyin murya yace "Ummi don Allah kiyi hakuri, duk bai kai haka ba" Ummi tace "Inyi hakuri da me??" Kasa cewa komai yayi, Ummi tace "Wllh in har akwatunan nan suka kwana gidan nan sai dai ka nemi wata yarinyar da xaka aura ba wannan ba Aliyu" Umma dai na xaune tana danna wayarta tana girgixa kafa, Abuturrab bai kuma cewa komai ba ya mike ya fita parlon, a main parlor ya tadda Hajja tsaye bakin kofar parlon da su Maimoon, sai ga mai gadi ya fito daga dakinta rike da akwatuna biyu a hannunsa, Hajja ta basa hanya tace "Yanxu saura nawa?" Mai gadin yace "Saura hudu" Hajja tace "To yi maxa..." Mai gadin yayi kofar gida da akwatunan ya saka au booth din mota da driver din Umma ya bude sannan ya koma ciki da sauri, Hajja ta kalli Jiddah dake tsaye wajen balcony din tace "Toh ke wa kike da suna, ki kwashi kananun da ya ajiye a nan ki kai mota da tsayuwar nan, ki daina lagwai lagwai kamar ba mace ba kinji??" Jiddah bata ce komai ba sbda bata son mata musu ta dau kit din biyu ta nufi gate, Banda hararan Hajja babu abinda Abuturrab yake daga inda yake tsaye, can ya nufi kofar kamar xai tashi sama, Hajja na ganin haka ta basa hanya da sauri, bayan ya fita ta kalli su Maimoon tace "Kun ga d'an banxan ko? Kunga irin dabancin nasa ko?? Da ban kauce ba bangajeni yayi niyyar yi fa, anya wannan Aliyun da na tafi Masar na bari kenan shekaru uku da suka wuce? o,o to baxan biyesa ba, ba ruwana ni ba yarinya bace, kuma sai dai ya bangaje Hauwa ko Usman, ko kuma yar Benuen can, amma ba ni ba tunda ban hada komai da shi ba ai" Jiddah na ajiye kits din bayan booth taki komawa cikin gidan tana tsaye jikin gate har ranta bata jin dadin abinda ke faruwa, Abuturrab ya fito compound din, kallon driver din Umma yayi yace "Wa yace ka saka akwatunan a bayan mota?" Drivern ya xagayo da sauri yace "Aa kawai ni bude booth nayi ake xubasu a ciki" Calmly Abuturrab yace "Toh sauko da su" Kallonsa Jiddah ta dinga yi da mamaki, Driver ya koma gun booth da sauri xai sauke kayan, kafin driver ya fara sauke kayan ta daure tana kallon Abuturrab tace "Ina son in maka wata tambaya don Allah..." Sai a sannan ya kalleta, tace "To ka d'an ce masa ya jira kafin ya sauke kayan, kaji?" Driver ya kalli Abuturrab din dake ta kallon Jiddah da mamaki, Ta koma gefensa tana kallonsa, kana ganinta kasan she is afraid of talking to him, gathering many courage ta fara magana tana wasa da fingers dinta "Dama ina son in san wacece Baabarka a cikin Aunty da Ummi, ni har yanxu ban sani ba" Daga sama har kasa ya kalleta, ta ci gaba da magana ba tare da ta yarda sun hada ido da shi ba tace "In dai Aunty ce Baabarka to kayi dai dai idan kace a sauke akwatunan nan, tunda ai ba a wasa da maganan uwa, idan kuma Ummi ce Baabarka...." Sai kuma tayi shiru, yana kallonta da kyau yace "Ina jin ki" Cikin sanyin murya tace "Kaga ni ban samu gatan sanin mahaifiyata ba, na taso cikin maraicinta, saboda maraici da rashinta yasa na taso cikin rashin gata da kula..." Hawaye ya kawo idonta tana gogewa tace "Da mahaifiyata na nan duk abubuwan da suka faru dani da nasan baxa su faru ba, ko yan uwanta ni ban samu daman sani ba, bansan ko tana da yayyi ko kanni ba, ban ma ta6a ganinta ba" Ta kasa ci gaba tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, shi dai kallonta kawai yake, cikin sanyin murya tace "Toh kaga duk wanda baya ba Baabarsa muhimmanci baxai ji dadin rayuwarsa ba, kuma xai hadu da fushin Allah" Sai kuma ta daga kai ta kallesa tace "Albarkacin haifanka da Ummi tayi kaji maganarta na yau kawai mana, tunda tace bata son a bar kaya a nan ka bari a tafi da su xai fi, ko kai baka son ka xauna lafiya da matar da xaka aura?" Hajja ce ta fito gate din gidan tana yafa gyalenta da yar jakarta a hannu tace "Ina matukin motar yake mu tafi" Drivern Umma ya xagayo da sauri yace "Gani Hajiya" Tace "A ina xan xauna a motar?" Bayan motar ya bude mata ta shige ba tare da ta kalli su Abuturrab ba tana cewa "Bari in fara yin gaba da kayan" tana shiga ta kulle motar, Drivern dake ta kallon Abuturrab yana jiran wani instruction din jin bai ce komai ba ya xaga ya shiga motar ya tada suka bar layin... Jiddah ta daga kai ta kallesa ganin kallonta yake ta sunkuyar da kanta gabanta na faduwa, ya gyara tsayuwarsa yace "Ohk, shikenan kin gama?" Shiru tayi da farko, sai kuma ta girgixa masa kai a hankali tace "Aa, yanxu don Allah kaje ka ce Ummi tayi hakuri ta yafe maka, sai kace mata Hajja kuma ta riga ta tafi da kaya" Yace "Koh?" Ta d'an kallesa, sai kuma ta sauke kanta ta gyada masa kai, yace "Ohk, kalleni" Kin yarda ta kallesa tayi, yace "Kalleni nace" Ta dake ta dago kai ta kallesa yace "Toh daga yau... Kika sake sako min baki a abinda ya shafi rayuwata sai na mareki, ke har xaki gaya min abinda xanyi da wanda baxan yi ba? " Jiddah dai bata ce komai ba, kawai ta juya ta nufi gate ya bi ta da kallon mamaki yace "Kee" ko waigowa bata yi ba, yace "Ba magana nake maki ba" Tayi shigewarta gate, shafa kansa yayi sai kuma ya bi bayanta. Parlor ya tadda ta xaune tare da su Maimoon, bai kalleta ba ya wuce bangaren Ummi, har sannan Ummi na xaune da Umma dake ta bata hakuri, kansa a kasa ya xauna kan rug din parlon, da kyar yace "Ummi don Allah kiyi hakuri ki yafe min, in sha Allah duk yanda kika ce xa ayi hakan xa ayi, kaya kuma na sa Hajja ta tafi da su can gidan Umma" Dama bai sa ran Ummi xata basa amsa ba, hakan yasa ya kalli Umma ita ma yace "Ku yi hakuri Umma, in sha Allah hakan baxai sake faruwa ba, duk yanda ku ka ce haka xa ayi, kaya kuma duk ranan da ku kace a kai sai a kai, kuyi hakuri don Allah" Yana kai wa nan ya mike ya nufi kofa duk suka bi sa da kallo, ba Ummi ba har Umma tayi mamaki sosai ba kadan ba, abinda bai ta6a yi ba kenan duk rayuwarsa karkari ya je ya ba stepmom din tasa hakuri ya bar gidan sai kuma randa aka gansa, Ummi tace "Wannan ba xuwan kansa bane..." Umma tace "Aa nima nayi mamaki, ko Hajja ce dai..." Ummi ta kalleta da sauri tace "Wacce Hajjar? Shi dai ya san what he is up to shiyasa ya shigo bada hakuri, amma this is so unusual of him, ni bai ma ta6a bani hakuri ba" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh koma dai menene tunda ya shigo kuma yace ayi hakuri, sannan yace Hajja ta tafi da kaya kawai kiyi hakuri yaya" Ummi dai bata ce komai ba. Abuturrab na fita Bedroom dinsa ya shiga ya sa makulli, wayarsa dake hannunsa ya fara ring ganin Abba ke kiransa ya daga, Abba yace "Kana ji na Aliyu?" Abuturrab ya xauna gefen gado yace "Ina ji Abba" Abba yace "Plss ka lallaba iyayenka duk yanda xa ayi kar a fitar da kayan nan daga gidan nan... It should remain their gobe a kai su" Abuturrab ya shafa kansa yace "Abba Hajja ae ta tafi da su" Abba yace "Ta tafi da su?? Amma baka yi making ko wani effort na hana tafiya da su ba Aliyu??" Yyi kasa da murya yace "Abba Ummi ta dau lamarin da girma ne, tayi fushi sosai, and...." Abba ya katsesa yace "And what nonsense? Ita kuma Hafsah fa? Ni nasan yawancin abubuwan dake faruwa gidan nan duk Ramlah ke xuwa ta hada, a kan me su basu hada lefe ba kuma su 6ata ma warce ta hada rai kana kallo Aliyu??" Shi dai Abuturrab yyi shiru, Abba ya katse wayarsa, kallon wayar Abuturrab ya dinga yi sae kawai yaji bai ji dadin abinda Abba ya fada ba har ransa, can ya mike ya koma parlon Ummi..... Hauka ne kawai Aunty bata yi ba bayan Aisha ta kai mata rahotun ai har an fitar da akwatuna xuwa gidan Umma, ta fito parlor tana kai koma inda take shiga ba nan take fita ba, xage xage ta dinga yi kamar yar maguzawa, su Maimoon da Jiddah dai na xaune parlorn, Umma da Ummi duk na jin ta, Abuturrab dake parlon Umminsa yace "Umma muje in ajiye ku gida yanxu tunda driver din bai dawo ba" Umma ta ki tashi, Sanin at anytime Umma na iya tanka Aunty yasa Ummi tace "Ramlah dare nayi ku tafi a ajiye ku a gida" Umma ta mike ta dau wayarta tace "Sai mun yi waya yaya" daga haka ta fita Abuturrab na biye da ita bayan ya ciro makullin motarsa a aljihu, Umma bata ko kalli Aunty ba tana kai xuciyarta nesa tace ma su Jiddah su taso su tafi, daga haka ta fita parlon, Mikewa Jiddah tayi ta xaga xata wuce ta bayan Aunty dake tsaye tsakar parlon dab da ita tana kumfar baki, Aunty na ganin haka ta fixgota a fusace ta sauke mata lafiyayyen mari tace "Don uwarki ta bayana xaki bi ki wuce duk ga hanya a gidan sbda ni sa'ar uwarki ce fitsararriya?? An aiko ki wajena ne xaki bi ta bayana, to koma wa ya aikoki ki koma kice masa na fi karfin sa, baki gan ni ba, kaji min dai yarinya xaki xaga ta bayana duk ga hanya a parlo??" Bude baki Abuturrab yyi ya tsaya yana kallon Aunty, Jiddah ta kasa motsawa tana dafe da kuncinta ta rufe ido, hakan ya kara tunxura Aunty ta fincikota tana jan kunnenta tace "Ooo rashin kunya xaki min?" Karasowa Abuturrab yyi parlon cikin annoyance yace "This is mean of u Aunty, me ta maki xaki mareta haka? Who does that? Akan me xaki mareta a fuska, what offense did she commit?" Sake baki Aunty tayi tana kallonsa, can tace "Ni kake tambaya me yasa na mareta Aliyu?" Ko kallonta bai yi ba ya kalli Jiddah dake shessheka yace "Fita...." Taki motsawa hawaye na xuba idonta ya Fixgo hannunta ya nufi kofa, Aunty ta bi sa da kallo baki bude, sae bayan da suka fito balcony ya sake hannunta ta nufi gate tana goge idonta, Umma na tsaye jikin motar Abuturrab dake waje tana jiransa, har suka isa gidan Umma babu wanda yace komai a motar, Abuturrab yyi parking kofar gida Umma ta bude motar ta sauka, ta nufi gate Abuturrab ya bi ta da kallo, Safiyya dake gaban motar ta sauka, Maimoon ce karshen sauka a motar, yana kallon Jiddah kafin ta wuce yace "Dawo ki rufe min motata da kyau" Dawowa tayi ta bude motar ta sake rufewa sannan tayi wucewarta ciki. Washegari lahadi da yamma Jiddah na xaune balcony tare da Yousuf hannunta rike da Literature da ya sa ta karanta masa, mota ce ta shigo compound din, tunda ta kalli motar sau daya ta ci gaba da karatun da take Yousuf na kallonta, Ummi ta fara saukowa motar sannan Abuturrab ya sauka, suka nufo entrance din gidan a tare, tun basu kai balcony din ba Abuturrab ke kallonsu, Da ladabi Yousuf ya gaida Ummi ta tsaya Balcony din ta amsa da fara'arta, Abuturrab bai ko kallesa ba ya shige parlon, Jiddah ta gaida Ummi sannan ta mike ta amshi ledan hannunta, Ummi tace "Ki xauna kiyi karatun ki Jiddah... Don't worry my dear" Jiddah tace "Bari in kai ciki Ummi" Daga haka ta amshi ledan ta shiga parlon Ummi ta bi bayanta, dakin Umma ta nufa tare da Ummi, bayan ta ajiye ledan ta fito parlor, satan kallon Abuturrab tayi taga idonsa na kan TV, sai ta kasa wucewa bata gaishesa ba, hakan yasa ta d'an tsaya tace "Ina yini" Bai ko kalli direction dinta ba balle ya amsa fuskarsa daure, tayi wucewarta waje, tana dawowa balcony din ta dau literature din da ta ajiye sannan ta xauna Yousuf na kallonta, murmushi tayi tana duba page din da take, sai ga Abuturrab ya fito, ya nufi motarsa ya shiga yayi horn mai gadi na bude masa gate ya fice daga gidan, Yousuf ya kalli Jiddah yace "Is he alright?" D'an murmushi tayi tace "Nima ban dai sani ba" Yousuf yace "Naga baki gaishesa ba" Tace "Aa na gaishesa a parlor" Yousuf yace "Go on with ur reading" ba musu ta ci gaba da karatun yana kallonta. Aunty ce kwance kan gadon sister dinta godiya, Aunty ta mike xaune tace "Ni fa duk abubuwan da aka yi a gidan nan bai dameni ba don Alhaji ya tsaya min kuma ya dawo yayi ta bani hakuri wllh, ita ma Hauwan taga bacin ransa wllh kuma komai ya xo da sauki tunda uwarsa ba gidan ta kwana ba, abinda ya dameni shine yanda har yanxu Aliyu ya ki ce min komai a kan lamarin, tun da ya shigo sau daya ina waya da Abban nasa a daren har yau da nake maki magana bai sake ce min komai ba, ko a waya kuwa, abinda bai ta6a min ba, bayan xuwa ya bani hakuri sai ya sake kirana ya ban hakuri sannan ya tura min text kuma to wannan karan wllh duk babu" Godiya tace "Kuma yana gidan?" Aunty tace "Jiya Monday dai ya koma bakin aiki da safe, kuma ko baya gidan ma ai yana kirana a waya, to ni duk ba wannan ba, abinda ya bani shock shine yanda yake querying dina a kan dalilin marin talakan nan da ya je ya kwaso mana a hayi...." Godiya tace "Wai ba kince an gama case dinta ba har ma ya saketa? To me kuma ya hadasa da ita" Aunty tace "Toh ai har yanxu tana gun kanwar uwarsa, ta amsheta wai xata riketa har sun sa ta a karatu" Godiya tace "Toh sai ya maki magana don kin mareta ko ko?" Aunty tace "Wllh kuwa Kyauta, cikin bacin rai ya gaggaya min magana wai a kan me xan mareta sannan ya kada keyarsa ya fita, ni tsabar shock ma ban samu bakin ce masa komai ba" Godiya tace "Aa to da akwai lauje cikin nadi a wannan batun naki, me yasa xai ji haushi har yyi magana don kin mareta" Aunty dai bata ce komai ba ta ta6e baki abun na sake dawo mata ranta na k'una, Godiya tace "Toh ko dai bai saketa din bane dai Hafsah" Aunty tace "Haba dai ga takarda ubansa ya sa ya rubuta kowa ya gani, kowa ya shaida babu wani aure tsakaninsu, kawai toxarta ni yake da niyyar yi dama, amma ba komai in dai ni ce ya xuba ido" Godiya tace "Gaskiya kam, to yanxu ranan juma'ahn da munafukar kanwar Hauwan xa ku je kai kayan??" Aunty tace "Aa Alhaji yace in bar masu kawai suje su kai kayan ba sai naje ba, kuma ina ga da wannan takadiriyar tsohuwar xa a, kinga gwara ai inyi xamana, abu dai namu, ta wani bangaren fa uwa nake a gun amaryar, iyaka kawai ki shirya ki bi su don ki kwaso min rahotu" Godiya tace "Aa gwara kam kiyi xamanki ni inje, don na lura da take takensu so suke wani abu ya billo daga bangarenki a sa yaron ya fasa auren Aneesar tunda ai an san uwar Aneesar aminiyarki ce" Aunty tace "Yauwaaa ashe kin gano godiya, haka suke so ni kuma ba shashasha bace duk xan bi su a nutse ayi auren, shi sa kika ga na fara ja baya, ayi komai a gama su ga ko xasu sake iko da Aliyu kuma a rayuwar nan, ba uwarsa ba, wllh har ubansa sai ya nuna baya yinsa, balle wata kanwar uwarsa can, don tun farko ma shi bai dauketa mutum ba, su da Aliyu kuma sai dai hange daga nisa al-qur'an" Godiya tace "Shkkn kuwa Hafsah" Aunty ta d'an yi dariya tace "Allah dai ya kai mu lokacin lafiya, ai ni yanxu ido xan xuba ma kowa in ta binsu a samu a daura auren cikin aminci Aneesah ta tare" Godiya tace "Amma fa hankalina bai kwanta da xaman wannan yar hayin ba tsakaninku, tunda kinga dole dai Ramlah xata dinga xuwa da ita wajen yayarta..." Aunty tace "Toh sai me idan tana tahowa da ita, shi fa Aliyu bayan auren nan ko gidan ba xuwa xai dinga yi ba, tsaf xan masa iyaka da gidan wllh, kawai dai idan ina bukatar wani abu in shirya in tafi gidansa amma shi da gidan nan sai hange daga nesa.." Godiya tace "To da kyau hakan, Allah ya nuna mana auren nan lafiya" Aunty tace "Ameen, satu biyu kamar gobe ne ai in sha Allah" Godiya tace "Haka ne, bari in dubo mana girkin ko ya nuna" Daga haka ta mike ta fita dakin. Ranan Juma'ah Umma da frnds din Ummi biyu sai wasu yan uwan Abba da Godiya suka tafi kai lefen Aneesah garin Abuja, Hajja ta so xuwa amma Abba ya hanata don kar ya kullaceta ya sa ta hakura kawai suka tafi, sai ta 6ige da cewa su Jiddah ai ita ba yarinya bace dama da xa aje kai lefe da ita, banda ma an rainata ai bai kamata ayi mata xancen kai lefe ba tunda dai ita ba yarinya bace, iyayen Aneesah sun amshi su Umma da mutunci ganin uban kaya na gani na fada da aka yo ma yar su, ga zobunan gwal manya har biyu a ciki, Godiya dai na ta kwashe rahotun kai ma Aunty, aka yi komai cikin mutunci da girmama juna sannan su Umma suka juyo xuwa Kaduna..... Abuturrab na kwance dakin hotel dake cikin garin Lagos idonsa a lumshe kafin lkcn da xa su yi piloting jirgi xuwa kano yayi wayarsa dake gefensa ya fara ring, ya bude idanuwansa ya dau wayar ganin Aneesah ce ya daga ya kai kunne yayi shiru, cikin wani salo tace "Mijinaaa" Calmly yace "Ya aka yi?" Ta lumshe ido tace "I love you my Captain... Ina sonka fiye da yanda kake xato a ranka, I can't wait in ga na mallakeka a matsayin mijina" Shi dai sauraronta kawai yake, ta kanainaiye murya tace "I can't wait a daura in 2 weeks time, I can't wait to be ur wife officially My captain" Yace "Amma kin san wajen aiki nake Aneesah, i tot it's something serious u want to say" Tace "Ban gane something serious ba, wannan da nake gaya maka ba something serious bane?" Yace "Amma ba da rana ina wajen aiki ba" Tace "Ohk haka xaka ce min captain?" Yace "Ohk, i love you, idan na sauka kano xan kiraki..." Katse wayar yayi ya sa flight mode yayi rub da ciki ya lumshe ido. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 07046881166 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare Shirye shirye kawai ake babu kama kafar yaro a gidansu Abuturrab kasancewar kwana uku kacal ya rage daurin aurensa da Aneesah, kai kana ganin wannan shirin da ake kasan ba karamin biki xa ayi ba na first child of the family, tuni Umma ta dawo gidan da yan matan ta har da Huraira mai aikinta, yan uwa da abokan arxiki kuwa duk sun fara tahowa daga garurruka daban daban, Kamar yanda Aunty ta sanar ma yar uwarta godiya haka tayi a wannan period din, don sosai ta kwantar da kanta komai sai dai taje ta samu Umma taji yanda xa ayi, duk kuma yanda aka ce bata musu, har hakan ya ba Umma mamaki hatta idan wani shawara tayi da Abba sai taje ta tattago Umma ta xo taji ko shawaran yayi, ganin haka Umma ta sake gaba daya don da farko ko sakar mata fuska ta ki yi, ashe hakan ba karamin kona ma Hajja dake ta lura da su rai yake ba, ranan laraba wanda ya rage saura kwana biyu daurin aure Umma ta shigo dakin Hajja rike da babban cooler din soyayyan nama xata ajiye Hajja tace "Meye haka?? Aa ba ruwana da tarkace Ramlah, fita da shi gaskiya ki kai dakin Hafsah tunda naga dai ku ke aurar da yaro ke da ita" Umma ta tsaya tana kallonta, Hajja ta ci gaba da kakka6e gadonta fuska daure tace "Haka kawai kya shigo min da wani katon rubabben cooler daki kamar wata rubabbiyar tsohuwa, a ina xan sa shi? Kinga da ruwana da sha'anin bikin ku ne, ba dai kawai nasan ni na haifi uban Aliyun ba" Umma ta juya ta fita da naman, Hajja ta bi ta da wani shegen kallo tace "Idan ba gulma ba sai ki kama Hafsah ki rike hannu bibbiyu kuna abu gaban kanku bakwa sako kowa, in dai Hafsah ce ni nasan tana da wani mugun kudurin a ranta ne... Ahaf mu je dai xuwa, ni dai ba Allah ya so 'ya ta na hanya gobe ba, duk ita xan sa kan komai na bikin nan ai tafi ku kusanci da Aliyun tunda kanwar ubansa ce ita, sannan matan Kabiru duk suna hanya su ma gobe kwa sha mamaki ke da Hafsar, idan ma barbadensu na yan garin Benue tayi ta baki mu dai mun fi karfinta sai dai ke din da yayarki tunda naga ba a tsaye kuke ba" Tun da Jiddah suka xo gidan ko kallon inda take Aunty bata yi balle har tayi abinda xai sa ta 6ata likimon da tayi ma kowa, Jiddah ma bata yarda hanya ta hadasu, da ta ga Aunty a waje take barin wajen, duk Aunty na lura da hakan, sai dai tayi kwafa a hankali tayi murmushi, ita dai babban damuwarta yanxu a daura auren nan ran friday Aneesah ta xama mallakin Abuturrab tukun, yawanci Jiddah na gun Hajja tun xuwansu, don Hajja bata sa kowa aiki sai ita, a dakinta ma take kwana, da taga bata ji motsinta ba xa ta sa a kira mata ita ko a nemota, sauran yan matan kuma dama ta ce babu abinda ya hadata da su sun ma rainata. Washegari Thursday da safe Jiddah da Nafisa kanwar Abuturrab da ke boarding suna sharan parlor kamar yanda Umma ta saka su, Maimoon kuma na goge goge aka bude kofar parlon, duk suka daga kai El-Basheer ne ya fara shigowa sannan Abuturrab dake biye da shi a baya, Jiddah dai ta ci gaba da sharan da take, Nafisa ta gaida El-Basheer cike da murnan ganinsa yace "Ashe kin girma da yawa Feenah" Rungume Abuturrab tayi tace "Yaya sannunku da xuwa" Ya ja hancinta yace "Yaushe kika dawo" Tace "Tun ran Tuesday fa yaya" yace "To ya karatu?" Tace "Alhmdlh" Maimoon ta gaida El-Basheer ya amsa mata with smile, sannan ta gaida Abuturrab ya amsa a takaice, Jiddah ta dago tana kallonsu tace "Ina kwanan ku" El-Basheer yace "Lafiya lau, ya kike?" Tace "Lafiya lau" Dama Abuturrab bai amsa ba banda wayarsa da ya hau dannawa, Jiddah ta ci gaba da sharanta, kallon El-Basheer Abuturrab yayi ganin yanda yake kallon Jiddar, ya maida wayarsa aljihu ya nufi dakin Hajja, El-Basheer ya kallesa sannan ya maida dubansa gun Jiddah yace "Are you Asthmatic?" Ta daga kai ta kallesa amma bata ce komai ba, Maimoon tace "Aa bata da Asthma" yace "Ohk" daga haka ya bi bayan Abuturrab xuwa dakin Hajja. Hajja na ganin El-Basheer tace "Kai ma kaje kayi ma kanka fada Bashir, ba wai ka dinga yawo kana bin sabbin angwaye xalo xalo a baya ba, da ka san ciwon kanka yanxu ba cewa xaka yi a hadaku da wannan mutumi Aliyu ba, balle duka duka da watanni nawa ya girmeka? Amma ka tsaya shashanci kai a dole d'an sarki, to ko ni da nake uwar sarki bana abinda kake yi wllh" El-Basheer yace "Toh kin samar min matar ne nace maki bana so Hajja? Ni na xata Masar da kika je xaki samo min mata daga can fa" Ta marairaice tace "Wllh nayi niyya Bashir, Nafisah ce ta hanani wai su ba a haka a can, toh kaga kuwa ai sai inyi shiru in koma gefe tunda idan na botsare masu suka maido ni Najeriya sai inyi yaya, amma yanxu tunda har ka bani wuka da nama idan Allah ya yarda baxan baka kunya ba, yanxun ma na fara maka sha'awar wata yarinya wllh, baka ganta ba kyakkyawa doguwa jazur da ita kamar balarabiya, da ta bude min gashinta kuwa sai da na gigice, ga ladabi da biyayya sannan bata da kiwiya, komai aka sata yi take cikin dadin rai ga shegen hakuri, ai ni tuni na fara maka sha'awarta sai gashi ashe kai ma ni kake jira" El-Basheer yace "Toh fah, a ina kika samo min ita Hajja" Hajja tace "Sakin wawa ce..." Abuturrab dake danna wayarsa ya daga kai ya kalli Hajja, El-Basheer yayi dariya yace "Sakin wawa kuma Hajja, bazawara kika samo min kenan?" Hajja tace "ka ji ka da wani xance Bashir, wllh babu wanda xai ce ta ta6a aure, yarinya ce fa yar karama bata wuce Nafisah kanwar mutumin nan dake xaune ba, kuma ai ni na samu labarin wannan auren da tayi ba aure bane don babu abinda ya ta6a shiga tsakaninta da mijin, a gantale aka yi auren kuma a gantale aka yi sakin, yar yarinya ce karama fa nake gaya maka wllh, sannan kakan Aliyu nima ai a bazawarar ya aureni tunda sai da na auri kakanka aka haifi Kabiru da Aisha sannan kishiyoyi suka fiddani, Allah ya hadani da kakan Aliyu ya aureni sannan na haifi su Usman da Nafisah" Shi dai El-Basheer murmushi kawai yake yace "Toh shkkn ai ni nasan baxa ki min xabin da xai cutar da ni ba Hajjaju" Hajja tace "Haba haba ai na cuci kaina kenan idan na cuceka, in sha Allahu xabi ne har xabi na maka, kar ka ji komai a ranka, bari dai mu gama da bikin wannan mutumin tukun" Abuturrab dai bai daina kallon Hajja ba, El-Basheer yace "Toh baxa mu samu ko d'an ruwan shayi ba, ni yunwa nake ji fa" Hajja tace "Kaji ka, ai magana xaka yi, har abincin ma akwai naga sun dafa idan kuna so a xubo maku" El-Basheer yace "Aa shayin dai, bamu yi breakfast ba" Hajja ta mike tace "Toh bari in sa a kawo maku" Fita tayi dakin xuwa parlor, har sannan su Jiddah na parlor, Hajja tace "Yar nan ajiye masu sharan su ki xo in sa ki aiki kinji" Jiddah ta ajiye broom din hannunta ta karaso gun Hajja, Hajja tace "Xuwa xaki yi kitchen ki wanke hannu da kyau, don baya son kazanta Bashir, bayan kin wanke hannunki ki dau babban faranti da naga suke fafa da shi a gidan nan ki daura masa flask da cokali da kopi daya sannan ki ajiye kayan shayi a gefe, to shi kuma dayan mutumin ban san ko xai sha ba don ko gaisheni ma bai yi ba, amma dai baxa a biye ta halinsa ba, shi ma ki dora masa kofi da cokali daya mu mayar masa da aniyarsa, ki tabbatar duk ki dauraye kofunan don kinsan sarakan tsafta ne su, kuma duk a wajena suka gado, bayan nan idan akwai burodi ki daura kan tray din duk ki kawo masu" Jiddah tace "Toh" sannan ta juya ta wuce kitchen, Hajja ta koma daki tace "Toh ba shikenan ba bakina alekum, da wannan gantalallun 'ya yan na saka sai in samu me xagina ma tunda ba isasshen tarbiya garesu ba" Jiddah tayi duk yanda Hajja ta ce mata, tray biyu tayi ta daura kayan shayin da bread din a daya, dayan kuma ta daura cups da spoon sai flask din a kai, na flask din da cup ta fara dauka ta fito kitchen din suka kusa cin karo da Aunty ta koma gefe da sauri, Aunty ta hade rai ta ja gefe, Jiddah ta sunkuyar da kai ta bi gefe ta fita don tun sassafe ta gaisheta bata amsa mata ba, Jiddah na shiga dakin Hajja, Hajja ta mike ta shimfida rug da sauri tana cewa "Yauwa yar albarka, sannu kin ji, taho ki ajiye" Jiddah ta sunkuya ta ajiye tray din tace xanje in dauko dayan, Hajja tace "Toh yi maxa" Shi dai El-Basheer kallonta kawai yake, ta juya ta fita, Hajja tace "Wllh ba sawa ba hanawa, tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin nutsattsiya me tarbiya irin wannan yarinyar ba, gashi bata fushi ko kadan yanda ka san ni ce ina karama" El-Basheer yyi murmushi yana shafa kansa yace "Toh ko dai canje xaki min da sakin wawan da kika ce" Hajja tace "Aa kai dai kayi shiru kawai ka kyaleni yanda ka gan ni, ban fiye son surutu ba gaira ba dalili ba...." Abuturrab kallon wayar hannunsa kawai yake amma babu abinda yake da wayar, Jiddah ta dawo da tray din kayan shayin ta ajiye, Hajja tace "Yauwa er albarka, sannu" Sai kuma ta kalli El-Basheer tace "Ko ta soya maka kwai, naga ta iya, jiya da uwar rikonta ta sa ta soya mata naga tayi sa da kyau snn bbu karni ga albasa ta yankasa rimi rimi a kai abun zar sha'awa, ni dai har Ramlah ta gama cin kwan nan banji karni ba" El-Basheer yace "Aa ba sai na bata wahala ba ta bari kawai" Hajja tace "O'o Allah ina ruwanka da wannan batun, kai dai ba a soya maka kwai ba ka hada da burodi ka ci, da tana da son jikinta ai baxan ma fara sa ta ba, kaga na bi ta kan yaran gidan nan" Jiddah ta kalli El-Basheer tace "Xan iya" Yace "Toh je ki soya" kofa ta nufa ta fita, Hajja ta kalli El-Basheer murya can kasa tace "Ga tsafta kamar tsatsonmu wllh, ko kai baka gani ba?" Shafa kansa kawai yake yana murmushi, tace "To ni dai ba ruwana, kawai a barni yanda aka gan ni ba banxa nake ba" Bayan kusan minti goma jiddah ta dawo da kwai rufe a plate da fork biyu a kai ta dora, ta sunkuya ta ajiye plate din kan carpet, Hajja tace "Allah yayi maki albarka kinji" Jiddah tayi murmushi ta mike suka hada ido da Abuturrab da ya dago kansa, sunkuyar da kai tayi ta nufi kofa ta fita, El-Basheer ya sauko ya fara hada shayin yana kallon Abuturrab yace "Hey dude come let breakfast" Abuturrab ya mike yace "Alhmdlh" Daga haka ya nufi kofa ya fice. Da yamma Jiddah na dakin Hajja ita da Nafeesah, El-Basheer ya shigo da sallama yace "Hajja xa mu je dauko su Maman Farida" Hajja ta washe baki tace "Ehh wllh yanxu mijin ya kirani wai sun sauka ashe" yace "Toh dama xance maki sai gobe ne, don ni daga can baxan dawo ba" Hajja ta xare ido tace "Saboda mene?" Yace "Aliyu xai karaso da su ni xan sauka gida in huta ne" Hajja tace "Aa ba ruwana ba haka Kabiru yace min ba, bai ce min xaka sauka a wani waje ba nan ba, nan din ba gidanku bane, sannan ba ga dakin Aliyu ba idan ma bak'in hali Aliyun ke maka ba ga dakin wancan yaron da ya gantale ba Salem yake kowa, ni tunda na xo har yau ban dora ido a kansa ba idan anyi magana sai uwar tace yana benue, tsafin suke koya masa a can din oho mu dai ga mu ga Allah, bikin d'an uwansa guda ma gashi babu alamar xai xo, ni dama a tsorace nake da yaron tun asali" El-Basheer yace "Toh xan dawo" Nafisah tace "Yaya don Allah in bi ka?" Yace "Airport din?" Hajja tace "Ehh mana ku tafi da ita ai yar makaranta ce" El-Basheer yace "Toh idan da mijin Nafisan xamu dauko fa" Hajja tace "Toh ai mijin tun da muka dawo da shi bai koma ba, Nafisar ce kadai ta taho ko yaro daya bata xo da shi ba ta bar ma wata makociyarta balarabiya me kirki, mijinta kuma na Habuja" El-Basheer yace "Ohk" Nafisah na jin dadi ta dau mayafinta, Hajja tace "Toh gaskiya ni bana son kai, idan har xa aje dake sai dai a tafi da wannan yarinya Jiddah itama tunda tare kuke, ita ma kuma ba 6are bace" El-Basheer yace "Toh ta dau mayafinta mu je" Nafisah tace "Amma Hajja kar ya Abuturrab ya koro mu fa" Hajja tace "Xai ko aika, ku mu je gun motar gaba daya" A tare suka fita, suka tadda Aliyu xaune cikin mota yana jiran El-Basheer, ganinsu gaba daya ya daure fuska, Hajja ta bude ma su Nafisah bayan mota, Ita dai Jiddah gabanta sai faduwa yake don mayafi ne ita ma jikinta, kallon mamaki Abuturrab ke masu gaba daya, can yace "Ina xa a kai wa ennnan?" Hajja tace "Usman ne yace a tafi da Nafisah su hadu da takwararta a Iyapot, ni kuma nace a tafi da Jiddah tunda a kan kunnenta aka yi xancen kuma mu bama nuna banbanci a xuri'armu" Abuturrab yace "Aa ni baxanje da kowa ba sai dai El-Basheer yaje ya dauko Aunty Nafisar a Airport" Hajja tace "Amma kasan ina lura da yanda ka raina ubanka, shi fa ya fada bani ba, albarkacin daga bakinsa hakan ya fito ai sai kayi masa biyayya ko ba ta dadin rai ba kayi abinda yace, ba fa goyasu xaka yi ba balle kace aiki aka hadaka da, ko wacce xaunawa xata yi a bayan mota har kuje ku dawo, gaskiya ka sake hali Aliyu, wllh Bashir ba haka yake ba kai dai bar shi da tsokana da mugunta, amma kai wllh kana da bakin hali" Abuturrab yace "Duk naji su sauka kawai" Hajja tace "Allah ya tsine min idan sun sauka, a kira min Usman" El-Basheer dake dariya kasa kasa bayan ya shiga front seat ya kalli Abuturrab yace "Plss let them, it's Abba's instruction" Dama Hajja ko sake kallon Abuturrab bata yi ba tana kallonsu Nafisah tace "Ku shiga kawai" Nafisah ta turo baki ta shiga motar tana kallon yayanta, Jiddah tace "Hajja ni ai kince xan wanke maki bandaki ko?" Hajja tace "Aa wancan me fuskar uwar tata xata wanke min, wato Aisha" Jiddah ta girgixa kai tace "Hajja ni xan wanke kawai su tafi" A fusace Hajja tace "Oo Allah ya ana yabonki sallah sai ki kasa alwala, bayan nabi duk na barbada ma duniya cewar baki da musu kuma yanxu ki nemi karyatani gaban yaran nan??" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Toh kiyi hakuri" Daga haka ta shiga motar, Hajja tace "Yauwa, ku je Allah ya tsare, idan kinga yalo a hanya ki tuna masu idan sun ga dama sun siya min to" Daga nan ta kulle motar tayi wucewarta ciki tana cewa "Da ban masa haka ba koran min 'ya yan xai yi, gwara ma yayi aure kowa ya huta wllh yaje can su ci kansu da matar ni dai xan dinga kai masu ziyara kawai da d'an rakiya" Tada motar Abuturrab yyi fuska daure ya danna horn mai gadi na bude motar ya fita compound din ya dau hanyar titi, ta madubi El-Basheer ke kallon Jiddah da ya lura she is uncomfortable yace "How is ur studies going Jiddah?" Nafisah ta kalli Jiddah dake gefenta, Tana wasa da gyalenta tace "Alhmdlh" Ya dinga kallonta kafin yace "Hope u are assimilating what u are being taught?" Ta d'an yi murmushi tace "Ehh" ya langwabar da kai yace "Ni ai ba da Hausa na maki ba ko" sake kallonsa tayi suka hada ido, sai kuma tayi murmushi, yace "Do you have any idea of where we are heading to now?" Ta kalli Nafisah dake ta kallonta tana murmushi, Nafisah ta gyada mata kai alamar tayi magana, Shi dai El-Basheer na ta jiran respond dinta, ta d'an kallesa tace "Ka sake fadan abinda kace" Yace "Ohk.. Did u have any idea of where we are heading to now?" Ta d'an kalli Abuturrab da fuskarsa babu yabo bbu fallasa yana kallon titi yana driving, cikin sanyin murya tace "Yes i have" El-Basheer yace "So where are we going to now?" Tace "Hajja said we are going to take Aunty at the...." Sai kuma tayi shiru, ya gyada kai yace "Yess good, ci gaba" Tace "Airport?" Murmushi El-Basheer yayi sosai yace "Ohh yes, Hajja said we are going to pick Aunty Nafisa from the Airport" Ta sunkuyar da kai ita ma tana murmushi, Nafisah dai sai kallonta take, El-Basheer yace "So can you brief me about ur self?" Ta d'an yi shiru sai kuma ta kallesa yace "I am all ears" Tace "My name is Hauwa Jiddah yusuf, i was born and brought up in kaduna hayin rigasa, i lived with my step mum not until..." Da sauri Abuturrab ya kauce ma mai mashin da ya kusa bugewa, Nafisah da taga yanda abun ya faru tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da mamaki El-Basheer yace "How manage?" Abuturrab ya sauke glass ya ba ma mai mashin din hakuri ya ja motarsa ya kara gaba ba tare da ya tanka kowa ba, El-Basheer yace "Are u sure hankalinka na kan tukin nan Aliyu?" Abuturrab bai tanka sa ba still yana driving din, El-Basheer yace "Toh Allah ya tsare" Maida dubansa yayi kan Jiddah ta madubin gaba yace "Go on Jiddah" tace "I am currently living with Umma at Unguwar Dosa..." Sai kuma tayi shiru, kallonta kawai El-Basheer yake, tayi murmushi tace "Shikenan" Yace "Yea, kinyi kokari sosai Jiddatul Khair, maa sha Allah" Ita ma murmushin tayi tana daga kai suka yi ido hudu da Abuturrab dake kallonta ta madubi, ta sunkuyar da kanta, Nafisah ma duk tana lura da kallon da yake ma Jiddah ta dinga fatan Allah ya sa kada yaje ya sake buge wani kuma. Aunty Nafisah ta rungume takwararta cike da murnan ganinta tace "Haka kika girma Nafisah" Nafisah dake ta washe baki tace "Aunty me yasa baki taho da su Farida ba?" Aunty Nafisah tace "Suna makaranta ne amma in sha Allah xa su xo wani lokacin" Sai a sannan ta kalli Jiddah, Jiddah ta gaisheta da ladabi, Aunty Nafisa ta amsa da fara'a tana kallonsu El-Basheer tace "Wacece?" El-Basheer yace "Yarinyar Umma ce" Aunty Nafisa tace "To madallah" Tuni Abuturrab ya wuce da trolley dinta, duk suka bi bayansa xuwa mota, bayan ya saka jakan a booth ya shiga driver seat, Su ma suka shiga motar sannan ya bar airport din, hira kawai El-Basheer ke yi tare da Aunty Nafisah da ta fita harkan Abuturrab ganin yanda ya tarbeta a airport, shi dai driving dinsa kawai yake, suna fara shigowa gari, Jiddah na kallonsa tunda ita ce setin kujeransa ta d'an matsa, El-Basheer ya kalleta ta gefen ido, a hankali tace "Yaya... Hajja tace a taho mata da Yalo wai" Abuturrab da ya ji ta sarai don setin ears dinsa tayi maganan yyi shiru yana driving dinsa, El-Basheer yace "Kina son wani abu ne Jiddah?" Ta kallesa tace "Aa Hajja ce tace a siyo mata yalo" El-Basheer yace "Ohk idan an gani sai a siya mata" Luckily suka samu yalon El-Basheer yace "Oga ka samu waje kayi parking a siya ma Hajja yalo" Abuturrab yace "Wa ennan rubabbun abubuwan" Daga haka ya ja motarsa ya ki tsayawa, Aunty Nafisah dai bata ce masu komai ba, El-Basheer yayi wani murmushi shi ma bai ce komai ba, sai da suka kusa gida Abuturrab yace "Aunty ya baki taho da zee ba?" Tace "Ban sani ba" Murmushi kawai yayi ya shiga layinsu, a kofar gida yayi parking, El-Basheer ne ya fara sauka, Aunty Nafisah ta sauka, snn Nafisah, Jiddah xata sauka Abuturrab yace "Tsaya" kallonsa tayi, ya hade rai yace "Ke har wani nishadi kike kiyi ta hira da kattin maza kina washe baki don baki da kamun kai koh? To daga yau na sake jin kin wani bude baki kina ma wani turanci xan baki mamaki, sannan ki ci gaba da yawo da kananun gyale" Ita dai kallonsa kawai take, yace "Saukar min a mota" bude motar tayi ta sauka ta wuce cikin gida ya bi ta da kallo..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Washegari har karfe goma na safe Abuturrab na dakinsa kwance, babu wanda ya san yana cikin gidan banda Aunty da ta shigo tun karfe takwas wai ya tura ma Aneesah kudin make up, wanda ya tura da farko yayi kadan, babu yanda ya iya haka ya tura kudin, bayan nan kuma bata sake shigowa ba. Goma saura yan mintuna El-Basheer ya shigo gidan tare da Ahmad, don ba gidan ya kwana ba, El-Basheer ya dinga kallon Abuturrab yana 'yar dariya yace "Wannan ai ko kaine amaryar sai haka, ka wani makale a daki tun jiya kamar wanda xa ayi ma auren dole, kamar dai ba Aneesah bace matar" Ahmad yyi murmushi shima yana kallon Abuturrab yace "Captain duk xullumin auren ne ya ramar da kai haka..." Abuturrab yace "Saboda ita ce xata aureni ba nine xan aureta ba ko?" Ahmad yace "Toh wa ya sani, ita dai tana can tana ta sabgar gabanta da kawayenta, kai kuma kana nan ka makale a daki" El-Basheer ya nufi kofa ya fita xuwa dakin Hajja, Hajja na ganinsa tace "Ina Aliyun?" El-Basheer yace "Yana dakinsa" Hajja tace "Dama yana gidan nan?" El-Basheer yace "Yana nan" Ta mike tace "Ni ba ruwana, gida duk jama'a sun cika kilan babu wanda ya bi ta kan ko ya ci abinci ko bai ci ba, ita Ramlah naga sai masu kudi kawai take ma marhaba tayi ta nan nan da su duk ina lura da ita, kaga ai ko shigowa ta tambayeni ko an kawo min kumallo bata yi ba wllh, gwara ma Hauwan ta kawo ma Nafisah da kanta...." El-Basheer ya bi ta da kallo yana murmushi har ta fita sannan ya xauna yana kallon Aunty Nafisah yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Lafiya lau Bashir, ashe baka kwana gidan ba" Yace "Ehh yanxu na shigo, ya gajiyan ku" Tace "Gajiya ta bi lafiya, karfe nawa ne daurin auren?" Yace "Sai an sauko Juma'ah in sha Allah" tace "To maa sha Allah" Ahmad ne ya shigo dakin da sallama, Aunty Nafisah tace "Bokan turai ina ta xuba idon ganinka tun jiya ban ganka ba" Yana murmushi yace "Sannu da isowa Aunty, ya hanya" tace "Alhmdlh Ahmad" Hajja na shiga dakin Abuturrab ta tsaya daga bakin kofa tace "Kunga abinda nake gudu ko? Yanxu tun safe babu wanda ya kawo maka kumallo kenan?" Ya d'an kalleta amma bai ce komai ba, tace "Toh ni ba ruwana wllh, wannan ai ba yi bane" Tana fadin haka ta fita, dakin da yan matan gidan suke ta tafi ta bude, bak'i ne kawai a dakin ta gama kare masu kallo tace "Tirrr" sannan ta fita tana girgixa kai tace "Abin dai ba tsari, wa xai yarda da wnn gayyar a Masar, wasu ma rabonka da su ya fi shekara talatin amma suna jin biki xa su taho riiii, ko yar shinkafar suke ma oho" Safiyya ta gani tace "Ke ina Jiddah?" Safiyya tace "Umma ta aikesu da Maimoon can gida" Hajja tace "Toh kije duk yanda xaki yi a kitchen ban sani ba, amma ki samu ruwan xafi da kofi me kyau ki dau kayan tea ki kai ma Aliyu, idan babu burodi ki xo in baki kudi kije ki samo masa, kowa fa ya karya a gidan banda shi don walakanci" Safiyya tace "Toh" daga haka ta wuce kitchen, Hajja to kama dakinta tana mita, Safiyya tayi duk yanda Hajja tace sannan ta kai masa daki, bayan ta gaishesa ta ajiye tray din, yana kallonta yace "Ina su Maimoon?" Tace "Umma ta aikesu" Yace "Ita da wa?" Tace "Jiddah da Nafisah" yace "Xuwa ina?" Tace "Can gida" tsayawa tayi jin bai sake cewa komai ba xata fita yace "Xo ki bani number Maimoon din" Safiyya ta dawo ta amshi wayarsa ta sa masa number Maimoon sannan ta mika masa, ta juya ta fita, dialing number yayi, Maimoon dake compound sun fito tare da Jiddah da Nafisa xasu wuce wajen kwalliya ta xaro ido tana kallon wayarta tace "Dama Ya Aliyu yana da number na, kuma me xai ce min yake kirana..." Dagawa tayi ta kai kunne a hankali tace "Assalamu alaikum" Daga daya bangaren ya amsa yace "Kuna ina?" Tace "Umma ta aiko mu gida" yace "Ke da wa?" Tace "Jiddah da Nafisah" Yace "Yaushe xa ku baro gidan?" Tace "Aa yanxu dai wajen tailor xa mu je amsan kayan da xa mu saka na dinner...." Ta d'an kalli su Jiddah, jin yyi shiru tace "Hello" yace "Ina jin ki, minti nawa xa kuyi wajen tailor din" Ta d'an turo baki tace "Yanxu xa mu dawo dai Yaya, amso kayan kawai xa mu yi" Yace "Toh ku sameni a daki idan kun dawo, gaba dayan ku" Tace "Toh" daga haka ta katse wayar ta ta6e baki tace "Toh me xa mu yi masa xa mu wani samesa a daki, ni ba da ni ba wllh, ko a ina ma ya samu Digit dina" Nafisah tace "Da kince masa ma daga wajen tailor din xamu je gun make up, ni bana son komai da xai hada mu da shi fahh" Maimoon tace "Kyalesa kawai, ba sai ya ganmu ba" Ita dai Jiddah bata ce komai ba har suka fita gate din gidan. Har karfe sha biyu da rabi su Maimoon basu koma gida ba, Abuturrab ya kira numberta sau uku ya ji a kashe, ya kira Nafisah ita ma numberta a kashe, yana xaune dakin Hajja da Ahmad da El-Basheer, dukkansu fararen shadda ne jikinsu xasu tafi masallaci, Ahmad ya kalli Abuturrab bayan ya kalli agogon wrist dinsa yace "Wai da wanda kake jira ne Captain, dubi fa lokaci..." El-Basheer yace "I'm still wondering also, yace mu jira ban san wanda muke jira ba" Hajja tace "Aa gaskiya ku bi sa a hankali, ku baku san duk fargaban aure bane, yanxu fa ana saukowa sallah sai daurin auren..." Abuturrab ya kalleta ta gefen ido ya mike ya fita daga dakin, Hajja tace "Toh Allah ya tsare Aliyu, Allah ubangiji ya sa a daura a sa'a ni dai" Sai bayan da suka shiga mota Abuturrab ya sake kiran Maimoon yaji wayar a kashe still.... Bayan an sauko Juma'ah aka daura aurensa da Aneesah a kan sadaki dubu dari biyu, abokan aikinsa sun masa solidarity sosai don sun samu halartar daurin auren, Ahmad don't want to believe yak'e kawai Captain yake, gaba daya he doesn't look someone happy but he is still smiling as if all is well, suna cikin mota Aneesah ta dinga kiransa yayi silencing wayar ya jefa cikin aljihu, El-Basheer yace "Ya dai da wannan shirun Capt, isn't today ur happy day, u are wedded to the love of ur life..." Captain ya gyara xama a motar yace "Okay saman motar ka so in hau don farin ciki?" Dariya El-Basheer yayi yace "Gaskiya that's what i was expecting, yau dai Aneesah da ka ishemu ta xama matarka" Ahmad dai driving kawai yake bai ce komai ba, El-Basheer yace "Nima Allah ya nuna min ranan da xa a daura min aure da xabin nan na Hajja duk da ban santa ba amma naji har ta kwanta min" Abuturrab ya kara gyara xama bai dai ce komai ba, Ahmad yace "Hajja ta maka wani xabi ne?" El-Basheer yace "Wllh fah, tace ta samar min mata so i will be next in sha Allah" Ahmad yace "A masar?" Dariya El-Basheer yayi yace "Aa nan kasar idan mun je yanxu xan sake tada mata xancen gaskiya don na zaku, yanxu fa ni kadai ne tuxuru cikin ku ko?" Ahmad yace "Atoh, ba dai ka tsaya wasa ba" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera still bai ce masu komai ba yana kallon wajen window. Suna isa gida Abuturrab ya bude motar ya sauka ya wuce ciki yana sake dialing number Maimoon still a kashe, ya wuce bangarensa kawai, Aisha ya kira bayan ya xauna gefen gado, yana fara ring ta daga yace "Maimuna sun dawo?" Tace "Aa suna wajen make up" Yace "A ina ake make up din?" Tace "Ni ban san wanda suka je ba, kasan ba waje daya muka tafi ba" Ya d'an yi shiru sai kuma ya katse wayar, Karfe hudu saura Jiddah suka shigo gida daga wajen make up, da farko taki yarda a mata make up amma sai da su Nafisah suka yi forcing dinta, idan ba sake kallonta kayi ba ma baxa ka ganeta ba, wato tayi kyau ne ba kadan ba duk da ba heavy make up aka mata ba, basu yarda sun sa ankon Dinner din daga can ba, suna shigowa compound suka hadu da Safiyya, Safiyya tace "Ke ina kika sa wayarki ya Aliyu na ta kiranki a kashe" Maimoon ta turo baki tace "Toh wai ma a ina ya samu numberta kuma me yake nemana xan masa?" Daga haka ta kara gaba su Jiddah na ta biye da ita, gud'a da ake ta yi a ciki ne ya tabbatar masu Amarya ta iso, don bayan daurin aure da awa uku aka kawota via flight tunda a kaduna xa ayi dinner din, Mutane ne cike gidan ba masaka tsinke, Maimoon tace "Mu tafi dakin Hajja kawai, kar ma a wani ya aikeni bayan nayi make up" a kulle suka ji kofar an sa makulli, wai ashe amarya na ciki, ga mutane cike bakin kofar dakin, Hajja ta bude kofar duk ta hada xufa cikin ubansun lace din jikinta ga dankunnenta na gwal dake ta sheki a kunnenta, cike da masifa take cewa "Wallahi ba a haka a Masar, mu bama haka a masar, bamu san haka ba a Masar, ita fa wannan amaryar ba ta gwal bace kowa xai ganta idan lokaci yayi, an wani xo an cika min kofar daki kamar ina bada sadaka, ni wllh idan xuciya ta debeni sai in mayar da amaryar tsakar gida yanxun nan, wannan fitina har ina" Maimoon ta dinga rabawa ta gefenta xata shige dakin Hajja ta fincikota tace "Kun ga bala'i ko, wacece wannan kuma" Maimoon tace "Hajja nice fa da su Jiddah don Allah ki bar mu mu shiga yanxu muka dawo" Hajja ta kankance ido tana kare ma Jiddah da Nafisah kallo tace "Shampoo aka ma fuskar ko me?" Maimoon ta shige ciki ta fixgo hannun Jiddah Nafisah ma ta shige dakin sai a sannan Hajja ta kulle kofar da makulli, Aneesah na can karshen dakin saman lallausan rug duk jikinta a lullube har fuskarta, daga gefenta kawayenta hudu ne, Hajja tace "Haba mutanen kasar nan kamar mayu ni Dijee, wllh har na yi adadin shekaruna a Masar ban taba ganin kwatankwancin haka ba, komai a nutse cikin tsari ake yin sa, duk fa rubabbu yan kauye ne suka cika bakin kofar, wani me kudin ne xai wani xo ya tsaya bakin kofa ya tsaya yace sai ya ga amarya kamar wata amaryar gwal, ba gata can na ganta ba sai hasken fata kawai malam, kawayen nata kuma duk bakake ne, kwalliya su ma ni ban gane kanta ba, Ai da sun sani su bari idan sun xo nan sai ku kai su inda aka maku kwalliyan Maimuna, naku yayi kyau sosai har ma ba na jiddah ba, wani ba sai yace ita ce amaryar ba" Maimoon ta dinga kunshe dariyarta, Aunty Nafisah tayi tagumi tana salati a xuciyarta, Ta cikin mayafi Aneesah da ta hade rai take leko Hajja, kawayenta kuwa sai danna waya suke ko wacce fuska a murtuke, Caraf idon Aneesah ya sauka kan Jiddah da ta durkusa jikin kujera, ita bata ma san ita ce jiddar da Hajja ke fadi ba don bata san sunanta ba, amma lkci daya ta gane ta, sosai gabanta ya fadi ta dinga kallonta, Aunty Nafisah ta dau wayarta dake ring ganin Aliyu ke kiranta ta daga, yayi kasa da murya yace "Aunty su Maimunan sun dawo?" Aunty tace "Ehh yanxu suka shigo" Yace "Toh ki turo min su gaba daya yanxu ina mota a kofar gida" Aunty tace "Toh" katse wayar tayi tana kallonsu Maimoon da cikinta ya kada jin ance eh sun dawo, Aunty tace "Wai ku je Aliyu na kiranku kofar gida" Aneesah dai sai binsu take da kallo ta cikin mayafinta, Maimoon ta mike kamar xata yi kuka, Nafisah ma ta tashi suka nufi kofa, ganin Jiddah bata taso ba Maimoon tace "Aunty banda Jiddah yace ne?" Tace "Aa ya dai ce ku je ban san da wa da wa ba" Hajja dake ta fifita duk da fankan dake aiki a dakin tace "Toh me xa su masa har su uku haka, su dai su je, ina ruwansa da wata Jiddah da bata kula kowa a gidan, kilan wani laifin suka masa... Ita dai nasan ba ruwanta tayi xamanta su suje, bata shiga sabgar kowa" Maimoon tace "Laifi kuma Hajja, mu ba abinda muka masa wllh, ko ganinsa ma ban yi ba yau gaba daya" Daga haka ta fice daga dakin tare da Nafisah, ta cikin mutane suka dinga kutsawa har suka fita kofar gida, can suka hango motarsa nesa da gidan, suka nufi motar, ya sauke glass yana kallonsu, suna isa motar Maimoon tace "Yaya ga mu, daxu wayana ya mutu ne sai da na dawo yanxu na jona a dakin Hajja" Yace "Ku nawa ku ka je make up din?" Maimoon tace "Ni da Nafisah da Jiddah" Yace "Ita tafi karfin ta fito ne?" Maimoon tace "Hajja ce ta hanata ta fito wllh" yace "To koma ki kira min ita kuma kar ki fada mata gaban Hajjan" Maimoon tace "Toh" daga haka ta juya da Nafisah suka bar wajen tana sauke ajiyar xuciyar relieve, suna komawa dakin Hajja, Hajja tace "Kiran me yake maku?" Maimoon tace "Aa kawai dai tambaya yayi min" Tana fadin haka ta xauna kusa da Jiddah murya can kasa tace "Yaya Aliyu yace kije" Jidda ta xaro ido tace "Ni kuma?" Maimoon ta cunkuleta tace "Don't allow this old woman to know" Jiddah tayi kasa da murya tace "Tare xa mu je da ku?" Maimoon tace "Aa ni kaya xan sa yanxu, ya gama magana da mu, ke kadai xa ki je" Lkci daya jikin Jiddah yayi sanyi, bata dai ce komai ba ta mike har xata dau gyalen da ta saka yau ta tuna sai yayi mata fada, Hijab din Nafisah dake kan kujeran Hajja ta dauka ta fita daga dakin, tana fita gate sae ga motar Ahmad tare da El-Basheer da wasu abokansu..... *Da babu dai gwara babu dadi ayi hakuri da ni yau, kun san mun haihu a group din mu jiya kuma duk da ni aka yi labor, Mrs Jay Allah ya raya baby Ameen*🙄 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Washegari har karfe goma na safe Abuturrab na dakinsa kwance, babu wanda ya san yana cikin gidan banda Aunty da ta shigo tun karfe takwas wai ya tura ma Aneesah kudin make up, wanda ya tura da farko yayi kadan, babu yanda ya iya haka ya tura kudin, bayan nan kuma bata sake shigowa ba. Goma saura yan mintuna El-Basheer ya shigo gidan tare da Ahmad, don ba gidan ya kwana ba, El-Basheer ya dinga kallon Abuturrab yana 'yar dariya yace "Wannan ai ko kaine amaryar sai haka, ka wani makale a daki tun jiya kamar wanda xa ayi ma auren dole, kamar dai ba Aneesah bace matar" Ahmad yyi murmushi shima yana kallon Abuturrab yace "Captain duk xullumin auren ne ya ramar da kai haka..." Abuturrab yace "Saboda ita ce xata aureni ba nine xan aureta ba ko?" Ahmad yace "Toh wa ya sani, ita dai tana can tana ta sabgar gabanta da kawayenta, kai kuma kana nan ka makale a daki" El-Basheer ya nufi kofa ya fita xuwa dakin Hajja, Hajja na ganinsa tace "Ina Aliyun?" El-Basheer yace "Yana dakinsa" Hajja tace "Dama yana gidan nan?" El-Basheer yace "Yana nan" Ta mike tace "Ni ba ruwana, gida duk jama'a sun cika kilan babu wanda ya bi ta kan ko ya ci abinci ko bai ci ba, ita Ramlah naga sai masu kudi kawai take ma marhaba tayi ta nan nan da su duk ina lura da ita, kaga ai ko shigowa ta tambayeni ko an kawo min kumallo bata yi ba wllh, gwara ma Hauwan ta kawo ma Nafisah da kanta...." El-Basheer ya bi ta da kallo yana murmushi har ta fita sannan ya xauna yana kallon Aunty Nafisah yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Lafiya lau Bashir, ashe baka kwana gidan ba" Yace "Ehh yanxu na shigo, ya gajiyan ku" Tace "Gajiya ta bi lafiya, karfe nawa ne daurin auren?" Yace "Sai an sauko Juma'ah in sha Allah" tace "To maa sha Allah" Ahmad ne ya shigo dakin da sallama, Aunty Nafisah tace "Bokan turai ina ta xuba idon ganinka tun jiya ban ganka ba" Yana murmushi yace "Sannu da isowa Aunty, ya hanya" tace "Alhmdlh Ahmad" Hajja na shiga dakin Abuturrab ta tsaya daga bakin kofa tace "Kunga abinda nake gudu ko? Yanxu tun safe babu wanda ya kawo maka kumallo kenan?" Ya d'an kalleta amma bai ce komai ba, tace "Toh ni ba ruwana wllh, wannan ai ba yi bane" Tana fadin haka ta fita, dakin da yan matan gidan suke ta tafi ta bude, bak'i ne kawai a dakin ta gama kare masu kallo tace "Tirrr" sannan ta fita tana girgixa kai tace "Abin dai ba tsari, wa xai yarda da wnn gayyar a Masar, wasu ma rabonka da su ya fi shekara talatin amma suna jin biki xa su taho riiii, ko yar shinkafar suke ma oho" Safiyya ta gani tace "Ke ina Jiddah?" Safiyya tace "Umma ta aikesu da Maimoon can gida" Hajja tace "Toh kije duk yanda xaki yi a kitchen ban sani ba, amma ki samu ruwan xafi da kofi me kyau ki dau kayan tea ki kai ma Aliyu, idan babu burodi ki xo in baki kudi kije ki samo masa, kowa fa ya karya a gidan banda shi don walakanci" Safiyya tace "Toh" daga haka ta wuce kitchen, Hajja to kama dakinta tana mita, Safiyya tayi duk yanda Hajja tace sannan ta kai masa daki, bayan ta gaishesa ta ajiye tray din, yana kallonta yace "Ina su Maimoon?" Tace "Umma ta aikesu" Yace "Ita da wa?" Tace "Jiddah da Nafisah" yace "Xuwa ina?" Tace "Can gida" tsayawa tayi jin bai sake cewa komai ba xata fita yace "Xo ki bani number Maimoon din" Safiyya ta dawo ta amshi wayarsa ta sa masa number Maimoon sannan ta mika masa, ta juya ta fita, dialing number yayi, Maimoon dake compound sun fito tare da Jiddah da Nafisa xasu wuce wajen kwalliya ta xaro ido tana kallon wayarta tace "Dama Ya Aliyu yana da number na, kuma me xai ce min yake kirana..." Dagawa tayi ta kai kunne a hankali tace "Assalamu alaikum" Daga daya bangaren ya amsa yace "Kuna ina?" Tace "Umma ta aiko mu gida" yace "Ke da wa?" Tace "Jiddah da Nafisah" Yace "Yaushe xa ku baro gidan?" Tace "Aa yanxu dai wajen tailor xa mu je amsan kayan da xa mu saka na dinner...." Ta d'an kalli su Jiddah, jin yyi shiru tace "Hello" yace "Ina jin ki, minti nawa xa kuyi wajen tailor din" Ta d'an turo baki tace "Yanxu xa mu dawo dai Yaya, amso kayan kawai xa mu yi" Yace "Toh ku sameni a daki idan kun dawo, gaba dayan ku" Tace "Toh" daga haka ta katse wayar ta ta6e baki tace "Toh me xa mu yi masa xa mu wani samesa a daki, ni ba da ni ba wllh, ko a ina ma ya samu Digit dina" Nafisah tace "Da kince masa ma daga wajen tailor din xamu je gun make up, ni bana son komai da xai hada mu da shi fahh" Maimoon tace "Kyalesa kawai, ba sai ya ganmu ba" Ita dai Jiddah bata ce komai ba har suka fita gate din gidan. Har karfe sha biyu da rabi su Maimoon basu koma gida ba, Abuturrab ya kira numberta sau uku ya ji a kashe, ya kira Nafisah ita ma numberta a kashe, yana xaune dakin Hajja da Ahmad da El-Basheer, dukkansu fararen shadda ne jikinsu xasu tafi masallaci, Ahmad ya kalli Abuturrab bayan ya kalli agogon wrist dinsa yace "Wai da wanda kake jira ne Captain, dubi fa lokaci..." El-Basheer yace "I'm still wondering also, yace mu jira ban san wanda muke jira ba" Hajja tace "Aa gaskiya ku bi sa a hankali, ku baku san duk fargaban aure bane, yanxu fa ana saukowa sallah sai daurin auren..." Abuturrab ya kalleta ta gefen ido ya mike ya fita daga dakin, Hajja tace "Toh Allah ya tsare Aliyu, Allah ubangiji ya sa a daura a sa'a ni dai" Sai bayan da suka shiga mota Abuturrab ya sake kiran Maimoon yaji wayar a kashe still.... Bayan an sauko Juma'ah aka daura aurensa da Aneesah a kan sadaki dubu dari biyu, abokan aikinsa sun masa solidarity sosai don sun samu halartar daurin auren, Ahmad don't want to believe yak'e kawai Captain yake, gaba daya he doesn't look someone happy but he is still smiling as if all is well, suna cikin mota Aneesah ta dinga kiransa yayi silencing wayar ya jefa cikin aljihu, El-Basheer yace "Ya dai da wannan shirun Capt, isn't today ur happy day, u are wedded to the love of ur life..." Captain ya gyara xama a motar yace "Okay saman motar ka so in hau don farin ciki?" Dariya El-Basheer yayi yace "Gaskiya that's what i was expecting, yau dai Aneesah da ka ishemu ta xama matarka" Ahmad dai driving kawai yake bai ce komai ba, El-Basheer yace "Nima Allah ya nuna min ranan da xa a daura min aure da xabin nan na Hajja duk da ban santa ba amma naji har ta kwanta min" Abuturrab ya kara gyara xama bai dai ce komai ba, Ahmad yace "Hajja ta maka wani xabi ne?" El-Basheer yace "Wllh fah, tace ta samar min mata so i will be next in sha Allah" Ahmad yace "A masar?" Dariya El-Basheer yayi yace "Aa nan kasar idan mun je yanxu xan sake tada mata xancen gaskiya don na zaku, yanxu fa ni kadai ne tuxuru cikin ku ko?" Ahmad yace "Atoh, ba dai ka tsaya wasa ba" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera still bai ce masu komai ba yana kallon wajen window. Suna isa gida Abuturrab ya bude motar ya sauka ya wuce ciki yana sake dialing number Maimoon still a kashe, ya wuce bangarensa kawai, Aisha ya kira bayan ya xauna gefen gado, yana fara ring ta daga yace "Maimuna sun dawo?" Tace "Aa suna wajen make up" Yace "A ina ake make up din?" Tace "Ni ban san wanda suka je ba, kasan ba waje daya muka tafi ba" Ya d'an yi shiru sai kuma ya katse wayar, Karfe hudu saura Jiddah suka shigo gida daga wajen make up, da farko taki yarda a mata make up amma sai da su Nafisah suka yi forcing dinta, idan ba sake kallonta kayi ba ma baxa ka ganeta ba, wato tayi kyau ne ba kadan ba duk da ba heavy make up aka mata ba, basu yarda sun sa ankon Dinner din daga can ba, suna shigowa compound suka hadu da Safiyya, Safiyya tace "Ke ina kika sa wayarki ya Aliyu na ta kiranki a kashe" Maimoon ta turo baki tace "Toh wai ma a ina ya samu numberta kuma me yake nemana xan masa?" Daga haka ta kara gaba su Jiddah na ta biye da ita, gud'a da ake ta yi a ciki ne ya tabbatar masu Amarya ta iso, don bayan daurin aure da awa uku aka kawota via flight tunda a kaduna xa ayi dinner din, Mutane ne cike gidan ba masaka tsinke, Maimoon tace "Mu tafi dakin Hajja kawai, kar ma a wani ya aikeni bayan nayi make up" a kulle suka ji kofar an sa makulli, wai ashe amarya na ciki, ga mutane cike bakin kofar dakin, Hajja ta bude kofar duk ta hada xufa cikin ubansun lace din jikinta ga dankunnenta na gwal dake ta sheki a kunnenta, cike da masifa take cewa "Wallahi ba a haka a Masar, mu bama haka a masar, bamu san haka ba a Masar, ita fa wannan amaryar ba ta gwal bace kowa xai ganta idan lokaci yayi, an wani xo an cika min kofar daki kamar ina bada sadaka, ni wllh idan xuciya ta debeni sai in mayar da amaryar tsakar gida yanxun nan, wannan fitina har ina" Maimoon ta dinga rabawa ta gefenta xata shige dakin Hajja ta fincikota tace "Kun ga bala'i ko, wacece wannan kuma" Maimoon tace "Hajja nice fa da su Jiddah don Allah ki bar mu mu shiga yanxu muka dawo" Hajja ta kankance ido tana kare ma Jiddah da Nafisah kallo tace "Shampoo aka ma fuskar ko me?" Maimoon ta shige ciki ta fixgo hannun Jiddah Nafisah ma ta shige dakin sai a sannan Hajja ta kulle kofar da makulli, Aneesah na can karshen dakin saman lallausan rug duk jikinta a lullube har fuskarta, daga gefenta kawayenta hudu ne, Hajja tace "Haba mutanen kasar nan kamar mayu ni Dijee, wllh har na yi adadin shekaruna a Masar ban taba ganin kwatankwancin haka ba, komai a nutse cikin tsari ake yin sa, duk fa rubabbu yan kauye ne suka cika bakin kofar, wani me kudin ne xai wani xo ya tsaya bakin kofa ya tsaya yace sai ya ga amarya kamar wata amaryar gwal, ba gata can na ganta ba sai hasken fata kawai malam, kawayen nata kuma duk bakake ne, kwalliya su ma ni ban gane kanta ba, Ai da sun sani su bari idan sun xo nan sai ku kai su inda aka maku kwalliyan Maimuna, naku yayi kyau sosai har ma ba na jiddah ba, wani ba sai yace ita ce amaryar ba" Maimoon ta dinga kunshe dariyarta, Aunty Nafisah tayi tagumi tana salati a xuciyarta, Ta cikin mayafi Aneesah da ta hade rai take leko Hajja, kawayenta kuwa sai danna waya suke ko wacce fuska a murtuke, Caraf idon Aneesah ya sauka kan Jiddah da ta durkusa jikin kujera, ita bata ma san ita ce jiddar da Hajja ke fadi ba don bata san sunanta ba, amma lkci daya ta gane ta, sosai gabanta ya fadi ta dinga kallonta, Aunty Nafisah ta dau wayarta dake ring ganin Aliyu ke kiranta ta daga, yayi kasa da murya yace "Aunty su Maimunan sun dawo?" Aunty tace "Ehh yanxu suka shigo" Yace "Toh ki turo min su gaba daya yanxu ina mota a kofar gida" Aunty tace "Toh" katse wayar tayi tana kallonsu Maimoon da cikinta ya kada jin ance eh sun dawo, Aunty tace "Wai ku je Aliyu na kiranku kofar gida" Aneesah dai sai binsu take da kallo ta cikin mayafinta, Maimoon ta mike kamar xata yi kuka, Nafisah ma ta tashi suka nufi kofa, ganin Jiddah bata taso ba Maimoon tace "Aunty banda Jiddah yace ne?" Tace "Aa ya dai ce ku je ban san da wa da wa ba" Hajja dake ta fifita duk da fankan dake aiki a dakin tace "Toh me xa su masa har su uku haka, su dai su je, ina ruwansa da wata Jiddah da bata kula kowa a gidan, kilan wani laifin suka masa... Ita dai nasan ba ruwanta tayi xamanta su suje, bata shiga sabgar kowa" Maimoon tace "Laifi kuma Hajja, mu ba abinda muka masa wllh, ko ganinsa ma ban yi ba yau gaba daya" Daga haka ta fice daga dakin tare da Nafisah, ta cikin mutane suka dinga kutsawa har suka fita kofar gida, can suka hango motarsa nesa da gidan, suka nufi motar, ya sauke glass yana kallonsu, suna isa motar Maimoon tace "Yaya ga mu, daxu wayana ya mutu ne sai da na dawo yanxu na jona a dakin Hajja" Yace "Ku nawa ku ka je make up din?" Maimoon tace "Ni da Nafisah da Jiddah" Yace "Ita tafi karfin ta fito ne?" Maimoon tace "Hajja ce ta hanata ta fito wllh" yace "To koma ki kira min ita kuma kar ki fada mata gaban Hajjan" Maimoon tace "Toh" daga haka ta juya da Nafisah suka bar wajen tana sauke ajiyar xuciyar relieve, suna komawa dakin Hajja, Hajja tace "Kiran me yake maku?" Maimoon tace "Aa kawai dai tambaya yayi min" Tana fadin haka ta xauna kusa da Jiddah murya can kasa tace "Yaya Aliyu yace kije" Jidda ta xaro ido tace "Ni kuma?" Maimoon ta cunkuleta tace "Don't allow this old woman to know" Jiddah tayi kasa da murya tace "Tare xa mu je da ku?" Maimoon tace "Aa ni kaya xan sa yanxu, ya gama magana da mu, ke kadai xa ki je" Lkci daya jikin Jiddah yayi sanyi, bata dai ce komai ba ta mike har xata dau gyalen da ta saka yau ta tuna sai yayi mata fada, Hijab din Nafisah dake kan kujeran Hajja ta dauka ta fita daga dakin, tana fita gate sae ga motar Ahmad tare da El-Basheer da wasu abokansu..... *Da babu dai gwara babu dadi ayi hakuri da ni yau, kun san mun haihu a group din mu jiya kuma duk da ni aka yi labor, Mrs Jay Allah ya raya baby Ameen*🙄 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 *Xanyi amfani da wannan dama in sanar ma masu posting min littafi a Facebook groups da masu karantawa cewar babu forgiveness between i and them.. xa kuma mu hadu a inda ya dace mu hadu... Which is the hereafter* 🙅🏻‍♀️ Ahmad dake xaune kujera me xaman banxa ya wara ido bayan El-Basheer yyi parking yace "Waow is this Jiddah??" Sunkuyar da kai tayi tana d'an murmushi ta koma gefe tace "Sannunku da xuwa" Shi dai El-Basheer kallonta kawai yake ta cikin glass din idonsa kamar yanda sauran abokan Abuturrab biyu dake bayan motar ke kallonta su ma, Ahmad ya sauka motar yana mata murmushi yace "Ina xa ki?" Ta nuna masa inda motar Abuturrab yake tace "Maimoon tace yana kirana" Ahmad ya kalli motar sae kuma yyi pretending bai gane wanda take nufi ba yace "Waye a nan?" Tace "Ya Aliyu" Ahmad yace "Uhnn ohk" he was thinking har sannan bata san sunansa ba ai, El-Basheer ya sauko motar yace "Irin wannan kwalliya haka Jiddoh" Ta daga kai ta kallesa shi ma tayi masa murmushi, and her smile was heart melting, shafa kansa yyi ya kalli Ahmad da yace "To mu je mu rakaki gun Aliyun" ita dai bata ce komai ba, Ahmad na kallon bayan motar yace "To ko kun xata a jirgi ku ke naga kun ki sakkowa" Dariya pilots din biyu suka yi still not coming down, Najeeb yace "Kasan akwai kyau that's breath taking..." El-Basheer ya nufi motar Abuturrab, Ahmad ya kalli Jiddah yace "To mu je" Tafiya ta fara yi ya bi bayanta, Ta glass Abuturrab ya dinga kallonsu da tight face dinsa, har suka iso gun motarsa, El-Basheer yace "Ka kashe waya ne?" Abuturrab yace "Ehh but na kunna yanxu" El-Basheer yace "Saura few hours for the dinner, mu je inda kace ynxu mu dawo, ga co pilots dinka can a mota" Abuturrab yace "Ohk to mu hadu a can din" Daga haka ya tada motar, ganin tafiya xai yi Ahmad yace "Kiran da kake mata fa?" Sae a snn Abuturrab ya kalli Jiddah dake tsaye, bbu yabo bbu fallasa yace "Ohk, ance ke Hajja ta ba makullin dakina?" Ta girgixa kai tace "Aa yanxu muka dawo" Bai tanka ta ba ya ja motarsa ya bar wajen, El-Basheer ya kalli Ahmad yace "Kasan da Airline din da suka dauki Aliyu xa su sake bincikan brain dinsa aikinsa baxai kwana a hannunsa ba ranan, am telling u at that moment xa su sallamesa wllh" Dariya kawai Ahmad yayi, El-Basheer yace "Didn't u notice he is behaving like someone with mental condition?" Ahmad ya kalli Jiddah yace "Kwalliyan ya maki kyau sosai Jiddah" El-Basheer ya kallesa ya fara tafiya xuwa gun motarsu, Ahmad yace "Sai mun hadu anjima wajen dinner" tace "Toh" daga haka ta wuce cikin gida. Bayan Magrib su Abuturrab na gidan El-Basheer duk sun gama shiryawa, Abuturrab dai na xaune yana ta danna wayarsa, ya kafa hularsa a kai, kana ganinsa kasan he is the ango, Ahmad na kallonsa yace "Pls are u cautious of time Captain" Abuturrab ya daga kai ya kallesa yace "Ohk, what about that?" Najeeb yace "Kar ka manta sai an fara xuwa can gida an dau amarya" Abuturrab yace "Eh na sani, and i suggest ku tafi ku daukota, ni xan tafi event center din with my ride, sai in jira xuwan ku a mota" Ahmad yace "Why not duk mu tafi tare?" Abuturrab yace "Duk fa daya ne dude" Ba wanda ya sake ce masa komai, bayan few minutes duk suka fita gidan a tare, ya riga su wucewa da motarsa. Jiddah ce tsaye tana kokarin daura mayafi a kan lafiyayyen head din da aka daura mata, she looks so beautiful with her new make up wanda Hajja ta tada bala'i ta saka mai make up din Aneesah ta yi mata, domin kuwa ana Magrib ta wanka wanda aka masu da yamma wai ita sae ta sake alwala, doguwar riga fitted aka masu gaba daya a ankon dinner din yan mata da Aunty ta fitar na wani lafiyayyen lace, Sounding so fed up Maimoon tace "Wllh ke dai Jiddah kina da matsala, duk a nan wa kika ga ya wani dau mayafi xai yafa? ba fa a sa mayafi a kan irin wannan shigan wllh, tun daxu kike ta bamu matsala kin kama kin wanke make up bayan kowa na rike da alwalansa ke kince baki san xance ba, da ba don Hajja ba yanxu ai baxa ki samu wani make up din ba..." Jiddah da taki sauraronta tace "Ni dai baxan iya fita haka ba..." Maimoon ta fixge mayafin tace "U will just look odd among us, kawai fa mota xa mu shiga a ajiye mu a wajen mu shiga, idan xa mu dawo ma mota xa mu hau a dawo da mu gida ba wai titi xa mu bi muyi ta tafiya a kafa ba" Jiddah ta dinga kallonta alamar ita fa bata gamsu ba, duk kawayen amarya dake wajen kallon Jiddah kawai suke, irin kyan da tayi ba don anko ne jikinta ba bbu wanda dama xai ce ba ita bace bride din, ita Aneesah dama can dakin Aunty aka kai ta ana shiryata, Jiddah ta ta6a jelan tulin gashinta da ya leko ta head din tace "Yanxu har gashina haka xan bar shi a waje?" Wani harara Maimoon ta watsa mata tace "Ae kuma sae kiyi...." Daga haka ta nufi wayarta dake ring, Jiddah ta bi ta da ido, bude baki Maimoon tayi da mamaki tana kallon screen din wayarta, can ta nemi waje ta xauna a hankali tace "Toh wai ni me nayi ma Yaya Aliyu?" Sae da ya kusa katsewa ta daga ta kai kunne ta marairaice murya tace "Na'am Yaya?" Yace "Kuna ina?" Tace "Mun shirya xa mu fito yanxu" Yace "Ke da su wa?" Tace "Ni, Aunty Safiyya, Aisha, Sister Ramlah, Nafisah, Jiddah da wasu baki yan mata biyu?" Yace "Duk wani mota ne xai kwashe ku haka?" Ji tayi kamar tayi kuka ta dai dake tace "Aa dama saurayin Aunty Safiyya ne xai kai mu don ba mota" Yace "Duk ku takwas din mota daya xai kwasa?" Ta murguda baki tace "Aa Yousuf ma ae xai xo yace yana hanya" Abuturrab ya xauna da kyau a kan driver seat din da ya d'an kwantar yace "Shi kuma wa xai dauka?" Tace "Aa kawai dai xai xo tunda mota daya baxai ishemu ba, sai ya dauki duk wanda xai dauka" yace "Wa ya kira Yousuf din?" Tace "Waya suka yi da Jiddah" Abuturrab yace "Ohk... Idan kun kusa sai ki kirani xan baki ajiya ne" Tace "Toh" yace "Aneesah da frnds dinta sun bar gida ne yanxu?" Maimoon tace "Aa ba a gama shiryata ba" Yace "Ohk ki tabbatar basu riga ku fitowa daga gida ba in baki sakon da nace" A hankali tace "Toh" daga haka ya katse wayar, Maimoon ta wani turo baki tace "Toh wai ni me ya hadani da shi ne yau yake ta kirana haka" Jiddah dai bata ce komai ba ta karasa cusa mayafinta a jaka kafin Maimoon ta farga, kamar yanda ya fada Maimoon ta harhada tawagarsu ta kannin ango suka fito don Saurayin Safiyya ya iso, Safiyya da su Aisha da Ramlah suka shiga motarsa, Maimoon na ganin kiran Yousuf ta daga nan ya sanar masu ya iso, Babu yanda Jiddah ta iya haka ta shiga gaban mota, gaba daya a kunyace take saboda shigar da tayi, Maimoon dai ta shige bayan mota da Nafisah da wasu yan matan biyu, Yousuf ya amsa gaisuwansu gaba daya yana murmushi, bayan sun hau saman hanya ya d'an kalli Jiddah murya can kasa yace "Me yasa kika fito haka Jiddah?" Tana wasa da jakarta dake kan kafarta ta girgixa masa kai kawai, bai kuma cewa komai ba, sai da suka kusa event center din wayar Maimoon ya fara ring, tana ganin me kiranta ta jinginar da kanta da kujeran motar murya can kasa tace "Na shiga uku" Can dai ta daga ta kai kunne tace "Na'am yaya" Yace "Kuna ina?" Tace "Gashi mun kusa muna hanya" Yace "Ke da wa?" Tace "Nafisah da wasu yan uwan Aunty" Ya xauna da kyau yace "Sai wa?" Ta kalli Jiddah dake gaban mota tace "Jiddah" yace "Ohk, idan kun sauka ke da ita ku taho parking space xan bar fitila a kunne yanda xa ku ga motata" a hankali Maimoon tace "Toh" ya katse wayar. Yousuf na parking ya juya yana kallon Jiddah yace "I am not happy at how u dress today" Ta kallesa, Maimoon da ta galla masa wani harara ta fara kokarin sauka motar tace "Toh mun gode yaya yousuf, Jiddah mu je mu amso sakon...." Daga haka ta sauka, Jiddah na kallonsa a hankali tace "Kayi hakuri, mayafina na cikin jakana xan saka" Yace "Toh saka yanxu" Ta d'an kalli Maimoon dake tsaye ta wani sha kunu tana jiran saukowarta, Tace "Xan saka da gaske idan na sauka" yace "Wani sako xaku amso?" Jiddah ta buda hannu tace "Nima ban sani ba" Yace "To karfe nawa xan dawo daukanku?" Tace "Kai dama ba dinner din ka xo ba?" Ya girgixa kai yace "Aa ba shi na xo ba, anjima idan kun gama ki kirani in maida ku gida" Tace "Toh" Maimoon tace "Jiddah ya fara kira fa..." Jiddah tana kallon Yousuf tace "Toh xan kiraka mun gode" Ya bi ta da ido har ta sauka, tuni dama su Nafisah ma suka sauka, ya ja motarsa ya bar wajen.. Maimoon na dialing number Abuturrab ya daga yace "Wai baki da hankali ne kin bar ni mota Ina jira tun daxu??" Buda baki tayi, sai kuma ta hade rai tace "Ai ban san wani parking space din bane kayi parking" yace "Na dama idan kin shigo wajen... Kar ki bari in sake kiranki wllh" ta murguda baki tace "Ohk" daga haka ta katse waya, cike da masifa tace "Ni fa bana son harka da yaya Aliyu wllh, ni ban san inda ya samu number na ba, gashi sai kirana yake yi ni dai yana damuna, sae kace yanxu ba ni na kirasa ba" Nafisah tace "Toh ni dai xan jira bakin hall tunda gate pass dinku na wajena baxan je wajen ya Aliyu ba mood dina ya baci" daga haka ta wuce, Maimoon na kallon Jiddah tace "Toh kin tsaya mu tafi mana, masifa fa yake ta yi" Jiddah tace "Toh wai ni sai na bi ki?" Maimoon tace "Cewa yayi ni da ke mu taho ni dai kar kisa yayi min jaraba mu tafi ya bamu tsiyar da xai bamu mu shiga hall, gashi can ana ta yi ba mu" Jiddah dai bata ce komai ba ta bi bayanta amma ranta bai so ba, tun daga nesa Abuturrab ya hangosu da yanda duk attention din maxa ya koma kansu, ya xauna da kyau yana kara kare masu kallo kamar wanda ya ga wani mugun abu, gaba dayansu kuma takalmi me heel suka saka, Maimoon na isa dai dai parking space din ta tsaya jikin wata mota ta fara kiransa a waya tana cewa "Ni wllh abun nan duk ya isheni, gashi sai jaraba yake ma mutane a waya kamar me" Yana fara ring ta murguda baki tana gunguni, duk Abuturrab na kallonta, sai da kiranta ya shigo wayarsa snn ya dallara masu fitilar motarsa, Maimoon ta saita fuskarta tana kirkiran murmushi bayan ta hangosa cikin motar dake nesa da su sosai, ta kalli Jiddah tace "Mu je gashi can" Bin ta Jiddah tayi suka nufi motar dake can ciki sosai, sauka yyi daga motar yana kallon Jiddah daga sama har kasa, haka nan taji gabanta na faduwa taji kamar xata gurde kafa ta fadi, komai na shape din jikinta sai da gown din ya bayyana, suna kusa dab da shi ta makale jikin mota taki yarda ta karasa, Maimoon ma da ta sha jinin jikinta ganin kallon da yake masu ta tsaya d'an gaba da Jiddah tace "Yaya wani sako xaka bamu?" Calmly yace "Xo ki amsa" Ta dake ta karasa gabansa, xuciyarta na bugawa, ya kalli Jiddah yace "Ke can xan biyoki in baki?" Ta ki yarda su hada ido ta karaso gefensa a hankali ta tsaya, Yana kallon Maimoon da kyau yace "Wato don na kira ki nace xan baki sako shine kike murgude murgude kike xagina baki san duk ina kallonki ba" Ta xaro ido tace "Wllh ban xageka ba yaya neman..." Gwabje mata baki yyi da karfi, ta kai hannu bakinta da sauri tana kallonsa, ya hade rai yace "Bace gabana kar in taka ki..." Juyawa tayi ta bar wajen kamar xata tashi sama, Jiddah gabanta ya hau faduwa ta bi Maimoon da kallo, lkci daya ta juya da sauri kamar ya san abinda xata yi ya fixgota, tayi narai narai da ido tana kallonsa amma ta kasa cewa komai yana ganin ynda kirjinta ke heaving, strictly yace "Tun daga gida kika fito a haka da wannan shegun kayan?" Ido ta kafesa da shi, cikin tsawa yace "Ba magana nake maki ba?? Ke wato kina ganin matsayinki daya da su Maimoon ko?" Bata ce masa komai ba taga ya fixgota ya xaga ta daya side din motar ya bude back seat fuska daure yace "Shiga" Ta fashe da kuka tana kokarin kwace hannunta tace "Ni me yasa baxa ka daina takurani ba, bayan kace...." Bata rufe baki ba taji saukan mari, ta dafe kuncinta, bayan few seconds ta dago kai tana kallonsa ko kiftawa babu, turata yyi cikin motar yayi banging door din, ya xaga xuwa driver seat ya dau wayarsa dake ta ring sannan ya kulle motar dake a kunne ba tare da ya kashe Ac dake aiki ba ya bar wajen walking majestically, ta bi sa da kallo hawaye masu xafi na sauka idonta. Wani kallo Ahmad ya dinga masa yana wondering daga ina yake, don tuntuni suke ta kiransa amarya ta iso su shiga hall amma no answer, Aneesah dake xaune cikin mota dae sai kallonsa take don ba karamin kyau yayi mata ba, sai da ya karaso sannan aka bude mata motar ta fito tana kallonsa tana murmushi, tsayawa yayi gefenta ya d'an hade rai murya can kasa yace "Wannan kwalliyan fa kamar jan laka" tayi kasa da murya a hankali tace "Jan laka kuma Baby? Kana nufin ban yi kyau ba" Yana gyara hularsa yace "Aa baki yi ba gaskiya, u look odd" Ko ba a fada ba xaka san bata ji dadin abinda yace ba don nan da nan fara'arta ya gushe, kuma duk yana lura da hakan, hannunta ya rike cikin nasa a hankali yana murxawa yana murmushi yace "Wasa nake, you look sweet, u look like a... Quee..." Sai kuma yayi saurin cewa "Princess, yes my princess" Wani murmushi tayi tace "Aa queen din dai, the queen of ur kingdom my king" Yace "Noo princess din dai" Duk kasa kasa suke firan nasu gwanin sha'awa a wajen, har dai daga karshe Mc ya bukaci shigowarsu da frnds dinsu cikin hall din. Wajen Dinner kam ya cika, kuma ya hadu iya haduwa, abun ya kawatar da jama'a sosai, babu abun ciye ciyen da babu a wajen, iyayi kuwa wajen kawayen amarya ba a cewa komai, sai kai komo suke a inda El-Basheer ke xaune, idan ba kusa da shi ka je ba sae ka rantse balarabe ne xaune wajen, shi kam banda danna wayarsa babu abinda yake lkci lkci ne yake dago kai, Ahmad da ya kallesa sai yyi murmushi don yasan El-Basheer ya take Abuturrab wajen miskilanci, kuma in kaga yayi shiru haka to abu bai masa ba, bai burgesa ba ko kadan.... Irin rawan da Aneesah ta tika sai ya sa ka fara tantamar anya kuwa ita ce amaryar, cire kunya tayi abunta ta sha rawarta don a mentality dinta abu ne sau daya a lifetime, ba wani dinnern xata sake ba gwara tayi enjoying day dinta, su Aunty kirjin biki sai ji ake da jama'a ba a can ba a nan, daga yatsunta har kunne xuwa wuya gwalagwalai ne, Ummi ce kawai da Hajja basu je wajen ba amma har mahaifiyar Aneesah da kakarta sun xo dinner din daga Abuja, kaf family dinta babu wanda bai hallaci wnn dinner ba, shi ko uban gayyan was absentminded all through, Har Aneesah ta d'an cunkulesa a kafa tace "Wai tunanin me kake ne haka Babyna, naga kamar hankalinka baya tare da kai" Ya kalleta yace "Na gaji ne mana... abu kamar baxa a gama ba, this is going to 2hrs now" Turo baki tayi tace "Toh ko kwana xa ayi meye a ciki? ranan farin cikinmu ne fa, kuma sau daya xaka yi hakan a rayuwarka, ba wani dinnern xaka sake ba" ya kalleta bai dai ce komai ba, shi dai El-Basheer tun da aka shigo wajen ya baxa idon inda xai ga Jiddah amma bai ga alamarta ba, an kira kannin ango fage sun fito sun taka rawa anyi hotuna amma babu ita a ciki, can ya hango Maimoon sai tikar rawa take da su Nafisah as if their life depends on it, dangin amarya da aka kira ya sa suka bar stage din, El-Basheer ya mike ya nufi Maimoon kafin taje ta xauna tana ganinsa ta washe baki tace "Yaya Bash ba mu yi hoto ba" Yace "Xa mu yi, where is jiddah?" Ta d'an bude ido, sai kuma tace "Oho ni dai daxu Ya Aliyu yace muje mu amshi sako... Kuma ni na rigata shigowa hall, tun daxu nake dubata ban ganta ba wllh" yace "A ina Aliyun yace ku amshi sako?" Tace "Daxu ne a parking space, to ko gida ta kai masa sakon, ni dai ban sani ba, nayi ta duba ta ban ganta ba wllh" Bai ce mata komai ba ya koma ya xauna, Sai kallonsa kawai Abuturrab yake kamar yasan tambayar da yaje yayi ma Maimoon.... Sai karfe goma da wani abu aka tashi dinner din, outside d hall Abuturrab ya shafa kansa ganin motar da aka ajiye masa shi da Aneesah da xai maidasu gida, Ahmad na kallonsa yana jiran jin me xai ce don ya san da magana a bakinsa, Abuturrab na kallon Aneesah yace "Get in" Shiga motar tayi ya daga mata gown dinta dake jan kasa ya mika mata, ta amsa tana murmushi tana kallonsa, shiga motar yayi shi ma, Najeeb ya shiga driver seat ya tada motar suka fita hall din... kawayen Aneesah suka shiga motar Ahmad yayi gida da su su ma, Dai dai kofar gidansu Abuturrab Najeeb yayi parking, Najeeb yace "Xa mu jira frnds dinta yanxu sai su shiga da ita ko?" Abuturrab yace "Aa ba sai mun jirasu ba, ba dai kawai shiga ciki bane" cike da shagwaba Aneesah tace "Don Allah Baby ka jira su iso ni kunya nake ji wllh, sai su Ummi su ganmu haka mu biyu ai da kunya" wani kallon gefen ido yayi mata bai ce komai ba ya bude motar ya sauka, Najeeb couldn't help it but laugh ganin da gaske wucewa ciki Aliyu xai yi yace "Captain plss ka jira frnds dinta su xo xai fi" Abuturrab yace "Noo ai na barta ta jirasu, i have to go and ease my self" Daga haka yayi wucewarsa, Aneesah da ta sha kunu ta bi sa da wani irin kallo.... Can backyard din gidan Abuturrab ya tafi ya ja kujera ya xauna yana jiran su shisshiga, lkci lkci yake kallon agogon wrist dinsa, bayan some minutes ya mike ya fita gidan, da kafa ya karasa bakin hanya, ya samu adaidaita ya koma can wajen event center din, har sannan da akwai mutane wajen, kansa a kasa ya nufi parking space wanda motoci sun ragu sosai, direct gun motarsa ya nufa ya ciro makulli ya danna lock din motar snn ya bude back seat, xaune ya ganta ta hade kai da gwiwa kamar mai bacci, tana jin an bude motar ta dago da sauri, bayan ja har kumbura sai da idanuwanta suka yi don kuka, ta sauke kanta kasa yace "Fito" Ba musu ta fito daga motar ba tare da ta kallesa ba, fixgo hannunta yayi ganin wucewa xata yi, ta fashe da kuka sosai tana kiciniyar kwace hannunta tace "Ni ka kyaleni, ka sake min hannu" Kalle kallen wajen ya fara yi ganin jama'ah xata tara masa, ya ja ta xuwa daya side din wanda akwai wata mota a parke, ya jinginar da ita da motarsa yace "Baki da hankali ne kike cewa in kyaleki" kuka kawai take tana fixge fixge taki yarda ta kallesa, tsawa yayi mata yace "Ba magana nake maki ba" Ta kuma fashewa da wani kuka tace "Ni wllh ka sakeni... Ban son haka" da ta ga baxai saketa din ba ta kai bakinta kan hannunsa xata gatsa masa cixo ya xaro ido ya saki hannunta lkci daya ya rungumota jikinsa, nan ma ta hau kiciniyar kwace jikinta amma ta kasa, hakan yasa ta hakura amma bata fasa rusa masa kuka ba kamar ranta xai fita, kukan da take kuma bai hanata jin yanda xuciyarsa ke bugawa ba, lkci daya ta jika masa shaddar jikinsa da hawayenta... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Free delivery anywhere* It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Jin yanda take kuka Abuturrab yayi kasa da murya still holding onto her yace "Gaya min abinda aka maki kike kuka...." Ganin ba amsa xata basa ba sai shessheka take, ya rufe idonsa ya bude cikin tsawa yace "Ya isa haka nan" kokarin kwatar kanta ta fara yi da karfi amma ta kasa... hakan yasa tayi lamo jikinsa tana kukan a hankali, gaba daya scent dinsa ya cikata, hannunsa taji a idonta ya goge mata hawayen sannan ya bude mota xai shigar da ita ta fara turjewa, ya d'an hade rai yace "Baxa ki shiga ba??" turasa tayi da duk strength dinta bata ankara ba kawai taji ya dauketa kamar ya dau yar shekara biyar, ta hadiye kukan da take tana xaro ido tace "Na shiga uku, meye haka..." Cikin motar ya shigar da ita ya xaunar ta kamo hannunsa tana sake fashewa da kuka hankali tashe tace "Don girman Allah kayi hakuri kar ka sake kulleni a nan, ina hada ka da Allah kayi hakuri...." Ya daure fuska yace "To rufe min baki" Hadiye kukan tayi da sauri ta rufe bakinta tana gyada masa kai, don har ranta take tsoron kada ya sake kulleta cikin motar, sai da ya ga tayi shiru snn ya shiga bayan motar shi ma ya kulle yana kallonta, ta sunkuyar da kanta yana kallon yanda kirjinta ke sama da kasa, yace "Yanxu tun daga gida kika taho a haka babu mayafi?" Ita dai bata ce komai ba xuciyarta na bugawa, a fusace yace "Tambayarki nake" Ta jawo jakarta a hankali tana nuna masa tace "Yana ciki" Yace "Amma ke baki ji kunyan tahowa a hakan ba maxa na kallonki a hanya?" ita dai bata ce komai ba, gaba daya a tsorace take fatan ta kawai kar ya sake kulleta cikin mota yayi tafiyarsa, yace "Tambayarki nake..." ta marairaice tace "Ai a mota muka taho, ni ba wanda ya gan ni" Yace "Wa ya kawo ku a motar?" Tsoron ce masa Yousuf take bata san dalili ba, yace "Baxa ki bani amsa ba?" Ganin yanda take kallon kirjinsa ya sunkuyar da kansa yana kallo shi ma, da sauri ta dauke kanta, xaro ido yyi ganin yanda farin rigarsa ya bace da powder da janbaki, ya kalleta yace "Kinga abinda kika min ko??" Ta kallesa tayi narai narai da ido tace "Kayi hakuri" Ya d'an hade rai yace "Inyi hakuri? Sai in ce ma matata me idan ta gani?" Ta kallesa amma bata ce komai ba, handkerchief ya ciro aljihunsa ya mika mata yace "Maida min rigata yanda take" Tana kallon handkerchief din tace "Xai goge kuma?" Yace "Oho" karba tayi ta fara goge shaddar a hankali, ya jinginar da kansa jikin motar yana kallonta babu ko kiftawa, ita dai taga sai kara bajewa powdern yake, bata san lkcn da wani dariya ya taho mata ba ta rufe bakinta da sauri ya dinga kallonta, ta marairaice tace "Allah baxai fita ba" Yace "Ba ruwana" Bata kuma cewa komai ba tana ta gurje wajen da handki din hannunta tana kuma jin yanda xuciyarsa ke bugawa, daga kai tayi a hankali suka hada ido, fuxgota yyi ta kusa fadawa jikinsa cikin husky voice dinsa yace "Daga yau kika sake fita da gyale xan sa6a maki, sannan karatu kike yi yanxu babu ruwanki da ko wani namiji ko waye shi" wayarsa ne ya fara vibrate a aljihunsa ya saketa ya ciro yana duba screen din wayar, lkci daya ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido kafin ya rufe ta riko hannunsa da sauri cikin rawar murya tace "Don girman Allah kar ka sake kulleni" kulle motar yayi ya xaga ya bude driver seat ya shiga, sai a sannan taji hankalinta ya kwanta... Har suka iso gida bai ce mata komai ba, can nesa da gate din gidansu yayi parking, kashe mota yyi ya juyo yana kallonta cikin duhun motar yace "Dama kar ki kuskura ki ambato ni idan aka tambayeki daga inda kike" ita dai bata ce komai ba sai kallonsa take, yace "Fito da mayafinki" A hankali ta bude zip din jakarta ta ciro mayafinta, yace "Sauka" Bude motar tayi ta sauka ya bi ta da kallo har ta isa gate ta shiga cikin gidan, Umma ce ke kokarin fitowa parlor da wata kawar Ummi da Aunty Nafisah, Umma na ganinta tace "Daga ina kike Jiddah?" Jiddah da gabanta ya fadi tace "Umma ni ban ga su Maimoon ba kuma baxan gane gida ba" Umma tace "Wa ya dawo da ke yanxu?" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Ya Aliyu" Da mamaki Umma tace "Aliyu?? A ina kika ga Aliyu kuma?" Cikin sanyin murya tace "Aa kawai nagansa ne ya koma can wajen shine muka hadu ya taho da ni gida" ita kanta Aunty Nafisah kallon mamaki take ma Jiddah, Umma dai ta juya bata ce komai ba ta koma ciki, Kawar Ummi ta bi bayanta, Aunty Nafisah tace "Toh shigo" A sanyaye Jiddah ta shiga parlon, babu kowa parlon sai few guess da yaransu, Aunty Nafisah ta wuce dakin Hajja, ita kuma ta wuce dakin da ta san su Maimoon suke, Tana shiga dakin Maimoon ta mike da sauri tace "Jiddah ina kika je, ko wajen dinner ban ganki ba" Jiddah ta cire gyalen jikinta ta ajiye jakar hannunta tace "Toh ai baki nemeni ba" bandaki ta wuce don yin alwala... Washegari tun asuba aka tashi gidan aka fara girke girken breakfast, su Maimoon da su Jiddah kuma duk aka hadasu da gyaran gida, Safiyya da Nafisah parlorn gidan suke gyarawa, Tun da Jiddah taga sun gama gyaran part din Ummi xa su na Aunty taji hankalinta ya tashi, tana kallon Maimoon tace "Ko dai inje in dinga gyara dakin Hajja don mu yi sauri" Maimoon tace "Aa wllh muje mu gyara na Aunty tare, Na hajjan ma muyi tare" Jiddah bata kuma cewa komai ba ta bi bayan Maimoon xuwa part din Aunty, yawanci duk yan uwan Aneesah ne a parlonta, Aneesah da kawayenta kuma na can bedroom dinta, Jiddah ta gaishe da manyan da ta gani a parlor suka wani amsa da kyar kamar dai sun santa, Maimoon dama bedroom ta wuce direct bata ko kallesu ba Jiddah ta bi bayanta, Aneesah da kawayenta suka daga kai suna kallonsu, Maimoon tace "Xa mu yi gyaran daki" wani kallo Aneesah tayi masu daga sama har kasa tace "Da mutane a ciki xa ku yi gyaran?" Maimoon tace "Atoh saka mu aka yi mu ma ai" Aneesah tace "Toh sai ku koma kuje kuce ma duk wanda ya aiko ku da akwai mutane a ciki" Jiddah dai bata ce komai ba tana tsaye, Maimoon ta wani ta6e baki tace "Toh mutane" Daga haka ta juya tayi ficewarta daga dakin, Jiddah suka hada ido da Aneesah da ta wani murtuke fuska kamar ta ga mugun abu, juyawa Jiddah tayi ta fita daga dakin ita ma, kawar Aneesah Naja tace "Wai wacece wnn da tsohuwar can na jiya ta dage sai mai make up dinki ta mata make up, sannan sai in ga tana ta wani shan kamshi tana daga kai ko kanwar Captain din ce ita ma" Aneesah ta jefa mata wani kallo tace "Kanwar Captain? Tab... Amma kin so neman magana, wa ya bata matsayin kanwarsa? Ke baki ga yanda take dari dari ba kice wani daga kai da shan kamshi, ai karere ce ita a gidan Awara da doya fa take soyawa a hayin rigasa inda train station yake, cin arxiki fa take kawai a gidan, ya talakawa ce nan ku ke gani mara galihu" Naja tace "Ke Aneesah, wllh na xata yar gidan ce yanda na ga an dage sai me kwalliyanki tayi mata" Aneesah ta ja wani dogon tsaki tace "Ni ki bar ma xancen raina baci yake wllh" Fauziyya tace "Toh Allah ya kyauta, nima dai ban xata karere bace a gidan, kuma na ganta fara kamar dai..." A fusace Aneesah tace "Don Allah ku bar xancen nan haka nan, nace maku yar Hayi ce, doya da dankali take siyarwa, kuma yar talakawa ce" tana fadin haka ta mike ta shige bandaki. Bayan azahar Jiddah ta fito sanye da Hijab dinta har kasa ta dalilin kiran da Yousuf yyi mata ta wayar Maimoon, yana tsaye jikin motarsa ta karasa gun motar da ladabi tace "Ina yini?" Yace "When did u leave the event center yesterday?" Tace "Ni ban duba agogo ba" Yace "Na kira Maimoon tace baku tare, where were u?" A hankali tace "Ba waje daya muka xauna ba" Yace "Toh wa ya dawo da ke gida" D'an murmushi tayi tace "Masu dawo da jama'a gida mana" Da ido suka bi motar da ya wuce su, motar yayi parking d'an gaba da nasu, Ahmad ne ya sauko sannan El-Basheer, Abuturrab ya bude back seat ya sauka shi ma, kallo daya yyi ma Jiddah ya nufi gate, El-Basheer ma ya bi bayansa, Ahmad ya karasa ya mika ma Yousuf hannu yana murmushi bayan sun gaisa yace "Ba mu ganka wajen Dinner dinmu ba jiya" Yousuf yace "Yeah naje amma ban dade ba" Ahmad yace "To madallah" sallama suka yi Ahmad ya shiga gidan, Yousuf ya jingina da mota yace "Guys din gidan nan i think suna da karancin ilimin mu'amalah da mutane" Jiddah ta kallesa kawai tayi murmushi yace "Yahhh, that pilot... i don't know but i wont call him an introvert, kawai dai bai san mutuncin d'an Adam bane, and i guess shi ma farin d'an uwansa ne ko?" Jiddah tace "Ehh" yace "Bird of the same feathers" Jiddah dai bata ce masa komai ba, Yousuf yace "Yaushe xaku koma gida da su Umma?" Jiddah tace "Kilan idan an kai amarya da yamma" Yace "Toh Allah ya kai mu, xa mu yi waya with Maimoon's phone" ta gyada masa kai kawai, yace "Take care Jiddah" Ta yi murmushi tace "Nagode" daga haka ya xaga xuwa driver seat ita kuma ta shiga cikin gidan, dakin Hajja ta nufa don dama aiki take mata Yousuf ya kira, tana shiga dakin Hajja dake xuba ma su Ahmad abinci ta daga kai tana kallonta tace "Toh wai saurayinki ne ya xo halan, naji shiru shiru" Jiddah ta nufi kayan da take linke mata don ta karasa, Hajja ta kalli Maimoon dake dakin tace "Halan dai saurayinta ne?" Maimoon tayi dariya tace "Ehh" Hajja tace "Atoh shi kuma baya gaida mutane ne, ai da sai ya shigo ya gaishemu yayi mana Allah ya sanya alkhairi haka ake yi" Jiddah ta ci gaba da linkinta, Hajja ta gama xuba abincin ta mike tace "Toh a kai masu can dakin, idan ba ni ba babu wanda xai masu haka, kowa na ta kansa a gidan" Maimoon ta mike ba tare da ta tsaya gyara plates din abincin kai ba ta dau tray din sai ga plate daya ya rikito kasa, Hajja ta amshe tray din da sauri tace "Je ki Allah ya isa" Wani kallo Maimoon tayi mata tace "Toh na sani ne?" Hajja tace "Nace maki wani abu ne, cewa nayi kije ke da Allah kawai" Maimoon ta fice daga dakin kamar xata tashi sama, Hajja tace "Algunguma kawai, wllh da gangan ta kifar, dama bata yi niyyar xuwa ba, yar mummuna da ita kawai, uban me na hada da ita banda dai uwarta kanwar matar d'a na ne, gayyar tsiya kawai, da a Masar ne dama babu wani dangantaka tsakanina da ita nan ne dai komai sai anyi karere" Ita dai Jiddah linkinta kawai take, Hajja ta sake xuba wani shinkafar tana ta mita, har ta gama sannan ta kalli Jiddah tace "Ki dauka ke ki kai masu, nima na so raina ya baci ne, banda haka ga ki, er arxiki irin albarka" Jiddah ta ajiye xanin hannunta ta karasa ta durkusa a hankali ta dau tray din ta nufi kofa, sai a sannan ta juya tace "A ina xan kai masu?" Hajja tace "Suna can parlon Usman" Jiddah ta fita dakin ta kama hanyar parlon Abba, sai da ta fara ajiye tray din ta murda kofar a hankali hade da sallama sannan ta dau tray din ta shiga ciki, waya na kare kunnen Abuturrab yana magana, El-Basheer kuma na xaune saman kujera idonsa a kan phone dinsa, karasawa ciki tayi ta ajiye tray din tana kallonsu tace "Ina yini" El-Basheer na kallonta da murmushi yace "How are u?" Tace "Lafiya lau" Daga haka ta mike ta nufi kofa El-Basheer yace "Who were u speaking with outside Jiddah" ta juyo tace "Yaya Yousuf ne" El-Basheer yace "Who is he?" Ta d'an yi shiru kafin tace "Family frnd din su Yaya Ahmad" El-Basheer bai kuma cewa komai ba, ta d'an kalli Abuturrab taga yanda ya sha kunu, juyawa tayi ta fice daga parlon. Bayan la'asar aka fara shirye shiryen kai amarya, gidan cike yake dam da jama'a yan kai amarya, motoci sun fi ashirin a compound da kofar gida duk na yan kai amarya, wajen Hajja aka fara kai Aneesah dake sanye da alkyabba fuskarta a rufe, aka xaunar da ita saman carpet Hajja na daga xaune kan tabarma ta daura kafa daya kan daya, tana kallon Aneesah tace "Ni dai bani da abinda xance, amma da a Masar ne kawai ce maki xa ayi ki bi yan uwansa da iyayensa sau da kafa, to sai ki ji dadin xama da shi, duk abinda yake so shine abun sonki.... Kinga dai shi me yan uwane barkatai kuma duk baxa su ki xuwa gidansa ba don haka kika iya allonki ki wanke, ko ni nan duk sanda na ga dama xanje gidansa tunda ni na haifi ubansa kuma a hannuna ya taso daga bisanni ya fita waje koyon tukin jirgin sama..." Aunty dake tsaye daga bakin kofa sai hararan Hajja take kamar ta kifa mata Mari, Aneesah dai sai satan mutanen dake dakin take da kallo duk da fuskarta a rufe yake, Jiddah ta gani xaune gefen gado rike da jakar da Hajja ta bata, ganin kallonta Jiddah ke ta yi ta wani tsuke fuska kamar tana ganinta, ita dai har ranta taji ta tsani jiddah, bata ta6a jin tsanar mutum yanda take ma Jiddah ba, she just hate her with passion, Hajja ta gama surutanta mara tushe aka daga Aneesah dake ta kallon Jiddah har lkcn, aka fitar da ita daga dakin, next aka kai ta gun Ummi, Ummi ma tayi mata duk nasihar da ya kamata, Umma ta daura da nata, daga karshe aka kai ta gun Abba da Uncles din Abuturrab, sai wajen hudu da rabi aka kai amarya mota, Hajja ta saka ma kofarta makulli ta mika ma Jiddah tace "Jefa min a jaka sai Allah ya mana dawowa kuma, mu xa mu kai ta" Saurayin Safiyya ne ya tafi da su Maimoon da Jiddah da safiyyar sai Nafisah gidan Abuturrab, tun da yayi parking out side gate Jiddah ke kallon gidan, kamar bata ra6a rayuwa a gidan nan ba, kofar gidan cike yake da motocin kawo amarya, Maimoon da su Jiddah suka samu suka shiga compound din, Jiddah dai na biye da su a baya har suka shiga parlon, taji gabanta ya fadi, komai na parlon an sauyasa xuwa sabo, jama'a ne cike parlon ana ta gud'a, Maimoon ta ja su Jiddah suka wuce sama, dakin da Jiddah ta xauna ta bude taga few mutane a ciki, kayan dakin ma duk an canza suka fito suka bude sauran dakunan da duk aka xuba ma furnitures, duk da Abuturrab ya sanar ma Aneesah ta gaya ma iyayenta ba a bangarensa xa a xuba mata furnitures din daki ba, taki sanar masu, can kuma suka kai kayan dakinta, Jiddah dai sai kallon parlon Abuturrab take, har sannan hotonsa na kayan pilot na parlon, ta rasa me yasa memory ke ta dawo mata, ba karamin kudi iyayen Aneesah suka kashe mata na kayan daki ba, don duk dakuna hudun dake gidan sun xuba kaya, can karshen gado ta xauna fuskarta a lullube Jiddah dai kallo daya tayi mata ta fita daga dakin ta bar su Maimoon a can ta koma downstairs ta xauna a parlor tana bin ko ina da kallo. Sai kusan karfe shidda aka fara watsewa daga gidan amarya shi ma Hajja ce ta fara sallaman mutane su tafi kada a 6ata ma yarinya gida, gidan ya rage daga Umma, Aunty, Aunty Nafisah da frnds din Ummi, sai wasu family, Jiddah dai sai jiran lkcn da Hajja xata tafi ta bi ta take don taga alamar su Maimoon basu da niyyar tafiya don har Saurayin Safiyya ya wuce, tana ta xaune parlor har magrib hakan yasa ta mike ta shiga bandakin dake parlor tayi alwala ta fito tayi sallah, bayan ta idar ta tafi sama ta bude dakin da take tunanin su Maimoon ke ciki xaune ta gansu suna ta hira, Tace "Wai baxa mu tafi gida bane?" Nafisah tace "Aa mu dai kila ma a nan xa mu kwana" Xaro ido Jiddah tayi, can tace "Toh ga jakar Hajja ni xan tafi" Maimoon tace "Toh wa xai maida ki gidan?" Jiddah tace "Akwai dari biyar din Umma a jakana xan yi amfani da shi" daga haka ta fita, xata sauko downstairs suka kusa cin karo da Aunty sake haurowa sama rike da abinci, sosai gabanta ya fadi ta koma gefe da sauri, Aunty ta kalli downstairs taga babu kowa parlon, fuska murtuke tace "Uban me kika taho yi gidan nan ke kuma?" Jiddah dai ta kasa cewa komai gabanta na faduwa, Aunty tace "To don ubanki sauka ki kama hanyar ki, ke a wa xaki biyo yan kawo amarya, munafuka kawai mayya, nace ke a wa??" Jiddah ta fara sauka a sanyaye, hankadeta Aunty tayi har sai da ta kusa faduwa, cike da tsanarta tace "Maxa fita, ke da gidan nan ai sai dai hange daga nesa" Jiddah bata ce komai ba ta sauka da sauri ta nufi kofa ta fita compound din gaba daya, duk jikinta yayi sanyi, slowly take tafiya a dogon layin wanda ko wani gida da fitilu farare da ya haska layin kamar rana, mota ne ya dallareta ta sunkuyar da kanta tana ci gaba da tafiya a hankali, reverse taga motar na yi yana komawa baya, ta kalli motar don bata ta6a ganin irinsa ba, lkci daya aka sauke glass din motar, ta dinga kallonsa, murmushi ya sakar mata yace "Hi...." Ta fara wasa da hijab din jikinta ta sake satan kallonsa, bude motar taga yyi ya sauka ya xagayo ta inda take yace "Assalamu alaikum" amsawa tayi a hankali, yace "Sorry na tsayar dake a layi ko?" Tace "Um" yace "Kin ganeni kuwa" ta sake kallonsa, d'an murmushi kawai tayi bata ce komai ba, Yace "Ina xa ki da daddaren nan?" Tace "Gida" da mamaki yace "Ba can bane gidan ku dama" ta kalli gidan Abuturrab da yake nuna mata, sai kuma ta girgixa kai tace "Aa, gidan yayanmu ne" Ya wara manyan idanuwansa yace "Ohh, shi yasa na daina ganinki kenan" murmushi tayi masa nan ma, yace "Toh mu je in ajiye ki gidan naku ynxu" Tace "Aa ai ban sanka ba" Yace "Really? Duk sanin da kika min a balcony?" Murmushi tayi tana kallonsa, ya bude mata front seat yana kallonta, sauke idonta tayi ta shiga motar ya kulle sannan ya xaga ya shiga driver seat, reverse yayi suka bar layin yace "Ya sunanki?" A hankali tace "Jiddah" As if counting his words yace "Jeedderh!!" Ta kallesa ya sakar mata murmushi wanda har sai da dimple dinsa ya lotsa ya kai fuskarsa dab da ita yace "I am Ali" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Jiddah ta sauke idonta daga kallonsa tana sake nanata sunansa a xuciyarta, Aliyu kenan yake nufi, Ali shi ma ai Aliyu ne... muryarsa ya katse tunaninta, taji yace "Wani anguwan xa ki?" Sake kallonsa tayi sannan tace "Malali...." tana fadin haka ta bude jakar hannunta da sauri jin waya na vibrate, sai a sannan ta tuna ai wayar Maimoon na wajenta tun daxu da Yousuf ya kira suka yi magana, ta fiddo wayar tana kallon screen din taga Ya Aliyu... Ta d'an kallesa tace "Nayi mantuwa na taho da wayar yar uwata xan mayar mata cikin gida yanxu" Yace "Ohh ohk, take ur time, bari in ajiye ki bakin gate and i will wait u there okay?" Dai dai gate din gidan Aliyu ya tsaya ta bude motar ta sauka sannan ta shiga compound din tana tafiya a hankali, wayar har ya katse ya sake kira, kafin ta shiga parlor ya sake katsewa, a nan gabanta ya hau faduwa tana tsoron kada ta sake ganin Aunty, da sauri ta wuce sama ta bude dakin da su Maimoon suke, duk suka juya suna kallonta, Maimoon tace "Kin fasa tafiyar kenan" karasawa tayi tace "Na mance na tafi da wayarki ashe a jakata, kuma ana ta kiranki amma dai ya katse.." Maimoon ta xaro ido tana kallon wayar da Jiddah ke mika mata tace "Lahh ashe wayar na gun ki na xata yana caji, wa ke kira?" Lkci daya mood din Maimoon ya canxa ganin me kiranta, cike da damuwa tace "Ni dai na shiga uku, wai ya Aliyu ke kirana, to me yasa?" Dagawa tayi ta kai kunne fuska daure, Kafin tace komai yace "Kuna ina?" Ta turo baki tace "Aa muna nan gidan amarya yaya..." Yace "Ke da wa da wa?" Tace "Ni, Aunty Safiyya, Aunty Ramlah, Nafisah, Aisha da Yusra, sai Jiddah amma ita xata wuce gida ynxu, mu kuma muna son mu kwana ne" murya can kasa tace suna son su kwanan don bata san me xai ce ba, instead sai taji yace "Wacece xata tafi?" Ta kalli Jiddah da har ta nufi kofa ta fita, tace "Jiddah" Yace "Xata tafi ina?" Maimoon tace "Wai gida, tace ita baxata kwana ba" yace "Gidan da babu kowa?" Maimoon tace "Nima dai haka na gani... Amma Ummi na nan ai" Yace "Bata wayar" ta mike da sauri tace "Toh bari in kai mata ta fita yanxu" Yace "Do that quickly" cikin hanxari Maimoon ta fita dai dai second stairs taga Jiddah a tsaye tana kallon parlor, Jiddah da bata ma san Maimoon ta fito daki ba, ta sauke idonta daga kallon da take ma 3 seater din parlon, ta ci gaba da sauka downstairs a hankali, Maimoon ta kwalo mata kira tace "Yaya xai maki magana" Daga haka ta karasa kusa da ita ta mika mata wayar, amsa Jiddah tayi tana kallon screen din sannan ta kai kunne, daga daya bangaren taji yace "Ina xa ki?" Tace "Gida" yace "Toh kar ki kuskura ki fita daga gidan nan ba tare da su Maimoon ba" shiru tayi ta ma rasa abinda xata ce, a takaice yace "Bata wayar" Ta mika ma Maimoon wayar, daga daya bangaren yace "Nafisah dama xan yi ma magana kai mata wayar yanxu" Maimoon tace "Toh" daga haka ta juya ta tafi kai ma Nafisah waya a daki ranta fari tass bai ce su wuce gida ba duk da ta sanar da shi xa su kwana, Gaba daya mood din Jiddah ya canxa, ta ci gaba da sauka a hankali ta nufi kofar parlon ta fita, har sannan Ali na jiranta bakin gate, ta karasa kusa da motar don glass a sauke yake, cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri don Allah brother dinmu yace mu kwana a nan kawai" Yace "Ohh really, to shkkn Jiddah, can i get ur digit plss?" Tace "Bana rike waya ae" ya xaro ido yana kallonta, yace "Saboda me?" Sincerely tace "Karatu nake yanxu" kallonta yake yi da kyau, but come to think of her age kamar ynda ya kiyasta a ransa sae ya yrda da abinda tace, ya shafa lallausan gashin kansa yace "Then how will i be contacting u?" Tayi shiru, yace "Amma yar uwarki na da waya ita ai" Tace "Ehh ai ta girmeni" Yace "Ohh ok, gobe da karfe nawa xa ku bar nan?" Tace "Nima dai ban sani ba" Yace "Toh xanyi sallama da safe hope it's okay?" Ta xaro ido tace "Aa idan yayanmu na nan fa" yace "Ohk sai yayi maki fada?" Ta gyada masa kai, shiru yayi, can yace "Okay then xan turo kanwata Khaleesat, she is just ur mate i guess, and kuna yanayi da ita sosai, ranan farko da na ganki a balcony daga nesa sai na ga kamar ita but i know i was mistaken coz tana boarding schl... She is available now sun yi hutu, and i want u two to be frnds..." Tayi murmushin karfin hali tace "Toh" Yace "Let me not keep u standing in sha Allah xata shigo da safe sai ta baki waya mu yi magana okay?" a hankali tace "Allah ya kai mu" murmushinsa me kyau yyi mata ta juya ta shiga compound din gidan, a parlor ta ci karo da Aunty da kawayen Aneesah rike da warmer din abinci iri iri sun fito daga kitchen, Da mamaki Aunty ta tsaya tana kallon Jiddah, can ta ajiye babban warmer din hannunta tana kallon hanyar stairs ta nufota, Jiddah ta fara komawa baya gabanta na faduwa, Aunty na nunata da yatsa tace "Wai ke wacce irin natattciya ce mayya? Ban koreki daga gidan nan ba kika kara dawowa don ubanki, kin ga wani bare a nan banda ke? Duk fa babu bare a gidan nan wllh, Me kika sake dawowa yi banda rashin xuciya don Allah, idan muna abu na family me yasa xaki dinga cusa kanki, wllh tunda nake ban ta6a ganin me naci mara xuciya irinki ba.. ke a wa xaki biyo jama'a xuwa gidan nan idan ba kin yada xuciyarki kare ya lashe ba, bamu hada komai dake ba fa, babu dangin iya balle na baba, yar talakawa dake ma idan ba kaddara ba da kuma Aliyu da ya ja mana wannan masifa da fitina me xai shigo dake irin wannan family din, ke kin ma samu waje ko waiwayon kauyanku baki yi kin shigo birni ko..." Jiddah ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, duk kawayen Aneesah na tsaye parlon suna kallonsu da alamar abun ya masu dadi, Aunty ta bude kofa ta hankadata waje a fusace tace "Fita ki bar gidan nan don uwarki, wllh kika sake dawowa sai na kwara maki tafasasshen ruwan xafi sai dai duk abinda xai faru ya faru" Juyawa Jiddah tayi ta fara tafiya, taji xuciyarta yayi mata rauni sosai, tun da aka fara shirin kai amarya dama tace ita baxata ba amma Hajja tayi ta fada wai ita ma xata fara koyon mugun hali irin nasu Aisha da Maimoon, xata fara yi ma mutane musu da taurin kai, haka ne yasa bata sake cewa komai ba aka shirya da ita aka tafi kai Aneesah, banda wannan bata tashi da intention din bin yan kai amarya ba don karatu ma tayi niyyar yi idan an tafi, da gefen hannunta ta share hawayen da ya gangaro fuskarta me xafi, tana fitowa kofar gida ta nufi titi da kafa, ta fi minti goma a tsaye tana jiran adaidaita sahu kafin ta samu daga karshe, har suka isa gida hankalinta baya jikinta, ta sauka ta basa kudi, snn ta juya xata shiga gate dai dai fitowar Aliyu daga gate din rike da makullin motarsa, kana ganin fuskarta kasan tayi kuka duk da ba me yawa ba, daga sama har kasa yake kallonta, yace "Tafi wajen motata ki jirani" cikin sanyin murya tace "Me xanyi a can? Don Allah ka barni in shiga gida" Yace "Are u questioning me?" Juyawa tayi ta nufi motar walking slowly, har ta isa gun motar ta tsaya, sai a sannan ya nufi motar ya bude back seat yana kallonta, hawaye ya kawo idonta tana kokarin ganin bai xubo ba cikin rawan murya tace "Don Allah ni baxan shiga ba, ka barni in je inyi sallah" Ya dinga kallonta, sai kuma ta juya masa baya ta fara kukan dake cin ta, sai a lkcn maganganun Aunty ke mata xafi sosai a xuciyarta, taji she really wants to go back to Hansai, don ita kadai ce idan tayi mata bata kuka kuma bata Jin xafi a ranta tunda a ko da yaushe kallon mahaifiyarta take mata, ita ta taso ta gani a matsayin baabarta, kuma ita take ma kallon baabarta, Kallonta Abuturrab ya dinga yi cause kana jin yanda take kukan kasan she is hurt, bin wajen yayi da kallo sannan ya kama hannunta ya shigar da ita motar, ta hade kanta da gwiwa tana rera kuka, ya xauna gefenta ya kulle motar yana kallonta yace "Jiddah" kin dagowa tayi, ya dago kanta yace "Me aka maki?" Girgixa masa kai kawai tayi, yace "Aunty ko?" Nan ma ta girgixa masa kai kawai, Tsawa yayi mata yace "Baxa ki bude baki ki min magana ba" ta kuma rushe masa da kuka, ya kamo hannunta yana kallonta, sai kuma ya ciro handkerchief a aljihunsa ya mika mata yace "Clean of those tears..." Bata masa musu ba ta amsa amma bata goge idon ba, ya karbe a hannunta ya fara share mata idon yace "Me Auntyn ta maki?" Taki ce masa komai, bayan few seconds yyi kasa da murya yace "Kiyi hakuri" Kamar jiran jin hakan take ta hade kai da gwiwa ta fara sabon kuka, ya dagota ya hade rai yace "Ba nace kiyi hakuri ba?" Cikin shessheka tace "Dama nace ma Hajja baxan je ba shine ta sa sai naje..." Bai ce mata komai ba sai kallonta yake but he is boiling from inside, mota ce tayi parking dai dai kofar gate aka bude motar Aunty ta sakko da wasu kawayenta suna ta labari, ya dinga kallonsu har suka shige cikin gida, Jiddah taji hankalinta ya tashi ganin Aunty ta dawo gidan, ta marairaice tana kallonsa tace "Don Allah ko xaka kai ni gidan Umma kilan ta koma gida..." Bai ce komai ba ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido ya shiga driver seat ya tada motar ya bar layin, a hanya aka yi ta kiran wayarsa, ya daga daga karshe, calmly yace "Kun ga Ahmad ni ba yaro bane da xa a wani jera dani kafin in shiga gidana, this isn't my first marriage, my first marriage ma babu wanda yayi min haka, i went home my self, don haka duk sanda nayi niyyar shiga gida xan shiga, yanxu ina wani sabgar ne..." Ahmad yace "Ohh really?" Abuturrab yace "Yes Ahmad, bana anguwan ma ni" Ahmad yace "To idan kaje gidan sai ka sallami kawayenta..." Abuturrab yace "Sun wahala in dai sallamata suke jira... xa mu yi magana good night" daga haka ya katse wayar, dai dai kofar gidan Umma yayi parking ya kashe motar, Jiddah da taji wani relieve ta bude motar ta sauka tana kallonsa tace "Sai da safe" Daga haka ta shiga gate din gidan ya bi ta da kallo. Gidansa ya wuce daga nan, Aneesah da kawayenta na daki banda complain babu abinda take, Fauziyya tace "Nima ban ta6a ganin haka ba wai kannin ango su wani xo gidan amarya suce xa su kwana ranan da aka kawota, wllh sai kinyi da gaske wajen tattaro hankalin mijinki gaba daya gareki ya share kowa ya daina ganin kowa sai ke, don wnn dangin nasa baxa su bari kiji dadin rayuwar aurenku ba" Aneesah tace "Baxa su bari in ji dadin rayuwar aurena ba??" Wani dariya tayi tace "Lokacin da shigowa gidan nan xae fara gagaransu xan kira in sanar maku, ni fa Captain da ku ke gani nawa ne ni kadai wllh, haka plan din yake dama" Naja tace "Atoh, dama wa xai xauna ya xuba ido, barin ma miji irin naki, wllh kar kiyi sanya Aneesah... Kowa tashi tsaye yake" Aneesah tace "Ni nasan bani da matsala da yan mata tunda nasan wanene captain, nasan root din matsalata a aurenmu kuma magancesa ba wani big deal bane wllh" Jin an bude kofar parlon duk suka yi tsit, Maimoon ta shigo cikin dakin tana wani cika tana batsewa tana kallonsu Fauziyya tace "Ya Aliyu yace idan kun gama xaman ku fito xa a maida ku can gida" Aneesah ta cire gyalen kanta da sauri tace "A maida su gida?? Budar kan fa??" Maimoon bata ko kalleta ba ta juya ta fice, Mikewa Aneesah tayi ta fice daga dakin bayan ta daura mayafi a kanta ta sauko downstairs, tsaye ta gansa a parlor, da mamaki tace "My Captain kace xa a maida su Fauziyya gida? As in how?" Yace "Ehh" ta daure fuska tace "Toh wai budan kan fa?" Calmly yace "Duk budewar nan da kika yi ma kan bai yi ba sai wani special one kike jira" Da mamaki take kallonsa, yace "Pls Aneesah I'm tired and i need rest now... idan xa su sakko in ajiyesu tare da su Maimoon su sakko, or i leave the house duk sanda suka tafi in dawo" Kallonsa kawai Aneesah take, sai ga su Maimoon da Aisha da Nafisa ko warce da jakarta a hannu tana cika tana batsewa suka sakko suka ma Aneesah sai da safe suka fita waje, juyawa yayi ya bi bayansu, ya fi minti goma xaune a mota yana jiran fitowar kawayen Aneesah uku amma shiru shiru, su Maimoon dai na xaune bayan mota, daga karshe ya tada motar ya maida su gida, ko sai da safen kirki Maimoon bata yi masa ba ta shige gate tare da su Aisha, sai a sannan tace "Da nace masa xamu kwana fa daxu bai ce komai ba don har cewa yayi in kai ma Jiddah wayar ita ma ta dawo ta kwana I don't know what made him Change his mind all of a sudden" Aisha dai sai ta6a bake take tace "To ba gashi dai mun dawo gidan ubanmu ba" Direct hotel Abuturrab ya wuce yyi lodging daki, sai da ya watsa ruwa sannan ya kwanta bayan ya kashe wayarsa. Har karfe biyun dare Aneesah bata yi bacci ba, bata ta6a xaton haka nata first night din xai kasance ba, yanxu duk abubuwan da aka ce tayi a wannan daren baxata yi ba kenan ya tashi a banxa, gashi tayi ta kiran layukansa duk a kashe, dama rashin mutuncin Aliyu ya kai haka bata sani ba, lallai kamar yanda aka ce mata xama ba nata bane, xaman kuwa ba nata bane, she needs to bring down Aliyu to d level she wants him to be for her, kawayenta uku na kwance saman gadon sun yi bacci abunsu hankali kwance, mikewa xaune tayi daga karshe ta fita parlor ta xauna tayi tagumi, duk irin burikan da ta ci ma daren nan ya tashi a banxa kenan?? a takaice sai wajen karfe hudu bacci barawo ya sace Aneesah, Washegari da safe aka kawo abinci daga can gidansu Abuturrab, Fauziyya ce ta bude kofar parlon ta amshi abincin a hannun su Safiyya ta kai masu can sama, bayan sun hada shayi me kauri ga uban kwai da dankali a gabansu Fauziyya tace "Wllh ki nuna ma Captain din nan bacin ranki, wacce amarya ce aka ta6a yi ma wnn walakancin da yayi maki, ni ko a tarihi wllh ban ta6a jin haka ba, kar ki kuskura ki amince masa duk dadin bakinsa sai kin gwara kansa shi ma kin rama... Wannan ai walakanci ne wllh, duk wani ango na xumudi a ranan da aka kai masa amarya amma banda naki angon...." Aneesah dai bata cewa komai amma gaba daya ranta a dagule yake, daga karshe ta mike ta dau wayarta ta fita, wani dakin ta shiga ta kulle ta yi dialing number Aunty, yana fara ringing Aunty ta daga tace "Amarya bakya laifi, har kun tashi? Fatan dai komai normal?" Aneesah ta fashe da kuka, Aunty ta xaro ido ta mike tsaye ta fita daga dakinta don akwai wasu baki, murya can kasa tace "Lafiya Aneesah me ya faru? Da matsala ne?" Cikin kuka Aneesah ta shiga ba Aunty labarin abinda Abuturrab yayi jiya, Aunty ta saki baki har Aneesah ta kai aya, can tace "Abinda ya maku kenan Aliyun?" Cikin kuka Aneesah tace "Wllh kuwa Aunty, ni da babu kawayena ma da baxan ji wnn kunyan da nake ji ba ynxu, duk fa sun san komai kar suje su yada ni a Abuja, har cewa suke ko a tarihi basu ta6a jin amaryar da aka yi ma wnn rashin mutuncin ba" Aunty da ranta ya dau tafarfasa tace "Shikenan, share hawayenki Aneesah, xan kiraki nan da anjima kadan, kiyi hakuri ko su Mumy kar ki sanar ma kinji!" Aneesah na shessheka tace "Toh" daga haka Aunty ta katse wayar tana wani huci ta hau dialing number Abuturrab taji a katse, rike baki tayi tana naxarin walakancin da xata masa, can tayi wani murmushi hade da kwafa ta koma daki xuciyarta na ci gaba da 6ararraka.... Karfe tara da yan mintuna Jiddah ta fito daga dakinsu sanye da kayan bacci dogo har kasa sai hula a kanta xata shiga kitchen, ita kadai ce a gidan sai Umma da Aunty Nafisah, su ma kuma basu tashi ba, Huraira na can gidansu Ummi bata dawo ba sbda aiki, tun asuba ta tashi ta gyara gidan gaba daya tayi wanke wanke ta share har balcony, ta tafasa ruwan Lipton da ta cika ma kayan kamshi ta juye a flask snn ta koma daki wajen karfe takwas amma bata yi bacci ba, yanxun ma yunwan da take ji ya sa ta fito xata hada shayi, bude kofar parlon taji anyi ta juya da sauri don tun da ta share waje ta shigo bata kulle kofar ba, da d'an mamaki take kallonsa, ya shigo parlon ya kulle kofar, sai da taga ya karaso cikin parlon ya xauna snn ta duka nan kasan carpet tana kallonsa tace "Ina kwana" har lkcn kayan jiya ne a jikinsa, ta mike don bata san ko ya amsa gaisuwar ko bai amsa ba ta koma daki ta saka hijab dinta snn ta fito ta wuce kitchen, mamakin abinda ya kawosa da sassafe ta dinga yi, ta dai hada shayi ta dau bread slice uku a kan glass plate snn ta fito har xata wuce dakinsu ta juyo taga kallonta yake, ta d'an tsaya tace "Xa a kawo maka shayi ne? Su Umma basu tashi ba" Maimakon ya bata amsa sai taga ya tashi yayi hanyar dakin Ahmad, ita kuma ta wuce dakinsu ta kulle kofar. Aunty ta rasa me ke mata dadi, ta rasa wanda xata kira tace ga abinda Abuturrab yayi, gashi El-Basheer ma wayarsa a kashe, to ko dai suna tare ne, ita Ahmad ba shiri take da shi ba balle ta kirasa, can dai daga karshe ganin har kusan goma wayar Abuturrab a kashe Kuma bata son Aneesah ta kira mutan gidansu tace xata sanar masu yasa ta yanke shawaran kiran Ahmad, luckily nasa ya shiga, sai da ya kusa katsewa Ahmad ya mike xaune daga kwancen da yake ya dau wayar mamaki ya kamasa ganin wai Aunty ke kiransa ya daga ya kai kunne, Aunty tace "Ahmad ya gajiya?" Yace "Ina kwana?" Tace "Lafiya lau, Aliyu fa?" Ahmad yace "Aliyu kuma? Ba yana can gidansa ba" Aunty tace "Bai can, kuma ba can ya kwana ba" Bude baki Ahmad yayi, Aunty tace "Kar ka min karya Ahmad, yanxu da gaske bakwa tare?" Ahmad yace "Wllh ni ina gidana, jiya tun karfe takwas muka rabu da shi ina jin" Aunty tace "Toh Shikenan" daga haka ta katse wayar, Ramlah dake gefensa ta kallesa tace "Me ya Aliyun yayi" Ahmad ya daga kafada yace "Ban san meke damunsa ba, wai bai kwana gidansa ba jiya" Ramlah ta xaro ido tace "Aneesar fa?" Ahmad yace "Tana can gidan i guess" Ramlah ta ma rasa abun cewa, Ahmad yace "Ko aurensa na farko da yaje yayi bai k'i kwana a gidan ba ranan da suka tare balle wannan" Ramlah tace "Toh ko dai Aneesan sun masa wani abu ne" Ahmad yyi dariya bai ce komai ba yana kokarin kiran layin Abuturrab shi ma ya ji a kashe. Karfe goma Jiddah ta fito ta ajiye cup da ta sha shayi a kitchen sannan ta dau wani cup din ta hada wani shayin, ta ajiye kan tray, kwai kwara uku ta soya da albasa shi ma ta daura a tray din, ta dau ledan slice bread din ta ajiye saman tray, sannan ta dau tray din ta fito, a hankali take tafiya xuwa dakin Ahmad, ta fi minti daya tsaye bakin kofar kamar me contemplating kafin tayi knocking a hankali, jin shiru ta sake kwankwasawa gently, bude kofar dakin aka yi ta koma baya tana kallonsa kamar yanda shi ma yake kallonta..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Juyawa yayi ya koma cikin dakin, ta karasa ta ajiye tray din a saman carpet din dakin, sannan ta mike tana kallonsa tace "Ina kwana?" Dauke idonsa yyi ya koma ya xauna gefen gado, ta juya ta fita ta kullo masa dakin, ya kai hannu ya dafa kansa hade da lumshe ido. Karfe sha daya Jiddah ta fito dakinsu bayan tayi wanka ta shirya, Umma dake xaune parlor tare da Aunty Nafisah ta kalleta tace "Ke kin karya kuwa Jiddah?" Jiddah ta karaso ta duka kasa kusa da kujera tace "Eh Umma" Aunty Nafisah dai sai kallonta take, ita dai kawai taji tana son Jiddah ganin bata da wani alama na hayaniya sannan tana da respect, Umma tace "Toh tafi ki daura shinkafa... yanxu xaki ga ranan tayi" Jiddah tace "Toh" sannan ta mike ta nufi kitchen, Aunty Nafisah ta bi ta da kallo har ta shiga sannan ta kalli Umma tace "Tun da ta dawo nan bata koma gidansu ba amma?" Umma tace "Aa bata je ba, to me xata je tayi, her parents are late, kishiyar mamarta ce a gidan ai, and I don't think she knows any of her relative gaskiya" Aunty Nafisah ta buda ido sosai tace "Amma kuma da mamaki ace dangin iyayenta basu nemeta ba har yanxu ai ko, Ummi tace min kusan 2 nd half months kenan fa, ae baxa ace bata da wasu dangi ba..." Umma tace "Wannan kuma ae a gun Aliyu xa a samu information din nan, tunda mu ko gidan nasu ma bamu sani ba har yau balle wani nata, and i don't even think it's necessary for now nan gaba duk xata nemesu idan Allah ya yrda wannan dole ne, yanxu dai i want her to get educated first, hakan kadai ne gatan da xa a iya yi mata" Aunty Nafisah tace "Haka ne kuma, amma da na xo naga yarinyar ban so Aliyu ya saketa ba wllh, yarinya ce me hankali da natsuwa sosai, kin ga ai da Ummi tayi dacen surka ta gari, amma wannan mata da aka kai jiya banga alamar abun arxiki ba, don naga alamar idonta a tsakiyar kanta yake, snn na ga kamar suna da wani alaka da ban san na meye ba da Aunty kuma ban ji dadin hakan ba, idan ma don yana son auren wannan ne ya sa ya saki Jiddar ai da sai ya hadasu su biyun tunda Allah ya hore masa...." Umma ta ta6e baki tace "Wannan kuma shi ya jiyo, Jiddah dai tayi masa nisa sai hange daga nesa yanxu, dama Allah ya hadasu ne don ya fiddota daga kangin rayuwar da take ciki a gun kishiyar uwarta, mu kuma mu riketa, indan ta ni ce kada ma ya nuna ya ta6a saninta har abada" Aunty Nafisah ta girgixa kai tace "Aa kar ki ce haka Hajiya Ramlah, ai kuwa har gobe bata da kamarsa don shine silar duk wani abun alkhairi da xai sameta a rayuwa ko kuma ince yake kan samunta a rayuwa, ni da xai nutsu yasan inda ke masa ciwo ya maida hankalinsa ma yace xai maidata...." Umma ta kalleta da sauri tace "Ya maida ta ina?" Aunty Nafisah tace "Ya maidata dakinta suyi xaman aure, ai saki daya yayi mata ko??" Umma tayi wani dariya tace "Xancen kike so Nafisah, Ai Aliyu ya makara, ke kinga walakanci da cin kashin da ya dinga ma yarinyar nan? Wllh kare baxai ci ba, Ai shi da auren Jiddah kuma sai kilan ko a lahira idan ana auren, amma dai a nan duniya kam ya gama aurenta, babu wani abu da xai sake hadata da shi, yaje can ya rungumi matarsa da ya auro jiya" Aunty Nafisah tace "Aa kar kice haka Hajiya baki san ikon Allah ba..." Umma tace "Wllh wllh kinji rantsuwar musulmi ko Nafisah? Aliyu have nothing to do with this girl again, Allah xai fiddo mata da dai dai ita wanda xai ga mutuncinta ba wanda xai dinga da na sanin aurenta ba yana cusguna mata sbda wasu dalilansa mara tushe" Aunty Nafisah tace "Ai bata yi kama da warce aka cusguna ma ba Hajiya... Dama can shiru shiru ce yarinyar" Umma tace "Da kika xo kika ganta da kyan gani ba, karewa ma tun ranan da suka tare ya saketa, sakin walakanci, sannan ya ajiyeta a gidan sbda shi isasshe ne, yayi ta wahal da yar mutane kamar wani ya aikesa ya aurota tun farko, kawai ki bari Nafisah amma babu wani abu da xai sake hadata da Aliyu da izinin Allah, ba dai wajena take ba" Tsit Umma tayi duk suna kallon Abuturrab da ya fito daga dakin Ahmad... kananun kaya ne jikinsa hannunsa rike da phones dinsa, ya karaso cikin parlon ya xauna kafin yace komai Umma tace "Waye wannan???" Ya d'an kalleta sai kuma yyi murmushi yace "Ina kwana Umma" Kin amsawa tayi tana kallonsa with surprise, ya kalli Aunty Nafisah ita ma ya gaisheta, da mamaki tace "Yaushe ka shigo gidan nan Aliyu??" Yace "Daxu..." Umma tace "Ita kuma Amaryar fa?" Yace "Suna can da kawayenta" Umma tace "Da sassafe ka baro gidan kenan??" Yace "Ehh" Aunty Nafisah tace "Ikon Allah, to amma har yanxu ana yayin kawayen amarya su kwana gidan amarya ni Nafisah?? na xata an daina wannan jahilcin tuntuni ai..." Umma tace "Atoh nima shi na gani, da nayi magana Hafsah kirjin bikin ce min tayi ai Amaryar sun yi magana da Aliyun kuma ya amince kawayenta su kwana tun ma ba a kawota ba, dalilin da yasa na kama bakina nayi shiru kenan bana son tashin hankali, shi yasa da su Maimoon suka ce xasu kwana gidan nima bance komai ba, a raina nace kowa ma ya kwana tunda haka ne" Abuturrab dai kallon Umma kawai yake don basu yi haka da Aneesah ba, Aunty Nafisah tace "Aa gaskiya wannan ba yi bane kuma bai kamata ba, Allah kuma ya kyauta" Umma tace "Ameen dai, kayi breakfast dai koh?" Yace "Eh nayi..." tace "A can gidan aka kai maku?" Yace "Aa a nan nayi" Umma ta kalli kitchen sannan ta kallesa da mamaki tace "A ina ka ga breakfast din, mu yan gidan ma yanxu muka tashi ai" Ya shafa kansa yace "Aa ta kawo min..." Aunty Nafisah da Umma duk suka kalli kitchen din, dai dai nan Jiddah ta fito, Aunty Nafisah tace "Jiddar ce ta kawo maka kenan" Yace "Ehh" Umma dai bata sake cewa komai ba ta ci gaba da kallon tv abunta. Ana kiran azahar Jiddah na kitchen tana gyara kayan miya da xata yi blending tayi stew, Aunty Nafisah da Umma kuma na can daki aka bude kofar kitchen din, da sauri ta juya ya shigo ciki ya kulle kofar, jikin cabinet ya jingina ya rungume hannunsa yana kallonta, Tana ci gaba da gyara kayan miyan da take tace "Akwai abinda xa a baka ne?" Yace "Aa.." Ta d'an kallesa sannan ta ci gaba da aikinta yace "Ajiye aikin nan ki saurari maganar da xan maki" Ba musu ta ajiye wukar hannunta ta wanke hannunta a sink sannan ta juyo tana kallonsa, bai yarda sun hada ido ba, yace "Instructions uku xuwa hudu xan baki" Ita dai bata ce komai ba tana ta kallonsa, yace "Na farko cikin instructions din shine ni bana son kina gaisheni a duk inda xaki gan ni... na biyu kuma duk sanda kike da bukatan wani abu ko wani iri ne ki dau wayar Maimoon kiyi min text ba sai kin gaya ma Umma ko wani ba, that is my responsibility, na uku kuma duk sanda su Umma xa su je can gidan mu you look for excuse da xai sa baxa ki bi su ba, kafin in baki instruction din karshe ina son ki fara gaya min shekarunki" Jin tayi shiru ya hade rai yace "Magana nake maki, shekarunki nawa??" a hankali tace "Baabarmu tace sha bakwai" Yace "Ohk, akwai wani da yace maki kin isa ki dinga xama kin hira da maxa ne?" Tayi shiru tana kallonsa, yace "To instruction din karshe kenan babu ruwanki da wani namiji koma waye shi, idan kuma aure kike so sai ki gaya min in ji, i will settle that" Tace "To amma kuma ae kace min kar in sake nuna ma na sanka, kuma yanxu gashi kana...." Katse ta yayi yace "Ae shi yasa nace ki daina gaisheni, kinga ae wanda baka sani bane baka gaishesa" tace "To kuma ai baxa ka so ka tambayi wanda baka sani ba yayi maka wani abun kuma..." Kallonta ya dinga yi da mamaki, tace "Tunda ban sanka ba ni baxan tambayeka ka min komai ba" yace "Amma ai ban sanki ba a lkcn da na taimakeki a hayin rigasa, why didn't u turn down d offer" ta d'an yi murmushi tace "Aa ka san ni mana, ai awara nake yi sannan kuma kana xuwa siya, kaga ai ka san ni..." Yace "To bari ki ji in gaya maki abinda baki sani ba, duk wani responsibilities dinki har gobe a kaina yake sbda wani dalili da ban...." Bude kofar kitchen din aka yi duk suka juya, ya fasa karasa abinda xai fada, Umma ta shigo kitchen din, ko kallonsu bata yi ba ta dau abinda xata dauka ta fita, Abuturrab ya kalli Jiddah yace "Na gama gaya maki abinda xan gaya maki" Daga haka ya juya ya fice daga kitchen din ta bi sa da kallo. Makullin motarsa ya dauka a dakin Ahmad ya fita ya bar gidan bai sallami kowa ba... Umma ce xaune daki inda take shiga ba nan take fita ba tana kallon Jiddah dake durkushe saman carpet ta sunkuyar da kanta ta kasa cewa komai duk jikinta yayi sanyi, Umma tace "To idan har baxan dinga gaya maki ki ji ba to xa a fara jin kanmu wllh, ina ruwanki da shi da har xaki ma tsaya ki sauraresa daga farko? Meye hadin ki da shi??" Cikin sanyin murya tace "Umma kiyi hakuri baxan sake ba in sha Allah" Ita dai Aunty Nafisah na tsaye jikin mirror tana kallonsu, Umma tace "Ke duk cin mutuncin da ya maki har kin mance da xaki sauraresa idan ba wauta da rashin sanin ciwon kai irin naki ba??" Jiddah ta girgixa mata kai kawai, Umma tace "Toh tashi ki fita, shi kuma xan ga uban da xai sake dawowa da shi gidan nan ai..." Mikewa Jiddah tayi ta fita, sai da ta kulle kofar Aunty Nafisah tace "Hajiya ni ban ga wani aibu ba don yayi magana da ita, ba fa rabuwar tijara ko rashin mutunci suka yi ba,, assuming he meant any harm toward her da tun farko bai shiga rayuwarta da xummar taimaka mata ba har ma iyayensa su santa, kawai dai abubuwa sun faru ne yanda Allah ya tsara amma kar kice xaki raba xumuncinsu...." Umma tace "Ni fa bance ta masa rashin kunya ko taki girmama sa ba Nafisah, kawai so nake ta rike maraicinta tayi abinda ke gabanta wato karatu, ganin cewar ita ba class dinsa bane yasa yayi mata duk abinda ya mata ba wani abu ba, ba gashi dai yanxu ya auri class din tasa ba, to a kan me xa ta ci gaba da sauraronsa?" Aunty Nafisah tace "Toh Allah ya kyauta" Umma tace "Ameen" Aneesah na xaune parlor tare da kawayenta uku dake ta shirye shiryen tafiya, duk sun cika parlon da surutu ita dai bin su kawai take da um um, amma tayi nisa tunanin da take, duk da how moody she is throughout d day bata yarda kawayenta sun lura ba, bude kofar parlon aka yi duk suka daga kai, Abuturrab ya shigo da sallama da shi kadai yaji kayansa, kallonsa Aneesah ta dinga yi babu ko kiftawa, ya karasa cikin parlon yana kallonsu Fauziyya with smile on his face yace "Kun yini lafiya" Fauziyya tace "Lafiya lau ango, jiya kuma sai muka ji ku shiru shiru kai da abokanka..." Abuturrab yace "Ohh yeah, toh kun ki bar min mata ku tafi, and all my frnds that are suppose to escort me sun koma saboda aiki, shi yasa nace to bari dai nasan xuwa yau xa ku tafi ku bar min amaryata, na daga kafa jiya, amma ashe i am mistaken kuna nan dai" Dariya duk suka yi banda Aneesah da ta kauda kanta imagining how to punish him, Fauziyya tace "Da ka kwantar da hankalinka ma yanxu shiryawa muke xa mu wuce in sha Allahu" Yyi murmushi yace "Toh ba sai na haura sama ba kenan bari in jira ku a mota, sai in ajiye ku train station...." Naja tace "Mun ko gode Captain" Ya d'an saci kallon Aneesah suka hada ido ya kashe mata one eye, ta wani sha kunu, ya juya ya fita parlon, har bakin motarsa ta raka kawayen nata da jakunkunan kayansu, a kan kafada ta yafa gyalen yyi mata kallo daya ya kauda kai duk kawayenta suka shiga motar suka sallami juna sannan ya kalleta sai na dawo, bata tanka sa ba ta shige gate din gidan, ya ja motarsa ya wuce. Aneesah na komawa ciki ta haura sama ta shiga parlonsa ta dau wayarta ta kira Aunty, aunty na dagawa tace "Ya dawo?" Tace "Ehh yanxu ya shigo, amma ya tafi kai su Fauziyya tashan jirgin kasa" Aunty tace "Toh kar ki wani nuna masa komai, kiyi kamar abinda yayi jiya bai baki haushi ba kinji, kiyi hakuri... Sannan ki kula duk yanda Safara'u ta ce maki haka xaki yi anjima kada ki yarda mistake ya shiga..." Aneesah tayi kasa da murya tace "Amma Aunty he is so smart kin sani" Aunty tace "Smart din banxa, ke dai kiyi abinda aka ce maki kawai" tace "Toh shkkn" Aunty tace "Yanxu dai kawai muyi waya gobe" Aneesah tace "Allah ya kai mu" Daga haka ta katse wayar, shiru tayi tana naxari iri iri a ranta, can tayi murmushi ta mike ta shiga daki. Abuturrab na ajiye su a train station din rigasa ya ciro dubu ashirin din da yayi withdraw kafin ya je gida ya mika masu, nan kuma yayi masu sallama yayi wucewarsa ba tare da ya damu yasan ko akwai jirgin ko babu ba, a ransa yace idan ma babu sai su wuce park, a hankali yake driving ya shiga d'an layin wanda ke shimfide da kwalta, dai dai layin gidan mai anguwa ya samu waje yayi parking sannan ya sauka ya karasa layin da kafarsa, saman tabarman dake kofar gidan ya xauna bayan ya gaisa da dattijan da suka wayesa a wajen, yana jiran mai anguwan da aka ce masa ya shiga gida ya fito yanxu, wani dattijo yace "Ya iyalin naka?" Abuturrab yace "Lafiya lau Alhmdlh" Dattijon yace "Madallah, Allah ya maka albarka" Abuturrab ya sunkui da kansa yace "Ameen" ba a dau lkci ba mai anguwan ya fito, ganin Abuturrab yace "Ikon Allah, sannu da xuwa Malam Ali" Abuturrab ya gaishesa da ladabi bayan ya xauna, mai anguwa yace "Ya kaje gida ranan? Nayi ta kiran layinka baya shiga kuwa" Abuturrab yace "Allah sarki, Ina jin na kashe wayar ne" Mai anguwa yace "Toh madallah, ya aiki fa...." Abuturrab yace "Aiki Alhmdlh, Dama na xo tasha ne shine nace bari in karaso mu gaisa" Mai anguwa yace "Ai ko mun gode Malam Ali, ya iyalin taka dai?" Yace "Lafiya lau" Mai anguwa yace "Toh Allah ya kauda fitina, ya ci gaba sa baku xaman lafiya" Abuturrab ya amsa da "Ameen" sannan ya ciro kudi aljihunsa ya ajiye nan gabansa yace "Toh xan koma in sha Allah, sai kuma wani lkcn" Mai anguwa ya rike ha6a yace "Baka gajiya Malam Ali??" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *EXCLUSIVE FABRICS &MORE* provides you with exclusive, and Affordable fabrics such as laces, Ankara,materials shoes,bags and so much more on wholesale and retail EXQUISITE, AND AFFORDABLE THANK U ❤️🤩 LOCATION: LAGOS *EXCLUSIVE_FABRICS_AND_MORE* Na siyar da kaya kamar Laces, Atampopi, Materials, Jewelleries,👡👠👜👛da dai sauran su Tana maraba da masu siyan daya koh sari Location : Lagos Tana aika kaya duk inda kake da yardan Allah 🤝🤝❤️🥰 09080058848 Abuturrab yyi parking kofar gidansu ya kashe motarsa ya sauka, suka gaisa da Mai gadi sannan ya shiga cikin gidan, bbu kowa parlon duk yan biki sun watse, ya wuce dakin Hajja ya bude kofar ganin Mahaifiyar El-Basheer xaune dakin ya sa shi yin sallama, Hajja dai kallo daya tayi masa ta ci gaba da xancenta tana cewa "Wllh baki ganta ba, babu sa wa babu hanawa, don dai kawai ni ina komai cikin sirri ne banda haka da har sunan yarinyar sai in fada maki ynxu, kuma ni ba abinda yasa na kara samun kwarin gwiwa sai ganin yanda Bashir din yayi na'am da xancen nawa, wllh ko musu d'an arxikin bai yi ba, da dai su o'o ne har ubana dake rami sai ya xaga, shi sa kika ga nayi ta ja baya da bikin nan ba ruwana aje a kunyata ma yarana ni a banxa, ai xamana Masar ya koya min iya xaman duniya, nasan yanda xan xauna da ko wani gantallale lafiya babu me jin kanmu" Murmushi kawai Hajiya Safinah mahaifiyar El-Basheer ke yi, Abuturrab ya karaso ya xauna kasa yace "Ina yini Mummy?" Da fara'arta tace "Lafiya lau Captain, yanxu muka dawo daga can gidan naka ai tare da Hajiya Hafsah, amaryar taka tace mana kaje kai kawayenta tasha ko?" Yace "Ehh" tace "Toh maa sha Allah, Allah ya bada xaman lafiya, ya kauda fitina tsakaninku" Yayi kasa da kai yace "Ameen" Sai a sannan ya kalli Hajja yace "Ina yini" Da sauri tace "Aa, ka dai gane ma idonka, lafiya lau na wuni wllh" Ya mata wani kallo ta gefen ido, Hajja tace "Kina ji na Safinah" Mummy tace "Ina ji Hajja" Tace "Kar ki dau maganata da wasa, tunda dai gobe xa ki koma kina isa gida, ko da mijinki na xaune fada ki yi sallama ki shiga kiyi masa duk bayanin nan da na maki, kinga ai tunda aka samu wannan mutumi yyi aure shi ma Bashir ya kamata yayi auren" Mummy tace "Haka ne Hajja" Hajja tace "Atoh, da a Masar ne ma wace shegiya xata kallesu duk sun tsofe a gida, mu fa a Masar sai ki ga d'an yaro shekara ashirin da biyu yayi aurensa gwanin ban sha'awa wllh" Mummy na gyada kai tace "Ikon Allah" Hajja tace "To ba ruwana wllh, idan xa ki dau maganata da muhimmanci ki dauka, ni anjima ma sai in sa a kira min waya in sa cikin dubara a turo yarinyar kamar dai xata kawo min sako sai ki ganta" Mummy tayi dariya tace "To ae Shikenan Hajja bari in je can bangaren Hajiya Hauwa" Hajja tace "Toh shkkn, xuwa nan da magariba xa ki ga an turo min yarinyar in sha Allah" Mummy dai na murmushi ta mike ta fita, Hajja ta kalli Abuturrab dake danna wayarsa tace "Har yanxu kuna can gwamutse da kawayen amaryar?" Yace "Toh ina ruwanki?" Yana fadin haka ya mike ya nufi kofa tace "Ji shashasha, to ni ina ruwana in ma shekara xa su yi a gidanka? Ba dai mun maka me wuyar mun aurar da kai sauran Bashir ba, sae kaje can ka karata da mummunar matarka sae haske kamar jinjirar xabiya, ni sai na ga wani kallon tara saura quarter ma take ma mutane kamar" Tuni Abuturrab ya fice daga dakin ya kulle mata kofa, wayarta ta dauka ta mike tace "Bari in je a kira min Ramlah, kawai ce mata xanyi ta xuba abinci ta ba yarinyar ta hadata da direba a kawo min kuma daga nan ina son ta wanke min bandaki, don duk ta fi sauran yan matan iyawa, kinga babu wanda xai xargi komai, daga nan tana xuwa sai in nuna ma Safinah" Tsaye Abuturrab yayi bakin kofa yana kallon Aunty, tace "Idan baxa ka karaso ciki ka kulle min kofa ba gwara ka fita don Allah Aliyu, bana son walakanci" Bai ce komai ba ya kulle kofar sannan ya karasa cikin dakin, tace "Yanxu kai abinda kayi jiya a tunaninka ya dace kenan Aliyu?" Yace "Aunty ni fa banyi komai ba, i instructed her to tell her frnds to come out so i can drop them home amma taki, ni kuma bana son tashin hankali kawai na bar masu gidan gaba daya na tafi hotel na kwana, a ina aka ta6a cewa sai kawayen amarya sun kwana gidan amarya ranan da aka kai ta?" Aunty ta jefa masa wani kallo tace "Ance din, ina ruwan ka da kawayenta dake daki daban ku kuna daki daban, yan matan da suka taso tun daga Abuja suka xo sun cancanci wannan walakancin a wajenka Aliyu? Tun da yan matan nan suka xo garin nan Hajja ke hantarar su, dalilin ma da yasa nace su kwana can din kenan, duka duka dai ai ba can xa su dauwama a gidan naka ba banda rashin hakuri irin naka, kuma banda ma kana son a tafi da matarka a baki meye na barin gidan?? wani ango ne ka ta6a jin yayi hakan" Abuturrab dai bai kuma ce mata komai ba, Aunty tace "Toh a gaskiya ka shiga hankalinka, kada in sake jin makamancin hakan, Aneesah dai ba abar rainawarka bace kasan daga irin gidan da ta fito kasan wacece ita, yar asali ce me dangi gabas da yamma kudu da arewa, kar kaga ka ta6a aure a gantale kun rabu a gantale, to ita wannan ba gantallaliya bace da danginta, yar usuli ce" Kallonta kawai Abuturrab yake babu ko kiftawa, Ta mike tana gyara daurin dankwalinta tace "Yanxu idan kaje sai kasan yanda xaka bata hakuri ta hakura, ni ma kuma dama na bata hakurin" Sauke hannunta tayi a fusace tana kallonsa tace "Wai ya haka ina magana ka kafe ni da ido kayi shiru kamar baka jin abinda nake cewa, are you okay??" Sauke idonsa yayi yace "Na ji ki" Daga haka ya juya ya fita daga dakin ta bi sa da wani irin kallo. Umma ta ajiye wayar hannunta tana kallon Aunty Nafisah da mamaki tace "Wai ki ji Hajja in ba Jiddah abinci tare da driver ta kai mata...." Aunty Nafisah tace "Ikon Allah, ba dai gidan xan tafi ba yanxu sai in tafi mata da shi kawai" Umma tace "Kin ji yanda ta dage kuwa, na ma ce mata karatu jiddan take Maimoon su taho da drivern, amma wai Jiddar ta taho da takardun kawai" Aunty Nafisah tace "Ki bar Hajja kawai ana magariba xan tafi tare da abincin in kai mata" Umma tace "To amma ki kirata ki sanar mata dai tukun kar tace an mata ba dai dai ba, ko ya kika ga" Aunty Nafisah ta dau wayarta ta shiga kiran Hajja, Hajja na dagawa tace "Hajjaju yanxu xan bar gidan Hajiya Ramlah sai in taho maki da abincin...." Hajja ta katseta a fusace tace "Oh oh naga bala'i, ni dai na shiga uku, ita katuwar ce ta tsara maki haka Nafisah? Yanxu ke fisabilillahi tare dake muka xauna a Masar, ke kinga suna haka? Me yasa xaki taho kasar mutane ki ari halin da ba taki ba ki dinga yin abun da ba ayi a Masar? Ga dai abinda nace ina so sai ayi ta min hanya hanya? Ita Ramlan don bata san ciwona ba har da cewa xata ba direba shi kadai ya kawo min abincin da xan ci, me na hada da direban xa a basa abinda xan xuba a ciki ya kawo min, dama mutum na yarda ya ci gaibu? Toh shkkn babu damuwa, ni baxan sake ce maku komai ba" Daga haka ta katse wayarta, Umma dai sai murmushi take, Aunty Nafisah tace "Toh Allah ya kyauta, baxan ma koma gidan ba yau sai gobe, a ba Jiddar ta kai mata" Umma tace "To ai nace ki bari goben kika ki, ai shkkn bari in ba Jiddan ta kai, amma tana mika mata driver ya juyo da ita don tana da karatu gobe" Hijab har kasa Jiddah ta saka, tana rike da warmer din tuwo da miya da xata kai ma Hajja, gaba daya mood dinta ya canxa jin aiken da Umma tayi mata, babban damuwarta kar ta je ta hadu da Aunty, a sanyaye ta shiga bayan motar ta xauna har suka isa gidan bata da walwala, driver yayi parking kofar gida, ta sauka a hankali hannunta rike da warmer din ta shiga compound din gidan, a hankali ta bude kofar parlon tana leka ciki, ido hudu tayi da Abuturrab dake gidan har sannan suna xaune parlon da El-Basheer da ya takarkare yana masa labarin ball, ta karaso cikin parlon, El-Basheer ya juya yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi da ladabi tace "Ina yini" murmushi ya sakar mata yace "Lafiya lau Jiddah, how are you doing?" Tace "Alhmdlh" yace "Daga ina kike haka?" Tace "Gida" Yace "That's cool..." Bata ko kalli Abuturrab da ya bi ta da kallon gefen ido ba tayi hanyar dakin Hajja, shi ma El-Basheer din da kallo ya bi ta, da sallama ta bude kofar dakin Hajja, Hajja ta amsa ta washe baki ganinta tana cewa "Sannu da xuwa Jiddah" Aisha dake xaune dakin ta bi Jiddah da wani kallo, Jiddah ta tsugunna ta ajiye warmer din hannunta tana kallon Hajja tace "Ina yini Hajja?" Hajja tace "Lafiya lau, shinkafa ta baki ki kawo ko me?" Jiddah ta girgixa kai tace "Aa tuwo ne" Hajja tace "Atoh da kyau, dama shi nake marmari" Mikewa Aisha tayi ta fita daga dakin, Hajja tace "Dama ba wani amfani take min ba, yar kazar da Bashir ya kawo min take ma ni kuma na boye kayana karkashin gado, tunda ba uwarta bace ta siyo min, shi wan nata Salem tun saukana daga Masar har yau ban gansa ba ance yana Benue, to ni ina ruwana kuma" Ita dai Jiddah bata ce komai ba, Hajja tace "Yanxun nan Bashir din ya fita ai da kun gaisa wllh" Jiddah tace "Ai mun gaisa" Hajja tace "Haba" Gyada mata kai Jiddah tayi, Hajja tace "A ina kika gansa?" jiddah tace "A parlor" Hajja tayi kasa da murya tace "Shi da wa?" Jiddah tace "Ya Aliyu" Hajja ta wani kyabe baki tace "Ashe bai tafi ba kenan, in gaya maki ni dai babu xagin da bai min ba daxu, amma ban biyesa ba don ba shine gabana ba wllh, ni tunda naje Masar na koyi xama da ko wani fitsararre, iyakar hakuri da kauda kai na koyo kam ba laifi a Masar" Jiddah ta d'an yi murmushi kawai, Hajja tace "Toh ba ruwana dai da wannan, yanxu ki tashi ki tafi bangaren warcan matar da ku ke ce ma Ummi, kiyi sallama sai ki durkusa ki gaishesu da ladabi gaba daya sannan kice don Allah Maman Bauchi kike nema, Idan aka nuna maki ita aka ce gata sai kice mata dama Hajja ce tace in kira ki, Shkkn sai ki taso abun ki ki fito kinji?" Jiddah tace "Toh" Hajja tace "Toh tashi kije" Mikewa tayi ta fita dakin, suka hada ido da Abuturrab a parlor ta dauke kanta tayi hanyar bangaren Ummi, El-Basheer ya shafa kansa yace "Kasan mene Captain" Abuturrab ya kallesa yace "Idan magana ce da ya shafi koma waye na cikin gidan nan I'm not interested Yarima" El-Basheer yace "A kan Jiddah ne maganar" Mikewa Abuturrab yayi ya wuce dinning area, El-Basheer ya bi sa da kallo yana murmushi... Duk yanda Hajja tace haka Jiddah tayi, Ummi na murmushi ta nuna Mummy tace "Gata nan" Jiddah ta kalleta sannan ta sunkuyar da kanta, Mummy tace "Ki ce mata gani nan xuwa" Jiddah tace "Toh" sannan ta mike ta fita parlon, muryar Aunty ta ji a main parlor tana cewa "Har gashi xa ayi isha baka tafi ba ka bar yar mutane ita daya a gida Aliyu, Wai me yasa bakwa gaya masa gaskiya Bashir" El-Basheer yace "No nayi masa magana Aunty, har ce masa nayi ya tashi in rakasa yace aa yana jiran wani abu ne, ina ta xuba ido in ga me yake jira" Abuturrab na kallon Aunty daga dinning area da yake xaune yace "Yanxu xan wuce, dama gidan akwai wasu coursemates dinta ne amma nasan may be sun tafi yanxu, i will be on my way" Jiddah dai tayi sum sum ta shige dakin Hajja kafin Aunty ta ganta gabanta na faduwa. Tana shiga dakin Hajja ba a dau lkci ba sai ga Mummy ta shigo ta nemi waje ta xauna tana kallon Hajja tace "Ga ni" Hajja na Murmushi tace "Toh xancen da muka yi daxu dake dai da yamma... kin tuna?" Mummy ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Na tuna" Hajja tayi dariya tace "Toh shine, ai dama na maki alkawari xaki santa yau din nan" Mummy dai sai d'an Murmushi take tana kallon Jiddah dake xaune kasan carpet kasa kasa, Jiddah tace "Hajja ana jirana a waje" Hajja tace "Direba ko?" jiddah tace "Ehh" Hajja tace "To yi maxa tashi kije, kice da Ramlah na gode, Allah ya tashe mu lafiya" Jiddah ta mike tace "Ameen" Sallama tayi ma Mummy sannan ta fita dakin, Hajja tace "Toh ita ce dae Jiddar" Mummy tace "Maa sha Allah" Hajja tace "Aa ba haka xaki ce ba" Mummy tace "To ya xan ce" Hajja ta marairaice tace "Yau naga jaraba, sai kice ehh ai kuwa tayi Allah ya tabbatar da alkhairi Hajja, haka ake magana me ma'ana" Mummy tace "Gaskiya ne tayi kam, Allah ya tabbatar da alkhairi" Hajja tayi Murmushi tace "Yauwa ko ke fa, in sha Allahu satin da xa a shiga xan xo bauchi gun kabiru" Mummy tace "Toh Allah ya kai mu, bari in je Hajja" Daga haka ta mike ta fita dakin, Hajja ta ta6e baki tace "Oho dai, kya ji da bak'in halinki... In dai jikana na so bbu ruwana da sarautarku ta karya can, yanxu fa sai tace ita a dole gimbiya take so ya aura don ita tana jikar sarkin Gombe, to ni ba ruwana bama haka, kowa mutum me daraja ne a wajenmu, kuma nasan Kabiru da Bashir baxa su watsa min duwatsu a ido ba..." Sai da Jiddah ta fara xuwa tayi ma Ummi sallama sannan ta fito main parlor, har sannan Abuturrab na tare da El-Basheer, Tana kallon El-Basheer tace "Sai da safe" Yace "Ohkk ba nan xaki kwana ba dama" Tayi murmushi ta girgixa masa kai tace "Kawo ni aka yi" Abuturrab ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya mike ya fita daga parlon, El-Basheer yace "Driver kowa?" Ta gyada kai tace "Shi" El-Basheer yace "To mu je in rakaki" Bata ce komai ba ya mike suka fita parlon a tare, kofar gida suka tadda Abuturrab tsaye jikin motarsa, Jiddah na kallon El-Basheer tace "Nagode, sai da safe" Ya sakar mata murmushi yace "Aiitt, Allah ya tashe mu lfya" Bude back seat tayi ta shiga driver ya tada motar suka bar layin, El-Basheer na kallon Abuturrab yace "Ya ne, are you ready to go home now" Abuturrab yace "Yeah, Sai da safe" Daga haka ya shiga motarsa ya tada ya bar layin. Abuturrab na isa gida ya fi minti goma xaune cikin mota a parking space kafin ya sauka ya shiga cikin gidan, kulle kofar parlor yayi yana bin parlon da kallo, plates ne da suka ci cin cin, dubulan da su alkaki da frnds dinta da goran ruwa da lemo, ga bone din kaji a wani plate din a gefe, carpet din duk an marmasa cin cin da dubulan, haurawa sama yayi ya nufi bangarensa ya bude kofar parlon, nan ma dai ledojin souvenirs ne a tsakar parlon da souvenirs din a ciki, ya bude kofar bedroom dinsa, xaune ya ganta gaban mirror daure da towel tana ta shafe shafe, kamshin turare iri iri ya cika dakin, kallo daya tayi masa ta ci gaba da abinda take gently, yace "Aneesah what happened naga parlon downstairs so irritating sannan ga parlona duk wasu tarkacen ledoji, what's d meaning of that?" Tace "Ohh xan xo in kwashe souvenirs din but downstairs gaskiya sai gobe cause har yanxu jikina da gajiya sosai, baka ji bayana ba sai ciwo yake min wllh, I'm so stressed out" Calmly yace "No Aneesah, but u can't leave my parlor that way, I won't sleeo comfortable, ban sa6a ganin haka ba, Kuma ban ta6a kwana a haka ba" Tace "Captain ba wai fa nace baxanyi bane, xanyi amma gaskiya sai gobe, haba duk gajiyan bikin nan dake tare dani ka tsiro min aiki kuma da daddaren nan" Juyawa yayi ya fice daga dakin ya sauka downstairs, ya wuce kitchen ya dau sweeper da abun kwasar shara ya dawo parlon, sai da ya fara tattara duk plates din da robobin lemo ya kai kitchen sannan ya dawo ya share carpet din tass, ya kai ya xubar... Xaunawa yyi a parlon for kusan minti ashirin kafin daga karshe ya mike ya kashe wutan parlon ya wuce sama, har sannan ledojin souvenirs din na nan yanda ya barsu, ya kwashesu gaba daya ya bude kofar balcony dake parlon ya watsar da su nan ya tabbatar babu komai xaune parlornsa bayan furnitures sannan ya kulle kofar balcony din ya wuce daki, a gaban madubin ya sameta still, dakin sai wani fitinannen kamshi yake, ta saka wasu tsinanannun kayan bacci, yyi mata kallo daya ya fara cire shirt dinsa ya wuce bandaki. Daure da towel ya fito, yana goge gashin kansa da karamin towel din a hannunsa, Aneesah ta bi sa da kallo sae kuma ta mike ta nufesa ta rungumesa ta kwanta bayansa kamar me rada tace "In maka shafan cream din ne?" Ya dakatar da goge gashin nasa yace "I am not rubbing anything Aneesah" ta xagayo gabansa still holding onto him cike da kissa tana masa wani irin kallon so tace "Sai me Babynah?" Yana kallonta kafin yace komai ta lumshe ido ta fara sumbatar bakinsa, daukarta yayi bai direta ko ina ba sae saman gado, cikin cool voice dinsa yace "I'm not in the mood Aneesah, ni ma gajiyar biki bai sakeni ba har yanxu...." yana fadin haka ya lakaci hancinta ya mike daga kan gadon ya tafi ya dau pajamas dinsa ya fara sakawa, Aneesah ta bi sa da kallon mamaki har sannan tana kwance, can side din gadon ya tafi ya xauna bayan ya saka pajamas dinsa, ya juya ya kalleta yace "I need hot tea" Ta masa wani kallo ta mike tace "Baxan iya ba..." tana fadin haka ta fice daga dakin, a parlor ta dau wayarta ta fita ta koma wani daki ta kulle ta shiga kiran Aunty, Aunty na dagawa tace "Lafiya Aneesah????" Cikin rawar murya tace "Aunty wllh fa kawai walakanci Aliyu ke ji, kinga yau ma ba shi da niyya" Aunty ta bude baki tace "Ke kuma sae kace ba mace ba Aneesah, ae sae abun ya lalace ya gantale idan ya wuce yau" Aneesah ta marairaice tace "Toh ni ya xan yi masa Aunty, ji fa kudin da mutum ya kashe ma" Aunty tace "Xuwa xakiyi kiyi duk yanda xaki yi komai ya kankama, koma meye kiyi ni dai, sae da safe ni ba a bangarena nake ba" Daga haka Aunty ta katse wayar, Aneesah ta fi minti uku tsaye tana naxari sannan tayi wani murmushi ta fita dakin ta nufi bangarensa. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *EXCLUSIVE FABRICS &MORE* provides you with exclusive, and Affordable fabrics such as laces, Ankara,materials shoes,bags and so much more on wholesale and retail EXQUISITE, AND AFFORDABLE THANK U ❤️🤩 LOCATION: LAGOS *EXCLUSIVE_FABRICS_AND_MORE* Na siyar da kaya kamar Laces, Atampopi, Materials, Jewelleries,👡👠👜👛da dai sauran su Tana maraba da masu siyan daya koh sari Location : Lagos Tana aika kaya duk inda kake da yardan Allah 🤝🤝❤️🥰 09080058848 Bude kofar dakin nasa tayi ta shigo, ta gansa xaune daya side din gadon ya kunna laptop, ta kashe wutan daki ya daga kai yana kallon direction din da take, a nutse yace "Ban gama abinda nake ba Madam..." Barin wajen tayi ba tare da ta kunna ba ta taho ta hau saman gado, bai ce mata komai ba ya mike ya tafi ya kunna ya dawo ya ci gaba da danna laptop dinsa ya wani sha kunu kamar bai ta6a dariya ba, hakan ya sace mata gwiwan abinda tayi niyya, ta koma ta kwanta tayi lamo a kan gado... Har wajen sha biyu yana operating laptop bata ga alamar xai kwanta ba, ga bacci da ya fara damun idonta, nan duk ita jira take taga ya kashe laptop din ya kashe fitilun dakin sannan taga dubaran da xata iya amma shiru shiru har bacci yayi awon gaba da ita bata shirya ba, sai da ya tabbatar baccinta yayi nisa sannan ya kashe laptop dinsa ya rufe ya ajiye yana kallonta, dama akwai lkcn da xai yi aure da Aneesah gasu a daki daya yaji ba shi da feelings din yin komai tare da ita, he is getting irritated at the thought of having any affair with her, ya rasa dalili kuma upon how clean he knows she is, shi dai yasan duk xamansu tare da kwana gida tare da suke, bai ta6a sa ran xai yi tarayya da ita ba tare da sunyi aure ba, kawai sai d'an abinda ba ka rasa ba, but all of a sudden ya ji he is irritated at her, kashe wutan dakin yyi ya bude kofa ya fita ya koma parlor yayi kwanciyarsa saman 3 seater ya lumshe ido yasan this is just for a while Aneesah tana da tsaftar da baxai ji wani irritation ba.... Da asuba yana dawowa masallaci bai hau sama ba yayi kwanciyarsa downstairs, sai karfe tara ya koma sama ga mamakinsa sai ya ganta xaune tsakiyar gado tana danna waya ko kayan baccin bata cire ba balle ace tayi wanka ko ta gyara daki, yanxu bedroom dinsa ne har nine ba gyara?? kallo daya yayi ma idanuwanta ya san kuka ta ci ba kadan ba, ya karasa dakin ya d'an kakkabe gefen bedsheet din ya xauna yana kallonta yace "You are angry at me right?" Kauda kai tayi taki cewa komai, yayi kasa da murya yace "Toh kiyi hakuri, but ina son mu yi magana ta fahimta da ke Aneesah" Ganin bata da niyyar juyowa balle ta kallesa ya mike ya koma daya side din nan ma ya kakkabe ya xauna yana kallonta ya kamo hannunta yace "There is something serious i want us to discuss...." Ita dai taki cewa komai, kamar me rada yace "Kar ki ga kamar ko bana son having affair tare da ke...." Ta fixge hannunta ta katse sa cikin fushi tace "Don't tell me anything" yace "No i need to pls, kema kinsan duk xuwan da kike yi gidana can Abuja iyakar abinda ke hadani dake romance, just that, kuma ban ta6a tsallake hakan ba, and now u are mine completely and i can do whatever i want with u, but sai dai I don't know... may be i was suppose to have told u this long ago Aneesah...." Ya d'an yi shiru, ganin kallon da take masa with much interest din son jin abinda xai ce, yayi kasa da murya a hankali yace "I have issues Aneesah..." kallonsa take ko kiftawa babu, can tace "Issues din me?" Yana wasa da hannunta a hankali yace "Issues with having intercourse" Tayi masa wani kallo tace "You must be kidding Aliyu, ni din ce ban sanka ba??" Yace "Aa baki san ni ba, ni ne nasan kai na, domin kina gani na kamar lafiyayye xai iya kasancewa ba haka bane... Don't be deceived by what u saw" Da mamaki take kallonsa ta ma kasa cewa komai, ya langwabar da kai shi ma yana kallonta, ta girgixa kai da sauri tace "Ban gane ba Aliyu" yace "Meye baki gane ba?" Tace "Naga dai baka ta6a making Attempt din yi ba ai kaga ka kasa" Yace "Ehh ko ban ta6a making any attempt ba ai xan fahimci wanene ni with out making Attempt" Ta girgixa kai tace "Noo, ni ban ga haka a tare da kai ba, ko a sannan ma ni nasan karfin hali kawai kake yi kana kyaleni don kawai baka da yanda xaka yi kuma baka son kayi sabon Allah amma ba wai don kana da wani issues ba, u are more than healthy" Ya d'an yi murmushi yace "I am sorry i am telling u this late Aneesah, amma ina da issues wanda nake neman magani a kai har yanxu... I am sorry i am letting u know it now" Buda ido tayi sosai tana kallonsa, can tace "Wai kai a ina ka ta6a making Attempt kaga kana da issues?" Yace "Aneesah nace maki ba sai nayi making any attempt ba, i knew my self, i knew my issues long ago, yanxu dai ina son wannan ya xama babban sirrinmu ni dake plss Aneesah, nasan kin aureni ne ba don komai na ba sai don sona da kike, in sha Allah xan fara neman magani daga yanxu, komai xai dai daita in sha Allah, kinji my wife??" Kasa daina kallonsa Aneesah tayi da mugun mamaki, is Aliyu kidding her? Mutumin da take tsoro saboda yanda take ganin yanayinsa a duk sanda suke tare shine yanxu xai ce mata yana da issues, mutumin da duk da sonsa da maitarsa da take wani bangare na xuciyarta na mugun tsoron ranan haduwarsu tunda ta gama sanin komai game da shi... kamar ya san tunanin da take yayi kasa da murya yace "I don't know if i have deceived u with what u saw or what u imagine, kinsan babu yanda Allah baya abunsa, amma ni ai nasan baxaki ki xama da ni duk da wnn matsalar tawa ba Aneesah, nasan kina sona ne so na tsakani da Allah" Sounding so pissed off tace "Wai ban gane kana da matsala ba, matsalar me takamaimai, don ni a sanin da na maka ban sanka a me wata matsala ba, dama wai mutum na sanin yana da matsala bai yi making any effort ba?" Cikin sanyin murya yace "Dama abinda na guda kenan ya sa ban sanar maki ba tun farko, i was afraid kar kice xaki bar ni, but sai gashi maganganunki sun nuna hakan" Jawota yyi jikinsa yace "Kinga ba wai fa yana nufin i can't touch you ba, it's just that I can't make love with u, amma komai kike so ni xan maki...." Lamo tayi jikinsa ita dai tana sake jin wutan sonsa na ruruwa a xuciyarta, a hankali yace "Say something Aneesah" Aneesah dai ta fada duniyar tunanin da ta tafi, ko ba komai tension guda daya ya sauka a kanta, cause she can't imagine dama idan Abuturrab ya gane she isn't a virgin, tun da aka kawota da wannan xullumin take xaune a gidan, shi sa take son ayi a wuce wajen hankalinta ya kwanta, tun ana sauran kwanaki bikin take ta fatan duk abinda suka yi da kudin da suka kashe bai tafi in vain ba, Girgixa kai tayi tana d'an murmushi tace "Ni kai nake so kuma xan xauna da kai a ko yaya kake my captain, amma kuma ai hakan baxai sa kace baxa ka dinga ta6ani ba ko?" Murmushi yyi duk da bata ganin fuskarsa yace "Sure xan maki duk abinda kike so mana Wife" Tayi kasa da murya tace "To amma kasan akwai abubuwan da idan ana yi ma mace xai sa tayi loosing virginity dinta ko?" Yace "Abubuwa kamar me?" Dago kai tayi ta kallesa ya wara mata ido yana sauraronta, a kunne ta rada masa, yace "Toh shkkn baxan maki shi ba, because i want to know u a virgin" Gabanta taji ya fadi sosai, ta girgixa kai tace "Toh idan baka min ba ai kuma baka fita hakkina ba tunda ba dayan xaka dinga yi ba" Shi dai murmushi kawai yake yaki yace mata komai, ta shige jikinsa kamar xasu hade waje daya, nan da nan yaji kamar kunnasa take son yi, ya d'an koma baya, cike da shagwaba tace "Kayi shiru" Yace "Ohk i want this as a secret between we both Aneesah, sannan duk wata bukatarki na yau da kullum xan maki duk don ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da yanda kika sameni" Ta lumshe idonta tace "In sha Allah my captain, i love you so much" Ya sauke wani boyayen ajiyar xuciya, yana sake kallon agogo wai har karfe goma saura mace na saman gadonta, kwantar da ita yayi ya mike yace "I want to take my bath, kinsan yau xan koma gun aiki fa" Ta xaro ido tace "Kai da ya kamata ka dau sati captain? Ko basu san aure kayi ba" Yace "No iyakar kwanakin da aka bani kenan, kinsan my first marriage an bani almost 2 weeks, and this is my second marriage...." Da mamaki take kallonsa kafin ta katse sa da sauri tace "Kai har kana da wani first marriage da kake tutiya da shi Captain?" Yace "Ohh toh ya xan kirasa? Aure ne shi ma ai" Ta hade rai tace "Wannan kuma ya rage naka, amma take note aurenmu shine first and last marriage dinka" Yana cire jallabiyar jikinsa yace "Toh ai wajen aiki babu ruwansu, a first marriage dina suka san wancan hutun da suka bani, wannan kuma second marriage..." Kallonsa kawai take from head to toe babu ko kiftawa, don Abuturrab ya kai namiji wanda ko wace mace xata so shi a matsayin mijinta, daga sama har kasa kawai take kallonsa tana sake imagining din discuss dinsu, wai yana da issues, Issues a hakan da take ganinsa? Kamar ya san tunanin da take ya juya yayi shigewarsa bandaki ya kulle, ta sauke wani ajiyar xuciya tana jin wani shaukinsa na taso mata, ta kwanta gefen gado hade da lumshe ido. Jiddah na tsaye dakinsu tana jera kayansu da mai wanki da guga ya kawo a press, Maimoon ce kwance dakin tana baccin wahala saboda cramps da ya sakota gaba ko boko bata je ba ranan, Jiddah kuma shigowarta kenan malamarta ta wuce, shine take gyaran kayan kafin Mu'allimarta na Islamiyya ta xo, Umma ce ta bude kofar dakin, tana kallon Maimoon tace "Ta samu bacci kenan" Jiddah tace "Ehh tayi bacci" Umma ta kalli Jiddah na few seconds kafin tace "Jiddah ki xo daki ki sameni idan kin gama" Jiddah tace "Toh" Umma ta juya ta fita, sai da Jiddah ta gama jera kayan nasu sannan ta fita xuwa dakin Umma, Umma na xaune kan arm chair dake dakin, Jiddah ta xauna saman carpet, duk da yanda gabanta ke faduwa don yawanci kiran Umma baya wuce warning xata mata, shima warning din a kan Abuturrab, to amma ai yau kusan wata kenan bata gansa da idonta ba, a hankali tace "Umma gani" Umma na kallonta tace "Jiddah baki ta6a xuwa kin sameni kince kina son Pad xakiyi al'ada ba" Jiddah ta sunkuyar da kanta a hankali amma bata ce komai ba, Umma tace "Ko baki fara ba ne?" Ta girgixa kai tace "Aa na ta6a yi sau biyu kuma ban sake yi ba" Umma tace "A ina kika ta6a yi?" Ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Ya dade, tun ina gun Baabarmu, lkcn ban daina xuwa islamiyya ba" Umma tace "Xai kai wata nawa?" Jiddah ta buda ido sosai tace "Umma xai yi kusan shekara biyu" Umma ta gyada kai tace "Ikon Allah, kuma shine baki sake ba har yau?" Jiddah tace "Eh" Umma tace "Toh tashi ki tafi" Mikewa tayi ta juya ta fita dakin, Umma ta bi ta da kallo tana tunanin meye ma'anar hakan, Jiddah na fita ta sauke ajiyar xuciya ita ko fata ta sake yi bata yi har abada, don bata mance wahalan da ta sha ba har sai da aka kaita chemist aka ta mata allurai, Iyah har ce mata tayi sumanta biyu. Ranan Friday da yamma Ahmad na xaune bedroom din Ummansa, ko minti talatin bai yi da shigowa ba Umma tace "Yauwa Ahmad ina son maka tambaya, Me ke janyo mace ta fara al'ada kuma ta daina sa ko ya dinga mata wasa?" Ahmad yyi shiru yana kallonta, can yace "Mace yar shekara nawa Umma?" Tace "Yarinya karama..." Ahmad yace "Irregular period kenan..." Umma tace "Oho nima ba tambayarka nake ba" Ya shafa kansa yace "Mai aure ce ko mara aure Umma?" Umma tace "Aa bata da aure" yace "That could be Hormonal Imbalance, too high or too low Thyroid hormone level, wannan shine dalilin in har mara aure ce... " Umma tace "To yana da medications ne? I mean is there anything that could be done about it?" Yace "Ehh ba xa a rasa ba Umma, amma akai ko ma wacece asibiti xai fi" Umma tace "Toh Shikenan" Bai kuma cewa komai ba amma can kasan xuciyarsa ya san Jiddah ce Umma ke magana a kai, Umma ta shigo da wata hiran, sun jima suna magana kafin ya mike yace mata xai je gidan Abuturrab don yana gari, Umma tace "Toh sai ka dawo" Yace "Daga can xan tafi gida Umma, sai gobe xan shigo in sha Allah" Tace "To ka gaida Ramlah" Yace "Xata ji in sha Allah" Ahmad na fita wajajen karfe biyar Umma ta sa Jiddah ta shirya suka wuce asibiti, Basu suka dawo gida ba sai bayan magrib, magunguna kawai aka dora Jiddah a kai, xata wuce daki rike da ledan maganin, Umma da ta xauna parlor bayan ta cire Hijab dinta tace "Baki dai manta dosage din ba ko? Duk da an ma rubuta a jiki ai" Jiddah ta juyo tace "Ban manta ba Umma" Umma tace "Toh kar dai kiyi wasa da shan su, Allah ya sa a dace" Jiddah tace "Nagode Umma" Daga haka ta wuce dakinsu, Umma ta kashe ya fi dubu talatin a magungunan da aka rubuta ma Jiddah a asibitin da suka je. Washegari asabar tare Ahmad ya shigo gidansu da Abuturrab, babu yanda Ahmad bai yi da Abuturrab su tafi dakin Umma ba don tana ciki amma yaki ya xauna parlor wai xa su gaisa idan ta fito, Ahmad ya wuce dakin Ummar tasa, Maimoon ce ta fito daga dakinsu da uniform din Islamiyyarta fuskarta kunshe cikin nikab, ganin Abuturrab xaune a parlor tace "Ina yini yaya" Kai kawai ya gyada mata, ta murguda baki daga cikin Nikab din ta nufi kofa, Safiyya ma na fitowa ta gaishesa tayi hanyar kofa, Kallon kofar dakin kawai yake, sai ga Jiddah ta fito tana kokarin daura nata nikab din, suna hada ido tayi turus a inda take, sai kuma ta dauke kanta ta nufi kofa ta fita parlon ta kulle kofar, mikewa Abuturrab yayi ya nufi dakin Umma ya kwankwasa sannan ya bude yayi sallama, bai shiga can cikin dakin ba ya gaisheta da ladabi daga bakin kofar, ta amsa masa tana tambayarsa aiki, yace "Alhmdlh" Umma na kallon Ahmad yace "Yaran nan basu tafi makarantar har yanxu ba ko?" Shi dai Abuturrab bai ce komai ba, ta mike ganin fita xata yi Abuturrab ya bata hanya ta fita, dubawa tayi ko sun tafi ganin sun tafi din ta dawo, Abuturrab yace "Dama na xo gaisheki ne Umma sai anjima" Tace "Toh nagode" Yana kallon Ahmad yace "Mu yi waya" Daga haka ya juya ya fita, har su Maimoon sun kai bakin titi da kafa tunda ba driver xai kai su ba, yayi parking a gefe yana kallon Safiyya yace "Ku shigo inyi dropping dinku" Sake baki Maimoon tayi cikin Nikab din, tunda take xata iya cewa bata ta6a shiga motarsa ba, ko a hanya ya ganka da ka hau motarsa gwara ya baka kudin mota ko kuma yayi kamar bai ta6a saninka ba, Ita kanta Safiyya mamaki ya cikata, ta dai bude gaban motar ta shiga, Jiddah dai bata ji dadin shiga motan da yace su yi ba, Maimoon ta fara shiga sannan ita ma ta shiga, jikin door din motar Jiddah ta makale ko da wasa bata kalli inda yake ba, Yayi breaking silence din motar bayan sunyi nisa yace "Yaushe Siyama xata dawo?" Safiyya tace "Tab, ta fara karatu fa a can yaya" Yace "To maa sha Allah" Maimoon ce tayi masa kwatancen inda makarantar tasu yake, yana isa makarantar yayi parking bakin gate, Safiyya ce ta fara sauka tana masa godiya, Jiddah ta bude side dinta ba tare da ta kallesa ba ta sauka motar ta wuce cikin makaranta ya bi ta da kallo, Maimoon dake masa godiya taga ya bi Jiddah da kallo ta d'an kikkifta ido tana kallonsa, can dai ta sauka motar ta kulle masa ta bi bayansu Jiddah da sauri, dafe Jiddah tayi bayan sun shiga gate tana xaro ido tace "Jiddoh ya naga Captain ya bi ki da kallo???" Jiddah ta kalleta da sauri tace "Waye haka?" Maimoon ta fashe da dariya tace "Ya Aliyu mana, wllh ina ta ce masa mun gode tsabar yanda ya bi ki da eyes bai ma san ina magana ba Jiddoh" Safiyya dake jin su tayi dariya tace "Kallon godiyan da bata masa ba yake mata, naga ko kallonsa bata yi ba ta sauka abunta ta wuce, kilan abinda ya basa mamaki kenan ya bi ta da kallo" Maimoon tayi shakaf da hannu tace "Habaa... no wonder, I for say, wllh kinga wani kallon da ya bi ki da shi, kuma da gaske ne baki masa godiya ba wllh, next time kar ma kiyi gigin sake shiga motarsa don disgaki xai yi wllh" Jiddah ta ta6e baki tace "Wannan ma banyi niyyar shiga ba" Ahmad yayi ma Umma sallama xai fita tace "Yauwa ina son magana da kai Ahmad, kuma kar kuyi missing train ko?" Ya kalli agogon wrist dinsa ya koma ya xauna yace "Da d'an sauran time, ina jin ki Umma" Ramlah dake xaune gefen gadon Umma rike da handbag dinta ta tashi xata fita Umma ta kalleta tace "Ina kuma xa ki, dawo kiyi xaman ki" Ramlah tace "Aa Umma xan shiga bandaki ne" Daga haka ta fita, Umma tace "Ji shashasha" Shi dai Ahmad murmushi kawai yayi, Umma tace "Makarantar boarding nake son da a sama ma Jiddah, Cause her capacity is now more than mere lesson, tana da kokari sosai Ahmad fiye da yanda kake tunani, Malamar ma ta bada shawaran kawai ta tafi boko da mates dinta she now have a standard root" Ahmad yace "Boarding kuma Umma? why not day, ai bata da wasa balle ace taje boarding, sannan gwara day din saboda koyon abubuwan yau da kullum, irinsu girki, da dai sauransu Umma, Jiddah bata da hayaniyar da xata iya xama a boarding school gaskiya" Umma tace "To ai ba sai me hayaniya ke xuwa boarding ba Ahmad" Umma tace "Yanxu dai shawarata kike nema Umma, kuma shawaran da xan baki shine a samar mata day ta fara daga ss1, she can do it" Umma ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Toh shkkn" yace "Yauwa Umma, kinga baxa ayi depriving dinta from full Islamic education ba in jeka ka dawo ne" Umma tace "Kuma haka ne, amma wacce makarantar kake ga xa a saka ta?" Yace "Tunda su Maimoon sun kusa gamawa kawai a nema mata wani daban ita ma, akwai wata makaranta not to far away daga gidana ko a samar mata a can?" Umma tace "Aa gidanka yayi nisa sosai gaskiya" Ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Toh sai ta xauna gidan nawa mana Umma" Wani kallo Umma tayi masa daga sama har kasa kafin tace "Toh baxata xauna ba" Dariya yayi yace "Kema kinsan Ramlah bata da matsala Umma and she can do so many cooking da Jiddah xata iya koya, don ma yanxu bata da lafiya sosai" Umma tace "To ubana nace Aa, daga nan xata dinga xuwa makarantar..." Yace "Toh shkkn Umma, sai driver ya dinga kai ta, idan xata dawo kuma ta samu abun hawa tunda kinga hanya ce" Umma tace "In dai am samu nan kusa kusa a samar mata admission kawai, don unguwar da kake yyi nisa" Ahmad bai kuma cewa komai ba, can ya mike yace "Toh shkkn Umma, xa mu yi waya kar muyi missing train" Umma tace "Toh Allah ya tsare hanya, ya kiyaye, kuma ku yi addu'a" Yace "In sha Allah" Daga haka ya fita dakin ya kulle mata kofa..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Assalamu Alaikum Everyone ba dogon labari bane ba🤗* *Sunana Ummu Nuwairah (Known as Mîkyããj Sããdy)* *Shin kina fama da kuraje ne ko tabo🤔,shin kina son ki haske? Shin kina fama da matsalar fata ne? Ko ko so kike ki haske me aji ba wai kamfala ba, ki koma santsin madara yaukin zuma🥰* *To matso kusa kiji 'yar mîkyããj Sããdy tazo miki da hadaddun kayan gyaran jiki, masu kamshi kaca kaca😍😍kuma a cikin kudi kalilan😃kayan mu ingantattu ne babu sight effects a ciki, kuma ina mai tabbatar miki in kika saya da izinin Allah sai kin dawo, kin kawo wasu, kema kuma ki fara sara💃🏻💃🏻* _Domin ganin kayayyainmu ku bibiye mu ta Instagram @mik_yaaj_saady WhatsApp no: 08061570778 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Em3E7rFyyhoGd7Upakosyk Bude kofar dakin nasa tayi ta shigo, ta gansa xaune daya side din gadon ya kunna laptop, ta kashe wutan daki ya daga kai yana kallon direction din da take, a nutse yace "Ban gama abinda nake ba Madam..." Barin wajen tayi ba tare da ta kunna ba ta taho ta hau saman gado, bai ce mata komai ba ya mike ya tafi ya kunna ya dawo ya ci gaba da danna laptop dinsa ya wani sha kunu kamar bai ta6a dariya ba, hakan ya sace mata gwiwan abinda tayi niyya, ta koma ta kwanta tayi lamo a kan gado... Har wajen sha biyu yana operating laptop bata ga alamar xai kwanta ba, ga bacci da ya fara damun idonta, nan duk ita jira take taga ya kashe laptop din ya kashe fitilun dakin sannan taga dubaran da xata iya amma shiru shiru har bacci yayi awon gaba da ita bata shirya ba, sai da ya tabbatar baccinta yayi nisa sannan ya kashe laptop dinsa ya rufe ya ajiye yana kallonta, dama akwai lkcn da xai yi aure da Aneesah gasu a daki daya yaji ba shi da feelings din yin komai tare da ita, he is getting irritated at the thought of having any affair with her, ya rasa dalili kuma upon how clean he knows she is, shi dai yasan duk xamansu tare da kwana gida tare da suke, bai ta6a sa ran xai yi tarayya da ita ba tare da sunyi aure ba, kawai sai d'an abinda ba ka rasa ba, but all of a sudden ya ji he is irritated at her, kashe wutan dakin yyi ya bude kofa ya fita ya koma parlor yayi kwanciyarsa saman 3 seater ya lumshe ido yasan this is just for a while Aneesah tana da tsaftar da baxai ji wani irritation ba.... Da asuba yana dawowa masallaci bai hau sama ba yayi kwanciyarsa downstairs, sai karfe tara ya koma sama ga mamakinsa sai ya ganta xaune tsakiyar gado tana danna waya ko kayan baccin bata cire ba balle ace tayi wanka ko ta gyara daki, yanxu bedroom dinsa ne har nine ba gyara?? kallo daya yayi ma idanuwanta ya san kuka ta ci ba kadan ba, ya karasa dakin ya d'an kakkabe gefen bedsheet din ya xauna yana kallonta yace "You are angry at me right?" Kauda kai tayi taki cewa komai, yayi kasa da murya yace "Toh kiyi hakuri, but ina son mu yi magana ta fahimta da ke Aneesah" Ganin bata da niyyar juyowa balle ta kallesa ya mike ya koma daya side din nan ma ya kakkabe ya xauna yana kallonta ya kamo hannunta yace "There is something serious i want us to discuss...." Ita dai taki cewa komai, kamar me rada yace "Kar ki ga kamar ko bana son having affair tare da ke...." Ta fixge hannunta ta katse sa cikin fushi tace "Don't tell me anything" yace "No i need to pls, kema kinsan duk xuwan da kike yi gidana can Abuja iyakar abinda ke hadani dake romance, just that, kuma ban ta6a tsallake hakan ba, and now u are mine completely and i can do whatever i want with u, but sai dai I don't know... may be i was suppose to have told u this long ago Aneesah...." Ya d'an yi shiru, ganin kallon da take masa with much interest din son jin abinda xai ce, yayi kasa da murya a hankali yace "I have issues Aneesah..." kallonsa take ko kiftawa babu, can tace "Issues din me?" Yana wasa da hannunta a hankali yace "Issues with having intercourse" Tayi masa wani kallo tace "You must be kidding Aliyu, ni din ce ban sanka ba??" Yace "Aa baki san ni ba, ni ne nasan kai na, domin kina gani na kamar lafiyayye xai iya kasancewa ba haka bane... Don't be deceived by what u saw" Da mamaki take kallonsa ta ma kasa cewa komai, ya langwabar da kai shi ma yana kallonta, ta girgixa kai da sauri tace "Ban gane ba Aliyu" yace "Meye baki gane ba?" Tace "Naga dai baka ta6a making Attempt din yi ba ai kaga ka kasa" Yace "Ehh ko ban ta6a making any attempt ba ai xan fahimci wanene ni with out making Attempt" Ta girgixa kai tace "Noo, ni ban ga haka a tare da kai ba, ko a sannan ma ni nasan karfin hali kawai kake yi kana kyaleni don kawai baka da yanda xaka yi kuma baka son kayi sabon Allah amma ba wai don kana da wani issues ba, u are more than healthy" Ya d'an yi murmushi yace "I am sorry i am telling u this late Aneesah, amma ina da issues wanda nake neman magani a kai har yanxu... I am sorry i am letting u know it now" Buda ido tayi sosai tana kallonsa, can tace "Wai kai a ina ka ta6a making Attempt kaga kana da issues?" Yace "Aneesah nace maki ba sai nayi making any attempt ba, i knew my self, i knew my issues long ago, yanxu dai ina son wannan ya xama babban sirrinmu ni dake plss Aneesah, nasan kin aureni ne ba don komai na ba sai don sona da kike, in sha Allah xan fara neman magani daga yanxu, komai xai dai daita in sha Allah, kinji my wife??" Kasa daina kallonsa Aneesah tayi da mugun mamaki, is Aliyu kidding her? Mutumin da take tsoro saboda yanda take ganin yanayinsa a duk sanda suke tare shine yanxu xai ce mata yana da issues, mutumin da duk da sonsa da maitarsa da take wani bangare na xuciyarta na mugun tsoron ranan haduwarsu tunda ta gama sanin komai game da shi... kamar ya san tunanin da take yayi kasa da murya yace "I don't know if i have deceived u with what u saw or what u imagine, kinsan babu yanda Allah baya abunsa, amma ni ai nasan baxaki ki xama da ni duk da wnn matsalar tawa ba Aneesah, nasan kina sona ne so na tsakani da Allah" Sounding so pissed off tace "Wai ban gane kana da matsala ba, matsalar me takamaimai, don ni a sanin da na maka ban sanka a me wata matsala ba, dama wai mutum na sanin yana da matsala bai yi making any effort ba?" Cikin sanyin murya yace "Dama abinda na guda kenan ya sa ban sanar maki ba tun farko, i was afraid kar kice xaki bar ni, but sai gashi maganganunki sun nuna hakan" Jawota yyi jikinsa yace "Kinga ba wai fa yana nufin i can't touch you ba, it's just that I can't make love with u, amma komai kike so ni xan maki...." Lamo tayi jikinsa ita dai tana sake jin wutan sonsa na ruruwa a xuciyarta, a hankali yace "Say something Aneesah" Aneesah dai ta fada duniyar tunanin da ta tafi, ko ba komai tension guda daya ya sauka a kanta, cause she can't imagine dama idan Abuturrab ya gane she isn't a virgin, tun da aka kawota da wannan xullumin take xaune a gidan, shi sa take son ayi a wuce wajen hankalinta ya kwanta, tun ana sauran kwanaki bikin take ta fatan duk abinda suka yi da kudin da suka kashe bai tafi in vain ba, Girgixa kai tayi tana d'an murmushi tace "Ni kai nake so kuma xan xauna da kai a ko yaya kake my captain, amma kuma ai hakan baxai sa kace baxa ka dinga ta6ani ba ko?" Murmushi yyi duk da bata ganin fuskarsa yace "Sure xan maki duk abinda kike so mana Wife" Tayi kasa da murya tace "To amma kasan akwai abubuwan da idan ana yi ma mace xai sa tayi loosing virginity dinta ko?" Yace "Abubuwa kamar me?" Dago kai tayi ta kallesa ya wara mata ido yana sauraronta, a kunne ta rada masa, yace "Toh shkkn baxan maki shi ba, because i want to know u a virgin" Gabanta taji ya fadi sosai, ta girgixa kai tace "Toh idan baka min ba ai kuma baka fita hakkina ba tunda ba dayan xaka dinga yi ba" Shi dai murmushi kawai yake yaki yace mata komai, ta shige jikinsa kamar xasu hade waje daya, nan da nan yaji kamar kunnasa take son yi, ya d'an koma baya, cike da shagwaba tace "Kayi shiru" Yace "Ohk i want this as a secret between we both Aneesah, sannan duk wata bukatarki na yau da kullum xan maki duk don ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da yanda kika sameni" Ta lumshe idonta tace "In sha Allah my captain, i love you so much" Ya sauke wani boyayen ajiyar xuciya, yana sake kallon agogo wai har karfe goma saura mace na saman gadonta, kwantar da ita yayi ya mike yace "I want to take my bath, kinsan yau xan koma gun aiki fa" Ta xaro ido tace "Kai da ya kamata ka dau sati captain? Ko basu san aure kayi ba" Yace "No iyakar kwanakin da aka bani kenan, kinsan my first marriage an bani almost 2 weeks, and this is my second marriage...." Da mamaki take kallonsa kafin ta katse sa da sauri tace "Kai har kana da wani first marriage da kake tutiya da shi Captain?" Yace "Ohh toh ya xan kirasa? Aure ne shi ma ai" Ta hade rai tace "Wannan kuma ya rage naka, amma take note aurenmu shine first and last marriage dinka" Yana cire jallabiyar jikinsa yace "Toh ai wajen aiki babu ruwansu, a first marriage dina suka san wancan hutun da suka bani, wannan kuma second marriage..." Kallonsa kawai take from head to toe babu ko kiftawa, don Abuturrab ya kai namiji wanda ko wace mace xata so shi a matsayin mijinta, daga sama har kasa kawai take kallonsa tana sake imagining din discuss dinsu, wai yana da issues, Issues a hakan da take ganinsa? Kamar ya san tunanin da take ya juya yayi shigewarsa bandaki ya kulle, ta sauke wani ajiyar xuciya tana jin wani shaukinsa na taso mata, ta kwanta gefen gado hade da lumshe ido. Jiddah na tsaye dakinsu tana jera kayansu da mai wanki da guga ya kawo a press, Maimoon ce kwance dakin tana baccin wahala saboda cramps da ya sakota gaba ko boko bata je ba ranan, Jiddah kuma shigowarta kenan malamarta ta wuce, shine take gyaran kayan kafin Mu'allimarta na Islamiyya ta xo, Umma ce ta bude kofar dakin, tana kallon Maimoon tace "Ta samu bacci kenan" Jiddah tace "Ehh tayi bacci" Umma ta kalli Jiddah na few seconds kafin tace "Jiddah ki xo daki ki sameni idan kin gama" Jiddah tace "Toh" Umma ta juya ta fita, sai da Jiddah ta gama jera kayan nasu sannan ta fita xuwa dakin Umma, Umma na xaune kan arm chair dake dakin, Jiddah ta xauna saman carpet, duk da yanda gabanta ke faduwa don yawanci kiran Umma baya wuce warning xata mata, shima warning din a kan Abuturrab, to amma ai yau kusan wata kenan bata gansa da idonta ba, a hankali tace "Umma gani" Umma na kallonta tace "Jiddah baki ta6a xuwa kin sameni kince kina son Pad xakiyi al'ada ba" Jiddah ta sunkuyar da kanta a hankali amma bata ce komai ba, Umma tace "Ko baki fara ba ne?" Ta girgixa kai tace "Aa na ta6a yi sau biyu kuma ban sake yi ba" Umma tace "A ina kika ta6a yi?" Ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Ya dade, tun ina gun Baabarmu, lkcn ban daina xuwa islamiyya ba" Umma tace "Xai kai wata nawa?" Jiddah ta buda ido sosai tace "Umma xai yi kusan shekara biyu" Umma ta gyada kai tace "Ikon Allah, kuma shine baki sake ba har yau?" Jiddah tace "Eh" Umma tace "Toh tashi ki tafi" Mikewa tayi ta juya ta fita dakin, Umma ta bi ta da kallo tana tunanin meye ma'anar hakan, Jiddah na fita ta sauke ajiyar xuciya ita ko fata ta sake yi bata yi har abada, don bata mance wahalan da ta sha ba har sai da aka kaita chemist aka ta mata allurai, Iyah har ce mata tayi sumanta biyu. Ranan Friday da yamma Ahmad na xaune bedroom din Ummansa, ko minti talatin bai yi da shigowa ba Umma tace "Yauwa Ahmad ina son maka tambaya, Me ke janyo mace ta fara al'ada kuma ta daina sa ko ya dinga mata wasa?" Ahmad yyi shiru yana kallonta, can yace "Mace yar shekara nawa Umma?" Tace "Yarinya karama..." Ahmad yace "Irregular period kenan..." Umma tace "Oho nima ba tambayarka nake ba" Ya shafa kansa yace "Mai aure ce ko mara aure Umma?" Umma tace "Aa bata da aure" yace "That could be Hormonal Imbalance, too high or too low Thyroid hormone level, wannan shine dalilin in har mara aure ce... " Umma tace "To yana da medications ne? I mean is there anything that could be done about it?" Yace "Ehh ba xa a rasa ba Umma, amma akai ko ma wacece asibiti xai fi" Umma tace "Toh Shikenan" Bai kuma cewa komai ba amma can kasan xuciyarsa ya san Jiddah ce Umma ke magana a kai, Umma ta shigo da wata hiran, sun jima suna magana kafin ya mike yace mata xai je gidan Abuturrab don yana gari, Umma tace "Toh sai ka dawo" Yace "Daga can xan tafi gida Umma, sai gobe xan shigo in sha Allah" Tace "To ka gaida Ramlah" Yace "Xata ji in sha Allah" Ahmad na fita wajajen karfe biyar Umma ta sa Jiddah ta shirya suka wuce asibiti, Basu suka dawo gida ba sai bayan magrib, magunguna kawai aka dora Jiddah a kai, xata wuce daki rike da ledan maganin, Umma da ta xauna parlor bayan ta cire Hijab dinta tace "Baki dai manta dosage din ba ko? Duk da an ma rubuta a jiki ai" Jiddah ta juyo tace "Ban manta ba Umma" Umma tace "Toh kar dai kiyi wasa da shan su, Allah ya sa a dace" Jiddah tace "Nagode Umma" Daga haka ta wuce dakinsu, Umma ta kashe ya fi dubu talatin a magungunan da aka rubuta ma Jiddah a asibitin da suka je. Washegari asabar tare Ahmad ya shigo gidansu da Abuturrab, babu yanda Ahmad bai yi da Abuturrab su tafi dakin Umma ba don tana ciki amma yaki ya xauna parlor wai xa su gaisa idan ta fito, Ahmad ya wuce dakin Ummar tasa, Maimoon ce ta fito daga dakinsu da uniform din Islamiyyarta fuskarta kunshe cikin nikab, ganin Abuturrab xaune a parlor tace "Ina yini yaya" Kai kawai ya gyada mata, ta murguda baki daga cikin Nikab din ta nufi kofa, Safiyya ma na fitowa ta gaishesa tayi hanyar kofa, Kallon kofar dakin kawai yake, sai ga Jiddah ta fito tana kokarin daura nata nikab din, suna hada ido tayi turus a inda take, sai kuma ta dauke kanta ta nufi kofa ta fita parlon ta kulle kofar, mikewa Abuturrab yayi ya nufi dakin Umma ya kwankwasa sannan ya bude yayi sallama, bai shiga can cikin dakin ba ya gaisheta da ladabi daga bakin kofar, ta amsa masa tana tambayarsa aiki, yace "Alhmdlh" Umma na kallon Ahmad yace "Yaran nan basu tafi makarantar har yanxu ba ko?" Shi dai Abuturrab bai ce komai ba, ta mike ganin fita xata yi Abuturrab ya bata hanya ta fita, dubawa tayi ko sun tafi ganin sun tafi din ta dawo, Abuturrab yace "Dama na xo gaisheki ne Umma sai anjima" Tace "Toh nagode" Yana kallon Ahmad yace "Mu yi waya" Daga haka ya juya ya fita, har su Maimoon sun kai bakin titi da kafa tunda ba driver xai kai su ba, yayi parking a gefe yana kallon Safiyya yace "Ku shigo inyi dropping dinku" Sake baki Maimoon tayi cikin Nikab din, tunda take xata iya cewa bata ta6a shiga motarsa ba, ko a hanya ya ganka da ka hau motarsa gwara ya baka kudin mota ko kuma yayi kamar bai ta6a saninka ba, Ita kanta Safiyya mamaki ya cikata, ta dai bude gaban motar ta shiga, Jiddah dai bata ji dadin shiga motan da yace su yi ba, Maimoon ta fara shiga sannan ita ma ta shiga, jikin door din motar Jiddah ta makale ko da wasa bata kalli inda yake ba, Yayi breaking silence din motar bayan sunyi nisa yace "Yaushe Siyama xata dawo?" Safiyya tace "Tab, ta fara karatu fa a can yaya" Yace "To maa sha Allah" Maimoon ce tayi masa kwatancen inda makarantar tasu yake, yana isa makarantar yayi parking bakin gate, Safiyya ce ta fara sauka tana masa godiya, Jiddah ta bude side dinta ba tare da ta kallesa ba ta sauka motar ta wuce cikin makaranta ya bi ta da kallo, Maimoon dake masa godiya taga ya bi Jiddah da kallo ta d'an kikkifta ido tana kallonsa, can dai ta sauka motar ta kulle masa ta bi bayansu Jiddah da sauri, dafe Jiddah tayi bayan sun shiga gate tana xaro ido tace "Jiddoh ya naga Captain ya bi ki da kallo???" Jiddah ta kalleta da sauri tace "Waye haka?" Maimoon ta fashe da dariya tace "Ya Aliyu mana, wllh ina ta ce masa mun gode tsabar yanda ya bi ki da eyes bai ma san ina magana ba Jiddoh" Safiyya dake jin su tayi dariya tace "Kallon godiyan da bata masa ba yake mata, naga ko kallonsa bata yi ba ta sauka abunta ta wuce, kilan abinda ya basa mamaki kenan ya bi ta da kallo" Maimoon tayi shakaf da hannu tace "Habaa... no wonder, I for say, wllh kinga wani kallon da ya bi ki da shi, kuma da gaske ne baki masa godiya ba wllh, next time kar ma kiyi gigin sake shiga motarsa don disgaki xai yi wllh" Jiddah ta ta6e baki tace "Wannan ma banyi niyyar shiga ba" Ahmad yayi ma Umma sallama xai fita tace "Yauwa ina son magana da kai Ahmad, kuma kar kuyi missing train ko?" Ya kalli agogon wrist dinsa ya koma ya xauna yace "Da d'an sauran time, ina jin ki Umma" Ramlah dake xaune gefen gadon Umma rike da handbag dinta ta tashi xata fita Umma ta kalleta tace "Ina kuma xa ki, dawo kiyi xaman ki" Ramlah tace "Aa Umma xan shiga bandaki ne" Daga haka ta fita, Umma tace "Ji shashasha" Shi dai Ahmad murmushi kawai yayi, Umma tace "Makarantar boarding nake son da a sama ma Jiddah, Cause her capacity is now more than mere lesson, tana da kokari sosai Ahmad fiye da yanda kake tunani, Malamar ma ta bada shawaran kawai ta tafi boko da mates dinta she now have a standard root" Ahmad yace "Boarding kuma Umma? why not day, ai bata da wasa balle ace taje boarding, sannan gwara day din saboda koyon abubuwan yau da kullum, irinsu girki, da dai sauransu Umma, Jiddah bata da hayaniyar da xata iya xama a boarding school gaskiya" Umma tace "To ai ba sai me hayaniya ke xuwa boarding ba Ahmad" Umma tace "Yanxu dai shawarata kike nema Umma, kuma shawaran da xan baki shine a samar mata day ta fara daga ss1, she can do it" Umma ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Toh shkkn" yace "Yauwa Umma, kinga baxa ayi depriving dinta from full Islamic education ba in jeka ka dawo ne" Umma tace "Kuma haka ne, amma wacce makarantar kake ga xa a saka ta?" Yace "Tunda su Maimoon sun kusa gamawa kawai a nema mata wani daban ita ma, akwai wata makaranta not to far away daga gidana ko a samar mata a can?" Umma tace "Aa gidanka yayi nisa sosai gaskiya" Ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Toh sai ta xauna gidan nawa mana Umma" Wani kallo Umma tayi masa daga sama har kasa kafin tace "Toh baxata xauna ba" Dariya yayi yace "Kema kinsan Ramlah bata da matsala Umma and she can do so many cooking da Jiddah xata iya koya, don ma yanxu bata da lafiya sosai" Umma tace "To ubana nace Aa, daga nan xata dinga xuwa makarantar..." Yace "Toh shkkn Umma, sai driver ya dinga kai ta, idan xata dawo kuma ta samu abun hawa tunda kinga hanya ce" Umma tace "In dai am samu nan kusa kusa a samar mata admission kawai, don unguwar da kake yyi nisa" Ahmad bai kuma cewa komai ba, can ya mike yace "Toh shkkn Umma, xa mu yi waya kar muyi missing train" Umma tace "Toh Allah ya tsare hanya, ya kiyaye, kuma ku yi addu'a" Yace "In sha Allah" Daga haka ya fita dakin ya kulle mata kofa..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *Assalamu Alaikum Everyone ba dogon labari bane ba🤗* *Sunana Ummu Nuwairah (Known as Mîkyããj Sããdy)* *Shin kina fama da kuraje ne ko tabo🤔,shin kina son ki haske? Shin kina fama da matsalar fata ne? Ko ko so kike ki haske me aji ba wai kamfala ba, ki koma santsin madara yaukin zuma🥰* *To matso kusa kiji 'yar mîkyããj Sããdy tazo miki da hadaddun kayan gyaran jiki, masu kamshi kaca kaca😍😍kuma a cikin kudi kalilan😃kayan mu ingantattu ne babu sight effects a ciki, kuma ina mai tabbatar miki in kika saya da izinin Allah sai kin dawo, kin kawo wasu, kema kuma ki fara sara💃🏻💃🏻* _Domin ganin kayayyainmu ku bibiye mu ta Instagram @mik_yaaj_saady WhatsApp no: 08061570778 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Em3E7rFyyhoGd7Upakosyk Bayan kwanaki kadan da Umma tayi magana da Ahmad sai gashi ranan wata Asabar ya shigo gida rike da admission form na Jiddah da receipt na kudin makarantar, Umma ta gama duba takardan da ya mika mata tsaf sannan ta kallesa tace "Ba nace maka makarantar yayi nisa ba Ahmad?" Yace "Umma kece fa kike ganin da Nisa amma ba wani nisa, sannan kan hanya ne ai..." Umma tace "Toh yanxu biya mana kudin makarantar kayi?" Yayi dariya yace "Ehh tawa gudunmawar kenan" Umma tace "Toh Allah yayi albarka, mun gode" Yace "Ameeen" Tace "Ina Ramlah?" Yace "Na ajiyeta gidan Captain" Umma tace "Ohk, yana nan kenan" Ahmad yace "Ehh yana gari, jiya ya shigo" Tace "Toh madallah" Ahmad yace "Xuwa monday sai a kaita schl din for documentation, in sha Allah hopefully xa su saka ta ss1, kinga in dai ya kara maida hankali a ss2 kawai sai tayi waec dinta" Umma tace "Toh Allah ya kai mu, da kana gari ne sai ku je tare ai" Yace "Ina nan har Tuesday" Umma tace "Toh shkkn sai ku je tare din xai fi" Yace "Allah ya kai mu" Daga haka ya nufi kofa ya fita. Karfe biyu Maimoon da Jiddah suka shigo gidan daga saloon sun je kitso, Umma ce xaune parlor tare da Hajja da ta yafa uban mayafi ga jakarta a gefe, daga ganinta kasan bata jima da shigowa ba, A tare Jiddah da Maimoon suka gaisheta, Hajja tace "Har anyi kitson?" Maimoon tace "Ehh" Hajja ta kalli Umma tace "Toh kince sai yamma xa su dawo kuma gasu ko minti ashirin ba ayi da shigowata ba sun dawo" Maimoon da Jiddah dai suka wuce dakinsu, Umma ta ajiye wayarta da take dannawa tace "Dama ba ce maki nayi in dai da layi saloon din xa su iya kai wa har yamma ba? Idan kuma babu layi xa su dawo da wuri? Haka fa muka yi dake Hajja" Hajja tace "Atoh A masar dai magana daya ake, ko don baki son ta rakani ne kika fadi hakan wa ya sani, ni fa nan da kike gani na Allah ne ke daura min son mutum ba wani mahaluki ba, ga can gantalalliyar can Nafeesah me yasa bance ta rakani ba? kice saboda bata gaisheni, sannan wannan bakar yarinyar Aisha sace sace take min a daki, komai aka kawo ta wawura ta boye, shi yasa bata da fasali wllh, to ni ba ruwana ta kaina nake bana biye su, yau dai ina tashi da sassafe nace ma Usman tunda wannan yaro Aliyu yayi aure muka kai masa amarya ban sake komawa gidan ba, kuma ko yanka ni xa ayi idan na hadu da amaryar a hanya yanxu dai ba ganeta xanyi ba wllh, Usman ya fahimceni yace in shirya in je to, barin ma yau Asabar yana gari yana hutu, to ni a gaskiya bana son tafiya ni daya kamar mayya, shine nace kawai direba ya kawoni nan in samu wannan yarinya Jiddah ta rakani muje, ita dama yar ki Maimuna tun wani fada da nayi mata ta daina gaisheni sai yau da taga idonki, banda jiddar babu me mun biyayya yanxu wllh tllh" Umma dai ci gaba da danna wayarta tayi kawai, Jin Hajja tayi shiru tace "Banda abunki Hajja ai jiya juma'ah da babu Islamiyya ya kamata ki xo ba yau da xa su tafi Islamiyya ba" Hajja tace "Toh yau Allah ya bani ikon bude baki ince xan je gidan amarya, ke fa Ramlah wani lokacin Sai in rasa gane inda kika dosa, sannan ni Usman bai wani ce in xo in nemi izininki in tafi da yarinya ba, kawai cewa yayi direba ya kaini in dauketa mu tafi, ni fa ba tsohuwar banxa bace Ramlah, banda tsautsayi babu abinda xai dawo dani daga Masar wllh, a can banda ganin girmana da mutuntani babu abinda larabawa ke yi, don dai Nafisah ta tafi gun mijinta a Habuja ne da ta baki labari da kanta, amma ku banda raini babu abinda ke tsakaninku da babba a kasar nan" Umma tace "Yanxu dai Hajja ga ki ga Jiddah, ni bance kar ki tafi da ita ba, maganan Islamiyya nake, malaman basu yarda da fashi ba" Hajja ta kundumo wani xagi tace "Su malaman Allah ne su da sai ace lallai sai abinda suka gindaya xa a bi? Ni me iya xuwa makarantar ce yanxu ince masu Jiddah baxata je ba sbda wani uzuri da ya taso" Umma tace "Toh rana dai na yi, sai ku tashi ku tafi" Hajja tace "Xuwa xa kiyi ki sanar mata ni ba ruwana duk an ma bata min rai, kamar warce xanje in siyar da Jiddar, ni da na sani ma ban yadda na dawo kasar nan ba wllh, yaushe xa a ga haka a Masar" Umma tace "Wannan Masar din dai Allah ya kai mu muga yanda ake yi a can din Hajja" Da sauri Hajja tace "Aa, ba ko wani gantallale ake bari ya shiga kasar ba ma, nima da yaya suka yarje min na shiga, ke dai kawai a bar kaza cikin gashinta" Dariya Umma tayi ta mike ta wuce dakinsu Maimoon, har sun fara shirin Islamiyya, Umma na kallon Jiddah da har ta saka uniform tace "Jiddah xaki raka Hajja gidan amarya wai" Jiddah tayi shiru tana kallon Umma tana son sanin wace amaryar tukun, Maimoon tace "Wace Amaryar Umma?" Umma ta ta6e baki tace "Gidan Aliyu wai" Sosai gaban Jiddah ya fadi, lkci daya mood dinta ya canxa har hakan bai boyu a fuskarta ba, Umma duk ta lura da hakan kuma, Umma tace "Kina kai ta dama xan baki kudin mota ki lallaba ki dawo, ko minti ashirin kar kiyi a gidan" A sanyaye Jiddah tace "Umma Islamiyyar fa?" Umma tace "To na gaya mata ta hau ni da fada, kawai kiyi hakuri ki rakata din, kuna isa gidan ki juyo abun ki" Jiddah tace "Toh Umma mu je da Maimoon idan ya so kawai sai mu wuce makarantar daga can" Umma tace "Ehh kuma haka ne, ku shirya ku fito, hakan ma shine dai dai, bari in sanar mata" Daga haka Umma ta juya ta fita ta koma parlor, tana kallon Hajja tace "Hajja ita da Maimoon xa su rakaki, idan ya so kuna isa gidan bayan sun gaisa da amarya sai driver ya karasar da su makarantar, da uniform a jikinsu ma xa su tafi, ina ga hakan xai fi ko" Hajja tayi tagumi tace "O'o Allah ina ganin jarabawa ni Dije, yanxu Ramlah ko ke kika haifi er nan Jiddah kya dinga min wannan axababben walakancin da kike min, ina ruwana da wata Maimu? Maimu da bata daraja kowa xaki hadani da? Dama ba Jiddah kawai nace ta rakani ba, a gaskiya a xo a kira min Usman, ya xaki dinga min kamar wata bare Ramlah?? Sannan da Aliyu bai je ya jajubo mana Jiddar ba a ina xaki santa ki nuna iko? A fa ta dalilin jikana ma aka san da wata jiddah a duniyar nan, ni dai wllh ki ajiye son kai kiji tsoron Allah Ramlah, ace a Masar ne ai sai anji dalilin wannan abinda kike min yanxu" Juyawa Umma tayi tace "Ni da ma kira kawai kika yi a tura maki Jiddar da wannan dogon xancen ba sai kin xo ba Hajja" Hajja tace "Oho dai ba ruwana da tashin hankali dake, ni yarinya ce da xan biye maki, banda dai kina kanwar Hauwa a ina xan sanki" Umma na shiga dakinsu Maimoon ta bude kofa tana kallon Jiddah tace "Ki canxa kaya ki xo ku tafi Jiddah" Daga haka ta bar dakin ta wuce nata dakin, Babu yanda Jiddah ta iya haka ta shirya cikin atamfa ta dau hijab dinta ta saka, Abinda Maimoon bata ta6a ganin tayi ba take yi a lokacin wato kumbure kumbure, fuskar nan nata kamar bata ta6a dariya ba kana gani kasan ko kadan ranta bai so ba, jakarta ta dauka ta fice daga dakin, ta wuce dakin Umma, Umma na kallonta tace "To ya xa ayi kiyi hakuri, amma kuna isa ki ce xaki Islamiyya ki fito, ga kudi a gaban mirror ki dauka kiyi kudin mota da shi" Jiddah ta karasa a hankali ta dau kudin sannan tace "Nagode Umma" Fita tayi daga dakin, bata san Umma ta ma fita jin takaicin rakiyar ba, Hajja na ganin Jiddah ta mike tace "Mu je, ai ba ita taje ta nemo ki a duniya ba da xata dinga nuna isa da iko a kanki, mata ta wani narka kiba uwa fanken Masar tana ma mutane rashin kunya kawai" Ita dai Jiddah bata ce komai ba ta bi bayanta tana tafiya a hankali, Driver na ta xaune mota yana jiran ranan fitowar Hajja, Hajja ta bude bayan motar tana kallon Jiddah tace "Toh shiga, halan ta kitsa maki karya da gaskiya ne, naga ranki kamar ba dadi" Ita dai Jiddah tayi murmushin karfin hali ta shiga motar, Hajja ma ta shiga ta kulle tace "Ae laifin wa enda suka bar ki a wajenta ne, kowa fa yasan matar bata da mutunci, nan da nan take maka mutum kotu ko ta kaisa gidan yan sanda ayi ta bala'i shi yasa kowa ke shakkarta a pamily, da akwai wani lkci da ta kira ma Hafsah yan sanda a kan ta xagi yar uwarta Hauwa, aka yi ta dauki ba dadi ana bala'i daga karshe dai Allah ya yayyafa ma abun ruwan sanyi, to idan tana ji da bala'i nima ai A ce, kawai nayi sanyi ne tunda naga su Masar basa haka, ni kuma sai inje in kai masu wani halin daban? Aa shi sa na daina wllh" Jiddah dai bata ce mata komai ba har driver ya kama hanyar gidan Aliyu. Suna isa gidan xai yi parking a kofar gida Hajja tace "Kai ya haka, baka san waye mai gidan ba, jikana ne fa, ni na haifi ubansa, ka danna masu han kawai a bude maka ka shiga" Yana danna horn mai gadi ya leko, Hajja sai kallon Mai gadin take ganin yaki bude gate din ya karaso gun motar tace "Ji wani yakunanne don Allah, kace masa kakar mai gidan ce kai Bala" Drivern ya sauke glass ya sanar ma mai gadin, yana hada ido da Hajja da ta wani sha kunu ya koma ya bude gate din, Hajja tace "Fitsara suke ma mutane idan sun samu waje wllh, banda haka shi xai ce bai ga kamanni ba, kawai neman magana malam" Driver ya ja motar xuwa cikin gidan, Kai kana ganin Jiddah xaka xata wani mugun waje aka taho da ita, gaba daya taki sakewa, driver na parking Hajja ta sauka, kafin tace komai Jiddah ta sauka ita ma, Hajja tace "o,o Na shiga uku, yanda kike yi da fuskar nan taki wani ba sai yayi xaton sato ki nayi ba er nan, a gaskiya Ramlah da kyar taga annabi, ni yanxu ta ya xan sa abinda ta kitsa maki kike ta daure fuska haka fisabilillahi, matar nan fa ta fita hanyata a kasar nan wllh" Jiddah ta kirkiri murmushi tace "Bata ce min komai ba Hajja" Hajja tace "To ni ba ruwana, ta ji da munafurcinta" Daga haka ta fara tafiya xuwa main entrance din gidan Jiddah ta bi bayanta, da sauri Hajja ta juyo tana kallon driver tace "Ka tafi kawai kai, Aliyun sai ya maida mu gida idan muka shirya" Amsa gaisuwar da mai gadin gidan ke yi mata tayi tace "Mai gidan na ciki?" Mai gadin yace "Ehh Baaba yana ciki" Hajja tace "To madallah" Daga haka ta yi gaba Jiddah na biye da ita, murda kofar Hajja tayi bayan ta murda ta ji sa a kulle, ta kalli Jiddah tace "Toh ko meye na garkame kofa da rana tsaka haka" Bata rufe baki ba aka bude kofar, daga sama har kasa yake kallonsu, sai kuma ya koma gefe still looking at Jiddah, Hajja ta shige parlon abunta, Jiddah dai sunkuyar da kanta tayi taki yarda ta kallesa, ya gama kare mata kallo sannan ya juya ya koma parlon yana kallon Hajja yace "Sannu da xuwa Hajjaj, daga ina haka?" Hajja ta rike ha6a tace "Ohh ikon Allah, aure me seta mutum, yaushe rabon xancen kirki ya hadani da kai Aliyu, yau wai kai ne ke min sannu da xuwa fuska a sake haka" Ya shafa kansa yana murmushi yace "Daga ina ku ke?" Tace "Daga gida wllh, na dai ce bari in xo gidan amarya yau" Ta gefen ido ya kalli Jiddah da taki xaunawa ta tsaya daga bayan kujera, muryar Hajja yaji tace "To ina amaryar?" Ya dauke kai yace "Tana sama" xata sakko yanxu, yana fadin haka ya xauna yana tambayarta mutanen gida, Hajja ta kalli Jiddah, girgixa kai tayi tace "Ban san haka er nan take ba sai yau da nace ta rakani, ashe ita ma duk kanwar ja ce, Duk Ramlah ta xugeta tunda muka kamo hanya take min wasu abubuwa me nuni da cewa bata son biyoni, ni ai na xata kirkin gaske gareta wllh, to banda haka meye xa ki makale jikin kujera kamar na kawo ki gidan yankan kai? Ni da na sani da Nafisah na taho duk da halinta ko Aisha" Jiddah ta karaso parlon ta xauna kasan carpet a sanyaye, mikewa Abuturrab yyi ya wuce sama, Hajja ta kalli Jiddah tace "Ba fa baren waje muka xo ba ki saki jikin ki, jikana ne ni na haifi ubansa, ke ma kuma ai kin san sa, kar ki bari matar tayi mana dariya tace mun xo muna ta dari dari a gidan, ki sake jikinki duk abinda kike so kiyi babu wani shakka, wllh bbu me hanaki kin ji" Jiddah tayi murmushin karfin hali, tana son cewa Hajja xata wuce Islamiyya amma ta kasa, don bata san me xai biyo baya ba, Hajja tace "Yanxu tashi ki tafi kitchen ki kwaso mana ruwa da lemo, ki duba robobin garanta ki dau faranti ki debo mana duk abinda kika gani ki kawo" Jiddah ta kasa mata musu amma bata tashi ba, Hajja tace "To tashi mana" Mikewa tayi rai ba dadi ta nufi kitchen din, ta fi minti daya tana kare ma kitchen din kallo, kitchen din na nan yanda yake banda kayan kitchen da aka cika masu tsada, ta dinga kallon wajen wanke wanke dake cike da dirty plates, ta kalli wajen gas taga duk yayi baki alamar ba a gogewa, bin kasan kitchen din tayi da kallon mamaki ganin how untidy it is, daukan plate tayi ta tana kare ma plate din kallo, kawai taje ta dauraye snn ta karasa store ta bude robobin da ta gani ta diba duk abubuwan ciki, wani tray ta dauka ta daura ruwan gora biyu da cups snn ta fito kitchen din, xaune taga Aneesah a parlor tana kallon Hajja dake ta xuba, Aneesah ta dinga kallon Jiddah da wani irin mamaki, don bata ma san da ita aka xo ba, Hajja tace "Yauwa, kinga kinyi dubara, sannu" Jiddah ta ajiye tray din hannunta ta d'an kalli Aneesah da mood dinta ya sauya lkci daya tace "Ina yini" Aneesah ta hau danna wayarta, Hajja tace "Gaisheki fa take Nanisa kike ko?" Aneesah ta daga kai tace "Ohk, sannu, lfya lau" Jiddah ta mike ta xauna saman kujera tana kallon Tv dake aiki, mikewa Aneesah tayi tace "Na gaisheki Hajja, ina d'an yin abu ne a sama" Daga haka ta wuce Hajja ta bi ta da kallo, ta rike ha6a murya can kasa tace "Tabdi" Jiddah dai kallon tv kawai take, Hajja tayi kasa da murya tace "Kaji min shegiya, ta sanki ne ta maki wannan walakancin ni ya su?" Saukowar Aliyu yasa Hajja tayi shiru, ta kallesa tace "Amma ba a nan parlon xa a yashe mu ba kamar marasu makabuli ko Aliyu" Yace "Mu je sama" Mikewa Hajja tayi ta kalli Jiddah tace "kwaso mana kayan flawan da lemon" Jiddah ta dau tray din ta mike suka hada ido da Abuturrab da sauri ta dauke idonta, Tuni Hajja tayi hanyar stairs Abuturrab ya bi bayanta, sai sannan Jiddah ta fara tafiya ta wani hade rai. Dakin da Jiddah ta xauna a lkcn da take gidan ya shigar da su, Hajja tace "Ba shakka, ko mutum xai yi sati a nan babu wanda xai san abinda yake ciki abunsa" Jiddah ta ajiye tray din ta xauna kasan carpet, Hajja ta cire mayafinta ta linke ta bude press ta ajiye, katon jakarta kuma ta rataye sa a bag rack, sai kallonta Jiddaj take da mamaki, ta juyo tace "Ki cire wannan Hijabin ki sha iska abun ki, ai nan ba bakon waje bane, gidan Aliyu ne fa" Jiddah tayi gathering courage tace "Hajja ni fa makaranta xan wuce yanxu dama, tunda akwai sauran lkci" Hajja ta kalli Abuturrab tace "Kaga jaraba ko, Ramlah ce ta koya mata haka fa kafin mu fito, to ko dai Ramlan nan kanwar uwar Jiddan ce bamu da labari??" Abuturrab dake kallon Jiddah, calmly yace "Baxa ki je ba" Hajja tace "Atoh dai, su makarantar basu san uxuri bane" Wani kallo Jiddah ta masa ta gefen ido lkci daya ta dauke kanta ta daure fuska, Da mamaki ya dinga kallonta babu ko kiftawa, can ya shafa kansa yace "Wani abincin xa ku ci Hajja?" Hajja tace "Ni ko tuwo aka samu a ban Aliyu" Yace "Ohk" sannan ya juya ya fita, Hajja tace "Ikon Allah, yanxu Aliyu ne ke nan nan da ni kamar wanda nayi ma wani abun arxiki, wllh ni tunda muke bai ta6a girmama ni ya mutunta ni irin yau ba, ohh Allah mai iko" Jiddah dai bata ce mata komai ba. Aliyu ya nufi bangarensa ya shiga parlor ya tadda Aneesah xaune tana shan lemon fata, idan ta sha sai ta jefar da fatan akan farantin da aka dauro lemukan a kai, yana mata wani irin kallo yace "Aneesah na sha gaya maki idan xaki ci abu plss ki daina ci min a parlor i detest that..." Ta kallesa daga sama har kasa tace "Naga dai ba ni na shigo da lemun ba kai ka kawo abunka ko" Yace "For heaven sake ya xa ki maida min parlor wajen cin abinci, what's d essence of d dinning area downstairs" Bata kuma basa amsa ba ta dau wani lemun tana sha a hankali tana jefar da kwallon kan faranti, gajeran wando ne jikinta da yar vess, yace "Tuwo grandma dita ke son ki girka mata ynxu" Ta sauke kafarta daga saman kujeran tace "Tuwo?" Yace "Ehh" wani dariya tayi tace "Yanxu kai ka ta6a ganin ko indomie na girka a gidan nan balle tuwo, wllh Aliyu ban san haka kake da takura ba sai da muka yi aure, kullum sai ka samu matsalar da xaka billo da shi idan ka dawo weekend, kace can datti, nan datti, can wari nan wari?? sannan ma tsaya tukun, ni ka gaya min xaka yi baki a gidan nan? To kaga baka sanar da ni ba, don da ka sanar dani akwai wata kawata chef sai in gayyato ta ta min girki in biyata, amma waye xai maka wannan wahala da tsakar ranar nan, beside ba naga tare da Me siyar da doya da dankali ta xo ba, ai ita ta sa6a wahala sai ta tashi ta shiga kitchen din ta girka masu in yunwa suke ji, don wllh wllh baxan iya ba, in ma ji da gajiyar wankin bayin da kasa nayi daxu mana" Kallonta ya dinga yi kafin ya juya ya fita daga parlon ta bi sa da wani shegen harara tana dauko wayarta dake ring, d'an xaro ido tayi ta katse wayar sannan ta saka shi a flight mode. Eatry Abuturrab ya tafi ya siyo take away din tuwo da gasasshiyar kaza, Hajja ta dinga washe baki bayan ya shigo masu da ledan tace "Allah maka albarka Aliyu, sannu kaji, matar taka bata yi girki bane?" Yace "Bata yi ba" Hajja tace "Toh Allah ya kyauta, haka fa Hafsah ta dinga yi ma Usman bata son girki" Abuturrab ya kalli Jiddah dake kwance ta juya masu baya nan ko takaici ne duk ya bi ya isheta tayi fashin makaranta, xaunawa yayi a dakin Hajja tayi ta jan sa da hira yana responding har aka kira la'asar, Jiddah ta sauka kan gadon ta shige bandaki ya bi ta da ido, Hajja ta kyabe baki murya can kasa tace "Uwar rikon ce fa ta kitsa mata karya da gaskiya, kaga ko yar cin cin din da alkaki ta ki ci wllh... Tun daxu sai nukurci take, taki sakewa" Abuturrab yace "Kyaleta, a nan xaku kwana" Hajja ta gyara xama tace "Atoh dai" mikewa yayi ya fita don xuwa yayi alwala ya wuce masallaci. Har kusan isha Jiddah bata ga alamar Hajja xata ce su tashi su tafi ba, ga wani abincin Abuturrab ya kawo, bayan ta idar da sallah tana xaune kan darduma a hankali tace "Hajja wai baxa mu wuce ba?" Hajja tace "Ke ba fa gidan 6are na xo ba, bari kiji in gaya maki, ni wllh bansan bakin hali gareki ba sai yau, gidan jikana ne nan fa, babu ruwanki da sanda xa mu wuce, ke dai iyakarki ba rakiya ba, xan kawoki inda xa a cuceki ne? Ni fa na rainesa yana karami, idan ban xo gidansa ba ina xanje, kuma a nan xan kwana wllh don xuwa gobe da safe nake son ganin iyakar xabiyar matarsa da ta xo ta gaishe mu a tsattsaye har yanxu bata sake shigowa ba, dadin abun kuma jikana ya saurareni gashi muna ta hiran yaushe gamo da shi don haka sai Allah ya kai mu gobe xan nuna mata ni er banxa ce" Jiddah ta ji kamar ta fashe da kuka, lkci daya hawaye ya kawo idonta ta mike ta koma can karshen gado ta xauna, Hajja ta kwashi take away din da suka ci abinci ta fita xuwa kitchen, Sai a sannan Jiddah ta fashe da kuka ta hade kanta da gwiwa, bayan kusan minti goma Hajja ta shigo dakin tana hura hanci tace "Tirrrrrr, ashe kazama Aliyu ya auro? Ke kinga kitchen dinta duk wari kuwa? Wllh da nasan haka kitchen din yake ni baxan ma fara shan ruwan gidan nan ba sai dai a fita a siyo min a waje, a garin yaya mace xata bar kitchen dinta haka ni Dije? Wllh sai da tsoro ya kamani, yaushe Aliyu shi ma ya lalace da son kazanta? A yanda na san sa a da fa har tunani muke ko aljanun tsafta ne suka auresa, to naga duk ya lalace ya xuba ido kitchen dinsa ya ru6e duk wari" Jiddah dai bata ko kalleta ba, Hajja ta xauna tayi shiru alamar dai tunanin kitchen din take kuma abun ya dameta, can tace "Tirrrr" Sai kuma tace "Huhuhu kazama ce wllh, kwanukan duk wari naji suke, ni kamar har da kiyashi naga suna yawo a kitchen din, ga dai kitchen har kitchen" Sai kuma ta kalli Jiddah murya can kasa tace "Wllh ban san ta ina xanyi wanke wanken bane kar inje in jika kitchen din abu ya kara lalacewa ai da nayi, amma ke tunda naga duk kun saba ki daure domin bama tsafta hakkinsa kije kiyi wanke wanken nan, wllh babu kyan gani kinji na rantse, to ko dai ba mace ya auro ba" Jiddah tace "Hajja bata sa ni in mata wanke wanke ba fa" Hajja ta kara yin kasa da murya ta marairaice tace "Na sani er nan, duk don a fita hakkin tsafta ne, wllh da Masar ne kitchen din nan ya tashi aiki, sai ma a iya rushesa kawai, domin Allah ki tashi ki je ki gyara, ai ba don yar iskar xa muyi ba, kawai don Allah, don tsafta xa mu yi" Jiddah ta dinga kallon Hajja, Hajja ta mike tace "To ai Shikenan bari in kwashi kwanukan in fita da su tsakar gida in wanke don a gaskiya idan xa su kwana a haka ni baxan kwana gidan nan ba ba ruwana, baxan ci amanar tsafta ba a gaskiya" Ganin da gaske fita xata yi Jiddah ta mike tace "Toh naji xanyi" Hajja ta koma ta xauna tana huci, Jiddah ta fita dakin, babu kowa parlon ta shiga kitchen din, tafi minti uku a tsaye tana tunanin ta inda xata fara, sai yamutse fuska take, can dai ta fara hada kayan wanke wanken waje daya.. Har karfe tara Jiddah na kitchen din, lkci daya kitchen din ya dawo fess duk ta gyara ko ina ta goge, tana wanke wajen sink din aka dauke wuta, lkci daya kuma taga kamar an kunna hasken waya a parlor, ko gama dauraye wajen bata yi ba ta kashe tap din xata fito kitchen din da sauri, ta kusa cin karo da shi, ta ki tsayawa xata bi ta gefensa ya rikota, kwace hannunta take son yi, ya ja ta xuwa kitchen din ya kulle kofar ya jinginar da ita jiki, ta buda ido sosai tace "Meye haka" ya kife wayarsa saman cabinet din kitchen ta daina ganin hasken komai, a tsorace tace "Wai meye haka" yace "Me ya hanaki cin abincin da na kawo maku??" Xuciyarta na bugawa tace "Ni wllh na ci kadan, ai nace mata na koshi ne, amma kuma na ci ai..." Gaba daya ta daburce, yace "To ni dodonki ne da kika ce baxa ki kwana a gidana ba" Ta dake tace "Toh ai ba dole sai na kwana a gidanka ba, ko ya xa ayi in kwana a gidan wanda ban sani...." xaro ido Jiddah tayi jin goshinsa a nata tana juyo breathing dinsa, sai kuma ta rufe ido a tsorace tana turasa da duk karfinta tana son kwace kanta amma ko gezau, bata ankara ba sai ganin abun tayi kamar a mafarki, and he gave her a perfect french kiss da ya gigitata ya rikitata, ba don rikon da yayi mata ba da tuni ta kai kasa dama. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you *EXCLUSIVE FABRICS &MORE* provides you with exclusive, and Affordable fabrics such as laces, Ankara,materials shoes,bags and so much more on wholesale and retail EXQUISITE, AND AFFORDABLE THANK U ❤️🤩 LOCATION: LAGOS *EXCLUSIVE_FABRICS_AND_MORE* Na siyar da kaya kamar Laces, Atampopi, Materials, Jewelleries,👡👠👜👛da dai sauran su Tana maraba da masu siyan daya koh sari Location : Lagos Tana aika kaya duk inda kake da yardan Allah 🤝🤝❤️🥰 WhatsApp me via.... 09080058848 Lkci daya Abuturrab ya saketa ta dalilin hasken wuta da ya dawo kitchen din, ta rufe bakinta a rikice ta juya ta bude kofar kitchen din ta fice da gudu, Aneesah na tsaye parlor bayan ta kunna solan gidan, ta bi jiddah da kallon mamaki barin yanda taga ta rufe bakinta da hannu har ta wuce sama, can ta kalli kofar kitchen din, sai kuma ta tafi can da sauri ta tura kofar xata shiga suka kusa cin karo da Abuturrab xai fito, ya d'an buda ido kafin yace komai ya juya mata baya, walking toward the gas yace "Na xata kinyi bacci ai...." Daga sama har kasa ta dinga kallonsa, yana tsaye gaban gas din bai yarda ya juyo ba tace "Me kake yi a kitchen Captain?" Yace "Gyaran kitchen din da kika bari kaca kaca" Sai a sannan ta bi kitchen din da kallo taga sai walkiya yake, ko ina yayi fess, sake kallonsa tayi tace "Who just left the kitchen now?" Ya dau lighter kamar xai kunna gas din yace "The person that helped in transforming the kitchen back to it normal sef..." Tace "To wannan juya min bayan da kake na meye haka?" Wani boyayyen ajiyar xuciya ya sauke ya daga wayarsa da ya fara ring duk da Ahmad ne ke kiransa ya kai kunne still backing her, Aneesah ta gaji da tsayuwarta ganin ba gama wayar xai yi ba gashi yayi backing dinta ta juya ta fice daga kitchen din, sai a snn ya d'an waiga, ya dau mug ya bude flask ya xuba ruwan xafi ya saka Lipton, sannan ya dau lime din da yake siyowa a kitchen din ya yanka uku yayi squeezing a ruwan lipton din... Hajja ce tsaye kan Jiddah dake xaune kasan dakin ta hade kanta da gwiwa tana shessheka, rai bace Hajja tace "Naga abinda ya fi karfina ni Dije, yanxu baxa ki bude baki ki gaya min me aka maki ba in san ta inda xan fara, matar gidan ce ta maki wani abun koko?" Jiddah taki dagowa hawaye sai sauka idonta yake duk jikinta yayi sanyi, Hajja bata sake ce mata komai ba ta juya ta fita daga dakin ta tafi can bangaren Abuturrab, da karfi ta kwankwasa kofar, Aneesah dake xaune saman kujera a parlon tana kokarin dialing number Aunty ta kalli kofar, jin an sake kwankwasa kofar kamar xa a cire ta mike a d'an fusace tace "Wai waye wannan" Tura kofar parlon Hajja tayi ta shigo ciki, tana huci tace "Ni dai kafin ince komai ina son sanin waye mai gidan nan tukun??" Aneesah tace "Haba dai.. ai ba girmanki bane shigowa wannan bangaren Hajja, duk abinda kike so da sai ki jira a fito....." Wani xagi Hajja ta mulmula mata tace "Ke har kin isa ki gaya min yanda xanyi a gidan jikana? Kaji min yar banxa, Ashe dama bayan bak'ar kazanta har da rashin kunya da fitsara kika iya ban sani ba? To wllh na fasa komawa wannan gantalallen Masar din dai tunda ba uban da na hada dasu, ina nan kasata Najeriya sai na nemo ma jikana auren tsaleliyar mata me bama tsafta hakkinsa, yar gayu me kamshi xan samar masa ba irinki kazama me wari ba, mata daga aure ko wata biyu ba ayi ba kin hallakar min gidan jika da kazanta ko ina banda tsutsa babu abinda yake fita, ko irin kamshin turaren nan na amare gidan nan bai samu gatan yi ba, to tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin mace kazama aminiyar dauda irin ki ba, amma duk ba wannan ya dameni ba, ya xan sa yarinya karama wanda kika kusa haifa ta tsaftace kitchen din da kika halaka yake fitar da tsutsa kuma ki saka min ita kuka babu gaira babu dalili??" Aneesah dai na tsaye sai kallon Hajja take baki bude with shock, Hajja tace "Ba kya kalleni kamar shashasha ba dama, wllh dole in nemar ma Aliyu mata me tsafta da son kamshi dai dai shi, ina ta kallonsa ganin ya d'an rame ashe kaxantar ki ne ke tsotse mana shi, to Allah ya isa wllh, mu kaf xuri'armu babu kazami...." A fusace Aneesah ta nufi kofa ta fice fuuuu, Hajja tace "Uwar kazaman Najeriya kawai, mata haka kazama na bugawa a jarida, dubi farin kafet din parlon nan fisabilillahi yanda ya fara fita hayyacinsa, parlon ma naji kamar karni yake wllh, ko da yake dai ba ruwana bari inyi shiru, ba abinda Usman ya aikoni inyi a gidan nan ba kenan, amma da yau kinji maganganu a kan kazantarki wllh" Aneesah na sauka downstairs ta tadda Abuturrab xaune ya gama shanye cup din Lipton da ya hada, tana shigowa parlon ta rushe masa da matsanancin kuka tace "Aliyu dama grandmum dinka xuwa tayi ta ci mun mutunci ta ci xarafina har gidana? Dama haka kuke ban sani ba?" Kallonta ya dinga yi don bai san me ya faru ba, sai ga Hajja tana sakkowa tana cewa "Wllh kinci albarkacin ba abinda Usman yace in xo inyi a gidan nan ba kenan, amma yau da na maki bankada iri iri, kuma gida muna nan babu yanda kika iya da mu tunda ba wani ya haifo min Usman din ba har Allah ya basa Aliyun" Da mamaki Abuturrab ke kallon Hajja yace "Me ya faru Hajja?" Tace "Me kuwa baxai faru ba Aliyu, daga na tura Jiddah ta farfado da kitchen din da ta fara hallakarwa kawai sai ta saka min ita kuka na rasa abinda tayi mata, yanxu haka yarinyar na can tana rusa kuka ta inda take shiga ba ta nan take fita ba kuma taki gaya min menene, da kyar fa Ramlah ta amince ta biyoni, yanxu in maida mata yarinya idanuwa a kumbure me kake tunanin xai biyo baya matar da ba mutunci gareta ba kowa ya san da haka..." Abuturrab ya d'an saci kallon Aneesah, lkci daya ta sake fashewa da kuka tace "Wllh baxan kwana gidanka ba yau Aliyu, ni ai bansan bayan duk hakurin xama da nake da kai a yanda kake akwai wani kalubalen dake tunkaroni ba...." Tana fadin haka ta wuce sama kamar xata tashi sama, Hajja tace "Oho dai Allah ya ishi Jiddah, kai kuma kayi ta istigifari don wnn ba karamin laifi ka aikata ma mahaliccinka ba ya jarabe ka da mata kazama, ni wllh kawai nayi shiru ne amma tun daxu da na shigo parlon nan naji yana wari" Tana fadin haka ta juya ta koma sama, Abuturrab ya d'an yi murmushi, shi dai ya ki tashi har sannan, Aneesah na komawa sama ta saka kayanta ta dau kaya kala biyu a karamin akwatinta ta dau hand bag ta yafe gyalenta ta fito, tana saukowa downstairs bata ko kalli Abuturrab ba ta nufi Kofa, ya bi ta da kallo yace "Ina xaki je Aneesah?" A mugun fusace tace "Wllh baxan kwana gidan nan da tsohuwar nan a ciki ba, baka ce min bayan hakurin da xanyi da kai har ita ma xanyi hakuri da ita ba, sannan ita wannan yar iskar mara asali da ta kawo min gida...." Dakatar da ita yayi yace "Tafi kije, Allah ya tsare" Bude baki tayi tana kallonsa, tace "Kace in tafi inje?" Fuska daure yace "Ehh, sai da safe" Kofa ta nufa fuu ta fice, ko kulle kofar bata yi ba ta nufi gate, ya mike ya karasa kofar ya kulle ya sa makulli. Hajja na komawa daki ta tadda Jiddah kwance ta takure waje daya, Hajja tace "Kiyi hakuri duk ni na ja maki don uwar rikon ki ma da kyar ta amince kika biyoni, ban san gidan er iska xa mu xo ba da ban fara xuwa da ke ba, amma kema wannan simi simin da kike baxai fissheki ba, gwara ki samu kiyi baki ki dinga kwatar kanki, naga kin cika wani sanyi kamar kankara, ai yanxu idan kace xaka yi sanyi sanyi a duniya kullum cikin cutarka ake, da kin gaggasa mata magana kin gaya mata irin kazantarta ai da ta kama kanta amma kin wani taho sama kina kuka kamar er yarinya, ni sai yanxu ma kika bani haushi wllh, da ba don Allah ya takaita aurenku da Aliyun ba ai kishiyarki fa xata xama, to a haka xa ki xauna kina mata kuka kullum??" Jiddah dai tayi shiru bata ce komai ba, har sannan xuciyarta bugawa yake, scene din abinda Abuturrab yayi mata ya ki daina dawo mata, ganin abun yake kamar afresh, Cike da damuwa Hajja tace "To ko dai wani mugun abun ta maki naga duk a firgice kike wllh, ki gaya min gaskiyar me ta maki Jiddah" Jiddah ta lumshe ido ta bude a karo na farko ta bude baki a hankali tace "Bata min komai ba" Hajja tace "Oho dai ita da Allah ni dai na gaya mata duk abinda ya kamata ta sani" Tana fadin haka ta sake fita daga dakin, Jiddah ta ji hawaye ya kawo idonta ta kai hannu bakinta da take jin kamar bai cire nasa ba har sannan, ita idan ba a tv ba bata ta6a sanin ana haka a reality ba ma, hancinta ta kai kayanta jin kamshin turarensa ya cikata, ta wani turo baki ta mike ta fara cire kayan, sai da ta cire tas sannan ta saka hijab ta kwanta tayi lamo saman gadon, scene din da bata so na sake dawo mata kamar a lkcn yake faruwa. Aneesah na xaune parlon kawarta Chef Salma, Salma tace "Kan bala'i!!! to ai ni duk a xancen ki babu abinda ya tsaya min irin yarinyar da kika ce ta biyo kakar tasa... Ita yar kauyen da ya saka ce ake miki sintirin xuwa gidan ki da ita? Sannan kuma ta bi ki da sharri haka? To me hakan ke nufi?" Aneesah ta fyace majina da handki din hannunta tace "Ai shine nake jiran kiran stepmom din tasa, wllh ni rabona da su gaba daya tun xuwansu da rana da nayi shigewata parlonsa, ban ganta ba balle har wani abu ya hadani da ita, amma ban san me taje ta gaya ma makirar tsohuwar ba ta shigo har bangaren mijina tayi min wankin babban bargo ta ci min mutunci" Salma tace "To kuma ai kinyi wauta barin gidan da kika yi, bar masu gidan fa kika yi kenan" Aneesah ta fashe da kuka tace "Captain din fa ce min yayi in tafi sai da safe" Salma tace "Toh ai dadi kakar da ita tsinanniyar yarinyar xa su ji, ke dai wani lkcn idan kinyi wani abun kamar er fari, ke da gidanki kawai ki hado kaya ki bar masu, wato sun ma ci nasara a kanki, sannan karyar da ita yarinyar tayi ma kakar Captain din ya xama gaskiya kenan tunda har kika bar gidan" Aneesah tayi wani murmushi tana girgixa kafa, Salma ta ta6e baki tace "Wllh sakwa sakwan da kike ma wnn pilot din yayi yawa, sai kace shine autan maza? Shi yasa har ya iya budan baki ya maki maganar banxa, banda kilan suna da wani kudurin a ransu meye na xuwa da yarinyar da ya saka gidan tun tale tale? Me ya kawota bayan ga kanninsa da cousins dinsa da xasu iya rako tsohuwar, to wllh ki farka daga wnn slumber din naki kina da aiki ja a gaba, da kyar idan ba sake cusa masa me dankali da doyan xa su yi ba" Aneesah ta sakko da kafarta daga saman kujera da sauri alamar xancen ya gigitata tana kallon Salma, er dariya tayi tace "Ka ji ki da wani xance, to babu wani aure tsakaninsu sai in ta sake wani auren, ya mata saki sau uku kenan, daya a lkcn auren na farko farko, sannan suna tare ma ya saketa, sai na karshen da Abbansa ya umarcesa da ya saketa kuma ya saketa din" Salma tace "Ke wa ya gaya maki haka?" Ta gyara xama tace "Aunty, kuma Aunty Safara'u ma taje wani waje haka aka ce mata babu aure tsakaninsu har abada, don haka mu kwantar da hankalinmu, balle ma captain ba class dinta bane shi ma ya sha fada, me xai ci da ita?? yar hayin rigasa ce fa bama birnin hayi ba kauyen hayi, ko numfashinta baxai so ya shakka ba balle wani abu ya hadasu" Salma tace "To har naji hankalina ya kwanta maki, da kika ce babu auren, amma duk da haka sai kin taka burki a daina taho maki da ita gida gaskiya, ba fa dangin iya ba na baba" Aneesah tace "Ita kanta tsohuwar xuwanta na farko da na karshe kenan tayi idan anyi duniya don manzon Allah, wllh ko da kudi aka hadota ta taho gidan Aliyu baxata sake xuwa ba" Salma tace "Yauwa, haka nake son ji dama, ki tashi xaune daga kwancen da kike wllh... Yanxu kowa ta kansa yake duk inda kika ji ance aiki na kyau ki cire kyashin kudi kije" Aneesah ta jawo wayarta ta daga ganin Aunty ke kiranta ta kai kunne da sauri, kuka ta sakar mata, nan kuma ta bata labarin duk abinda ya faru, Aunty da ta kakance idonta tace "Kina nufin tare da shegiyar taje maki gida?" Aneesah tace "Wllh kuwa" Aunty tace "Toh ke banda shashanci meye na barin gidan, wato Hajjar taji dadi kenan ma kin bar masu gidan" Aneesah tace "Aa wllh Aunty ni baxan iya xama ba suna ci mun mutunci kuma babu abinda Aliyun yace, sannan da kansa yace in tafi" Aunty tace "Toh abinda xai faru yanxu ki dauko jakar taki ki taho nan gida, Abbansa na gari ai, maza ki taho yanzu, kuma wajen maida magana duk ki san abubuwan da xaki kara a xancen, ai in sun san wata basu san wata ba" Aneesah tace "Toh" Aunty tace "Wai ya ma baki wannan kudin kuwa?" Aneesah ta tabe baki tace "Ina fa, ce min yayi sai sabon wata da xa a shiga..." Aunty tace "Anya Aneesah kinyi amfani da maganin karshen da na baki a daren ku na farko kuwa?" Aneesah tace "Aunty sai dai na xo gidan, yanxu xan fito dama gidan Salmah na taho" Aunty tace "To na gane, taho gidan maxa yanxu" Driver Salmah ta saka ya kai Aneesah can gidansu Abuturrab. Har wajen karfe sha daya Abuturrab na xaune downstairs tare da Hajja da babu irin labarin Masar da bata masa ba, with much interest yake sauraronta yake biyeta duk da labarin ba dadi yake masa ba, ya gyara xama yana kallon agogo yace "To ai nan ma akwai turarruka masu kamshi ba can kadai ba" Hajja tace "Inaaa har yau banji turare me kamshi irin ta Masar ba, akwai wani turare da Usman ya bani wai dubu hamsin ya siya ni dai yana can na jefa cikin kwambodi.... to ba kamshi" Yace "Toh bari in dauko maki wani turarena yanxu ki ji kamshinsa ko ya kai na Masar din" Mikewa yayi yace "Ki jirani yanxu in dauko maki" Hajja tace "Toh yi maza, kaga idan kamshin ya min sai ka bar min kawai" Yace "Ba damuwa" Daga haka ya haura sama, gently ya murda kofar dakin ya bude, kwance take saman gadon ta rufe duk jikinta da hijab dinta idonta a lumshe, ya karasa cikin dakin ya kulle kofar, kallon switch din dakin yayi kafin ya nufeta walking slowly ya tsaya kusa da gadon yana kallonta, ya kalli kayanta da ta linke ta ajiye sannan ya kara kallonta, daga hijab din da ta lullube jikinta yyi yaga babu abinda ke jikinta sai undies, lkci daya ya sake hijab din ya juya ya fita dakin ya tafi bangarensa yana shiga bedroom dinsa ya kashe wutan dakin ya fada saman gado yayi rub da ciki. Hajja ta gaji da xama, ta sha gyangyadinta har ta gode Allah sannan ta mike wajen karfe daya ta wuce sama tana cewa "Gantalallen ba sai yace min bacci yake ji ba sai da safe, me hali dai baya fasa halinsa kawai..." Tana bude kofar daki taga Jiddah durkushe kusa da gado ta hade kanta da gadon, Hajja tace "Meye haka?" Ta dago da kyar tana kallonta ta girgixa mata kai, a fusace Hajja tace "To meye kika wani rungume gado kamar me nakuda?" Jiddah dai ta kasa ce mata komai, Hajja tace "A gaskiya da na sani baki biyoni ba, daga abun arxiki? Me ya sameki?" Jiddah ta kara girgixa mata kai kawai, Tabe baki Hajja tayi ta Kashe wutan dakin tace "Baxan iya da wahalanki ba bacci xanyi wllh, babu wanda xai shiga hakkin bacci na" Tana fadin haka ta kwanta daga kwanciya kuma sai minshari, Jiddah tayi ta juye juye... tun tana daurewa har ta kasa ta dinga hawaye tana yarfe hannu, rabonta da irin ciwon nan da take ji yanxu tun tana gun Babaarta, har karfe biyu Jiddah na durkushe yanda take, da ya lafa mata sai ya fara kuma... Shesshekarta ya farkar da Hajja, Hajja ta mike xaune sai kuma ta tashi ta kunna wutan dakin, xaro ido tayi ta kalli agogo ta kalli Jiddah sannan ta bude kofa ta fice, bangaren Aliyu ta nufa ta buga kofa, Abuturrab dake xaune saman kujera a parlon ya rike kansa ya juya da sauri yana kallon kofar, Hajja ta sake bugawa, xai mike daga kan kujeran yayi kicking ruwan Lipton din lemun tsami dake cup a ajiye daga kasa kusa da shi, lkci daya ya malale saman carpet din parlon, tsallakewa yyi ya nufi kofar ya bude, cikin tashin hankali Hajja tace "Aliyu awa uku kenan wancan yarinyar bata ko rintsa ba, sai kuka take na rasa me ke damunta, ni fa tsorona Allah tsorona tijaran da Ramlah xata min a kanta" Da mamaki yace "Me ya sameta?" Hajja tace "Ina xan sani Aliyu ko kwanciya taki yi, tana can duke kamar me nakuda nayi nayi ta gaya min meye taki" Abuturrab yace "Ina xuwa" Daga haka ya koma daki ya dau jallabiyarsa ya saka sannan ya fito, yana gaba Hajja na biye da shi suka isa dakin, Yana bude kofar dakin suka ganta durkushe kofar bandaki tana kwarara amai, Hajja tace "Na shiga uku ni Dije ta kashe bandakin, wani aman arxiki ne baxa ta shiga can ciki ba sae a bakin kofa?? Tirrrrr" Abuturrab ya karasa da sauri ya duka kusa da ita yace "What's wrong with u?" Ta kasa basa amsa ya dagata xuwa cikin bandakin, Hajja ta fice daga dakin hankali tashe tace "Baxan iya ba wllh, ko ni ya na kare da nawa aman balle na wani..." Abuturrab ya wanke mata fuskarta bayan ya xuba ruwa gun aman, xai cire mata Hijab din jikinta ta rike gam tana xaro ido amma taki yarda ta kallesa, hade rai yayi yace "Cire hannunki" Da kyar cikin kuka tace masa "Aa bana so wllh" lkci daya ya fixge hijab din a jikinta da karfi, ta turasa ta durkusa a kasa hankali a tashe tana cewa "Wayyo na shiga uku don girman Allah ka bani hijabina ka fita" Yana kallon ko ina na jikinta yace "Me yake damunki?" Duk a gigice take tace "Ai naji sauki" Yace "Saukin me" Taki yarda ta kallesa tace "Don girman Allah kayi hakuri ka fita" Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tana kara rufe jikinta, shi dai kallonta kawai yake, can ya d'an shafa kansa ya ajiye mata hijab din saman washing machine ya juya ya fita bandakin, banda rawa babu abinda jikinta yake, tun da take bata ta6a ganin irin wannan iskanci ba, ko a gaban mace bata ta6a tsayawa a yanda take yanxu ba, gaba daya ta nemi ciwon cikin da take ta rasa, ta kalli jikinta ta kara takurewa waje daya xuciyarta na bugawa, ta fi minti biyar a haka kafin ta mike da sauri ta figi hijab dinta ta saka gabanta na faduwa, ta makale jikin kofa sannan ta leka dakin a hankali, ido hudu tayi da shi yana tsaye har lkcn a dakin, da karfi tayi banging kofar bandakin ta sa makulli, ganin haka ya shafa kansa ya juya ya fita, xaune yaga Hajja a corridor din ta shimfida darduma sai xuba gyangyadi take, yayi mata kallo daya ya wuce bangarensa, throughout daren nan Abuturrab bai rintsa ba, banda juye juye babu abinda yake, idan ya gajiya da kwanciyar saman gadon ya koma kujera a parlor, har aka kira sallah. Karfe takwas Jiddah ta lallaba ta saka kayanta da Hijab tana kallon Hajja dake kwance kan darduma tana bacci, ta dau jakarta ta nufi kofa a hankali ta bude ta fita, kallon direction din bangaren Abuturrab tayi kafin ta sauka downstairs da sauri, mai gadi ne ya bude mata gate ta fice fittt daga gidan.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Har Jiddah ta isa bakin titi waigen layin take xuciyarta na bugawa, tana ta tsaye har ta samu adaidaita ta hau ta gaya masa inda xai kai ta, dai dai kofar gidan Umma mai adaidaita sahun yayi parking ta sauka ta ciro kudin da Umma ta bata jiya a jaka ta mika masa, ya bata canji sannan ta shiga cikin gidan... Babu kowa parlon don su Maimoon sun tafi Islamiyya, ta karasa kitchen don gaida Huraira dake aiki a ciki, Huraira tace "Dama Umma tace sai yau xaki dawo da aka ji shiru har dare jiya" Jiddah ta d'an yi murmushi kawai tace "Umma bata tashi ba?" Huraira tace "Bata tashi ba ko" Juyawa Jiddah tayi ta wuce dakinsu, sai da ta fara shiga bandaki ta wanke baki tayi wanka ta fito ta shirya cikin doguwar riga bayan ta gama shafe shafenta sannan ta kwanta, da ta runtse ido abinda Abuturrab yayi mata kawai take gani, tana ganin hakan kuma sai gabanta ya fadi, ita har yanxu ganin lamarin take kamar a mafarki, da yake bata wani samu baccin kirki daren jiya ba nan da nan bacci me nauyi ya dauketa. Karfe sha daya saura Umma ta fito daga dakinta ta dalilin kiranta da Huraira taje tayi wai tayi bakuwa, Tsaye taga Hajja a parlon sai hura hanci take, Umma ta karaso tana kallonta tace "Lafiya Hajja?? sannun da xuwa" Hajja ta dakatar da ita tayi mici mici da ido tace "Jiddah ta dawo??" Umma ta kalli Huraira dake bayan kujera a tsaye, Huraira tace "Ehh ta dawo tun daxu amma tana daki tana bacci" Umma ta kalli Hajja, Hajja ta rushe da kuka ta nemi kujera ta xauna tace "Toh a gaskiya Allah ya isa, wannan daga min hankali da tayi taje don kanta, idan kuma ke kika koya mata hakan kema kije don kanki... Kuma ni ban san haka take ba da ban fara xura jiki ina kulata tun farko ba, ashe su Maimu da Aisha kananun yan iska ne a inda wannan yarinya jiddah take ban sani ba?? Amma ba komai nasan duk karatunki ne ta dauka ba wani abu ba" tana fadin haka ta fyace hanci, Umma da ranta ya gama baci tace "Kawai sai in xaunar da ita don rashin aikin yi ince ta baro gidan da ku ka je da sassafe ko Hajja??" A fusace Hajja tace "Oho... Xaki aika wllh, waye bai sanki da halinki ba? dama kuma da ya kika bari ta bini, bai sai da na hadaki Allah... annabi ba?? ni dai ai na gode Allah da ta dawo gida lafiya abu bai sameta a hanya ba balle hukuma su garkameni ko jikana, wai kawai ina farkawa daga bacci barawon da ya sace ni da asuba sai naga daki wayam babu mata babu dalilinta, ban kawo komai a rai ba ina ta jan carbi har kusan karfe tara, nace kai bari dai in sauka in duba ko kumallo take nema mana a kitchen, ina sauka naga gidan wayam babu ita babu isilinta, na duba inda takalmanmu suke naga ai babu nata sai nawo kwallin kwal kamar maye, da gudu na koma sama na taso wancan mutumi Aliyu shi ma dai ya fito muka yi ta bulayin neman yarinya a cikin gidan, banda kuka da rokon Allah ya taimakeni babu abinda nake a lkcn, daga karshe ya bada shawaran mu taho nan kilan ta dawo, shine fa na taho ko wanka banyi ba yanxu haka, abinda ban ta6a yi ba a Masar, gudun fitinarki ma gashi can yaki shigowa yana can xaune cikin mota, to yana da gaskiya mana tunda bai san ko yarinyar ta dawo ko bata dawo ba, daga ni har shi sai ki iya sa a garkame mu kadan da aikin ki" Umma ta kalli Huraira tace "Kira min Jiddah" Huraira ta tafi daki, a durkushe taga Jiddah ta daura kanta saman gado idonta lumshe, baccin ma gaba daya ba me dadi tayi ba banda mafarkan Abuturrab babu abinda take, ga ciwon ciki da ya matsa mata, Huraira tace "Lafiya Jiddah" Da sauri ta bude idonta sai kuma ta dago kanta daga saman gadon ta nuna mata cikinta alamar yana mata ciwo, Huraira tace "Subhanallah sannu kinji, xaki iya fitowa kuwa, Umma na kiranki" Jiddah ta daure ta mike ta dau hularta ta saka sannan ta fito parlor, wani kallo Hajja ta dinga mata daga sama har kasa, Jiddah ta kasa kallonta ta karaso parlon ta durkusa, a hankali tace "Ina kwana Umma" Umma tace "Lafiya lau, why did u leave without telling anyone?" Jiddah ta girgixa mata kai kawai bata ce komai ba, Umma tace "Ki bude baki kiyi min magana" a hankali tace "Umma cikina ke min ciwo" Hajja tace "Kaji sharri?? Dama ba gari muke jira ya waye a kai ki asibiti ba? in ni kina tunanin tsohuwar banxa ce don me baki sanar ma me gidan cewar xaki koma gidanku ba xaki tafi ki bar xuciyoyin mu a gantale da fargaba??" Umma tace "To ayi hakuri Hajja, Allah ya huci xuciyarki" Hajja tace "Aa bbu ruwana wllh, sai kinga tijaran da nayi ma matar gidan a kanta jiya, shine ni xata watsa min kasa a ido?" Umma da mitan ya fara isarta tace "Toh ke yanxu ya kike son ayi Hajja? Komawa gidan xa kiyi tare da ita yanxu?" Jiddah da taji gabanta yayi wani irin faduwa ta fashe da kuka ba tare da ta shirya ba tace "Wllh cikina ciwo yake min Umma" Hajja ta rike ha6a tana kallon Umma tace "In koma ina da ita? Matar da ta kashe mana baccin jiya duk a xaxxaune muka kwana a gidan kamar almajirai, aa tunda ta dawo gida lafiya Alhmdlhi, nima xuwa xanyi ya ajiyeni a gida ashe matar gidan yaji tayi daga jin mun xo, to ni ina na sani, sai yau da safe yake gaya min" Umma dai tace "To Allah ya kyauta, kiyi hakuri Hajja" Hajja ta juya ta nufi kofa tace "D'an ba kara, tunda dai ta dawo xan turo Aliyun ya shigo ya gaisheki mu san inda dare ya mana" Mikewa Jiddah tayi ta wuce daki kamar warce aka tsikara jin xancen Hajja na karshe, Umma ta bi ta da kallo, Hajja na fita kofar gida tana kallon Abuturrab dake xaune cikin motarsa tace "So tayi ta tona mana asiri Allah bai yi ba, gata can munafukar tana ciki, ka shiga kawai ka gaida uwarka muyi ta kanmu, mu dai ba ta dawo gidan lfya ba Alhmdlh" Abuturrab yace "Ke kin ganta a ciki?" Hajja tace "To da fa? Wai sai ta fashe da kukan munafurci daga Uwar tace mu koma tare, bata san nima ta sire min ba baxan sake xuwa da ita ko ina ba, har abada kuwa, jiya kaga abinda dai ta dinga mana cikin dare kamar me cikin wata tara" Abuturrab ya shafa kansa yace "To shigo mu tafi" Hajja tace "Aa rufa min asiri so kake Ramlah tayi dani idan mun tafi tace na hanaka shiga ka gaisheta?? Kaje ko minti daya ne ka gaisheta ka fito kawai" Bude motar Abuturrab yyi ya sauka, Hajja tace "Kayi maxa ina jiranka" Umma na xaune parlon tana ma Jiddah dake xaune kasa kusa da ita magana a kan me yasa xata bar gidan da sassafe, ita dai Jiddah bata ce komai, Abuturrab yyi sallama bakin kofa, sosai gabanta ya fadi tayi kasa da kanta kamar me neman allura a kasan, Shi ma tun da ya kalli inda take sau daya bai sake kallo ba, ya dai karaso parlon ya xauna saman kujera yace "Ina kwana Umma" Umma tace "Lafiya lau, an tashi lafiya" Yace "Alhmdlh, ya gida" Tace "Lafiya lau" Kamar yanda Jiddah taki dago kanta shi ma haka ya ki kallon inda take, Bayan few seconds yace "Hajja na jira na Umma" Umma tace "Toh Allah ya tsare" mikewa yayi yace mata sai anjima sannan ya nufi kofa, Jiddah dai taki dagowa ko da wasa, Umma sai kallonta take kamar dai tana son gano wani abu, bayan fitar Abuturrab tace "Me ya sameki jiya da daddare a can gidan?" A hankali Jiddah tace "Ciwon ciki nake yi?" Umma tace "Ikon Allah, amma da sauki yanxu?" Tace "Idan yayi min sauki sai ya fara kuma" Umma tace "Toh Allah ya sauwake bari anjima Ahmad ya xo sai ya baki magani ko kuma aje asibiti" Jiddah dai bata ce komai ba, Umma tace "Kin karya?" Girgixa mata kai tayi, Umma tace "To tafi ki karya" Mikewa tayi a hankali ta nufi kitchen Umma ta bi ta da kallo ganin duk tayi wani irin sanyi. Hajja na shigowa parlon Abba ganin Aunty da Ummi sai Aneesah a parlon ta dinga bin su da kallo tace "Wacece wannan kuma?" Lkci daya Aunty ta murtuke fuska, Ummi tace "Sannu da xuwa Hajja" Hajja tace "Yauwa me ke faruwa a nan din?" Abba dake xaune shi ma parlon yace "Sannu da xuwa" Hajja tace "Ba batun sannu da xuwa ba, xaman me ake a nan?" Dai dai nan Abuturrab ya shigo parlon da sallama, tun karfe tara Abba ya kirasa yana nemansa a gida, suna mota kuma yake sanar ma Hajja cewar Abba yace yaje, Kallo daya yayi ma Aneesah da ta sha lullubi da babban gyale wanda da alama Aunty ce ta 6ata, ya dauke kai ya xauna saman carpet yana kallon Abbansa yace "Ina kwana Abba?" Abba yace "Lafiya lau" Kallon Ummi yayi ya gaisheta, snn ya gaida Aunty da tayi masa banxa, Hajja dai na tsaye kansu kamar soja, Abba yace "Ga kujera Hajja" Hajja tace "Aa bar ni in tsaya abuna, mu da muka sa6a tsayuwa a Masar" Aunty na kallon Abba tace "Alhaji i think we can leave the sitting for now, may be in the evening" Abuturrab ya kalleta yace "Yau xan koma aiki in sha Allah" Wani shegen kallo Aunty tayi masa tana kallon Aneesah tace "Tashi mu je" Hajja tace "Ta tashi aje Ina? Ina ce k'aran jikana ta kawo ko? to wllh sai kun ga walakanci da tarban tsiyar da matar nan tayi mana ni da Jiddah, ni dai har hawaye sai da nayi a boye don tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin anyi haka ba a Masar, sannan gida dai in baku labari da muka shiga duk wari, wllh ta rubar masa gida, kitchen kuma dai ya fara wasu irin tsutsa, bandakin gidan duk sunyi gantsa kuka, to banda lalacewar yaran kasar nan daga nayi mata gyara sai ta kawo karata da na jikana har a wani xauna xa ayi meeting a kanmu?? Ehh lallai yau nake ganin lalacewa a Najeriya" Abba dai yyi shiru bai ce komai ba, haka Ummi da kanta ke kasa, Aunty sai tafarfasa xuciyarta yake tana kallon Hajja, Hajja ta ta6e baki tana gyara yafin gyalenta tace "Hatta abincin da xa mu ci sai da yaron nan ya fita ya samo mana, to ina girki xai yiwu a wnn axabbabben kitchen din duk wari, salon ma mu ci mu tsuge da xawo idan an girka, wllh da ido daya nayi bacci a gidan sbda datti da kazanta, to bari kuji ita yar rakiyar tawa ma da ciwon ciki ta kwana a gidan tsabar kazantar gidan kuma ni nasan hakan na da nasaba da ruwan da muka sha na gidan, yanxu haka tana can baiwar Allahn tana jinya gun uwar rikonta ni dai duk ni na ja mata bani da bakin magana, to idan ba rashin kunya ba shine har xata kwaso kafafuwarta kamar kara tace ta xo kawo kararmu, bayan duk hakurin da jikana ke yi da ita?? Lallai ma, ai ni da Masar har abada jikana na wannan halin, in sha Allahu sai na samar masa mata me tsafta irinsa warce xata dinga gyara masa gida" Abba na kallon Aunty da turanci yace "Su tashi su tafi kawai da Aneesah" Kamar jira take ta mike ta daga Aneesah suka fice daga parlon tana huci. Hajja ta kalli Abba ta ta6e baki sannan ta kalli Abuturrab da ya sunkuyar da kansa tace "Tashi mu je o, Allah ubangiji ya kawo maka karshen jarabawar nan da kake ciki" Daga haka ta nufi kofa abunta.... Bayan azahar Ahmad ya shigo gidan Umma, bayan sun gaisa da Umma yace "Su Maimoon sun tafi Islamiyya ne?" Umma tace "Ehh sun tafi Jiddah dai ce bata je ba, bata jin dadi" Yace "What's wrong with her?" Umma tace "Wai ciwon ciki take, dama jira nake ka xo" Yace "Wani irin ciwon ciki tace?" Umma tace "ka kai ta asibiti kawai, ai nima ba sani xanyi ba" Yace "To Allah ya sauwake" Umma tace "Ameen" yace "Tana daki ne?" Umma tace "Ehh bari Huraira ta kirata idan ba bacci take ba" Umma na fadin haka ta kirawo Huraira, Huraira ta tafi dakinsu Maimoon, kwance ta tadda Jiddah saman gado tayi shiru, Huraira tace "Ya jikin Jiddah?" Jiddah ta mike xaune tayi murmushi tace "Naji sauki" Huraira tace "Toh Allah ya kara lafiya, Umma na kiranki' Jiddah tace "Toh" Sannan ta sauka saman gadon, tun da safe bata sake jin ciwon cikin ba, amma gaba daya jikinta a sanyaye yake, hakan ne da Umma ta gani yasa tace ta xauna gida kawai ta xata duk ciwon cikin ne, Jiddah na fitowa parlor ta xauna kasa ta gaida Ahmad dake kallonta ya amsa da murmushi fuskarsa yace "Ya jikin?" Tace "Naji sauki" Umma tace "Cikin ya maki sauki?" Jiddah ta gyada mata kai tace "Ehh ya daina yanxu Umma" Umma tace "To sannu, Allah ya sauwake" Ta sunkuyar da kanta tace "Ameen" Ahmad yace "Why not ta dakatar da amfani da drugs da aka rubuta maku a hospital for the meantime Umma?" Umma tace "Kana tunanin shi ke sa mata ciwon?" Yace "Ta dai dau break na wani d'an lkci a gani" Umma tace "Toh shkkn" Yace "Xan siyo mata pain reliever yanxu" Umma dai sai kallon Jiddah take ganin yanayinta, Ahmad yace "Umma gobe kika ce xa a kai ta makarantar ko?" Umma ta kallesa tace "Ehh" Yace "Toh idan xan koma gida sai mu tafi tare da ita, idan ya so gobe da safe sai mu je makarantar" Umma tace "Daga nan din baxa ka iya xuwa ka dauketa ba?" Yace "Toh shkkn Allah ya kai mu" Umma ta kalli Jiddah tace "Tashi ki je ki ci abinci" Ba musu Jiddah ta mike ta wuce kitchen. Sai kusan la'asar Ahmad ya shirya xai koma gida, bayan yayi ma Umma sallama tace "Shkkn kawai ta dau kayanta kala daya ko biyu ku tafi can gidan din" Yace "Ohk toh" Umma ta tafi da kanta daki wajen Jiddah ta sanar mata xa su tafi gidan Ahmad tare, ta dau kayanta kala biyu, Jiddah bata mata musu ba tayi yanda Umma tace sannan ta fito parlor rike da jakarta. Huraira dake tunanin har sannan Jiddah bata jin dadi ne ta amsar mata jakar ta kai motar Ahmad, Ahmad yyi sallama da Umma, jiddah ma tayi mata sallama, Umma tace "A gaida Ramlah" daga nan suka fita gidan, Suna shiga motar Ahmad yaga missed calls din Abuturrab har uku a wayarsa da ya bari a cikin mota, Sai da ya tada motar yyi reverse sannan yayi dialing number Abuturrab din, yana dagawa Ahmad ya kai kunne yace "Ya aka yi?" Dariya Ahmad yyi yace "Ni fa wllh kana bani mamaki Captain, ga dai matarka ka bi ka takurani in maka prescription drug? Are u even okay?" Jiddah dake xaune gefensa cikin motar taji gabanta ya fadi jin sunan da ya ambato, Ahmad yace "Toh ka taho gida ka amsa, ina driving yanxu..." Daga haka ya katse wayar yana maida hankalinsa kan titi, sai da suka yi nisa yace "Kin ma san gidana kuwa Jiddah?" Ta kirkiri murmushi tace "Um na sani, mun je sau uku" Yace "Would u like to stay in my house ki dinga xuwa makaranta daga can?" Jiddah ta d'an buda ido ta kallesa, yace "Yea, sai ki xauna ke da Ramlah koh??" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you MG'S SKINCARE In akaji gangami labarin kidane,sun shahara sun tumbatsa sunkai sunwuce tunanin duk wani meson Adama dashi aharkar gyaranfata d walwalinta, Yar uwa haske ko qyalqyale kikeso kiyi Abu yaci tura? Kyan fuskarda ko yar uwarki mace kance dama dama kikeso? Kokuma ke kuraje d tabbuna suka lahanta mki fuska har ake ganinki d wani idon n daban, Nankarwace tayimiki zanen kura a kyakyawar fatarki? Kokumade Mai kikashafa be amshekiba yasa duk kika koma ruwa biyu Nan fari Nan baqi? To duk kuzo insha Allah kudai naku y qare gdan kukazo, Munkawo shahararrun kayangyaran jiki Sabulu, Man shafawa, Man fuska, Scrub, Cleanser, Glow oil, Dukdan qawarmaku d matsaltsalunku, Da 11k kachal zatasa kihaske kizama kalar madara qirar models, Set 11k Sabulu 3k Student package:7k Munakuma bayarwa in pieces duk afarashin mesauki.kayanmu bbu fariya ko tutiya angwada andawo,ankumayi farinciki d hkan,Kuna iya samummu d wadannan numbobin, WhatsApp, 08062991549 or 07046881166 or 07067210195 Call only 08064532391 Instagram: glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Idanba wadannan numbobinba to gaskiya b mg's bane, available in Kaduna and Kano only, thanks for always trusting us,our returning customers we really do appreciate wadanda sukeda burin Siya munamaku fatan alkhairi ubangiji ybaku yenda zakuyi,Allah Kuma yqaro mna dukiya me amfani ta hanyar halalinmu. Murmushi kawai Jiddah tayi bata ce komai ba, Ahmad bai kuma ce mata komai ba shi ma, suna isa wani babban pharmacy yayi parking yana kallonta yace "I am coming let me get u pain reliever, Umma tace kina ciwon ciki ko?" Ta gyada masa kai ya kashe motar ya sauka ya shiga cikin pharmacy din, ba a wani dau lkci sosai ba ya fito da ledan magani, ya shiga motar yana kallonta ya ajiye mata kusa da ita yace "Ko kina bukatar wani abun daban, akwai Supermarket a nan..." Ta girgixa kai tace "Aa bana bukatar komai" Yace "Ohk" sai da suka hau saman titi ta d'an kallesa amma bata ce komai ba, ganin haka yace "Say what is in ur mind Jiddah, be free with me and take me as ur elder brother" Ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Ni yanxu baxan iya xuwa in ga Baabarmu in gaisheta ba?" Da d'an mamaki yace "Baabarku? Me xaki yi mata idan kinje, ko kuma me xata maki ita?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Babu amfanin xuwa wajenta a yanxu dai Jiddah, idan kinyi hakuri wataran babu wanda xai hanaki xuwa gareta, when the rightful time comes da kanki ma xaki je ba sai wani ya kai ki ba kin ji?" Cikin sanyin murya tace "Toh, amma kuma akwai wata tsohuwa a layinmu ana ce mata Iyah, tana da kirki sosai, ko ita ma baxan iya xuwa in gaisheta ba?" Yace "Baki tunanin xata gaya ma Baabarku kin je?" Ta girgixa kai da sauri tace "Aa baxata fada ba, ai ita ba haka take ba, ita ce fa ke taimakona lokacin da nake gun babarmu, har abinci tana bani idan tana da shi" Yace "Toh yanxu kina son a kai ki can kenan?" Ta gyada masa kai a hankali, ya d'an yi shiru yana ci gaba da driving dinsa, kallon agogon wrist dinsa dake nuna karfe hudu da wani abu yayi, sannan yace "Kinsan me Jiddah?" Jiddah na kallonsa ta girgixa masa kai, yace "Ki bari ko gobe da daddare in kai ki, tunda kina gidana, i think it will be more safer..." Jiddah tace "Toh nagode" Yayi mata murmushi kawai. Suna isa gidansa yayi parking a space din parking sannan ya sauka motar ita ma ta sauka, tana biye da shi suka shiga gidan, Xaunawa tayi a parlor shi kuma ya wuce bedroom dinsa sanin Ramlah na can tana bacci, xai shiga dakin sai gata ta fito, ya d'an buda ido yace "Ashe ba bacci kike ba" Ta turo baki tace "Ina ice cream din?" Yace "Ohh kinga na mance wllh, I'm sorry anjima xan fita sai in siyo maki, fito ku gaisa da Jiddah" Ramlah tace "Da gaske?" Yace "Ehh" a tare suka dawo cikin parlon, Ramlah ta xaro ido tace "Lallai sis Jiddah ce yau a gidanmu, ashe xa ayi ruwa da kankara" Jiddah tayi murmushi tace "To ai ina xuwa" Ramlah ta karaso ta xauna kusa da ita tace "Aa sau biyu ina ga kika taba xuwa, ina fa sane, to ya su Umma?" Jiddah na murmushi tace "Lafiya lau, ya jiki?" Ramlah tace "Naji sauki Alhmdlh" mikewa tayi ta dau jakar Jiddah tace "Mu je ciki to" Jiddah ta mike ta bi bayanta, Ramlah ta kai ta dakin visitors, sosai Ramlah taji dadin xuwa Jiddah gidanta, Ramlah tace "Gashi ni banyi girki ba wllh, ko in dafa maki indomie kafin a daura dinner?" Jiddah tace "Daga gida fa muke, ai na ci abinci" Ramlah tace "Toh bari in kawo maki ruwa" Bata jira cewar Jiddah ba ta fita dakin, sai da Ramlah ta daura ruwan shinkafa a gas snn ta dau tray ta daura Chivita drink da ruwan gora sai glass cup ta dawo daki ta ajiye tana kallon Jiddah tace "To ga ruwa ki sha sis Jiddah" Jiddah ta d'an yi murmushi tana kallon hancinta dake shige da na Abuturrab, har idanuwansu iri daya ne, dama kuma duk a cikinsu ita tafi kama da shi, Ramlah ta xauna tana ta jan ta da hira, tun Jiddah na shiru shiru har dai ta fara biye mata, lkci daya Ramlah tace "Ohh na manta na daura ruwan shinkafa a gas, bari in xuba shinkafar in dawo" Jiddah tace "Toh bari in wanke in xuba maki" Ramlah ta nufi kofa da sauri tace "Aa wllh... Ai ba wani aiki bane" Daga haka ta fita, xaune ta tadda Abuturrab a parlor da Ahmad, Ta d'an buda ido sai kuma ta washe baki tace "Yaushe ka xo yaya?" Karasawa tayi ta duka gefensa tace "Welcome Yaya, ina yini?" Ya kalleta yace "Lafiya lau, ya gida?" Tace "Alhmdlh, ya aiki?" Yace "Fine Alhmdlh" mikewa tayi ta wuce kitchen, Ahmad dake shafa beard dinsa yana kallon Abuturrab yace "ina jin ka great Captain" Abuturrab yace "Kana jina na me wai, kai fa idan kaga mutum na neman abu a wajen ka ka dingi walakantasa kenan" a takaice Ahmad yace "Toh ka tafi asibiti kawai" Abuturrab ya dinga kallonsa, Ahmad yace "Yes, nasan kana da mata baxan rubuta maka wannan maganin da kace ba, ko dai Hygiene din ne bai kai yanda kayi expecting ba? Abu d'an sauki tunda kana da wadata sai ka kara aure kawai" Da dariya Ahmad ya kare maganar, Abuturrab dai ya kasa ce masa komai, Jiddah ce ta fito parlon rike da tray din lemon da Ramlah ta kai mata don xuwa kitchen ta taimaka ma Ramlah da girkin da tace xata yi, Tsaye tayi bakin corridor din dakunan ganin Abuturrab a parlon kafin ya ganta ta juya da sauri har tana tuntube ta koma ciki ta shige daki ta kulle kofar gabanta na faduwa sosai, Abuturrab ya kalli direction din don rufe kofa kawai yaji, can ya kalli Ahmad yace "Who is there?" Ahmad yace "Bakuwa muka yi" Abuturrab yace "Ohk" Ramlah ta fito kitchen ta ajiye masa ruwa da drink tace "Amma yaya ba yau xaka koma kano ba ko, naga yamma yayi" yace "Gobe da safe in sha Allah" Yana fadin haka ya dau bottle water daya ya bude ya sha ya mayar ya ajiye sannan ya mike yace "Sai anjima...." Ahmad dai sai murmushi yake yana kallonsa, Ramlah tace "Yaya ka tsaya ka ci abinci mana pls..." Yace "What are u cooking?" Tace "Shinkafa da miya ae bai da wahala" Yace "Idan naje can gida xan ci, yanxu gida xan wuce" Daga haka yayi ma Ahmad sae da safe ba tare da ya kallesa ba ya nufi kofa ya fita. Gidansu ya tafi, direct ya tafi bangaren Umminsa, fitowa tayi daga bedroom jin an bude kofar parlor, ganin shi ne ta koma dakin, ya bi ta har can, xaunawa yyi gefen gado sannan ya gaisheta, ta amsa tana kallonsa, bai kuma ce mata komai ba tace "Me ya hadaka da matarka?" Ya kalleta yace "Ummi ita da Hajja ce, ni ban mata komai ba wllh" Tace "Why did u create room for that, me yasa baka dakatar da Hajjar ba?" Yace "Sanda suka yi ma ni bana gidan, and na bata hakuri but she didn't listen to me tayi tafiyarta kawai" Ummi dai tayi shiru tana kallonsa, can tace "Are you okay?" Daga kai yayi ya kalleta sai kuma yayi murmushi yace "Did u notice anything mum?" Tace "Are u answering my question with a question?" A hankali yace "Kawai ki taya ni da addu'a Ummi" tace "Me ke faruwa?" Ya girgixa mata kai yace "Ba komai addu'a kawai nake bukata" Tace "Saboda ni ai bani da matsayin da xaka gaya min matsalarka ko?" Ya kalleta a hankali yace "Ko daya Ummi, ni kaina ban san me ke damuna bane" Tace "Toh Allah ya yaye maka" Yace "Ameen" Yace "Ummi in a month time xamu fita waje fa..." Tace "Xuwa yin me?" Yace "Aa wani babban mutum xa mu yi piloting" Ummi tace "Toh Allah ya kai mu, sai ku dawo yaushe?" Yace "Ban sani ba dai, sai yanda suka ce" Ummi tace "To Allah ya tabbatar da alkhairi" Yace "Ameen" tace "Yanxu ka tashi kaje ka ba matarka hakuri ka dauketa ku tafi gida tare, ba sai an sake wani xaman ba" Shiru yyi, Ummi dai na lura da shi, can yyi kasa da murya yace "Ummi Aneesah bata son xaman lafiya tare da ni, I don't know why she changed all of a sudden from who I knew her to be, kamar ana xugata kullum, kinga bata mutunta ni bata kunyar gaya min ko wani magana ya xo bakinta, sannan i wish u can come one day ki ga yanda ta mayar min da gida, kawai fa sai dai tayi wanka ta fesa turare abinda ta iya kenan, tsaftace muhalli Zero, girki Zero, ibada Zero, kullum sai nayi fama da ita a kan sallah, I'm so tired and fed up Mum, ko wata biyu fa ba ayi ba, har xullumin dawowa weekend nake wllh Ummi" Ummi da tayi shiru tana kallonsa taji tausayin d'an nata amma taki nunawa, can tace "Toh me yasa baxa ka daukar mata mai aiki ba?" Da sauri ya kalli Ummi yace "House help kuma Ummi? Warce ta xauna kafin ita a gidan duk da karancin shekarunta da rashin wayewarta ai ban daukar mata mai aiki ba, kuma komai na gidan ita ke yi, sannan ni ban ta6a dawowa weekend naga ba dai dai ba" Ummi dake kallonsa kasa kasa tace "Wacece ta xauna kafin ita?" Shiru yayi bai ce komai ba, Ummi tace "Wai Jiddah kake nufi?" ya daga kai yana kallon Ummi amma bai ce komai ba, Ummi ta tabe baki tace "Ni a iya sanina warce ta xauna kafin ita ai ba matsayin mata ka dauketa ba a lokacin ko? Wannan kuma matarka ce ta sunna...." Shi dai bai ce komai ba, Ummi ta ci gaba tace "Don haka sai kayi hakuri da duk abinda ka gani, da yanda ka gani, na farko dai ba wani ya nemo maka yarinyar nan yace ka nemeta ka aura ba..." Ya marairaice mata yace "Ummi to ai ni da muka hadu da ita da farko ba wai soyayya muke ba, kuma ni ban ta6a tunanin xan ma aureta ba, kawai dai ta kan kirani mu gaisa ne time to time, sai kuma WhatsApp chat, a airport din Abuja muka hadu taje gun uncle dinta, ni kuma mun sauke jirgi, and she requested my digit na bata kawai don ban iya walakanci ba, sai kuma coincidentally na dawo wani weekend na ganta a gidan nan ta xo gun Aunty da aunt dinta ashe Mum dinta close frnd din Aunty ce" Ummi dake ta kallonsa tace "Sai aka yi yaya? Sai aka ce ka so ta dole har ka aureta?" Yace "Aa Ummi but Aunty ce ai..." Sai kuma yayi shiru, Ummi ta tabe baki tace "Kaga Aliyu rabani da wannan labarin da na sani, yanxu dai kawai kayi hakuri ka nema mata house help, da xata dinga tsaftace maka gidan ka, sai kuma ka ci gaba da hakuri da sauran halayen nata tunda dai auren soyayya ku ka yi ba auren kiyayya ba" Bai iya yace komai ba, Ummi dai sai kallonsa take, amma can kasan xuciyarta tausayinsa take, she understands what he is going through, barin shi da yayi detesting kazanta with passion, ita har ta mance rabon da ya shigo dakinta balle har ya dade haka yana xance da ita kai tsaye, Ya d'an ja tsaki underneath his breathe yace "Karamar yarinya ma da ta kusa doubling age dinta warce ta tashi a ghetto bata irin abinda take yi na kazanta wllh, tun daga balcony nake jiyo kamshi lkcn da yarinyar ke gidan idan na dawo gida, for once ban ta6a shiga kitchen naga dirty utensils ko daya ba, ni har kunyar wani nawa nake ya xo gidana yanxu, dama a garin nake sai in dinga gyarawa ni kullum, kawai ita abinda ta sani sai tayi wanka ta fesa turare ta xauna tana danna waya, sai tara kawaye a gida" Ummi tace "Toh wai ita kuma wannan karamar yarinyar da kake sa wa a baki kake comparing da matarka meye hadinka da ita ne, why don't u face ur life ka daina mentioning dinta a lamarin ka, did she have anything to do with u again xaka sa ta a bakin duniya" Ya kalli Ummi amma bai ce komai ba, Ummi tace "Ni ka tashi kaje ka same matarka ka bata hakuri ka dauketa ku tafi gida, Allah ya ci gaba da daidaita ku, ba ruwana da matsalar cikin gidanku, it's something u should have known before marrying her" Abuturrab yace "But how mum, kullum fa fes fes xaka ganta a titi, waye xai san xata yi haka?" Ummi tace "Allah ya kyauta" Ya kwanta saman gadonta yace "Ni sai na ci abinci Ummi, kuma ba yanxu xan tafi ba sai after isha, kullum fa sai nayi takeaway din abinci bata girki" Sharesa Ummi tayi ta mike ta nufi kofa ta fita, Aisha ce ta kawo masa abinci dakin, tana ajiyewa ta juya ta fita, shi kam ko kallonta bai yi ba, can ya mike ya sauka kasa ya dau plate ya fara dibar abincin. Aunty ce tsaye bedroom dinta tare da Aneesah dake xaune gefen gado tana kallonta, bata dade da dawowa gidan ba tun fitar da tayi bayan Hajja ta tarwatsa meeting din daxu, Aunty ta xuge jakarta bayan ta dau abinda xata dauka a ciki sannan ta dawo kusa da Aneesah ta xauna ta ajiye mata kwalaban turarruka uku a gabanta tace "kinga wannan, sai bayan mun koma asibiti ko xuwa gobe sun kara tabbatar maki babu wata matsala sannan bayan kin koma gida sai kiyi amfani da su" Aneesah tace "Aa kawai gwara ayi sabon dinkin Aunty, ni ina ji a jikina ba dai dai nake ba" Da mamaki Aunty tace "Kamar yaya?" Aneesah tace "Ni dai kawai ayi hakan, ko nawa ne xan biya ai" Aunty ta tabe baki tace "Toh shkkn, amma wllh Aliyu yayi mugun raina maki wayo, sannan ni banga laifinsa ba kece babbar wawuyar da kika yarda wai yana da matsala, a gidan ubanwa yake da matsalar mutumin da har gidansa kin sha xuwa ki kwana? Ko ke duk xuwan da kike gidansa a Abuja kin ga alamar yana da matsala?" Aneesah ta tabe baki tace "Ban ta6a ganin haka ba wllh, kawai shi dai baxai yi intercourse ba sbda gudun sa6on Allah amma ba don bashi da lafiya ba ko wani abu, amma babu abinda baya min ai, ce min yayi of recent ya samu matsalar" Aunty tace "Wllh ni ban yarda da kanwar uwar nan tasa ba don ita ma waye bai san tana shige shige ba kilan taje ta hango aikinmu ne tasa aka lalata, shine yake ta maki hanya hanya..." Aneesah tace "Toh ai da kin tambaya inda kika je daxu" Aunty tace "Wllh na manta shaff ban tambayi mutumin ba, amma akwai wani da xan kira anjima a benue, xai sanar da ni komai, yanxu kuma sai ki kirgo dubu talatin na turaren nan ki bada" Aneesah tace "Ina na gansu Aunty, har yau fa nace maki kudin nan da kika ce in tambayesa sai min yawo da hankali yake, yace yau yace gobe" Aunty tace "Rabu da shi don ubansa, xa muyi maganinsa nan ba da dadewa ba, muna nan dake sai account dinsa ya dawo hannunki gaba daya" Kwankwasa kofar dakin aka yi, Aunty ta jawo pillow ta ture kananun kwalaban turaren a karkashi da sauri, Aka bude kofar Abuturrab ya shigo da sallama kansa a kasa, Hade rai Aunty tayi ta mike ta dau Hijab dinta ta saka ta shimfida darduma ta hau sallahn isha, Aneesah dai sai wani cika take tana batsewa tana danna waya, ya ja stool ya xauna ya fiddo nasa wayar yana dannawa, yana ta xaune har Aunty ta idar da sallah, sannan ya kalleta yace "Ina yini Aunty" a takaice Aunty tace "Lafiya lau, sai yanxu ka ga damar shigowa bayan ina ganin sanda ka shigo gidan tun kafin magrib?" Yana kallonta yace "Dakin Ummi nake ai" Aunty tace "Toh yayi kyau, ai da baka fito ba ka dauwama a can din" Shi dai bai ce mata komai ba, ta dau carbinta tana ja, bayan few seconds yace "Dama xuwa nayi in baku hakuri Aunty a kan abinda ya faru, ni bana nan lkcn da Aneesah suka samu matsala da Hajja, ban ma san me ya faru ba har yanxu, na kuma bata hakuri tun a daren jiyan amma taki saurarata tayi wucewarta" Aneesah ta katse sa a fusace tace "Wllh karya ne Aunty, da bakinsa ya umarce ni da in tafi" Kallonta Abuturrab ya dinga yi yace "Ni nake maki karya?" Tace "Toh tunda baka ji kunyar yin karyan ba nice xan ji kunyar karyata ka Aliyu" Aunty na kallon Abuturrab tace "Ni tambayar da xan fara yi maka a nan shine me wancan dabbar taje yi gidan ka tare da Hajja?" Da mamaki yace "Dabba kuma, ai Allah ma bai ce a siffanta mutum da dabba ba Aunty, dabba fa kika ce" Aunty tace "Ohh ni xaka ma wa'axi? To nace mata dabbar sai kayi yanda xaka yi yanxu, kanwar uwarka ce ita din ko ta ubanka?? Ko uban meye hadinka da ita xaka ce kar in kirata da dabba? Ka bani amsar tambayata uban me ya kaita gidanka Aliyu?" Cikin tsawa ta kare maganar, Ya sauke idonsa kasa yace "Nima ganinta kawai nayi tare da Hajja i don't know how" Aunty ta mike tana tafe hannu tace "Toh tayi xuwan farko tayi na karshe, duk ranan da kauyancinta da gidadancinta ya sake kadata ta bi wani ma ba Hajja ba xuwa gidanka dama nace tana shigowa Aneesah ta kirani, xan kuma dau makullin mota in fita inje gidan sai kuma nayi mata abinda har ta koma ga Allah baxata manta ba don ubanta, duk ranan da ta sake gigin xuwa gidan Aneesah wllh wllh sai na lahira ya fi ta jin dadi, sai na walakantata walakanci mafi muni, sai na mata toxarcin da har jikokinta sai ta ba labari wllh" Abuturrab kallon Aunty kawai yake ko kiftawa babu, can dai ya dauke kansa, Cikin bacin rai Aunty ta ci gaba tana cewa "Idan ba kwadayi da jakanci ba uban me xai sa tayi sha'awar komawa gidan da aka saketa ta fito, me xai kai ta?? To wllh ta kiyayeni bani da kyau, idan ta ci gaba da shiga gonata sai na sa ta bi duniya ni ba imani ne dani ba al-qur'an, su Ramlah yan iyayi da suka ga xa su iya riketa su ci gaba da riketa din, amma duk ranan da gidadancinta ya fada mata karya ya kaita gidanka to kuwa ranan xata yi da ta sanin haifota da matsiyatan iyayenta suka yi" mikewa Abuturrab yyi ya nufi kofa Aunty tace "Gidan ubanwa xaka ina magana Aliyu?? Aliyu ba da kai nake ba??" bude kofar yayi ya fice ya bar masu a bude ko kullewa bai yi ba, Aunty ta bi sa da kallo baki bude har ya fita kofar parlor gaba daya. Abuturrab na fita bangaren Ummi ya koma, Ummi na kallonsa tace "Kaje ka bata hakurin?" Kasa ce mata komai yayi saboda yanda xuciyarsa ke tafarfasa, Ummi ta lura da yanayinsa ta ci gaba da aikinta da take yi kawai, bayan kusan minti uku yace "Ummi ki kira Aneesah kice ta sameni a mota, idan kuwa bata fito ba xan yi wucewata" Ummi tace "Ka kira uwar dakin taka ka gaya mata mana, ba ita tafi kusa da Aneesar ba, sannan ina ce ma a bangarenta take" Abuturrab ya mike yace "Next weekend idan na dawo xan xo in dauketa in sha Allah, sai da safe" daga haka ya nufi kofa Ummi tace "Aliyu" tsayawa yayi, sai kuma ya juyo tace "Tell me what happened" Yace "Ummi kawai ni bana son abinda Aunty take yi ina raga mata ne kawai saboda Abba but idan ta ci gaba da shiga gonata i can go to d extent i am not suppose to, she is getting me pissed off" Ummi ta rike ha6a tana kallonsa da mamaki a ranta kuwa cewa tayi yau kuma?? Can ta d'an yi murmushi tace "Toh me ya hadaka da uwar dakin taka, dama ana jin kanku ashe" Abuturrab yace "She should just stay away from my personal life nd issues, that's all, xan jira a mota ki kira ki gaya masu idan kuma bata fito ba wucewata xanyi, sai da safe" Daga haka ya fice daga dakin Ummi ta bi sa da kallo, daukar wayarta tayi ta shiga kiran Aunty, Aunty na dagawa tace "Hafsah ki turo min Aneesah" Aunty ta wani kyabe baki tace "Aneesah kuma?" Ummi tayi shiru bata ce komai ba, Can Aunty tace "Toh dama sallah take bari ta idar" Ummi ta katse wayarta, sai bayan minti shidda Aneesah ta shigo parlon Ummi ta xauna saman kujera ta gaida Ummi, Ummi ta amsa tace "Ki je ki saka hijab dinki ki dau jakarki mijinki na jiranki a mota, sai kuma ayi ta hakuri, shi dama xaman aure d'an hakuri ne, kowa hakuri yake, ke kuma sai ki gyara duk abinda baya so, shima xai gyara in sha Allah, Hajja kuma ba lallai xaki sake ganinta a gidan ba ma, kiyi hakuri ki bi mijinki ku tafi kin ji" Aneesah tayi kasa da kanta, bayan wani d'an lokaci tace "Toh" sannan ta mike ta nufi kofa, Ummi ta bi ta da kallo har ta fita, tana komawa ta sanar ma Aunty yanda suka yi da Ummi tana tabe baki, Aunty ta ja wani dogon tsaki tace "Toh baxa ki je ba wllh, ita a wa xata tsomo baki cikin lamarin nan? Ina ruwanta! A cikin kayan miya wacece ita a lamarin Aliyu??" Aneesah dai sai ta6e baki take, can tace "Kinsan me Aunty tunda har kirana tayi ta min magana ki bari kawai inje kar ta saka ni a baki" Aunty tace "Ta saka 'ya yanta a baki dai ba ke ba wlh, kamar tana wani tabuka abun kirki a kan lamarin Aliyun da xata wani tsomo baki a wannan case din, ta ma ji da mugun abinda ke cinta kullum a xuciya mana da shiru shirun da take na algungumanci" Aneesah ta mike tace "Ko kayana ma baxan dauka ba Aunty xan dai tafi da turarrukan cikin hand bag" Aunty tace "Toh ya xancen xuwa asibitin gobe, ni fa dalilin da yasa nace baxa ki tafi yau din ba kenan" Aneesah tace "Sai in taho idan ya koma aiki gobe da safe, nasan da sassafe xai wuce kano ai, yawanci yanxu haka yake yi, ni bana son wancan matar tace nayi disrespecting dinta ne amma da sai in tsaya" Aunty ta ja tsaki ta xauna gefen gado tace "Dama goben ki xo da wuri, Kinga dai dai kenan kafin ya dawo wani weekend din anyi duk abinda xa ayi an wuce wajen" Aneesah ta saka hijab dinta ta xuba duk turarrukan a jaka sannan tayi ma Aunty sai da safe ta fita. Har suka isa gida Abuturrab bai ce ma Aneesah komai ba ita ma haka, banda danna wayarta babu abinda take, ta sauka motar ta bi bayansa xuwa cikin gidan, xaunawa parlor yyi yana kara regretting furnitures da aka xuba ma Aneesah a bangarensa, ko kallonsa bata yi ba ta haye sama ta wuce bangaren nasa, kwafa yyi ya mike ya haura sama ya bude dakin da su Hajja suka sauka ya shiga ciki, tsaf Hajja ta gyara dakin kafin su fita neman jiddah daxu da safe, don cewa tayi babu inda xata tafi bata gyara dakin ba haka kawai ta shiga hakkin tsafta, har bandaki sai da ta wanke, banda kamshi kuma babu abinda dakin yake, cire kayansa yayi ya shiga bandaki dake cikin dakin, bayan yayi wanka ya jima xaune dakin kafin ya sauka downstairs ya shiga kitchen, har sannan kitchen din fess tun gyaran da Jiddah tayi masa, ya dinga bin kitchen din da kallo kafin ya dau mug ya tafasa ruwan xafi ya hada shayi ya fito, a parlor ya sha shayin, yana ta xaune har kusan sha daya kafin ya mike ya wuce sama, babu yanda ya iya ya nufi bangarensa don daukar jallabiyarsa, Aneesah ce durkushe dakin hannunta rike da karamin towel tana goge turarrukan da suka fashe da sauri, har wani rawa hannunta yake, jakarta ta dauka xata ciro charger bata san a bude yake ba duk kayan ciki suka jirkice ciki har da turarrukan da aunty ta bata daxu wanda nan take biyu suka fashe wani kamshi ya gauraye dakin, tana ganinsa ta mike da sauri ta wuce bandaki da towel din, ya bi ta da kallo.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Makulli Aneesah ta sa a kofar bandakin bayan ta shiga gabanta na faduwa, ta ajiye towel din a karamin bucket ta tara ruwa ta dau sabulu ta fara wanke hannunta ba ji ba gani... Karasawa Abuturrab yyi yana jan kafa ya xauna gefen gado, har bayan minti sha biyar Aneesah bata fito daga toilet din ba, mikewa yyi ya dau jallabiyarsa ya fita dakin, sai da Aneesah ta tabbatar hannunta baya kamshin turaren sannan ta bude kofar bayin a hankali tana leko dakin, ganin baya nan ta sauke wani ajiyar xuciya ta fito, dama kayan bacci ne jikinta ta dau wayarta tayi plugging sannan ta kashe wutan dakin tayi kwanciyarta.... Har karfe daya saura Abuturrab bai yi bacci ba yana dai kwance da abinda ya damesa, idan ya juya ta daya side din gadon sae ya sake komawa daya side din, lkci daya ya mike xaune ya dafe kansa, sae kuma ya sauka saman gadon ya bude kofa ya fita ya sauka downstairs ya wuce kitchen ya jona ruwa a kettle, yana ta tsaye yana kallon kettle din sae kawai ya kashe socket din ya wuce sama, bangarensa ya nufa bayan ya shiga parlon ya karasa ya bude bedroom dinsa, hannu ya kai jikin bango ya kunna switch din dakin, bacci take hankali kwance ya kashe switch din ya karasa gun gadon ya hau, cikin bacci Aneesah taji kamar hannu a jikinta ta bude ido a hankali, lkci daya ta mike tace "Meye haka Captain?" Xaro ido tayi tana kokarin turasa ganin abinda yake shirin yi tace "Wai meye ne Captain, what is this u are doing" Rungumeta yayi jikinsa underneath his breathe yace "I need you today...." Sosai gabanta ya fadi ta fara turasa da duk karfinta tana cewa "You need me when i am on my period Captain?" Gani tayi kamar yana son confirming din abinda ta fada, bata san lkcn da ta fashe masa da kuka ba tana turjewa tace "Don Allah ka bari captain, meye xaka wani taho min kamar wata akuya bayan ni ban...." Bai bata privilege din ci gaba da magana ba, da farko gani take kamar xata iya kwatar kanta gunsa amma ya gwada mata ba karfinsu daya ba, hakan yasa ta fara masa magiya tana basa hakuri hankali tashe tana ce masa she is not in d mood amma kamar bai ma jin abinda take cewa, Aneesah bata ta6a shiga tashin hankali da firgicin da ta shiga a lkcn ba, banda rawa babu abinda jikinta yake tana hadasa da Allah ya bari, cikin not less than 10 mins komai ya faru... Tunda ya koma gefenta take satan kallonsa tana shessheka tana kukan tsoro, ga xuciyarta da take ji kamar xai fado don bugawa, gashi ita ba ganin fuskarsa take ba balle taga expression dinsa, Ita dai har ta gaji da satan kallonsa tana kuka ganin kamar ma bacci yake don ko motsawa bai yi ba balle ya kalli inda take, ta lallaba ta matsa kusa da shi xata ta6asa, sauka taga yayi daga saman gadon tun kan ta ta6asa ya nufi kofa, ta bi sa da kallo gabanta na ci gaba da bugawa sai da ya fita ta fashe da kukan gaske na tashin hankali... Abuturrab na komawa dakin da ya fito ya sa makulli ya shiga bandaki da sauri jin cikinsa ya hautsine.... Har kusan asuba Abuturrab bai yi bacci ba duk da sallah da ya dau lkci yana yi, after subhi prayer yana xaune parlor deeply in thought, sai kuma ya dau wayarsa yayi dialing number Ahmad, Ahmad ya shigo daki kenan dawowarsa daga masallaci ya nufi wayarsa da mamakin wanda ke kiransa by this time, ganin Abuturrab ne ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren Abuturrab yace "Good morning" Ahmad yace "Morning..." Abuturrab ya d'an shafa kansa yace "Dama ina son maka tambaya ne" Ahmad yace "Alright i am all ears" Abuturrab yace "I want to know more about Virginity, what it is, and how it is" Buda ido Ahmad yayi sosai yace "Tohhh" sai kuma ya kalli Ramlah dake xaune saman darduma, kofa ya nufa yace "Ban gane tambayar ka ba" Abuturrab yace "Meye baka gane ba a ciki?" Ahmad na fitowa parlor ya nemi kujera ya xauna, Abuturrab yace "I'm serious Ahmad, ka bani amsar tambayata don Allah" Ahmad yace "No ina mamakin hadin Pilot da tambayar ne... But anyway virginity da Hausa shi ake ce ma budurci, kuma idan aka ce Virgin ana nufin wanda bai ta6a intercourse ba, weather a male or a female..." Abuturrab yace "To ya ake gane someone that is a virgin?" Ahmad yace "Mace ko namiji?" Abuturrab yace "Both" Murmushi Ahmad yyi yace "Ita mace akwai wani thin membrane lining da ake kira da hymen a jikinta, and it will seem a bit difficult to penetrate in her, don dole sai anyi breaking hymen din, and in some cases they will be shedding of a little blood, mind u in some cases nace, wasu matan kuma ba sai ta hanyar intercourse kadai hymen dinsu ke breaking ba, d'aga abu me karfi, tsalle tsalle, hawan bishiya ko keke, and many stuffs like that, yana sa suyi loosing hymen dinsu, but duk da haka ba wai xa a ji su kamar sun ta6a samun affairs bane idan an kusance su, don't quote me wrong... sae dai kawai baxa su yi shedding blood din nan ba, infact masu hymen din ma ba ko wacce ne ke fitar da jini ba...." Katse sa Abuturrab yayi yace "Amma kuma ya ake gane warce ta sa6a sex da warce bata ta6a ba?" Ahmad yace "That's so easy, warce bata ta6a ba u neva find it easy to penetrate in, they are alot of struggles, and u ur self will know u just need to be extra gentle on her...." Katse sa Abuturrab yyi yace "Alright thank you, sai anjima" Ahmad yace "But why all this questions?" Abuturrab yace "Karin ilimi" D'an murmushi Ahmad yyi yace "Ohk that's great" Abuturrab yace "Sai anjima" daga haka ya katse wayar, ya jefar a gefensa ya jinginar da kansa da kujera. Sae kusan karfe shidda ya tashi ya wuce dakin da ya kwana yyi wanka, xaune yyi gefen gado thinking of how to get his cloth from his room without seeing Aneesah, ganin lkci na ta wucewa kuma driving xae yi xuwa kano ya mike ya wuce can bangarensa kawai, Aneesah na kwance kan gado ta dunkunkune cikin bargo tunani iri iri a ranta, bata san ya encounter dinta da Abuturrab xai kasance ba yau, ko wani hukuncin xai dauka a kanta oho, to amma taya ma xai gane ita ba virgin bace bayan tana da tabbacin bai ta6a sex ba balle ace yayi da wata har ya banbance, sannan ma duk da rashin virginity din nata sai da taji axabarsa, kenan dai a matsen take, kuma ba lallai ya ma gane ba virgin bace ita, ita dai kadai take ta tunani kala kala, kana ganinta kasan she is so tense and disturb, duk irin burin da ta ci na yanda haduwarta da shi xai kasance ya wargaje, ko armashi abun babu banda axaba, tsoro da tashin hankalin me xai biyo baya, to amma duk da haka ita tasan tana da taste dinta kamar yanda ake yawan gaya mata, shi dai kawai ba ya gamsu ba ina ruwansa da yanda ya sameta, kilan ma bai gane komai ba ita ce ke ta damun kanta, ta ina xai wani san virgin da warce ba virgin ba abinda bai ta6a yi ba, Abuturrab bai ko kalli saman gadon da take ba ya wuce gun kayansa, ta bisa da ido tana tunanin abinda ma xata ce masa, lkci daya ta fara shesshekan kuka, ya dau kayansa da jakar laptop dinsa ba tare da ya kalleta ba still, ganin xai fita cikin rawar murya tace "Naka tukuicin kenan after deflowering ur wife Captain?" Tsayawa yyi ya juya ya kalleta yace "Did u say deflower?" Shiru tayi gabanta na mugun bugawa tana kallonsa daga kwancen da take kamar er mage, yayi wani murmushi yace "I wished so Aneesah, but my trust got betrayed by u, i regret doing what i did yesterday...." Cike da karfin hali ta mike xaune ta dake tace "Ur trust got betrayed?? How Captain?? Wannan wani irin magana ne?" Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka ta girgixa kai tace "Amma ka bani mamaki, yanxu so kake kace min maxa nake bi ko me?? Dama ashe baka fi kowa sanin halina ba Captain? Bayan kai ka ga alamar akwai wani wanda nake kulawa har muka yi aure?" Sai kuma ta kara rushewa da matsanancin kuka tace "Tunda nake ban ta6a zina da wani d'a namiji ba Allah shaida, idan ina yi kai ma da ka sani ai don irin wannan abun baxai boyu ba, bani da wanda nake kulawa da ya wuce kai, me na maka xaka saka min da haka a ranan da ka kusance ni..." Abuturrab bai ce mata komai ba ya juya ya fice daga dakin ta bi sa da kallo tana hadiye abu da kyar. Bayan ya shirya ko sallama bai mata ba ya fice daga gidan cikin motarsa, yana driving ya kara dialing number Ahmad, bayan Ahmad ya daga yace "Ahmad i still have more questions" Ahmad yace "Alright go on" Abuturrab yace "Kace not everyone ke shedding blood due to reasons u listed.... haka ko?" Ahmad yace "Yes" Abuturrab yace "But how about if u just find ur self in without any stress, me hakan ke nufi, or ana samun irin wannan cases din gun warce bata ta6a sex ba?" Ahmad yace "Noo!! if u should go in freely, to ko ma wacece ta ta6a sex wllh, continuously ma kuwa, and probably for long take abunta shi sa ma kayi noticing hakan lkci daya...." Abuturrab dai yayi shiru yana sauraronsa, Ahmad yace "And let me tell u something, in dai mace ta sa6a sex before marriage to memory din wanda ta sa6a da shi din will remain in her brain, da kyar ta iya rabuwa da shi duk da fa ga mijinta, yawancinsu basa iya tsayawa a matrimonial home dinsu without following men outside, it's just like a curse, ko da sun dau vow din repenting to ina gaya maka na yan shekaru ne... xa su koma idan ba Allah ne ya so su da Rahama ba" Shi dai Abuturrab bai ce komai ba, Ahmad yace "Are u okay now?" Abuturrab yace "Sure nagode, i am on my way to kano, thank you... Sai anjima" Ahmad yace "Alright safe trip" Katse wayar yayi ya ci gaba da tukinsa. Tun da Aneesah taji fitar motarsa a gidan ta hau kiran Aunty, Aunty na dagawa ta fashe da kuka tace "Aunty na shiga uku..." Aunty dake kwance kan gadonta ta mike xaune da sauri tace "Me ya faru?" Cikin kuka tace "Wllh kawai daren jiya Aliyu ya far min, duk yanda nayi kokarin stopping dinsa hakan bai yiwu ba har sae da yayi" Aunty ta bude baki tace "Yayi?? To sai aka yi yaya ynxu?" Tana kuka tace "Tun jiyan ya ki kulani bai ma kwana dakin ba, sae yau da safe ya xo daukan kaya yake ce min i betrayed his trust, kinga wllh ynxu ma haka ya tafi kano ko sallama bai min ba" Aunty ta saki salati tace "To garin yaya hakan ya faru, garin yaya kika yarda kinsan halin da kike ciki Aneesah?" Kuka kawai take tace "Wllh he forced him self in me Aunty, nayi kokarin preventing hakan amma ni ba karfinmu daya ba" Aunty tace "Tabdi, to ni yanxu me xance??" Aneesah ta dinga goge idonta ko da wasa bata ce ma Aunty turaren da ta bata ne ya fashe ba, Aunty tace "Toh abinda xai faru duk inda xaki nemo kudi ki nemo a samu a rufe bakinsa kawai" Aneesah tace "Sai in dau zinarina in siyar, I can't imagine Aliyu yace xai rabu dani sabida haka, wllh ina sonsa sosai Aunty" Aunty tace "Ya rabu da ke?? Ji wani mugun alkaba'i, ke fata kike ya rabu dake ma kenan? Akan wannan d'an abun xai rabu dake kamar warce ta kashe mutum? Mata nawa ne aka aurar bbu budurcinsu kuma suna xaune qlau da mazajensu? Rabu da d'an iska xai ma sakko ne, ke dai kawai ki siyar da zinarin ki turo min kudin a tura benue" Aneesah tace "Toh Aunty, ynxu xan fita kasuwa in siyar sae in tura maki kudin" Aunty tace "To yi maxa, kar ki wani damu abunki, ubansa ma yayi hakuri da hakan balle shi gantalalle, shaff mancewa xai yi idan na sa ayi aikin..." Aneesah tace "Toh nagode Aunty, bari inje, xan kiraki" Aunty tace "To yi maxa" daga haka ta katse wayar, ko wanka Aneesah bata yi ba tun daren jiyan balle aje ga sallah, ta saka doguwar rigar atamfa ta xumbula hijab dinta sannan ta saka zinarin a jaka ta fita daga gidan. A ranan Ahmad ya kai Jiddah makaranta kamar yanda ya ce da Umma, Tunda yyi duk registration din da komai ya tafi ya barta kawai ta fara karatu Monday din... Da yamma karfe hudu da kansa yaje daukota daga school din, amma sanin halin Ummarsa sae ya wuce da ita can gida kawai, Umma tayi farin cikin fara makarantar Jiddah sosai, ita dai Jiddah na xaune kasa kan carpet tana murmushi, Umma tace "Toh tashi kiyi sallah ki ci abinci" mikewa tayi ta wuce dakinsu, Ahmad ya kalli Umma yace "Kince daga nan xata dinga tafiya ko Umma?" Umma tace "Eh xata dinga xuwa daga nan" Yyi murmushi yace "Ga dai sauki amma ke baki so Umma" Umma tace "Saukin me?" Yace "Kashe transport" Umma tace "Kai yanxu ka bada shawarar a bar kamarta da Ramlah a gida kai kana can gun aiki, to wa xai dinga gaya masu gaskiya ko ya sa su kan hanya, shiririta kenan kawai" Yace "Kema dai kinsan Ramlah bata da shiririta Umma, sannan Jiddah ma na da hankali da nutsuwa sosai, kinga from monday to Friday idan taje schl sae ta xo nan Friday din da yamma ta maki weekend, ina ga xae fi wllh" Umma tace "Shkkn kuma babu me sa mata ido kan karatun?" Yace "A nan ma kinsan bbu me sa mata ido amma take yin karatunta wholeheartedly" Umma ta ta6e baki tace "Toh ae shkkn, sae ta tafi can din, amma friday ta dawo nan tayi weekend" Yace "In sha Allah Umma" Sae kusan biyar da rabi suka bar gidan suka koma gidan Ahmad, a hanya yake bata hakuri kan gidan Iya da bai kai ta ba tunda ta koma schl, Jiddah tayi murmushi kawai tace "Toh Allah ya kai mu wani lkcn" Ranan friday Abuturrab na shigowa garin kaduna gidan Umma ya nufa direct, yana parking a kofar gida ya shiga cikin gidan, Umma ce xaune parlor suna hira da Huraira, yayi sallama ya shiga parlorn, sanye yake da fararen shadda da suka amshesa sosai, sae da Huraira ta gaishesa sannan ta bar parlon, Ya xauna saman kujera yana kallon Umma yace "Ina yini" Umma na kallonsa tace "Lafiya lau, daga ina haka?" Yace "Daga gida" Tace "Madallah, ya kwana biyu?" Yace "Alhmdlh..." Sallama aka yi bakin kofar Umma ta daga kai tare da amsa sallaman, ta shigo parlon sanye da hijab dinta gogagge har kasa da jakarta a hannu, ta gefen ido yake kallonta har ta karaso cikin parlon ta nufi Umma ta durkusa nan kasa kusa da ita a hankali tace "Umma ina yini" Umma tayi murmushi tace "Lafiya lau Jiddah ya karatun?" Ta sunkuyar da kanta tace "Alhmdlh Umma" Abuturrab dai kallonta kawai yake, Umma tace "Ya su Ramlar" Jiddah na wasa da fingers dinta tace "Tana gaisheku..." Umma tace "Ahmad din ya shigo ne?" Jiddah ta girgixa mata kai tace "Aa" tunda ta lura da cewar Abuturrab ne xaune parlon duk da ba wai kallonsa tayi ba taki yarda ta dago kanta gaba daya, Umma tace "Toh yayi kyau, kije ki xuba abinci ki ci" Tace "Umma na ci abinci" Umma tace "Ohk to kice ma Huraira ta kawo ma Aliyu ruwa" Mikewa Jiddah tayi still bata yarda ta kalli direction din da yake ba ta wuce kitchen din, satan kallonta yake har ta shiga kitchen din, sai kuma ya kalli Umma yaga wani kallo da take masa... *Sorry for the late night update* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 Abuturrab ya dauke kansa, Umma tace "A hado maka da abinci ne?" Girgixa kai yayi yace "Aa" Jiddah na ba Huraira sakon Umma ta fito ta wuce dakinsu, Huraira ta fito da ruwan ta ajiye ma Abuturrab, knocking aka yi bakin kofa Huraira ta karasa bakin kofar ganin driver ne ta kalli Umma tace "Umma Musan ya dawo" Umma tace "Ohk to ya jirani" Huraira ta koma ta gaya ma drivern abinda Umma tace, Abuturrab ya dau bottle water ya bude yana kallon Umma yace "Umma fita xa ki yi?" Umma tace "Ehh yanxu kuwa" Tana fadin haka ta mike ta wuce dakinta ta dau hijab da purse dinta, tana fitowa parlon shi dai bin ta kawai yake da kallo, ta xauna saman kujera ta kira Huraira, Huraira na xuwa tace "Kira min Jiddah" kallonta kawai Abuturrab yake, Huraira ta wuce daki sai ga ta sun fito tare da Jiddah, Umma tace "Dauko Hijab dinki ki rakani" Jiddah tace "Toh" sannan ta juya, Abuturrab dai sai kallon small mum din tasa yake, banda danna wayarta babu abinda take, Can ya shafa kansa a hankali yace "Umma ina xa ku?" Tace "Kwana biyu banje na gaida Yaya ba, can xanje yanxu" Yace "Nima can, xan tafi na dai fara xuwa nan in gaisheki ne" Umma tace "Allah sarki, ai ka kyauta" Yace "Toh in ajiye ku can din?" Umma tace "Idan ka ajiye mu wa xai maido mu, gwara mu tafi da driver ko awa nawa xanyi xai jira in gama sannan ya maido mu gida" Abuturrab yace "Ae xan kai har bayan isha a can, duk sanda xa ku dawo sai in dawo da ku sannan in wuce gidana" Umma tace "Toh ai shkkn idan ba takura" Umma ta mike ta wuce kitchen don juye pepper soup din da tayi ma Ummi, Jiddah ta fito daki sanye da hijab din da ta xo da shi, hada ido suka yi da shi, ta juya da sauri ta wuce kitchen, babu 6ata lkci Umma ta fito kitchen Jiddah na biye da ita rike da warmer din pepper soup, Abuturrab ya mike yace "Ina jira a mota Umma" Umma tace "Eh yanxu xa mu fito" Umma ta gama ba Huraira instructions din da xata bata sannan suka fito parlon da Jiddah, driver dake tsaye parking space Umma ta nufa tace "Musa kawai kayi tafiyarka na samu ma wanda xai ajiye ni can gidan" cike da ladabi Musa yace "Toh shkkn Hajiya, Allah ya tsare" Umma tace "Ameen, sai gobe kenan" Daga haka ta nufi gate Jiddah na biye da ita a baya being very careful kar ta 6ata hijab dinta da abinda ke cikin warmer din hannunta, back seat Umma ta bude ta shiga, Jiddah ta shiga bayan ita ma ta kulle motar, Umma na kallonsa tace "Idan ka samu wajen siyar da fruits a hanya" Yace "Ohk" daga haka ya tada motar ya bar layin. Dai dai wajen masu siyar da fruits yayi parking kamar yanda Umma ta umarcesa, Umma ta ciro kudi ta mika masa tace "Apples kawai sai grapes" Ya kalli kudin ya sauka motar yace "Akwai kudi a jikina" daga haka ya kulle motar ya tafi gun masu fruits din, bayan some minutes ya dawo, ya bude back seat yana mika ma Umma ledan amma Jiddah yake kallo, Umma ta kallesa tace "To ita kake ba ledan ko ni Aliyu? idan ita ce sai ka xaga ta can mana" Tana fadin haka ta amshe ledan xata rufo door din motar, shi dai bai ce komai ba ya koma driver seat, Jiddah dai na makale at the far end of d car don bata ma son su hada ido mistakenly ta madubi. A kofar gidansu yayi parking, Umma ta sauka, Jiddah ma ta sauka rike da warmer din ta bi bayan Umma da sauri, Direct bangaren Ummi suka tafi, Jiddah dai na xaune kasa bayan sun gaisa da Ummi da ta fito daga daki, Ummi tace "Toh ki xauna kujera mana Jiddah" Murmushi kawai Jiddah tayi bata ce komai ba, Umma tace "Ko a gida ma kafin ta xauna a kujera sau daya tayi xamanta a carpet ya fi a kirga" Ummi tace "Ikon Allah, to ina su Maimoon?" Umma tace "Suna dawowa boko suka tafi gidan Hajiya Zainab" Ummi tace "Haba, tana garin nan dama?" Umma tace "Aa last week ta shigo" Ummi tace "Allah sarki" Umma tace "Jiddah kuma ai nace maki tana gidan Ramlah ta fara karatu ko?" Ummi tace "Ehh haka kika ce, Allah ya bada ilimi me albarka da amfani" Umma tace "Ameen, Hajiya Hajja fa? Kwana biyu ba a je min ba" Ummi tayi murmushi tace "Shekaranjiya ta tada rigiman a kai ta gombe wajen mai martaba, amma yau kuma wai sai naji suna hanya kilan ma sun kusa, mun yi magana da El-Basheer din da safe" Umma ta tabe baki tace "Toh Allah ya kyauta, meye amfanin tafiya me nisan da ko kwana uku baxa ayi ba" Dariya kawai Ummi tayi, aka bude kofar Abuturrab ya shigo da sallama, xaunawa yayi ya gaida Umminsa, Ummi ta amsa tana kallonsa, Umma tace "Shi ya kawo mu, yaje can gida gaisheni shine yace bari ya ajiye mu tunda nan xa mu xo" Ummi tace "Maa sha Allah, Ina matar taka??" Yace "Tana gida" Ummi tace "Toh yayi kyau, shekaranjiya ma ai ina jin ta xo nan wajen Hafsah, amma ni dai ban ganta ba su Nafisah ke gaya min" Abuturrab dai yyi shiru bai ce komai ba, Umma dai ta ta6e baki tana kallon Tv, Ya kalli Ummi yace "Ummi akwai abinci?" Umma ta wani kallesa tace "Amma da nayi maka magana a can gidan me ka ce min?" Murmushi kawai yayi, Ummi ta kalli Jiddah tace "Akwai abinci kitchen ki dibar masa Jiddah" Sosai gaban Jiddah ya fadi ta kalli Ummi, Umma dai bata ce komai ba, Jiddah ta mike a hankali ta nufi kofa, Abuturrab na kallon Umminsa yace "Aunty na nan?" Ummi tace "Sai kaje ka duba" Bai ce komai ba, sai kuma ya mike yace "Bari in gaisheta in dawo yanxu" Daga haka ya nufi kofa daga Ummi har Umma suka bi sa da kallo, Umma tace "Mu je ciki akwai magana yaya" Ummi ta mike tace "Toh" a tare suka shiga bedroom din Ummi... Abuturrab na fitowa bangaren Ummi kitchen ya nufa direct, Jiddah ta juya da sauri jin an shigo kitchen din, suna hada ido ta juya masa baya, kana ganinta kasan duk a tsorace take ta ma rasa me take yi, sai kuma ta tuna miyan ganyen xata xuba a bowl, tana cikin xubawa taji muryarsa yace "Saboda nace ki daina gaisheni shi yasa idan kika gan ni sai ki min kallon banxa ki wuce right?" Kasa ce masa komai tayi amma banda bugawa babu abinda xuciyarta yake gashi taki juyowa, bude kitchen din aka yi ta juya da sauri, Mai aikin gidan ce ta shigo ganin Abuturrab ta koma xata fita, da sauri Jiddah ta ajiye bowl din miyar hannunta ta fice ta kofar da tagani a kitchen din wanda ke a bude, da mamaki ya bi ta da kallo, har ta xagayo gaban compound din gidan waige waige take ko ya biyota amma bata ga haka ba, mai gadi ya bude gate sai ga mota ya shigo, ko parking din motar ba a yi ba, motar na tsaye tsakar compound din aka bude back seat sae ga Hajja ta sauko da katon jakarta, Jiddah ta karasa gunta don amsan jakarta, Hajja sae kallonta take can tace "Wannan kafafuwa naki haka kamar a Masar, kinsan su ma haka kafafuwansu yake farare tass da yake larabawa ne, to ke kuma ba balarabiya ba sae dai ko sadaka yalla" Jiddah dai tayi murmushi ta amshi jakar Hajja tace "Sannu da dawowa Hajja" Hajja tace "Yauwa wajen d'ana sarkin Bauchi naje, ai da ke nayi niyyar xuwa Usman ya hanani wai inyi ta kaina, banda haka da na kai ki kinga ikon Allah, to ina takalman naki kike yawo haka ke kuwa? Ita mace ae ba a santa da yawo babu takalmi ba, barin ke da taki kafar kamar ta 'yan Masar" El-Basheer ya sauko daga mota yana kallon Jiddah, Jiddah ta d'an kallesa tace "Ina yini?" Yayi murmushi yace "Lafiya lau Jiddah, how are you doing?" Tace "Alhmdlh" Hajja tace "To ki tsaya ku gaisa a tsanake idan kun gama sai ki taho min da jakata kin ji" Daga haka tayi wucewarta, Jiddah ta d'an kallesa, Murmushi yayi yace "Ya karatu?" Tace "Lafiya lau" yana kallon kafafuwanta yace "Ina takalmanki" Tace "Aa ta kofar kitchen na fito ne" Yace "To muje ciki" Tana gaba yana biye da ita suka wuce parlor din gidan, Abuturrab na xaune parlor Hajja na tsaye sai basa labari take, shi kam ko kallonta baya yi banda danna wayarsa da yake, Jiddah ta shigo parlon tare da El-Basheer, Hajja ta kallesu tace "Har kun gama gaisawa?" Jiddah dai bata ce komai ba tayi hanyar dakin Hajja da jakarta bayan ta saci kallon Abuturrab, Hajja ta bi bayanta murya can kasa tana cewa "Ki daina abu kamar er kauye 'yar nan, kamata yyi ki buda baki kuyi tadi da shi sosai, ba wai ki ta sunkuyar da kai kina murmushi ba, ubansa fa shine sarkin Bauchi gaba daya, kuma ni na haifi uban, na ya6a da hankalinki ne shi sa nake ta cusa masa ke, amma naga ke kuma kina abu kamar wawa, haba kar kyanki ya tashi a banxa mana er nan" El-Basheer na kallon Abuturrab da ya ki dago kai yace "Na kira ka daxu wayarka a kashe" Abuturrab ya kallesa yace "Ohk kilan na kashe then, ya hanya" El-Basheer yace "Wannan mata ta fiye fitina wllh, i have to drive her all the way from kano, and in sha Allah gobe xan koma Bauchi" Abuturrab ya mike yace "Toh muje can gidana, tafiya xan yi nima" El-Basheer ya d'an buda ido yace "Ae ban gaisa da su Ummi da Aunty ba" Abuturrab yace "Duk basa nan, if u are going mu tafi yanxu don ni tafiya xanyi, gobe idan xaka koma Bauchin sai kaxo kayi masu sallama da safe" El-Basheer ya d'an shafa kansa yace "Ohk, i can even still come back at night in gaisa da su" Abuturrab yace "Eh xai ma fi" Daga haka suka fita parlon, a hanya Abuturrab yayi masu take away din abinci, El-Basheer na kallonsa da mamaki yace "Aneesah bata yi girki bane?" Abuturrab yace "Ehh bata jin dadi" El-Basheer yace "Toh Allah ya sauwake" Abuturrab yace "Ameen" sai da suka kusa gidan Abuturrab ya fara xullumin condition din da xai je ya tarar da gidan nasa with El-Basheer. Amma ga mamakinsa yana bude kofar parlor yaji wani kamshin turaren wuta me dadi ya doki hancinsa, ga sanyin Ac da ya cika parlon, suka shiga ciki tare da El-Basheer, the parlor was more than clean, banda kyalli babu abinda kayan kallon parlon suke, bin ko ina Abuturrab ya dinga yi da kallo yana mamakin anya gidan nasa ne kuwa wannan, El-Basheer ya xauna yana sauke wani numfashi yace "Gidan Amare daban yake, so cool" Daga sama Aneesah ta sauko da atamfa riga da skirt da ya kamata ta kashe dauri, fuskarta kuma tayi light make up, tayi kyau sosai kamar a sace a gudu, da murmushi ta karaso cikin parlon tace "Sannunku da xuwa, bako muka yi captain" El-Basheer yace "Fatan mun same ku lafiya amarya?" Tana ci gaba da murmushi tace "Alhmdlh, u are welcome" karasawa tayi kusa da captain ta xauna gefensa tace "Welcome my captain" Yana gyara xama yace "Yauwa thank you" Murmushi bai gushe a fuskarta ba ta mike ta wuce kitchen, sai gata ta dawo da ruwan gora biyu da drink sai cups, ajiye masu tayi tace "Ga ruwan sanyi" El-Basheer yace "Thank you Aneesah" Ta xauna one sitter tana kallon captain dake ta danna wayarsa, El-Basheer ya dau ruwa ya fara sha, tace "A kawo abinci yanxu?" Sai da captain ya daga kai ya kalleta jin abinda tace, tayi fari da ido tace "Eh, ko sai anjima" El-Basheer yace "Aa kawo min ni dai, Captain sai ya ci take away din da yayi" Ta mike ta dau ledan take away din ta wuce kitchen tana cewa "Shi ma baxai ci ba, ga dai abinci nayi" Captain ya bi ta da kallo, manyan warmers kusan biyar ta kawo parlon ta dire kan carpet, ta koma ta dauko plates, da serving spoon ta ajiye masu tana murmushi tace "Bismillah" daga haka ta wuce sama, El-Basheer ya sauka kasan carpet yana bude warmers din, Abuturrab ma sae kallon warmers din yake, wani lafiyayyen fried rice ne a warmer daya, dayan kuma wainar shinkafa sai tiriri yake, ga hadadden miyar taushe dake ta kamshi, wani warmer kuma peppered chicken ne that looks so enticing, last warmer din pepper soup din kayan ciki shi ma sai kamshi yake, kallon foods din kawai Abuturrab yake, tuni El-Basheer ya fara diban abubuwan da xai diba, Abuturrab ya ci gaba da danna wayarsa, sai kuma ya mike ya wuce kitchen, ko ina fess a kitchen din babu kayan wanke wanke, ya fara dube duben inda xai ga take away din da ta dauke a parlor bai gani ba, hakan ya sa ya bude kofar kitchen yaga a bola ta jefar, ya fi second biyar yana kallon ledan abincin kafin ya gyada kai ya kulle kofar ya fice daga kitchen din, ya dawo parlor ya xauna, El-Basheer yace "Kai baxa ka diba abincin ba?" Ya girgixa kai yace "Na ci abinci a can gida ai" Yace "Ohkk" Abuturrab da El-Basheer suna tare parlon har kusan magrib, ita dai Aneesah na sama, duk da yunwan da Abuturrab ke ji amma ya ki cin abincin, ana kiran magrib suka yi alwala a toilet din downstairs, Abuturrab yyi mamakin ganin toilet din ma fess, ana idar da sallah bayan sun fito masallaci El-Basheer yace ma Abuturrab xai koma can gida don su gaisa da su Ummi tunda gobe da safe xai koma, Abuturrab yace "Toh bari in dauko makullin motar" yana shiga ciki ya dauko makullin motarsa ya fito suka wuce can gidan, El-Basheer ya nufi bangaren Ummi don gaisheta, shi kuma ya tafi dakin Hajja, Hajja na gyara labulayenta Jiddah kuma na durkushe tana sa turaren wuta a garwashin da Mai aiki ta kawo ma Hajja a kasko, Hajja na ganinsa tace "Aliyu wllh bauchi da naje baka ga wata yar yarinya da na maka sha'awa ba, duka duka yarinyar bata wuce Jiddan nan ba, amma abinda yasa ban ce masu komai ba saboda ban san irin tsaftar yarinyar ba, kaga yanxu shi Bashir warce nake sa ran hadashi da ita nasan tsaftarta, to ita wancan gaskiya ban sani ba" Abuturrab dai bai ce mata komai ba, Hajja tace "Duk kwanan nan da kai nake kwana a raina nake tashi, saboda nasan kana cikin jarabawar auren mata kazama, amma in sha Allahu ka sha kurumin ka ina nan ina maka fafatuka, yanda na samar ma Bashir yar kirki me tsafta kai ma haka xan samo maka, Shi kansa Kabiru yyi farin cikin wannan xabin da nayi ma Bashir, uwarsa kuma babu abinda xance da ita sae dai ta ci kanta ni ba ta ita nake ba... Yanxu Usman nake jira ya dawo inji ynda xa a yi, ko shi ne xai xama waliyyin yarinyar to... Bashir kuma yace min shi dai a shirye yake ko gobe ne a daura, amma ae ba gaggawa ake ba ina laifin ma nan da sati uku" Abuturrab yace "A ina kika samar masa matar?" Hajja ta wani kallesa tace "Aa wannan kuma ba ruwan ka ae, wllh Kabiru yace min ya amince indai Bashir din na so, ae karfin xuwa na Bauchin kenan..." Abuturrab ya shafa kansa ya ki cewa komai, can ya kalleta yace "Toh ban ci abinci ba, yunwa nake ji" Hajja tace "Aa ba ma ga yunwa ba a gidan nan, ga dai abinci kaca kaca ka wani ce yunwa, bari wannan yarinyar Nafisah ta shigo ta xubo maka, naga lafiyayyen girki aka yi a gidan, ae Hauwa dama Allah ya hore mata iya sarrafa hatsi" Yace "Sae Nafisa ce xata ban abinci?" Hajja tace "Aa nima sae in je in xubo maka, meye a ciki" yace "To ita warcan baxata iya xuba min ba" Hajja ta kalli Jiddah dake duke da turaren wuta kusa da ita har sannan tace "To ke tashi ki xuba masa" Jiddah ta wani 6ata fuska, Hajja dae sae kallonta take, can ta mike ta nufi kofa ya bi ta da kallon gefen ido, Hajja ta rike ha6a a hankali tace "Sae naga kamar ta fara kiwiya ita ma, to ni dae fa kar ta sa inji kunya a kan abinda nake shirin yi, ko dai tana boye wasu halayyanta ne ban sani ba" Mikewa Abuturrab yyi ya fita daga dakin... Yana shiga kitchen din ya kulle ta juya tana Kallonsa kamar dama tasan xae biyota, ya rungume hannunsa yace "Yanxu ma ki fita ta inda kika fita daxu" Ita dai bata ce komai ba ta ci gaba da dibar masa abincin a hankali, yace "Bude kofar ki fita nace" still taki kallonsa, tsawa yayi mata yace "Baki ji na ne" Ta kallesa kamar xata yi kuka tace "In fita in je ina?" Yace "Inda kika je daxu" Ganin ya nufota ta tafi ta bude kofar ta fita tana kallonsa xuciyarta na bugawa, banda hasken wata babu wani haske a wajen, fitowa taga shi ma yayi bayan ya kashe fitilar kitchen din, bata san lkcn da ta tattare skirt dinta ba da xumar fallawa a guje yayi hanxarin cafkota da sauri, sannan ya kulle kofar kitchen din, iyakar tsorata ta tsorata a lkcn, ta marairaice masa tayi kasa da murya tace "Don girman Allah kayi hakuri ka sakeni... Wllh yanxu Umma xata fito mu wuce gida kar ta fara nemana, tace min yanxu xa mu tafi" Yace "Toh ta nemeki din mana ina ruwana??" Kasa ce masa komai tayi amma scene din ranan a kitchen din gidansa ne ke dawo mata wanda hakan yayi mugun daga mata hankali, duk a tsorace take, ya daure fuska yace "Saboda nace ki daina gaisheni na lura har wani nishadi kike duk sanda kika gani, kuma confidently kike wucewarki..." Tayi narai narai da ido tace "To amma ai kai kace in daina gaisheka, kuma abinda kace min ai shi nake yi" yace "Amma kuma ai murna kike don baki gaisheni?" Ta kasa ce masa komai gabanta na mugun faduwa, sai kuma ta fara kauda fuskarta saboda saukan breathing dinsa da take jiyowa don dab da ita yake, yace "Ohk ni kike dauke ma fuska?" Ta fashe da kuka tace "Ni don girman Allah ka sakeni ana jirana, don Allah fa nace maka...." Tana ganin xai juyo da fuskarta saitin nasa ta rufe fuskar nata a jikinsa hankali tashe tace "Don Allah kayi hakuri bana so wllh" wrapping dinta yyi jikinsa yace "Xan sake ki amma sai kin bani amsar tambayar da xan maki yanxu" Banda bugawa babu abinda xuciyarta ke yi tana jiran jin tambayar tasa, ga kamshinsa me dadi da ya cika hancinta, duk taji ta kasa ci gaba da tsayuwa, xata xame kasa yace "Kee" a hankali tace "Na gaji don Allah ka bar ni in tsugunna" da bango ya hadata ta rufe idonta da sauri, sai kallon fuskarta yake a duhun, taji yace "Duk xaman da muka yi dake a gida daya ki lissafo min abubuwan da na maki na rashin adalci..." A hankali ta bude ido tana kallonsa, yace "Ina sauraronki" Ta girgixa kai tace "Aa babu" ya dafa shoulders dinta yace "Karya kike" Tace "Ba karya nake ba, ban tuna abinda ka min na rashin adalci ba" Yace "To ina son ki tuna sai ki gaya min" Tayi shiru, shi dai kallonta kawai yake, murya can kasa tace "Amma me yasa kake ta6ani bayan kasan ni ba muharramarka bace, nasan kuma ka fini sanin hukuncin...." wani xaro ido tayi jin cold lips dinsa a wuyanta, da duk karfinta ta turasa shi kuma ya rungumeta gaba daya, ai kam neck dinta ya sha kisses iri iri ba a cewa komai tun tana iya turasa har ta hakura ta kasa komai, switch din fitila da aka kunna a kitchen ya sa ya saketa da sauri, without looking at her ya bar wajen, xamewa tayi kasa ta hade kanta da gwiwa amma hawayen ma ta nemesa ta rasa sae sauke numfashi take... Tunda makullin motarsa na jikinsa gate kawai ya nufa ya fice ya shiga motarsa ya wuce gida, ko kallon Aneesah dake xaune parlor duk ta cika turaren wuta bai yi ba ya haura sama yaki xuwa bangarensa ya bude wani daki ya shiga ya kulle kofar da key ya wuce bandaki direct.... Maimoon ta mike xaune ta kunna switch din dakin dake gefenta tana kallon Jiddah cikin muryan bacci tace "What happened Jiddah?" Ganin Jiddah taki bata amsa kuma taki dagowa ta sauka kan gadon ta nufi kofa ta fita xuwa dakin Umma.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 Umma na shigowa dakin ta karaso kusa da gadon tana kallon Jiddah tace "Lafiya Jiddah?" Jiddah ta dago kanta da kyar hawaye na sauka idonta amma ta kasa cewa komai, Umma tace "Ciwon cikin ne?" Ta gyada mata kai kawai, Umma ta kalli agogo dake nuna karfe hudu saura, fita tayi daga dakin ta dau wayarta ta shiga kiran layin Ahmad, har ya katse ba a dauka ba, Umma ta tsaya tana ta tunanin yanda xata yi kuma, gashi ita bata driving da duhu, har ta fara tunanin kiran driver dinta sai ga Ahmad ya kira, dagawa tayi tace "Sorry i woke u up Ahmad, kana gari ne?" Ahmad yace "Aa ban shigo ba, me ya faru Umma?" Umma tace "Wllh ciwon cikin Jiddah ne ya tasar mata, ni kuma ba driving nake a duhu ba..." Yace "Subhanallah, bata taho da magungunanta bane?" Umma tace "Ka siya mata wasu maganin ne?" Yace "Ehh na siya mata a can gida, But Umma Captain na gari ai, ki kirasa sai ya taho ya kai ku asibitin" Umma ta sake kallon agogo, sai kuma tace "Toh shkkn" Daga haka ta katse wayar, Number Aliyu ta nemo a contact sannan tayi dialing number, Abuturrab na kwance ya samu bacci kenan kiran Umma ya shigo wayarsa, da yake baccin nasa bai wani nisa ba ya bude ido da kyar yana kallon wayar tasa, mikewa xaune yyi ya jawo wayar da mamakin me kiransa at that time, number Umma ya gani a screen, ya daga ya kai kunne, Umma tace "Sorry na tashe ku Aliyu, idan ba damuwa ka taho gida yanxu xa ka kai mu asibiti..." Yace "Subhanallah.. waye ne ba lafiya?" Umma tace "Idan ka xo xaka gani" a hankali yace "Toh" daga haka ta katse wayarta, Mikewa Abuturrab yayi duk da idanuwansa da suka masa nauyi don throughout first hours of the night idonsa biyu ya kasa bacci, har sae kusan karfe uku da wani abu sannan ya samu sauki bacci ya daukesa, daukar wayarsa yayi ya fita daga dakin... Ya tafi bangarensa ya bude kofar parlon a hankali sannan ya karasa bedroom dinsa nan ma he was so careful opening d door, Aneesah na kwance tayi dai dai saman gado tana baccinta, ya karasa gun kayansa ya dau kayan da xai dauka sannan ya nufi kofa xai fita kenan yaji cikin muryan bacci tace "Captain" Juyawa yayi ya kalleta, ta mike xaune tace "Ina xaka by this time, naga ka dau kaya?" Bai tanka ta ba ya fice daga dakin ta bi sa da kallo, ya koma dakin da yake yana cikin shiryawa ta shigo ta kulle kofar, bai ko kalleta ba ya ci gaba da buttoning din shirt dinsa, ta karaso kusa da shi, sai kuma ta durkushe kasa ta hade hannunta cikin rawan murya tace "Captain auren soyayya muka yi da kai fa ba auren kiyayya ba, wannan altitude din da ka tsiro yana sa min ciwon xuciya, don Allah idan wani laifi nayi maka kayi hakuri ka yafe min ba don halina ba" sai kuma ta fashe da kuka, ya girgixa kai yace "Ni nace kin min wani abu ne?" Cikin kuka tace "Gashi nan you are ignoring me and giving me altitude for the pass 8 days now, don Allah ba don ni ba kayi hakuri, albarkacin irin son da nake maka kayi hakuri" Shi dai bai ce mata komai ba, tana shessheka tace "Idan ma aikin gida ne da bana yi ai kaga yanxu dai na fara yi, har girki ina yi yanxu... in sha Allah kuma xan dore da haka, kawaye kuma na daina barin su xo min gida daga yanxu, ni dai don Allah ka daina shareni haka ina shiga damuwa sosai Mijina" Ya dau makullin motarsa yace "Xan je Umma na kirana xan kai su asibiti" Tace "Subhanallah, waye babu lafiya?" Yace "I don't know, sai naje" Tace "Toh don Allah in sa hijab mu tafi tare" Ya kalleta yace "No, it's of no need" Ta marairaice tace "Me yasa kake yawan gwaleni a abubuwa da dama ne Captain, i just want to feel belong in ur family, har yanxu fa babu wani bond tsakanina da su, and it's not suppose to be so, allow me to always mingle with them don Allah, kaga yanxu ai Umma xata ji dadi idan ta gan mu tare" yace "Bayan wanda ku ke yi da Aunty? I mean the bond u are talking about" Tace "Ai Aunty daban Captain, har yanxu fa ko gidan Umman ma ban sani ba, don Allah kar kace min Aa captain, ka bari mu tafi tare, ni fa ba kowa gareni a garin nan ba sai kawaye kai ma ka sani" Bata jira cewarsa ba ta mike ta fita ta koma bangarensa ta dau hijab dinta har kasa ta saka kan doguwar rigan baccin jikinta, ta feshe duk jikinta da turare sannan ta fito, dai dai nan shi ma ya fito daga dakin da yake, ya fara sauka downstairs yana rike da makullin motarsa ta bi bayansa, Abuturrab bai ce mata komai ba ta bude daya side din motar ta shiga, mai gadi da Abuturrab ya kwankwasa ma kofa ya fito da sauri ya bude masu gate, Mai gadin na tsaye gefe har Abuturrab ya fitar da motar sannan ya kulle gate din yana daga masa hannu, Abuturrab ya jira har masu gadin layin suka bude gate din layin sannan ya fita, yana isa layinsu Umma nan ma gate a kulle, hakan yasa ya dau wayarsa ya shiga kiran Umma, Umma na dagawa yace "Umma xa ku iya fito naga ba a bude gate na shigowa layin ba" Umma tace "Toh bari mu fito" daga haka ta katse wayar, Aneesah ta kallesa tace "Toh kayi horn mana kilan masu gadin xa su fito sae kayi masu bayani ko" Ya girgixa kai yace "No need" Idonsa na kan gate din gidansu Umma that's not too far from the gate leading to d street, bayan few minutes aka bude gate din gidan, Umma ce ta fara fitowa tana rike da hannun Jiddah Maimoon na biye da su, Ya dinga kallonsu kamar yanda Aneesah ke stressing idonta tana son ganin su waye suka fito, bude motar yayi ya sauka ya kulle sannan ya karasa ya shiga layin ta karamin gate din da ke a bude, Umma ta sake Jiddah da ta durkusa kusa da wani flowern wani gida xata yi amau, Ya isa har inda suke a tsaye yace "Me ya sameta Umma?" Umma dake kallon Jiddah cike da tausayinta ta sauke ajiyar xuciya tace "Wai ciwon cikin dae..." Dukawa Abuturrab yyi yana kallonta shi ma, cikin low voice yace "Sorry..." Jiddah dai bata ce komai ba ta mike da kyar don ta kasa aman, Tun da Aneesah ta lura kamar Jiddah ce ba lafiya mood dinta ya canxa gaba daya, lkci daya ta fara da ta sanin fitowa da tayi ta biyosa... Ba don baxa ta samu abun hawa ba da kawai sauka xata yi ta koma gida abunta, Maimoon ta daga Jiddah ganin bata yi aman ba suka ci gaba da tafiya, Abuturrab na kallon Umma yace "Tun yaushe take ciwon cikin?" Umma tace "Ban san sanda ya tasar mata ba, Maimoon ce ta shigo ta tasheni..." Abuturrab bai kuma cewa komai ba har suka isa gun motar yana kallon Jiddah, ya bude back seat Maimoon ta shiga ciki tare da Jiddah, Umma ma ta shiga bayan motar, ya xaga ya shiga driver seat, Aneesah tayi kasa da kai tace "Ya mai jikin Umma?" Umma tace "Alhmdlh, mun taso ku ko" Tace "Aa babu komai Umma, Allah dai ya bata lafiya" Umma tace "Ameen" wani babban asibiti Abuturrab ya kai su, bayan su Umma sun sauka motar Aneesah ta kalli Abuturrab murya can kasa tace "Amma dai likita na attending masu xamu juya ko captain??" Ya kalleta yace "Amma tun farko sai da nace kar ki biyoni ko??" Ta hade rai tace "What did u mean? Asibitin xa mu xauna har a sallamesu kenan saboda Ramlah ce bata da lafiya ko Aisha?" Bai tanka ta ba ya bude motar ya sauka, rai bace ita ma ta bude motar ta sauka tana masa wani irin kallo, kulle motarsa yayi ya bi bayansu Umma... Admitting din Jiddah aka yi a hospital din saboda karin ruwa da xa ayi mata, sosai take jin jiki wai duk a hakan ma tana da dauriya ba kadan ba, Umma na xaune bayan ta idar da sallan Asuba a ward din da aka kwantar da su wayarta ya fara ring, Maimoon ta mika mata wayar, Umma ta daga ganin Ahmad ne ke kiranta, bayan sun gaisa yace "Ya jikin nata Umma?" Umma tace "Ta samu bacci yanxu, an sa mata ruwa..." yace "Toh Allah ya sauwake, ya bata lafiya" Umma tace "Ameen" Ahmad yace "Captain ya tafi ne" Umma ta kalli Abuturrab dake xaune shima shigowarsa kenan daga masallaci tace "Aa bai tafi ba" Ahmad yace "Ohk, na kira bai daga bane" Umma tace "Ko wayar na mota" Ahmad yace "Toh shkkn xan kira anjima" Umma tace "Allah ya kai mu" Tana katse wayar ta kalli Abuturrab tace "Aliyu ku koma gida kawai, tun da har ta samu bacci, she will get better in sha Allah... Daga nan ku ajiye Maimoon ma a gida" Abuturrab dai bai ce komai ba, Aneesah dake xaune kan plastic chair ta kalli Abuturrab din ta gefen ido ta ji abinda xai ce, Yana kallon Umma yace "To shkkn, Allah ya bata lafiya" Umma tace "Ameen, Allah yayi albarka" Kallon Maimoon da ta mike yayi sannan ya nufi kofa, Aneesah ta mike tana kallon Umma tana kirkiran murmushi tace "In sha Allah, xan dawo anjima Umma, Allah ya bata lafiya" Umma tace "Ameen, mun gode Aneesah, Allah yayi albarka" Tace "Ameen" ko kallon Jiddah bata yi ba ta fice daga ward din, Umma na kallon Maimoon tace "Ki dauko mata wani hijab din, may be with an extra clothe, sannan ki taho da toothpaste and brush, idan su Huraira sun gama breakfast sai ku kira driver ya taho da ku anjima, nima ki dauko min wani hijab din kar ki manta" Maimoon tace "Toh" sannan ta fita ward din. Karfe takwas da yan mintuna Abuturrab ya shiga dakinsa bayan yayi wanka ya shirya cikin kananun kaya, kwance ya tadda Aneesah har sannan tana bacci tun bayan da suka dawo wajen karfe shidda da asuba, Karasawa yyi saman gadon ya kai hannu ya buga gefen gadon, ta bude ido a hankali don tun bude kofar parlon da yayi ta farka, yace "Yanxu babu wani abu da xaki girka a kai asibiti??" Buda ido tayi sosai tana kallonsa sai kuma ta mike xaune tana ci gaba da kallonsa keenly tace "Abu kamar me fa Captain?" Yace "Breakfast...." Bude baki tayi sai kuma ta tafe hannu tayi wani dariyar rainin hankali tace "Saboda Aisha ko Ramlah ce kwance gadon asibiti ba lafiya ko??" Kafeta yyi da ido, ta ja wani tsaki tace "Wllh ka xo da wata bidi'a Captain, kawai saboda ga kanwar uwata Safara'u kwance gadon asibiti sai in tashi da sassafe in fara hada breakfast, to bari kaji wllh ko Maimoon ce bata da lafiya sai na ga dama xanyi girki a kai asibiti balle wata banxa can mara asali, gayyar....." Dakatar da ita yayi cikin tsawa yace "Enough Aneesah, baxa kiyi ba baxa kiyi ba, final!! Kar ki gaya min maganan banxa..." Aneesah ta masa wani kallon banxa daga sama har kasa ta sauka kan gadon ta shige bandaki abun ta tana cewa "Ka xata tun farko da nasan ita ce ba lafiya xan ma fara katse bacci na in fita cikin dare..." juyawa yayi ya fita daga dakin xuciyarsa na tafarfasa, yana komawa downstairs ya kira layin Maimoon, tana dauka yace "Anyi breakfast ne a can gidan?" Maimoon tace "Ehh driver muke jira yanxu ya kai mu asibitin" yace "Ohk, i am coming now" daga haka ya katse wayar, yana isa gidan Umma ya dau Maimoon da Safiyya suka wuce asibitin, har sannan Jiddah bata tashi ba, Umma na kallon Abuturrab yace "Ya ku ka koma gida" yace "Lafiya lau" Maimoon na kallon Umma tace "In hada maki shayin Umma?" Umma tace "Aa ai baxan iya sha a nan ba, tun da kun xo bari kawai in koma gida sai in dawo anjima idan na kintsa" Maimoon ta mayar da cup din tace "Toh shkkn" Umma ta mike, Abuturrab ya kalleta yace "Toh bari in ajiye ki gidan Umma" tace "Toh nagode" Tare Umma ta koma da safiyya da tayi shirin Islamiyya, Abuturrab na kallonta yace "A Islamiyyan xa a ajiye ki ke?" Tace "Ehh" sai da ya fara ajiyeta a Islamiyyarsu sannan ya kai Umma gida, bayan ta sauka daga motar ta saka masa albarka ta wuce ciki, barin layin yayi yana hawa saman titi kiran Ahmad ya shigo wayarsa, dauka yayi ya daga ya kai kunne Ahmad yace "Ka koma asibitin ne?" Abuturrab yace "Aa" Ahmad yace "Ohk anjima xan shigo in sha Allah, ka tambayi Umma if there is anything sai kayi masu tunda kaga ba kowa..." Abuturrab dake ta sauraronsa ya tabe baki yace "Umma tace tana yawan ciwon cikin, and what is the cause?" Ahmad yace "Da ka shiga ka tambayi likitan da yayi admitting dinsu mana" Abuturrab yace "Kai na tambaya" Ahmad yace "Ohk tunda ni ka tambaya bari in baka amsa, duk xamanku tare da ita a gidanka ka ta6a ganin tayi Period?" Abuturrab ya juya ido yace "Period? Meye hakan?" Dariya Ahmad yayi yace "Al'ada" Shiru Abuturrab yyi, Ahmad yace "Toh bata al'ada, da Umma ta ga hakan sai ta kai ta asibiti aka daurata kan magunguna, tun sannan kuma shine take ciwon mara..." Abuturrab yace "Toh dole ne sai anyi jinin?" Ahmad yace "Of course dole ne, although wasu matan basa yi kuma suna haihuwa a haka, akwai mata da yawa da xaka ga a shekara sau biyu suke al'ada kuma suna haihuwarsu lafiya lau babu wani abun dake damunsu, so in her case...." Abuturrab ya katse sa yace "What i want to understand here now is, so ake ta fara al'adan yasa aka kai ta asibiti ko me?" Ahmad yace "Eh mana, ana son sanin ko nata normal ne ko kuma Hormonal Imbalance ne ya janyo hakan, idan Hormonal imbalance ne kaga dole sai an ci gaba da yi mata medication har Allah yasa ta fara din, sannan ciwon maran da take ai jini ya kamata tayi ba ciwon mara me tsanani haka ba" Abuturrab ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Allah ya sauwake" Ahmad yace "Ameen..." Abuturrab yace "Sai anjima" daga haka ya katse wayar. Asibitin ya sake komawa, yana shiga ward din Maimoon ta daga kai ta kallesa da mamaki, a ranta kuwa cewa tayi me kuma ya dawo da wannan mutumin nan, tunda Jiddah dake xaune saman gadon ward din hannunta rike da cup din shayi ta hada ido da shi ta sunkuyar da kanta taki dagowa, Maimoon ta mike tana kallonsa tace "Ga kujera yaya" Yace "Nace maki xan xauna?" Ta girgixa kai ta koma ta xauna a ranta tace oho dai, ya kalleta yace "Ke me ya hanaki xuwa islamiyyar?" Ta xaro ido tace "Toh ai yaya saboda xan tsaya da Jiddah a asibiti ne Umma xata koma gida, kaga babu kowa a nan din" Ya d'an kalli Jiddah da taki dago kanta yace "Tace maki bata ji sauki bane?" Maimoon ta kalli Jiddah, ta washe baki tace "Wai kin ji sauki Jiddoh?" Ko kallonta Jiddah bata yi ba, Shi dai kallonta kawai yake, mika ma Maimoon cup din shayin tayi, Maimoon tace "Har yanxu kina jin aman?" Jiddah ta girgixa mata kai kawai, Maimoon tace "Amma ya isheki?" Jiddah ta gyada mata kai, Maimoon ta amsa Abuturrab yace "Mayar mata ta shanye" Maimoon ta d'an kallesa tace "Cika mata cup din fa..." Dakatar da ita yayi yace "I said give it back to her" mika ma Jiddah tayi, Jiddah tace "Ni amai nake ji" Yace "Eh amsa idan kin shanye sai kiyi aman" Karban shayin tayi a hankali a hannun Maimoon, ya ciro ATM card dinsa a wallet dinsa ya mika ma Maimoon yace "Ki ciro min kudi" ta kallesa da sauri tace "A ina yaya? Ai babu Bank a kusa..." Yace "Ko ma ina xaki ciro kije ki ciro ba ruwana" nan da nan mood dinta ya canxa ta amshi Atm card din ta mike tace "Nawa xan ciro?" Yace "Talatin" Kofa ta nufa tana cika tana batsewa, ya bi ta da kallo har ta bude kofar sai kuma ta juyo ganin kallonta yake ta seta fuskarta tace "Yaya pin din fa?" Yace "Ki kira Ramlah ki tambayeta" Ficewa tayi daga ward din ta kulle kofar, ya kalli Jiddah ganin ta ajiye cup din saman gado ta hade kai da gwiwa, karasawa yyi ya dauke cup din shayin ya ajiye a table yana kallonta, ta dago tana rufe idonta yace "Are u still feeling pain?" Da kyar kamar xata yi kuka tace "Yanxu ya fara" Kafin yace komai ta fara kokarin sauka daga saman gadon ya bi ta da ido har ta shiga bandaki, yana ta tsaye har ta fito daga bandakin amma ta ki karasowa cikin ward din, bayan few seconds yace "An kawo maki wani kayan ne?" Kasa kallonsa tayi kuma taki cewa komai, yace "Magana nake maki" bata dago kanta ba tace "Ai ban sani ba" ya nufi jakar da Maimoon ta kawo daxu ya bude, Hijab ya gani da doguwar riga sai undies da sabulu da sponge, satan kallonsa kawai Jiddah take, ya dau sabulun da sponge ya nufeta ya mika mata, amsa tayi ta juya ta koma bandakin, ya karasa saman gadon ya cire bedsheet din ya bar shi saman gadon snn ya fita ward din, nurses dake reception ya samu bayan sun gaisa da wata yace "Plss ki tura cleaner ward din farko, the bedsheet needs to be changed" Tace "Alright" ya juya ya fita xuwa wani babban kanti dake cikin asibitin, babu abinda ba a siyarwa a wajen, yana kallon matar dake ciki yace "Do u sell Sanitary pads?" Matar tace "Yes" guda uku ya siya ya bata kudi sannan ya juya ya koma cikin asibitin, cleaner din ya tarar a ciki tana canxa xanin gado, bayan ta gama ta fita da na da, ya xauna kan kujera, bayan kusan minti sha biyar Jiddah ta fito daga bandakin, pad din da ya ajiye saman table ya nuna mata ta dinga kallon ledan sai kuma ta karasa ta bude tana kallon abun ciki, bata yarda ta kalli inda yake ba ta tafi gun jakan kayanta ta dau pant tana bobboyewa shi dai kallonta kawai yake, ta mike ta dau pad din ta koma bandaki, bayan ta fito ta dau wani Hijab din ta sa, gaba daya ta kasa kallonsa don wani kunyarsa taji take yi, yana kallonta yace "Kina jin ciwon cikin yanxu?" Ta girgixa masa kai ba tare da ta kallesa ba, bai kuma ce mata komai ba ya fiddo wayarsa yana dannawa, ta gaji da tsayuwarta sannan ta koma kan gadon ta kwanta ta lumshe ido, nan da nan bacci ya dauketa.... Karfe goma Maimoon ta shigo ward din fuskar nan nata babu annuri ta mika masa kudin da Atm card dinsa, yace "A ina kika samo?" Tace "Nima ban san wajen ba" Ta nufi Jiddah tace "Har kinyi wanka?" Ganin bacci take Maimoon ta xauna kawai, Maimoon tace "Lah canxa xanin gadon aka yi?" Abuturrab dai bai ko kalleta ba, Hannu ta kai kan ledan pad dake ajiye tace "Meye wannan kuma?" Xaro ido tayi ganin pads har uku, ta saci kallon Abuturrab sai kuma ta mayar ta ajiye sannan ta xauna kan kujera, mikewa Abuturrab yayi ya nufi kofa ya fita. Yana fita Maimoon ta shiga tada Jiddah a hankali, Jiddah na bude ido tace "Wa aka kawo ma pad Jiddah? Kuma wa ya kawo?" Jiddah ta bi dakin da kallo ganin Aliyu baya nan ta mike xaune, Maimoon dake ta kallonta ta xaro ido tace "Ko dai Period kika fara?" A hankali Jiddah ta gyada mata kai, Maimoon ta kara xaro ido tace "Kar dai Ya Aliyu gani yayi yaje ya siyo maki pad din, gashi ma naga an canxa bedsheet" Jiddah ta d'an turo baki, Maimoon ta kyalkyale da wani dariya tace "Atoh wllh shi yaga duhu, amma ke garin yaya kika bari ya gani? Tabb" Jiddah ta marairaice tace "Na tashi na shiga bandaki ban san na ma yi stain ba, kuma bedsheet din ma yayi stain" Maimoon sai xare ido take, sai kuma ta kara fashewa da dariya tace "Toh sai yace maki me da ya gani?" Jiddah tace "Ni bai ce min komai ba, kawai xuwa yayi yaje ya siyo pad din" Maimoon ta tabe baki tace "Ai ko shi yaga duhu, yanxu dai wannan pad din sai kiyi wata biyar ma kina amfani da kayanki bai kare ba, har mu ma mun samu, kinsan fa shi ya Aliyu bai iya siyayyan hankali ba, don ma ba pack din gaba daya ya siyo maki ba, amma don Allah da wani ido kika kallesa bayan yaga period dinki" Jiddah ta ji kamar ta fashe da kuka, Maimoon tace "Idan nice ke wllh ko a gyalena fuskewa xanyi ai bani nace ya gani ba" Jiddah dai bata kuma cewa komai ba amma ita kanta tasan taji kunya sosai ba kadan ba, she wish that never happen... Har yamma da aka sallami Jiddah Abuturrab bai koma asibitin ba, Ahmad ne yayi driving dinsu ya maida su gida, Umma har lkcn bata san Jiddah ta fara period ba, balle Ahmad, suna komawa gida Jiddah ta wuce daki ta kwanta sai bacci..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 Da daddare Jiddah ta fito daga dakinsu, ta karaso cikin parlon ta xauna tana kallonsa da murmushi fuskarta a hankali tace "Ina yini" Ya d'an kalleta yace "Lafiya lau Jiddah, ya jikin?" Tace "Naji sauki, ya su Mommy" yace "Alhmdlh... kin sha bacci" ta d'an kallesa tace "Wai tun daxu ka xo?" Yace "Yea, almost an hour and a half now, kina ta bacci abun ki" Rufe fuskarta tayi tace "Ayya, to yaushe ka dawo, na xata wata daya kace min xaka yi" ya shafa beard dinsa yana murmushi yace "Ai kawai na xo dubaki ne xan koma gobe in sha Allah" Ta wara ido tace "Tun daga Lagos din ka xo dubani?" Yace "Yahh, is there anything wrong with that?" Ta girgixa kai tana murmushi, yace "Da Maimoon tace min anyi hospitalizing dinki i was so disturb, shine kawai na biyo flight xuwa Kaduna just to check on u" a hankali Jiddah tace "Toh nagode" Yayi mata murmushi yace "Amma kinji sauki sosai yanxu ko?" Tace "Um naji sauki sosai, Alhmdlh" Yace "Maa sha Allah" bude kofar parlon aka yi duk suka juya, tun da ya shigo yake kallonsu, Shi dai Yusuf ya maida dubansa kan Jiddah da ta sunkuyar da kanta, Abuturrab ya karasa dinning ya ajiye ledan hannunsa sannan ya dawo parlon ya d'an kalli Yousuf yace "Good evening" Yusuf ya daga kai ya kallesa yace "Good evening, ya aiki...." Abuturrab ya nufi kofa ya fita yace "Alhmdlh" Bayan few minutes Yousuf ya kalli Jiddah yace "I will be on my way now Jiddah, my flight will be around 8 tomorrow" Ta kallesa tace "Toh bari in gaya ma Umma" Yace "Noo, u don't need to, xan kirata idan na tafi" Tace "Toh shkkn" mikewa yayi ita ma ta tashi ta rakasa xuwa waje, a compound yana kallonta yace "Ya karatun?" Tace "Lafiya Alhmdlh" Yace "Ki maida hankali don ki samu kiyi waec next year kin ji?" Tace "Toh nagode" Bakin gate ta rakasa ya ciro kudi a aljihunsa ya mika mata yace "Ban kawo maki komai ba, so u can get whatever u wish" Ta dinga kallon kudin memories din lkcn da Abuturrab ke xuwa wajenta a hayi ya hau dawo mata, shi kadai ne ya ta6a bata kudi da yawa haka ta ba Baabarsu, wajensa ta fara ganin kudi da yawa, Yousuf dai kallonta kawai yake ganin yanda take kallon kudin, can tayi murmushi tana girgixa masa kai tace "Aa nagode" Yace "Ni na baki ki amsa Jiddah" Daga kai tayi suka hada ido da Abuturrab dake tsaye jikin motarsa a bit far from them, ta sauke idonta tace "Ni bana bukatan komai don haka ba abinda xanyi da kudi, nagode Allah ya saka da alkhairi" Yousuf ya dinga kallonta, sai kuma yace "Ni nace kina bukatar wani abun ne!" Ita dai bata ce komai ba, yace "Toh shkkn sai da safe" Yana fadin haka ya xaga ya shiga motarsa ta juya ta koma cikin gidan, dakinsu ta shiga direct ta kulle kofar tayi kwanciyarta, Maimoon da ke danna laptop tace "Sai ga yaya Aliyu ya xo yau ma" Jiddah ta kalleta tace "What about that?" Maimoon tace "Atoh ni naga kwanan nan sai yayi ta xuwa gidan nan bayan mu sai mu shafe wata da watanni bamu gansa ba in dai ba Ya Ahmad na nan ba, to shine abun ke bani sleepless night..." Tagumi tayi bayan ta fada hakan, Murmushi Jiddah tayi tace "Za ki ga Sleepless night" Maimoon ta fashe da wani dariya tace "But on a serious note me ke kawo Ya Aliyu gidan nan don Allah?" Jiddah tace "Toh ki tambayesa mana" Maimoon tace "Ni kaza??? Bari dai kawai in sa a raina saboda yana son su yi sulhu da Umma ne yake sintirin xuwa, kinsan fa Umma haushinsa take ji tun lokacin bikinsa da wnn ajebo din, amma bari dai in ci gaba da xuba ido ko xan gano wani abun daban" Jiddah ta juya mata baya bata ce komai ba, abinda ya faru daxu a hospital ne ya fado mata, ta turo baki sai kuma ta kulle idonta da sauri. Kwana uku Jiddah tayi tana period kafin ya dauke har a lkcn kuma Umma bata san tayi ba, amma throughout period din babu wani ciwo da ta ji, sai dai bata iya cin abinci ne kawai. Ranan talata ta koma gidan Ramlah ta ci gaba da karatun ta.... As usual ranan friday da yamma Abuturrab ya shigo gidansa from Kano state, Aneesah ta fito daga kitchen tana sanye da kananun kaya ta karaso da sauri ta rungumesa warmly tace "Welcome back my captain" Ya d'an kalleta yace "Thank you" Ta durkusa ta fara cire masa cover shoe din kafarsa, da kansa ya karasa cirewa yayi wucewarsa sama, ta bi sa tana rike da jakar laptop dinsa da ya ajiye... Har ya fito wanka tana dakin ta shigo masa da abinci ta baxa kan carpet da zobo drink, ya gama shiryawansa cikin kananun kaya, cike da shagwaba tace "In xuba maka abincin yanxu ne My Captain?" Yace "Na ci abinci tun after juma'at prayer" Lkci daya ta hade rai tace "What did u mean then??" yace "I mean xan ci anjima in sha Allah, yanxu Abba na kirana ne" bata fuska tayi ya gama abinda yake ya dau car key yace "Sae na dawo" daga haka ya nufi kofa ya fita, da sauri ta mike ta bi bayansa tace "Captain nima yau nake son xuwa gaida su Ummi fa" Ya girgixa kai yace "Ni kin ga sauri nake yanxu, sai dai gobe" Tabe baki tayi har ya fita parlorn. Abuturrab na isa gida a waje yayi parking ya shiga ciki, parlon Abbansa ya nufa yayi sallama bakin kofa har aka amsa masa sannan ya shiga, Abba ne xaune parlon da uncle dinsa Alhaji Umar, ya xauna kasa duk ya gaishesu, bayan few minutes Abba yace "I wanted asking you about that girl with Umma" Abuturrab ya daga kai ya kalli Abba, Abba yace "A wani anguwa suke a can hayin rigasa?" Abuturrab ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Me ya faru Abba?" Abba yace "Babu abinda ya faru, sani muke son yi..." Ya sauke idonsa sai kuma yace "Ni ban san sunan anguwan ba" Abba yace "Amma kasan anguwan ai ko?" Da kyar yace "Na sani" Abba yace "Toh madallah" Alhaji Umar yace "Ko kuma kawai ka dangana mu da gun mai anguwan tunda ka san sa" Abuturrab yace "Abba wani abu ya faru ne?" Abba yace "Not at all, gobe asabar tunda kana nan sai mu tafi gaba daya" Abuturrab bai kuma cewa komai ba, Abba yace "I think that's all" Mikewa Abuturrab yyi yace "Xan je in gaida su Ummi" Abba yace "Alright" fita yayi daga parlon, ya tafi dakin Hajja, Hajja tayi masa kallo daya ta karasa dage labulayen dakin da take yi, yace "Ina yini" sai da ta fara kallonsa don tabbatar da cewar da ita yake sannan tace "lafiya lau" Tsintsiya ta dauka tace "Yanxun nan muka gama waya da Kabiru, kaga da nayi masu bori ai gashi an dau maganata da muhimmanci, da fa gantalar da xancena aka so yi, basu san ni er banxa bace idan tsiyata ta tashi, amma duk Safinah ce munafukar.. tun farko naga yanda ta dau maganar tawa ai" Abuturrab dai kallonta kawai yake, Hajja tace "Shi ma El-Basheer din mun yi waya da shi daxu ai..." Abuturrab yace "Me ke faruwa?" Hajja ta kallesa tace "Aa wannan kuma sirrinmu ne, babu ruwanka, kai wa kake gaya ma sirrinka balle mu bude maka cikinmu?? Kaji min mutumi dai, ko a Masar wanda ke yi da kai da shi kake yi ko da kuwa jininka ne..." Mikewa Abuturrab yyi ya nufi kofa ya fice daga dakin, Hajja tace "Da dai ya fi maka, nan nan nan ka auro dangin xabiya har aka gama bikin nan babu karen da yayi shawara da ni balle in tofa Albarkacin bakina, mu dai duk yanda aka ce mana haka muka dinga yi kamar shashashai, daga karshe ma ashe er iska kazama ka auro.. to ka dai yi ma kanka wllh" Abuturrab na fita bangaren Ummi ya tafi, Bayan sun gaisa, Ummi da ta lura da mood dinsa tace "Is there anything?" Ya girgixa kai yace "Nothing" Ummi ta ci gaba da aikin da take, bayan few minutes Abuturrab yace "Daxu kafin mu taho daga Abuja Abba ya kirani yana nemana, and na xo yanxu sai yake tambayata unguwar su Jiddah" Ummi ta kallesa tace "Wacece Jiddah?" Abuturrab yyi shiru yana kallonta, Ummi tace "Ohh... sure ni ma ya tambayeni nace masa sai dai a kiraka..." yace "Toh me ke faruwa Ummi?" Ummi tace "Baka tambayesa ba kafin ka fito?" Shiru yyi, Ummi tace "Toh nima ban sani ba kam" Mikewa yayi yace "Xan koma gida sai anjima" Ummi tace "Toh Allah ya kiyaye" ya nufi kofa ya fita, kallo daya yayi ma bangaren Aunty ya fice daga gidan gaba daya. Ahmad ne xaune dakin Umma yana kallonta yace "Me yasa Hajja take haka ne wai Umma?" Umma ta ta6e baki tace "Ni kuma idan ka tambayeni in tambayi wa? Abun dai gashi nan gashi nan kamar wasan yara, amma laifin su Alhaji Usman din ne dake biyeta ai" Ahmad yace "How will that even be possible? Shi El-Basheer din ne yace masu haka?" Umma tace "Kaga wannan xancen bacin rai yake sa min Ahmad" Ahmad ya mike yace "Xan kira Bashir din yanxu" daga haka ya fita dakin, nasa dakin ya koma ya xauna gefen gado sannan yyi dialing number El-Basheer yana fara ring ya daga, suka gaisa sannan Ahmad yace "Kana Bauchi ne?" El-Basheer yace "Yeahh..." Ahmad yace "Wani labari nake ji wajen Hajja shine na kira so i can confirm from u" El-Basheer yace "Labarin me kenan fa?" Ahmad yace "Auren da kake nema" El-Basheer ya d'an yi dariya yace "Ohh really? Nima nake neman ma kaina kenan" Ahmad yace "Haka nake tunani" El-Basheer ya girgixa kai yace "Aa su dai suke nema min, ni ba ruwana" Ahmad yace "Ban gane ba ruwanka ba, dama xa ayi abu without ur consent ne?" El-Basheer yace "You heard me right Ahmad, su suke nema min aure ba ni ke nema ba" Ahmad yace "Toh Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi" El-Basheer yace "Ameen" Ahmad yayi masa sai anjima sannan ya katse wayar... Abuturrab na xaune main parlor din gidansa tare da Ahmad, Ahmad yace "Magana xaka min ba shiru ba Captain" Abuturrab yace "Ni ban gane tambayar nan taka ba" Ahmad yace "Ohk haka kace?" Abuturrab ya gyara xama yace "But me yasa wnn thinking din ma ya xo maka at the first place Ahmad, u can see i am happily married with my wife, menene xai sa kayi tunanin i have anything to do with that girl? Da ina da ra'ayinta ai kome xai faru ni baxan amince in saketa ba lkcn da su Abba suka min umarnin yin hakan" Ahmad yace "Is that so?" Abuturrab yace "Yes" Ahmad yace "Ohk then, i was mistaken kenan, cause ni a nawa tunanin if u have nothing to do with something baxa ka dinga bibiyan abun blindly ba..." Abuturrab ya dakatar da shi yace "They are some kind of talks dake 6ata min rai.. what are u insinuating now?" Ahmad yace "Nothing!!" Abuturrab ya ja tsaki yace "Da ina da intention din xama da ita babu wanda ya isa ya sa in saketa.... Balle ma duk su gama haukansu" Ahmad yace "I am glad i cleared this now" Mikewa yyi yace "Sae mun yi magana" daga haka ya nufi kofa, Abuturrab ya jinginar da kansa jikin kujera ya bi sa da ido. Da daddare Jiddah ta fito wanka kenan tana shiryawa Maimoon ta shigo dakin rike da wayarta tana xaro ido ta mika ma Jiddah wayar murya can kasa tace "Ya Aliyu" Da mamaki Jiddah ke kallon wayar, can ta amsa ta kai kunne jin shiru tayi sallama murya can kasa, daga daya bangaren taji yace "Kina jina?" Tace "Eh" yace "Duk wanda xai ce ki kai sa can gidanku a hayi kice baki san hanyar gidan ba" Tayi shiru tana sauraronsa, calmly yace "Kin ji abinda nace maki" Tace "To saboda me?" A takaice yace "Saboda haka nace maki" kasa ce masa komai tayi, taji ya katse wayar, tana kallon Maimoon ta mika mata wayarta, Maimoon ta amsa tace "Me yace maki?" Girgixa kai tayi tace "Abu yayi misplacing a hospital yake tambayata ko na gani" Maimoon dau ta juya ta fita bayan ta ta6e baki. Xaunawa Jiddah tayi gefen gado ta kasa ci gaba da abinda take tana tunanin to wa xai tambayeta gidansu a hayi. Washegari Asabar tun safe Abba ke kiran Abuturrab wayarsa a kashe, Hajja sai cewa take "Yau naga bala'i.. to wai baku san gidansa bane Usman, ko kuma mu tafi a dau yarinyar ai baxata rasa sanin hanyar gidansu ba tunda ba kwakwalwar kaza ce ita ba da xata mance gidansu, amma kun tsaya kuna ta kiran mutumi dake can yana bacci tare da matarsa, ranan ma fa da muka je gidan da Jiddah suna can suna ta bacci da rana tsaka har da garkame kofa" Abba yace "Toh sae a je da yarinyar ta nuna unguwar nasu" Aunty ce tsaye dakinta tana waya duk abun duniya ya isheta, Godiya tace "To ai duk laifinki ne Hafcy, da tun farko kin fito min da haka ai ni da tuni naje anyi abinda xa ayi an gama" Aunty tace "Ni kinga abinda yasa ban ce maki komai ba naga suna yawan waya har ma da chatting sai na fara tunanin ko abinda nake so ya kasance ne ke son kasancewa a raina, ashe ba haka bane" Godiya tace "Yanxu shi yariman da bakinsa yace yana son shegiyar yarinyar?" Aunty tace "Ji wata magana, da bai ce yana sonta ba neman auren me xa aje yi kuma, bbu wanda xai masa dole, da yardansa shi sa kika ga abun ke son yi nisa, wai yau fa xa aje can gidansu yarinyar" Godiya tace "Toh bari dai xan kira ki xuwa anjima" Daga haka ta katse wayar, Aunty ta xauna gefen gado tayi tagumi, Yarima da take ma Aisha sha'awa ne xa a nemi a makala ma wata can mara asali da dangi da kaf duniya bbu wanda take jin tsana irin ita, sake kiran Number mum din El-Basheer tayi amma har ya katse ba'a dauka ba, ta ja tsaki tace "Ko ina ta jefar da waya haka nake ta kira tun daxu" Kusan a guje Aneesah ta nufo Abuturrab ganin ya dau wayarta ta kwace tace "Wayana ne ai captain, naka na parlor" Ya dinga kallonta, sai kuma yace "Kira xan yi" tace "Naka fa?" Yace "A kashe yake" Tace "A kashe kuma, to me yasa baka sa a caji ba" Yace "I switched it off ba wai bani da caji ba" Tace "Toh bari in baka karamin wayana wnn ba credit" Bai ce mata komai ba ta karasa ta dau karamar wayar sai da tayi deleting duk out going da incoming sms snn ta kai masa wayar, amsa yayi ya fita parlor, ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya, downstairs Abuturrab ya sauka yayi dialing number El-Basheer dake kansa, yana fara ring ya daga, Abuturrab yace "How are you doing?" El-Basheer yace "Alhmdlh, ya aka yi wayarka a kashe?" Abuturrab yace "Na shiga bathroom da shi ya fada cikin ruwa" El-Basheer yace "Hard luck, grandma tace ana ta kiranka ka kashe waya" Abuturrab yace "Saboda me xan kashe waya" El-Basheer yace "Ai ban sani ba" Abuturrab ya shafa beard dinsa yace "Jiya na samu labarin matar da aka samar maka" El-Basheer yace "Ashe baka samu labarin da wuri ba kenan" Abuturrab yace "Amma nayi mamaki" El-Basheer yace "Mamakin me" Abuturrab yace "Warce Prince ke da niyyar aure" El-Basheer yyi murmushi yace "Sai dai kuma kasan ba prince din yayi ma kansa xabin ba" Abuturrab yace "A seventeen year old girl? Sai kace ka auri me kenan?" El-Basheer yace "Hajja xa mu yi ma wannan tambayar" Abuturrab yace "Kuma ka bani mamaki" El-Basheer yace "Na me fa?" Abuturrab yace "Ban yi tunanin xan rabu da abu ka dawo ka nuna kana son abun ba, in saki mata kace xaka aura" El-Basheer yace "Saboda hakan haramun ne?" Abuturrab yace "Whatever, amma it's more a less of abun kunya hakan da kayi, Allah ka bani mamaki" El-Basheer yace "From the beginning i was never serious with Hajja saboda ina ga kamar abinda baxai ta6a faruwa bane, amma wannan words din da ka fada min yanxu ya sa naji dole ma sai na auri Jiddah, kuma ka xuba ido ka gani... Till then" daga haka ya Katse wayar, Abuturrab ya dinga kallon screen din.... Ummi da wata frnd dinta tare da Aunty suka tafi can gidan Umma don nufin tafiya gidansu Jiddah tare da Jiddar, bayan Umma da Ummi sun kebe a daki Umma tace "Yanxu yaya menene amfanin wannan abun da Hajja ke shirin yi, duka duka shekarun yarinyar nan nawa, ko secondary din ma baxa a bari ta gama ba, yaushe ta samu yancin kanta har xa a fito da wani xancen aure a kanta? Don Allah ni dai a san yanda xa ayi a janye maganan nan wllh banyi farin ciki da shi ba, ina ita ina family dinsu El-Basheer? Yarinyar da har yanxu bata samu karatun kirki ba, takaicin da ta sha a gidan Aliyu ai kadan ne da wanda xata je gidan sarautan nan ta fuskanta... " Ummi tace "Kar ki yarda Hajja ta ji wannan abinda kike gaya min, nima na fara kawo mata hakan tace bakin ciki nake ma yarinyar saboda Bashir bai ce yana son Nafisah ba... Tun daga sannan na ja bakina nayi shiru, mu dai namu kawai fatan alkhairi" Umma tace "Aa wllh idan tsoron gaya mata gaskiya kuke sai ni in buda baki in gaya mata abinda ke raina, ya muna xaune lafiya xata dawo daga Masar duk ta bi ta daga mana hankali haka, ba fa Bashir din yace yana so da kansa ba, duk hade hadenta ne da rikicin tsufa irin nata, ni baxan amince da hakan ba gaskiya, yarinyar da nake so har university sai ta fara kafin aure... Sannan ni akwai d'an aminiyata ma a kasa" Ummi ta juya ta fita daga dakin kawai, Umma dai sai tafarfasa xuciyarta ke yi, Aunty kuwa na xaune parlor bakin ciki na ta cinta ita ma, Jiddah ta fito dag dakinsu ta durkusa ta gaida Ummi, sannan ta gaida frnd din Ummi da Aunty, Ummi tace "Xa ki gane anguwar ku Jiddah?" Jiddah tayi shiru tana kallonta, Can ta girgixa kai a hankali tace "Aa" Ummi tace "Baxa ki gane ba??" Jiddah ta gyada mata kai, Umma dake tsaye parlon taji dadi har ranta da Jiddah tace baxata gane gidansu ba... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada Instagram -fareeskinglow_89 TikTok-fareeskinglow Facebook page-fareeskinglow WhatsApp -08031898240 Ummi ta kalli Umma tace "Ahmad ai xai gane gidan shi ko?" Umma tace "Anya kuwa? Amma dai bari in kirasa in tambayesa" Daukar wayarta tayi ta wuce daki, bayan few minutes ta fito tace "Ai kam bai sani ba wai shi ma" Ummi dai kallonta kawai take, Aunty tace "Tunda duk basu sani ba ai sai mu wuce gida kawai a nemi wani solution din, don baxa mu kama hanyar xuwa inda bamu sani ba gaskiya," Umma tace "Ai ko dai" Haka nan su Ummi suka koma gida, Aunty farin ciki fal xuciyarta, ai ko ita kadai ta isa ta hana xuwa gidansu Jiddah.... Hajja ce xaune parlon Abba ta dafe kai, cike da bakin ciki tace "Huhuhu... mutane dai yanxu tsoron Allah wuya yake masu ni Dije, da kyar al'ummar yanxu ke tsoron Allah wllh, yo banda rashin tsoron Allah ba a san gidan Aliyun bane da baxa a je a tisa keyarsa ya kai mu gun dangin yarinyar ba? Ko kuna da wata manufa da kuke boyewa a ranku ne ban sani ba, ni dai wllh ban ta6a sanin Masar rahama bace sai da na baro can, wllh da can ne duk haka baxai dinga faruwa ba, yo ina hakan xai faru kowa ya tashi ya girma da tsoron Allahnsa" Abba yace "Yanxu ya kike so ayi Hajja, ba fa sauri ake wannan lamarin ba..." Hajja ta dakatar da shi a fusace tace "Aa wllh sauri nake, kune dai baku sani ba, yanda xa ayi yanxu kuma shine a tashi a tafi gidan wancan mutumi Aliyu, idan kuma duk baxa ku ba, ni da kai na sai in dau gyale in je in dau yarinyar mu tafi gidan Aliyun in sa shi gaba ya kai ni unguwar tunda shi ya san asalinta" Abba yace "To gaskiya idan haka xaki dinga axalxalan lamarin nan ni Hajja xan cire hannuna, sai shi Mai martaban ya taho da kansa..." Hajja ta runtse ido tace "Qul Usman, kar ka sake fadin haka wani sai yace bakin ciki kake wllh, nima don na kai xuciya nesa ne da haka xance wllh, ba fa wani yasa gantalallan d'an ka ya saketa ba Usman, bakin ciki kake ma d'an yayan naka ne? Aa to gaskiya har ka ban tsoro, da kaina xan tashi yanxu in shirya in tafi gidan Aliyun, ai ba bakona bane gidan, irin wannan lamarin ance maka ana bin sa da sanyi sanyi ne" Tana fadin haka ta mike ta fice daga parlon, sai da ta fara sa aka kai ta gidan Umma wai xa ta tafi gidan Aliyun tare da Jiddah, daga can shi kuma sai ya kai su hayin, Umma dake tsaye bayan kujera tace "Toh ai bata nan Hajja sun tafi Islamiyya, kuma ba ma gidan nan take ba yanxu tana gidan Ahmad ne" Hajja na kallonta daga sama har kasa tace "Waye kuma Ahmad, ana magana sai ki dinga wani sako Ahmad... Ita kuma ba sai ki kira makarantar kice a turota gida ba, ko su basu san uxuri bane" Umma tace "Hajja idan kin je can gidan Aliyun kuma Allah ya sa kin samesa..." Da sauri Hajja ta katse tace "Yana nan ba inda xai je ana hutun karshen mako, ke dai kiyi ta kanki ki fada abinda xaki fada in tashi..." Umma tace "Shkkn, sai ya kai ki har gidan tunda nasan baxai rasa sani ba, amma xancen a kirawo makaranta ace yarinya ta dawo a katse mata karatu bai taso ba balle ma ni bani da number shuwagabannin makarantar" Mikewa Hajja tayi ta nufi kofa murya can kasa tace "Aniyarki ta baki, mata kin narka kiba kina ta xuba ma mutane iko, yaushe xa a ga haka a Masar, 'ya yan bakin ciki kawai... Daga ke har Uban Aliyun" sannan ta fita.... Daga sama har kasa Aneesah ke kallo Hajja bayan ta bude kofar, can ta ja gefe ta kauda kai tace "Sannu da xuwa" Banxa da ita Hajja tayi ta shige parlon kai tsaye ta tafi kan kujera ta xauna, Aneesah ta bi ta da wani shegen hararan tsana, ita dai kaf kaduna bayan Jiddah bata da wanda ta tsana kuma kamar Hajja, Hajja tace "Zo ki kira min mijinki ni wajensa na xo ba wajen wani ba, kuma sauri nake yi" Babu yabo babu Fallasa Aneesah tace "To ai baya nan Hajja, da kin kirasa kafin ki xo...." Ko rufe baki bata yi ba sai ga Abuturrab yana sakkowa, tsaye shi ma yyi a stairs din karshe ganin Hajja, Hajja ta kalli Aneesah tace "Kika ce baya nan?" Aneesah tace "Ohh ban ma san ya shigo ba, ni ina kitchen ne" Hajja ta ja tsaki ta mike tace "Mu je Aliyu, ba xama na xo yi ba..." Bai yi musu ba saboda Aneesah ya bi bayanta suka nufi kofa, Aneesah ta kirkiro murmushi tace "Toh baki sha ko ruwa ba Hajja, ga girki ma ya kusa nuna yanxu" Hajja tace "Aa wllh Alhmdlh, ai daga gida nake, kuma ni wajen jikana Aliyu na xo ba xama na xo yi ba dama" Daga haka ta fice Abuturrab ya bi bayanta, Da sauri Aneesah tace "My captain abincin fa?" Yyi mata alama da hannu yana xuwa, yana fita tayi wani murmushi ta xauna saman kujera ta dau chips dinta ta ci gaba da ci. Suna fita parking space Hajja tace "Kaga da kyau ai da muka fito tunda maganar sirri ne, baxan bar wata 6are can taji cikinmu ba, wai don rashin kunya tayin ruwa take min saboda in sha in tsuge da gudawa, kai hancinka baya jin karnin da parlon nan ke yi ne kamar an fasa danyen kwai, ko iyayenta basu mata irin turarurrukan wutan xamanin nan da naga ana yi ne, wllh fa kazama ce, da a Masar ne dole a raba wannan auren naku don guje maka wata cutar, toh dai ba ruwana da abinda bai shafeni ba, yanxu so nake mu hau mota ka kai ni gidansu yarinyar nan Jiddah, naji ance a hayin rigasa take koh?" Ya dinga kallon Hajja kafin yace "Ehh, me xaki je kiyi a can?" Tace "Aa wannan sirri na ne, yanxu muje ka kai ni, ni kadai ma na ishi inje gun iyayen nata... Waye kuma Usman ko Umaru" Abuturrab yace "Toh bari in dauko makullin motar" Tace "Toh yi maxa" tana tsaye har ya shiga ya fito rike da makullin motarsa, ya bude mata back seat ta shiga sannan ya shiga maxaunin driver ya tada motar, yayi horn aka bude masa gate ya fita, Hajja tace "Ina gamawa da Bashir kai ma xan samar maka xukekiya mai tsafta kamar Jiddah, ko don saboda ka tsira da lafiyarka" Ta madubi yake kallonta, tace "Kar fa a ga ina ta koda tsaftar wannan yarinya Jiddah wllh tana da shi ne, ni fa na sha gwada in ga ko tsaftar ganin ido take amma wllh ashe ba haka bane, kaga ko shara ka sa ta duk sai ta bi ta dage ko mai ta gani ta share fess, sannan idan ta gyara maka gado sumul sumul kamar kar ka bar kowa ya hau... Sannan naga ta san muhimmancin turaren wutan nan na xamani, tana gama gyaran daki take sakawa, bandaki kuwa da na sa ta ta wanke sai da nayi xaton 6atan hanya nayi da na shiga, wllh har wani talli yake gwanin ban sha'awa, abinda kanninka su Aisha da Nafisah basu da shi, Allah bai basu ba... Toh amma dai ban sani ba ko ganin ido take, idan ma shi din ne dai ai ta iya aikin duk da haka, wasu ma na ganin idon basu iya ba" Abuturrab dai bai ce mata komai ba, har suka shigo Hayi Hajja bata yi shiru ba surutu kawai take a motar, tafiya kawai yake har ya kusa karshen kwalta, ya ga wani d'an gida da aka rushe kusan rabinsa kasancewar a bakin titi yake, har sannan kuma ba a gyara gidan ba don kamar ma anyi abandoning din gidan ne, waje ya nema yayi parking yana kallon wajen rusasshen karamin gidan, can ya kalli Hajja ya nuna mata yace "Ga gidan can Hajja, naga kamar kuma ba kowa yanxu" Hajja ta sauko da sauri tace "Ba kowa kamar yaya? Wannan kuturum gidan ne gidansu Jiddar?" Yace "Ehh" karasawa tayi tana kallon wasu da suka kasa kayan siyarwansu a kasa tace "Ke yarinya ina masu rubabben gidan nan?" Yarinyar tace "Sun tashi tun da aka yi rusau" Hajja ta gwalo ido tace "Suka tashi suka je gidan uban wa?" Yarinyar ta buda hannu alamar bata sani ba, Hajja ta kalli Abuturrab da ya jingina da motarsa ya rungume hannu yana kallonta, tace "Kai kaji wai sun tashi ba a san inda suka je ba" Ya daga kafada shi dai bai ce komai ba, Hajja tace "Yau naga abinda ya isheni, yanxu babu wanda xa mu tambaya me d'an wayo a nan ko an san inda suka koma, ai dole baxa su wuce cikin hayin ba dai tunda dai naga alamar talaucin nasu ba na wasa bane..." Abuturrab yace "An ba ma wani gadinsu ne da xa su fadi inda suke? kinga kawai mu tafi Hajja, ranan nan ya fara damuna..." cike da masifa Hajja tace "In tafi ina banyi abinda ya kawo ni ba, ko wiwi kake sha ne?? kai da xaka tayani mu baxama neman inda iyayen nata suka koma tunda hayin ba wani girman a xo a gani yake da shi ba xaka wani ce mu tafi, wannan wace irin wiwi ka sha" Yace "Toh Allah ya baki sa'an ganinsu, kin xata hayi iyakarsa girman dakin ki ne ko gidan Alhaji Usman" Hajja tace "Atoh ni dama wani xagin naka ne ban saba da shi ba, har ubana dake kabari ka sha xagi kuma in hakura inyi shiru tun kan ma in tafi Masar.... Amma dai ni ba mahaukaciya bace baxan kulaka ba, kuma in sha Allahu ina nan har sai na hadu da iyayen nata sannan in tafi..." Hannu ya sa a aljihu ya ciro dubu daya ya sakala mata a katon jakarta yace "Duk ranan da Allah ya sa kika gansu sai ki dawo gida, ni dai na tafi, kin xata nan Masar din ki ne" Daga haka yayi shigewarsa mota ya wuce, Hajja ta gyara tsayuwa ta bi sa da kallo har yayi nisa. Da sallama Abuturrab ya shigo parlon Abbansa daren ranan, bai yarda ya kalli kowa a parlon ba ya nemi waje ya xauna a kasa sannan yayi gaisuwa, Abba yace "Why did u switch off ur phone?" Ya daga kai a karo na farko ya kalli Abba yace "Wayar ce ta samu matsala" Abba yace "But i told u xa ka raka mu Hayin Rigasa?" Yace "Abba ni ai ban san gidansu ba..." Abba yace "Sai ina ka sani?" Shiru Abuturrab yyi, Abba yace "Wajen mai anguwa?" Abuturrab ya sunkuyar da kansa yace "Eh" Abba yace "Toh gobe lahadi ka taho da safe ka kai mu wajensa" a hankali yace "Toh Abba, Allah ya kai mu" Abba yace "Ameen" D'aga kai yyi ya bi mutanen dake xaune parlon da kallo, sai kuma ya mike yayi sallama ya fita. Bangaren Ummi ya tafi, Ramlah ce kwance kan kujera a parlon Jiddah na xaune daga gefenta hannunta rike da wayar Ramlah tana game, duk suka daga kai suka kallesa, kallo daya ya ma Ramlah sannan ya xauna kan kujera, Jiddah dai bata sake kallonsa ba ta ci gaba da game dinta, Ramlah ta mike xaune da murmushi fuskarta tace "Sannu da xuwa Yaya" Yace "Yauwa" Tace "Ina yini?" Yace "Lafiya" Ta koma ta kwanta tace "Ya Aunty Aneesah?" Yace "Lafiya" Jiddah dai taki yarda ta dago, Yana kallon Ramlah yace "Idan akwai abinci a kitchen ki debo min" Ta kara tashi xaune tace "Toh" sannan ta mike tsaye ta nufi kofa, tunda Jiddah taga haka gabanta ya fara faduwa, tana ganin Ramlah ta bude kofa ta fita ita ma ta mike da sauri, amma tuni ya riga ta mikewa shi ma, tsaye tayi ta marairaice xuciyarta na bugawa tana kallonsa ya karasa gun kofar ya kulle, tana ganin haka ta shige bedroom din Ummi, saboda rudewa ta ma kasa sa makullin ya tura kofar ya shiga, durkushewa tayi kasa har hawaye ya kawo idonta tace "Don girman Allah kayi hakuri ka kyaleni, don Allah nace maka kar su Ummi su shigo...." Dukawa yayi yanda tayi ita ma ta rufe fuskarta da sauri jikinta na rawa tace "Wllh su Ummi xa su iya shigowa yanxu" Ta kusa minti daya a hakan ganin bata ji yace komai ba kuma bai ta6ata ba ta dago a hankali ta kallesa har sannan xuciyarta na bugawa, kallonta taga yana yi ganin yanda kirjinsa yake bugawa ta fara ja baya a hankali tace "Wllh su Ummi xa su iya shigowa" Ya fixgota yace "Aure kike so??" Ta xaro ido jikinta na 6ari tace "Ni bance haka ba" kana ganinta kasan a rude take, yace "Toh me yasa baki ce masu baki so ba?" Ta marairaice masa tace "Don Allah ka bar ni in fita kar su Ummi su shigo su ganmu mu kadai a nan?" Yace "Sai aka yi yaya idan sun ganmu?" Buda baki tayi tana kallonsa ta girgixa masa kai tace "Ai bai kamata ba..." Runtse ido tayi bayan ya kara fixgota har tana jiyo saukan breathing dinsa yace "A wajensu da wajenki ne bai kamata ba...." Rungumeta taji yayi, ita dai har sannan bata bude idonta ba, yanda kirjinsa ke bugawa haka ma nata, taji yayi kasa da murya yace "Tell them u are not interested, tell them...." Sai kuma yayi shiru, haka kawai taji jikinta yayi sanyi ta buda ido a hankali... babu abinda ta gani a lkcn sai ranan farko da ta fito daga cikin gidansu a hayi ta gansa tsaye kofar gidansu ya xo bata hakuri, a hankali ta daga kai ta ga idonsa a rufe suke, hannunta taji ya kamo cikin nasa, ta kalli hannun nasu sannan ta kara daga kai ta kallesa taga har sannan idonsa a rufe suke, lamo tayi jikinsa tana kara jin bugun xuciyarsa, bata san dalilin da ya sa taji hawaye ya taho mata ba, Saukan hawayen nata da ya ji a jikinsa ya sa ya bude idonsa ya kalli fuskarta suka hada ido, ganin hawayen da take yi ya hade goshinsa da nata murya can kasa yace "A ganin ki ina takura ki ko?" Ita dai bata ce komai ba har sannan hawaye na sauka idonta, a hankali yace "I want nothing but the best for u, ban shiga rayuwarki da wata manufa na daban da ya wuce taimakonki da inganta maki rayuwa ba, may be i was mistaken... a lot happened and are still happening..." Shiru yayi sai kuma ya rufe idonsa holding her more closer to him, calmly yace "I don't know.. i was mistaken at many thoughts then... Things turn out the way they weren't suppose to" Xaro ido Jiddah tayi jin an bude kofar parlor ta turasa da karfi, a tare suka mike tsaye, yana kallonta kafin yace komai ta bude kofa ta fice da sauri, Ramlah ce ta shigo parlon da abinci, Ramlah dai sae kallonta take ganinta a bedroom din Ummi, Jiddah ta nufi kofa ta fita don ta ki yarda su hada ido, Ramlah ta xauna kan kujera amma gaba daya kanta ya daure, sae kallon kofar dakin Ummi take, bayan few minutes dai ta mike ta nufi kofar ta bude a hankali, tsaye ta gansa kusa da window staring into space, Ramlah ta yi yake bayan sun hada ido tace "Dama na kawo maka abincin ne Yaya ashe kana ciki" Yace "Ohk" juyawa tayi ta fita, ta koma saman kujera ta xauna a hankali with different thought in her mind. Ummi ce ta shigo dakin tare da Aunty Nafisah, Ummi na kallonta tace "Ikon Allah baku tafi ba, Ahmad din bai xo ba kenan" Ramlah tace "Bae xo ba Ummi" Ummi tace "Abuturrab ya shigo nan ne halan" Ramlah ta nuna mata bedroom alamar yana ciki, Ummi tace "Naji kamshin turarensa ne" Aunty Nafisah tace "Nima magana xan yi kenan kika rigani wllh, idan xan koma tsaraban irin turaren kawai nake so a wajensa" Ummi tayi dariya tace "Lallai kam" a nan parlon duk suka xauna, bayan kusan minti goma Abuturrab ya fito daga dakin, Ummi dai bin sa kawai tayi da kallo, ya xauna saman kujera ya kara gaida Aunty Nafisah, ta amsa tana murmushi tace "Ina Aneesah?" Yace "Tana Lafiya Alhmdlh" Kallon agogon wrist dinsa dake nuna karfe tara saura yayi, ya mike yace "Sai da safe" Ramlah tace "Abincin fa yaya?" Ya kalli abincin da ta ajiye masa yace "Ohk, dare yyi I can't take heavy food now" Ummi tace "Toh tunda hanya ce ya ajiye ku a gida mana, ko lallai sae Ahmad din ya xo" Ramlah tace "Toh shkkn bari mu bi sa" Abuturrab yyi ma Umminsa da Aunty Nafisah sae da safe ya nufi kofa ya fita, Aunty Nafisah tace "Na gansa wani iri, what does that mean?" Ummi ta ta6e baki tace "Ae a haka yake kullum" Aunty Nafisah tace "Haka kuma?" Ummi tace "Dama shi bai da fara'a ae, sannan ba a sanin cikinsa balle kasan me ya damesa" Aunty Nafisah tace "Toh Allah ya kyauta" Ramlah ta dau jakarta da na jiddah tayi ma su Ummi sai da safe, Ummi tace "Jiddar fa?" Ramlah tace "Kilan tana dakin Hajja, can xan je in duba..." Daga haka ta fita, Jiddah na xaune tayi jigum tana ta kallon Hajja dake ta surutanta, amma kusan duk bata ma san abinda Hajja ke cewa ba, Ramlah ta shigo tana kallonta tace "Taso mu tafi Jiddah" Hajja tace "Toh xa ku tafi, Ahmad din ya xo ne?" Ramlah tace "Ehh" Hajja ta tabe baki tace "Shi dai baya ba mutane komai, bakar rowa kamar uwarsa wllh" Ramlah dai ta juya ta fita, Jiddah na kallon Hajja a hankali tace "Sai da safe" Hajja tace "To Allah ya kai mu, ai ni ban san gidan Ramlah kike ba da na dinga kai maku xiyara a kai a kai tunda babu wani babba a gidan, Shi kuma Bashir idan ya aiko wayar xan amsa in ajiye maki, kuma babu shegen da ya isa yace baxa kiyi amfani da shi ba da rai na dai" Murmushi Jiddah ta kirkira ta mike ta fita, sai da ta fara xuwa tayi ma su Ummi sallama sannan ta fito, parlor ta tarda Ramlah na jiranta, ta amshi jakarta a hannun Ramlah sannan suka fita, har suka fita kofar gida babu wanda yace komai cikinsu, Jiddah ta dinga kallon motar da Ramlah ta nufa, lkci daya jikinta yyi sanyi sosai ta bi bayanta walking slowly, back seat Ramlah ta bude ta shiga, a hankali ta kai hannu gaban motar ta bude ta shiga sannan ta kulle, Abuturrab na kallon Ramlah yace "Ke gidanki xa a ajiye ki ai?" Ramlah ta kalli Jiddah da d'an confusion, sai kuma tace "Ohk to shkkn" Jiddah ta xaro ido tana kallonsa sai kuma ta kalli Ramlah, ya tada motar suka bar layin. *fear Allah and pay for Jiddatul Khair before reading* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Parking Abuturrab yyi a kofar gidan Ramlah, Ramlah ta bude motar xata sauka, Jiddah ma ta bude xata sauka, Hijab dinta taji ya rike gam daga kasa, ta kallesa da mamaki amma ta ma rasa abinda xata ce, Ramlah ta kulle motar bayan ta sauka tana jiran ganin ko saukowa Jiddah xata yi, Jiddah ta marairaice tana rike da handle din kofar motar murya can kasa tace "Meye haka wai, ka sakeni in sauka mana" Abuturrab ya hada ido da kanwarsa dake tsaye still waiting for Jiddah to come down, a hankali ya sake Hijab din Jiddah ta bude motar ta sauka da sauri, Ramlah ta masa murmushi tace "Sai da safe yaya" Nodding kawai yayi, tuni Jiddah har ta shige cikin gidan, Ramlah ta bi bayanta... Karfe sha daya da wani abu Ramlah na kwance kusa da Ahmad dake operating laptop dinsa, tace "Doctor" ya kalleta yace "Yess dear" Tace "Ina son in maka tambaya ne dama" Ya bar danna laptop din da yake yace "Ina jin ki" Tace "Nasan yaya baya boye maka komai da ya shafi rayuwarsa da dai sauransu..." Murmushi Ahmad yayi yana kallonta, tace "Ka gaya min gaskiya ko da akwai wani alaka tsakanin sa da Jiddah" Yace "Me yasa kika min wannan tambayar?" Ta d'an yi shiru sai kuma tace "Naga wasu abubuwa ne da suka yi confusing dina" Yace "Kamar me?" Ta gyara kwanciya tace "Daxu a can gida muna xaune tare da Jiddah ya shigo yace in je in debo masa abinci, bayan na dawo da abincin sai ban gansu a parlor ba, i dropped the food sai ga Jiddah ta fito daga bedroom din Ummi, she didn't say a word ta fita, i was so surprise bayan few minutes na karasa dakin na gansa shi ma a ciki, sai kuma still daxu ya ajiye mu a gida, xata sauka mota naga ya rike hijab dinta but duk basu san na gani ba" Kallonta kawai Ahmad yake babu ko kiftawa yana sake assimilating din abinda tace, can yace "Sai aka yi yaya?" Tace "I don't know what she told him kuma daga baya naga ya saketa ta sauka motar" Ahmad dae yyi shiru, Ramlah tace "Tun daxu abun ya tsaya min, cause I am confused" Ahmad ya jawo laptop dinsa ya ci gaba da abinda yake, Ramlah tace "Ko akwai wani abu da ake boye mana ne Doctor?" Ahmad yace "I am confused just as u now Ramlah" Ramlah bata kuma cewa komai ba, Bayan few minutes ta mike ta fita dakin, dakin da Jiddah take ta nufa ta bude a hankali tana kallon cikin dakin, kwance ta ganta idonta a lumshe ta lullube da hijab dinta maimakon blanket da ke ajiye gefe, ta fi minti biyu a tsaye har xata juya Jiddah ta bude ido, mikewa xaune Jiddah tayi tace "Kina son wani abu ne?" Ramlah ta sakar mata murmushi tace "Nothing naga baki kashe wuta bane" daga haka ta kashe fitilar dakin ta juya ta fita ta kulle kofar, Jiddah ta lullube har kanta da Hijab din jikinta ta lumshe ido... Karfe daya da rabi na dare Abuturrab na kwance Aneesah na gefensa kamar xata shige jikinsa tana bacci, lumshe ido yyi ya bude, ya mike xaune a hankali being very careful not to wake Aneesah ya sauka kan gadon ya nufi kofa ya fita parlor ya xauna saman kujera ya rike kansa, ya fi minti talatin a nan sai kuma ya mike ya tafi bandaki ya dauro alwala ya fito... Washegari da ciwon kai sosai Abuturrab ya tashi, hakan bai hanasa ya shirya ya fita gida karfe goma ba ya tafi can gidansu, sai da ya jira na kusan minti talatin sannan suka dau hanyar Hayin rigasa da Abbansa, Alhaji Umar, da wani aminin Abban nasa, shi yake driving so absentminded, har suka iso hayi yayi parking dai dai layin Mai anguwa, kasa ce masu komai yayi, shi dai Abba kallonsa kawai yake ganin yayi parking babu wata magana, ya saci kallon Abban nasa, suna hada ido ya bude motar yace "Abba xa mu karasa ciki da kafa babu nisa" Daga haka ya sauka sauran ma duk suka sauka, Xaunawa Abuturrab yyi saman tabarman dake kofar gidan Mai anguwa suka gaisa da mutane biyu dake nan, Abuturrab ya d'an shafa kansa yace "Gun Mai anguwa muka xo" wani matashi yace "Ayya ai bashi da lafiya yau kwanansa uku a shika" Kallonsa Abuturrab ya dinga yi babu ko kiftawa, sai kuma yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un... Allah ubangiji ya tashi kafadunsa" Suka amsa da Ameen, mikewa yayi yana kallonsu Abba dake tsaye suna jin duk abinda Abuturrab yyi da matasan, Abba da Alhaji Umar da abokinsa suka ma Mai anguwan fatan samun lafiya sannan suka koma gun mota, Abba yace "Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi, idan ya samu laifi sai a dawo ayi magana" Shi dai Abuturrab bai ce komai ba ya tada mota tunani iri iri a ransa, gida ya maida su Abba sannan ya karasa bangaren Ummi ya gaisheta, Ko minti uku bai yi a parlon Ummi ba aka bude kofar, Aunty ta shigo tana kallonsa tace "Wato da ni kake gaba a gidan nan ko Aliyu, sai dai ka shigo ka yo bangaren uwarka idan ka gama abinda ya kawoka ka fice kayi tafiyarka, to kayi ta banxa in dai nice wllh, dama uban me kake tsinana ni da shi banda ma ni da nayi tsaye kan lamarinka tun baka kai haka ba, in dan ta ita uwar taka ce ka xata xaka kai matsayin da kake yau?? To wllh kayi da ni Aliyu, kuma ni nasan tsinanniyar da ta shiga tsakanina da kai, nasan musabbabin duk wannan abinda kake min, xa kuma tasan ni er halaq ce...." Tana gama fadin haka ta fita tana huci, Shi dai danna wayarsa kawai yake, Ummi dake dakinta duk tana jiyo Aunty ta ta6e baki ta gama abinda take ta fito, gaisheta yayi bayan ta xauna, ta amsa tace "Akwai wani abun da tayi maka ne wanda ban sani ba take maka gori yanxu?" Yana danna wayarsa yace "Ko daya Ummi, ni babu wani abu da ta ta6a min" Ummi tace "Ohk, to me ya hadaka da ita yanxu baka shiga ka gaisheta?" Yace "Ra'ayi" Tace "Kamar yanda for years kayi ra'ayin dena shigowa gaisheni sai ka ga dama" D'an murmushi yayi yace "Aa Ummi" Tace "Toh Allah ya kyauta" Shi dai bai ce komai ba, tace "Har yanxu kuna samun matsala da Aneesar ne?" Ya kalli Ummi yace "Me kika gani Ummi?" Ummi tace "Sai naga abu xan tambayeka?" Ya girgixa kai yace "Aa Ummi, tana gyarawa yanxu" Ummi tace "Toh gaya min meye damuwarka Aliyu" Ya daga kai yana kallon Umminsa, Ummi tace "Tell me" Yyi kasa da idonsa, sai kuma ya mike ya koma gefenta ya xauna yyi kasa da murya yace "Ummi addu'a kawai nake son ki taya ni da shi" Tace "Baxan yi ba sai ka gaya min me ke faruwa" Yyi shiru ya rasa abinda xai ce, bayan few seconds cikin sanyin murya yace "Ummi , I don't know how everyone is going to take this, but..." sai kuma yayi shiru yana jin xuciyarsa na bugawa, Ummi tace "Bother not... Go ahead tell me what's happening, i might take it softly" ya marairaice mata yace "Might kuma Ummi, you just have to take it softly" tana kallonsa tace "Ina sauraronka" Ya d'an kalli kofa, Ummi na ganin haka ta mike tace "Mu je daki to" Mikewa yayi ya bi bayanta xuwa dakin. Driving Abuturrab yake a hankali har ya isa gida, bayan yayi parking ya sauka motar, baka ta6a fadin wani kalan expression ne a fuskarsa a lkcn, yana shiga parlor Aneesah ta leko daga kitchen tace "Welcome back my Captain" Yace "Thank you" tace "Na gama hada maka kayan, kaje ka duba ko sun yi" yace "Sai nayi sallah" Bandaki dake parlon ya shiga ya dauro alwala ya tafi masallaci don lokaci yayi, Aneesah ta karasa ta dau wayarta dake ringing bayan ya fita, ganin Aunty ke kiranta ta daga ta kai kunne, daga daya bangaren Aunty tace "Kar ki kuskura yayi tafiyar nan baki amshi abin nan ba Aneesah" Aneesah na ci gaba da taunar cingam din bakinta tace "Sai kace ina hauka Aunty, na fa gaya maki yanxu lafiya muke xaune babu komai wllh, duk abinda nace yana yi, girki kuwa kan ya dawo weekend chef salmah ta xo ta min varieties in xuba a deep freezer, sai dai in ciro inyi warming, kuma wllh yana ci yanxu, gida kuma kafin ya dawo nake sa almajirai su shigo har sama da dakinsa su share tsaff, in basu batattun kwanuka ta can bayan gidan su wanke, iyaka in kunna burner in cika turaren wuta... " Aunty tace "Toh kun kara hada shimfida kuwa?" Aneesah tayi wani dariya tace "Na fa ce maki Aunty Safara'u ma ta yo min sako me yawa last week bayan wanda kika kawo min, lafiya lau komai ke tafiya yanxu" Aunty tace "Toh madallah haka nake son ji, ni kuwa kinsan har yau ko xuwa gaisheni a bangarena baya yi, to amma ni nasan tun bayan da ya rabu da tsinanniyar yarinyar nan da naji ana ce ma Jiddah hakan ya faru, duk gaba daya ya canxa min ke kyace ni makiyarsa ce" Aneesah tace "Ikon Allah, to ita Jiddar haka xaki xuba mata ido Aunty??" Aunty tace "Ahaf ashe wasa da ni kike... Anjima dai ina nan shigowa in amshi kudin nan na ranan..." Aneesah tace "Aa Aunty ki bari ko jibi don nasan kafin ya tafi dole xai ban kudi me yawa" Aunty tace "Toh shkkn Allah ya kai mu, xan je anguwa ne dama da yamma, so duk da haka xan biyo din dai" Aunty tace "To sai kin xo" Daga haka ta katse wayar.... Ramlah na kwance parlor da yamma taji sallaman Hajja, mikewa xaune tayi don kofar ma a bude yake tun bayan da Jiddah ta tafi Islamiyya, Hajja ta shigo tace "Sannu, a nan ana ta fama ko, ai uwarki ma lokacin da take da cikin Aliyu haka ta xabga uban laulayin nan dai kamar baxata yi ba, to ke gwara naki naga kina narkan abinci abun ki, kawai sai dai yawan kwanciya kamar ruwa, cikin na kwari duk xaki daina jin haka wllh" Ramlah dai sai murmushi take tace "Sannu da xuwa Hajja" Hajja ta karaso tace "Yauwa, sannu ina mijin naki?" Ramlah tace "Ya fita baya nan" Hajja tace "Toh gwara hakan, Jiddah fa? na samu labarin a nan take abunta yanxu" Ramlah tace "Ehh amma ta tafi Islamiyya" Hajja tace "O'o kullum dai ace taje Islamiyya, irin wannan xuwan Islamiyyan nata haka ai ya ci ace ta sauke, kullum fa tana hanyar Islamiyya kamar dai a Masar, to Allah ya bata ilimi me amfani, duk da dai tana da gaskiyarta" Hajja ta ajiye ledan hannunta a hankali kan center table tace "Har gida aka kawo min wannan ledan in gaya maki, ni dai sai riritasa nake kamar kwai abunka da kayan amana, to ynxu karfe nawa suke tashi daga wannan Islamiyyar dai?" Ramlah tace "Ta ma kusa shigowa, tun biyu ta tafi" Hajja tace "Atoh wannan kuma wani irin karatu ne kamar su suka fi kowa tsoron Allah" Ramlah dai ta tashi ta tafi kitchen, Ruwa ta kawo ma Hajja a kan tray da lemo da cup, ta dibar mata jollof din spaghetti da yaji hanta da beef wanda Jiddah tayi ta daura fork a kai da soyayyun kaji, duk ta daura kan tray sannan ta fito parlon ta ajiye kusa da Hajja tace "Ga abinci Hajja" Hajja tace "Kina wannan tofe tofen yawun xaki kawo min abinci Ramlah? Aa ni dai Alhmdlh sai da nayi nak kafin in fito daga gida" Ramlah ta tafi tayi kwanciyarta bata ce mata komai ba, Hajja ta sa hannu ta xare goran ruwan tace "Gwara gwara wannan din dai, dama har gidan Aliyu nake son xuwa saboda naji labarin safaran turarruka yake, sai ya bani ko guda uku ne, Nafisah ma naji wai ta rokesa turaren ai" Ita dai Ramlah kallo kawai take, Bude kofar aka yi Jiddah ta shigo da sallama, Hajja na ganinta tace "Toh Alhamdulillah, sannu da xuwa Jiddah" Jiddah na ganinta sai da gabanta ya fadi, ta karasa parlon ta xauna saman carpet a hankali tace "Ina yini Hajja?" Hajja tace "Lafiya lau, ga sakonki nan tun daga bauchi aka kawo, babu wanda yasan meye a ciki banda ni da aka gaya ma, nima din dai ba budewa nayi ba tunda ni ba yar boko bace" Jiddah ta dinga kallon fancy leda din, Hajja tace "Toh dauka ki duba mana" Dauka Jiddah tayi ta fiddo abinda ke cikin ledan, kwalin latest Iphone ta gani cikin ledan, Ramlah ta xaro ido ta mike xaune tace "Hajja wa ya siya mata wannan?" Hajja ta kalleta tace "Aa kuma ai wannan ba ruwanki Ramlah, ke dai kawai ki mata fatan alkhairi, da fatan kashewa lafiya" Ajiye wayar Jiddah tayi tace "Toh ai ni Umma basu ce xan rike waya ba yanxu" A fusace Hajja tace "Waye kuma Umma?? Yar bakin ciki ce fa matar nan fitowa fili ne bata yi ta nuna, ita ta isa tace baxa ayi abinda nace ba, banda Aliyun da ya tsinto mana ke a can hayi kina galantoyi, wanda ma da muka je gidan naku shekaranjiya gani muka yi an rushe d'an kuturun gidan da baldoza ba komai sai fili, ai ina ga babu wani da ya isa ya hanaki amfani da wayar nan a yanxu dai, don ko Usman yayi yunkurin yin hakan xan nuna masa bacin raina ainun balle wata mata can da ta narka uban kiba, da Masar ne ita wannan dama da tuni an kwantar da ita a asibiti baxa ayi shawara da yan uwanta ba ma, toh wacece kuma Umma a wajenki banda dai tana kanwar Uwar shi Aliyun da yayi sanadin kawo ki cikinmu, ni dai ba ruwana a dinga yin abu bisa tsari, ina ma laifin kice inje ince mata xaki fara amfani da waya" Jiddah dai tayi shiru bata ce komai ba, Ramlah sai kallon Hajja take daga kwancen da take, Hajja ta sharce xufar da ta hada don fitina tace "Balle ma jikana ne ya bada wayan nan a kawo maki, toh ina ruwanta kuma banda dai fitina take son ja ma kanta ita Ummar, yo fitina mana... daga masarautan bauchi fa wayar ta fito ba ma kasuwa ba, to tayi ta kanta don babu wanda xai duba cewa kanwar Hauwa ce ita, hukuntata xa ayi yanda ya kamata" Babu dai wanda ya tanka Hajja, Tana bude goran ruwan hannunta tace "Yanxu ki tashi ki cire uniform mu je ki rakani gidan Aliyu, shi kuma ina ta jin jita jitan xai fita waje da wani babba a jirgi amma kun ga ni ai ya ki gaya min, ko da yake dai baxan biyesa ba, titin ma da ya yasar dani a hayi shekaranjiya ban gaya ma kowa ba, bakina alekum na dawo gida na shige daki na, tinda mu 'yan Masar dai da hakuri aka san mu..." Jiddah da duk hankalinta ya tashi ta dinga kallon Hajja ta ma rasa abinda xata ce, yanxu abu biyu ne ya dameta a rai, na farko Hajja tace wai an rushe gidansu, to me yasa xa a rushe gidansu su da ba a kan titi suke ba, ina babaarsu da Bibalo suka koma kenan yanxu?? Tunanin hakan yayi mugun daga mata hankali, na biyu kuma rakiyar da Hajja tace xata mata gidan Abuturrab, Ramlah ta mike ta tafi bandaki Hajja ta bi ta da kallo tana yamutse baki, tana dawowa daga bandakin ta kalli Jiddah da sauri tace "Tashi muje kada magariba tayi mana kin ji" Ramlah tace "Amma Hajja ai Ya Ahmad bai san xata fita ba, kuma babu kowa gidan sai ni kadai..." salati Hajja ta rafka tana kankance ido tace "Waye kuma Yaya Ahmad? Ina ruwana da shi? Me na hada da shi?? Kanin uban jiddan ne shi ko ko? Ku dai kun cika daukan magana wllh, shi yanxu ya isa hanata ta bi ni" Ramlah tace "Toh ai wajensa take dai yanxu" Hajja tace "Ja can ki ji da tsamin yawunki, ina ruwana da ke da Ahmad din, gashi nan ai ya hadaki da wahala kullum yana hanyar Abuja..." Jiddah ta kalli Hajja tace "Hajja ni fa ina da karatu gobe muna da jarabawa" Hajja ta dinga kallonta, can tace "Ni xaki walakanta ina yabonki sallah xaki kasa alwala?? Gidan jikana fa nace ki rakani ba gidan wani 6are ba, gidan nan kuma na samu labarin kin kusa wata uku a cikinsa, to meye don nace ki rakani xaki gatsa min wannan magana haka ba dadi" Jiddah dai ta sunkuyar da kanta a ranta tana tunanin no amount of words can allow her go to Aliyu's house this evening, mikewa Hajja tayi ta dau jakarta ta nufi kofa, Jiddah taki yarda ta dago, Ramlah dai ta ma rasa abinda xata ce har Hajja ta fita parlon, Ramlah tayi kasa da murya tace "Ko dai xaki rakata don asirinmu ya rufu Jiddah??" Jiddah ta girgixa kai calmly tace "Ni baxan je gidan wannan matar tasa ba wllh, dama dai bata nan ne, kuma ba gwara ta sa a kira mata shi ya xo ba, amma sai inyi ta wani xuwa gidan mahaukaciyar a saboda me?? Baxan je ba" Ramlah sai kallon Jiddah take ganin yanda take maganar kamar she have grudges with Aneesah, murmushi Ramlah tayi tace "Ki dai yi hakuri, idan ya so kar ma ki shiga cikin gidan sai ki jira ta a waje" Jiddah tace "Na fa ce baxan je ba" Tashi tayi ta wuce daki Ramlah ta bi ta da kallo, sai kuma ta mike ta isa window tana lekan waje taga ko Hajja ta fita compound din, Tsaye ta ganta mai gadi na mata danne danne a waya alamar xai mata kira, Ramlah ta juya da sauri ta koma.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Bayan few minutes Ramlah ta sake komawa ta leka compound sai bata ga Hajja ba, wani ajiyar xuciya ta sauke ta wuce dakin da Jiddah take, tana cire Uniform ta sameta, Ramlah ta jingina da kofa tace "Toh Aneesah ta maki wani abu ne da baxa ki je gidan nata ba Jiddah?" Jiddah taki kallonta tace "Bata min komai ba, kawai dai baxan je bane..." Ramlah tace "Amma ai nace idan ma kin rakatan xa ki iya kin shiga kiyi tsayuwarki a waje har ta fito" Jiddah tace "Kofar gidan ma baxan iya tsayawa ba" Murmushi kawai Ramlah tayi ta juya ta fita daga dakin. Ranan Friday da daddare Aneesah na xaune parlor downstairs bayan Magrib tana kallon wani indian Series tana shan fruit salad, ta ji footstep ana saukowa downstairs din, daga kai tayi ta gansa yana sakkowa, lkci daya kamshinsa ya baxa ko wani lungu da sako na parlon, kafin tace komai yace "You still haven't pray Aneesah" Tace "I know, ina xaka je da daddaren nan haka Captain?" Ya shafa beard dinsa yace "Wajen Budurwa ta" tayi wani dariyar da bata shirya ba tace "Hmm, kar Allah ya nuna min wannan bakar ranan, ni fa kasan wani abu captain?" Yana sakkowa yace "Sai kin fada" tace "Wllh duk ranan da yau aka ce da gaske kayi wata budurwa Allah xan iya kashe koma wacece har lahira, sai dai nima a daureni...." Yana kallonta bayan ya sakko parlon yace "Toh duk ranan da aka ce nayi wani auren fa?" Ta kallesa kamar baxata ce komai ba don gaba daya mood dinta ya canxa, sai kuma tace "Wai ka auri wata matar a duniya bayan ni?" Yace "Ehh" Wani murmushin ta kuma yi tace "Gwara a bar xancen kawai Captain..." Sai kuma ta hade rai tace "Kasan Allah? Wllh wllh xan iya kasheta in kashe kaina sannan kai ma in kashe ka duk mu hadu a lahira" Da mamaki ya dinga kallonta ganin how serious she is, cikin bacin rai tace "Wllh duk ka bata min mood wnn xancen da kayi captain, mu fa kaf xuri'armu fa ba a mana kishiya wllh, Aunty Salaha ma da aka yi ma satin amaryar uku ta bar gidan babu wanda ya koreta" Shi dai Abuturrab kallonta kawai yake ganin da gaske ran nata ya baci sosai, D'an murmushi yyi yace "Sai na dawo..." Ta mike babu yabo babu fallasa tace "Wai ina xaka da daddaren nan ne?" Yace "Ban ma Umma sallama ba, daxu gida kawai naje" kauda kai tayi ta ta6e baki, sai kuma ta kallesa tace "Toh bari in saka hijab mu je tunda ban ta6a xuwa gidan nata ba dama" Yace "No, ni kadai xanje, duk ranan da kika shirya sai kije ki gaisheta" Da mamaki take kallonsa tace "Ban gane No ba, yanxun idan naje laifi ne?" Yace "Eh saboda sai da xanje mata sallama sannan kika san xaki gaisheta" Bai jira cewarta ba ya nufi kofa ta bi sa da wani irin kallo xancensa na sake yawo a kanta wai duk ranan da aka ce yayi wata matar fa?? Tabb shi me ma ya kai sa fadin wannan mugun xance, ai daga ita ya rufe aure har karshen rayuwarsa, ita ce first and last dinsa, shi din nata ne ita kadai, tsaki tayi ta koma ta xauna ta ci gaba da kallonta amma ba cikin dadin rai ba... Abuturrab na parking ya dau wayarsa yayi dialing number ya kai kunne, wayar na fara ring aka daga, ya amsa gaisuwarta yace "Ki turo ta ta amsar maku sako!" Ramlah tace "Wa xan turo yaya?" Yace "Warce ke gidanki" Kallon agogo tayi don anyi isha, sai kuma ta mike ta fita xuwa dakin Jiddah, Jiddah ta gama sa kayan baccinta kenan tana shafa turare kafin ta dau takardanta ta fara karatu saboda exams da take da shi gobe Ramlah ta shigo, tsaye Ramlah tayi bakin kofar tana kallonta, Jiddah ta ajiye turaren hannunta tace "You need something?" Ramlah tace "Wai sako xaki amso a kofar gida" Jiddah ta dinga kallonta tace "Sako kuma? Sakon me? Kuma wajen wa?" Ramlah tace "Ya Aliyu" sosai gaban Jiddah ya fadi jin sunan da Ramlah ta ambato, Jiddah ta girgixa kai tace "Sakon me da daddaren nan, maimakon kice ya shigo da shi ki amsa don Allah, ji fa karfe nawa" Ramlah dai ta ma rasa abinda xata ce, Jiddah ta tafi ta dau takardanta ta xauna gefen gado, irin ita baxata je din nan ba, wayar Ramlah dake hannunta ne ya fara ring, ta daga ta sa handsfree tana kallon Jiddah, daga daya bangaren yace "Kuna bata min lokaci" Ramlah ta d'an fara kame kame, sai kuma tace "Yaya ko dai in fito in amsa ni? ita naga ta kwanta ne" Calmly yace "Taso ta" Tace "Wai dama exams..." Katse ta yyi yace "Ki taso ta nace" a hankali tace "Toh Yaya" ya katse wayar, Ramlah ta kalli Jiddah da ta 6ata fuska kamar xata yi kuka jin duk abinda yace, cikin rawar murya tace "Bayan ya Ahmad bai sani ba xan je kofar gida amsan sako, to gwara ki kirasa ni dai" Ramlah ta xaro ido tace "Ince masa me, salon ya kira yayan?? ke dai kawai ki sa hijab dinki ki daure kije kiga sakon meye" Jiddah ta girgixa kai da kyar tace "Ni baxan iya fita ba wllh, dubi fa agogo" Ramlah tace "Toh me kike so in ce masa bayan kinji yanda muka yi da shi Jiddah" Jiddah ta kwanta kan gadon ta lullube tace "Da gaske fa ni baxan je ba kawai ki kashe wayarki gaba daya, tun da rana me yasa bai kawo sakon ba" Ramlah dai ta rasa abun cewa tana ta tsaye, sai ga kiransa ya sake shigowa, ta xaro ido tace "Na shiga uku Jiddah ki rufa min asiri ki tashi kije, ni dama ba ni ya kira ba, bakin gate ne fa kawai xaki tsaya ya baki sakon da yace ki juyo ki shigo, wllh ban san kuma me xance masa ba idan na daga kiran nan" Ganin ya kusa katsewa ta daga tana rawar baki tace "Yaya na kuma ga tana wanka ne..." Yace "Ramlah" ta xaro ido tace "Na'am yaya" Yace "Mika mata wayar" karasawa tayi ta ajiye wayar kusa da Jiddah tace "Ga ta" Jiddah tayi narai narai da ido tana sauraronsa, yace "Fito ki amshi abinda nace yanxu, minti biyu na baki..." daga haka ya katse wayar, Jiddah ta mike xaune har hawaye ya kawo idonta, Ramlah na lallabata tace "Ki daure ki je pls Jiddah ai nan da kofar gida ne, kawai yana mika maki sai ki shigo kin ji" Mikewa Jiddah tayi daga kan gadon ta bude wajen kayanta ta dau hijab har kasa ta saka sannan ta fita, tun da ta isa gate gabanta ke faduwa, tana fita taga motarsa ta karasa tana tafiya slowly ta tsaya kusa da motar ta tsaya, sauke glass yayi yace "Shigo ki amsa" kamar xata yi kuka tace "Don Allah ka bani a nan, wllh ya Ahmad...." Yana kallonta directly in the eyes yace "Shiga nace" Sosai hankalinta ya tashi ta rasa yanda xata yi, da kansa taga ya bude motar ta matsa gefe ganin kallon da yake mata sai kawai ta shiga xuciyarta na bugawa, amma bata kulle motar ba, yace "Kulle min mota" Ta xaro ido tace "Don girman Allah ka bani sakon in koma wllh karatu nake gobe ina da exams, kaga dare yayi" da kansa ya kulle motar ya tada motar, hawaye ya shiga sauka idonta tace "Na shiga uku don Allah ka bude min in fita" barin layin yayi ba tare da ya saurareta ba, ta fashe da kuka sosai tana kallonsa cikin tashin hankali.... Bai ko kalleta ba ya ci gaba da driving dinsa, jingina tayi da kujeran motar tana kuka a hankali, bayan tafiyar kusan minti ashirin taga sun shiga wani katon shopping mall wanda wajen kamar da rana saboda fitilu da ya haska ko ina, ya nemi waje yyi parking ita dai bin wajen take da kallo gabanta na faduwa, sauka yyi daga motar ya xaga ta inda take ya bude motar, kasa kallonsa tayi shi kuma bai ce mata komai ba, bayan few seconds ta goge idonta ta sauka daga motar ya kulle, tafiya ya fara, da farko ta d'an yi jim ta bi sa da kallo, amma tsoron kada ya bace mata ta bi bayansa da sauri, tare suka shiga ciki tana bin wajen da kallo, inda ya ta6a kawota ya mata siyayya Washegarin ranan ta na farko a gidansa ne, cart ya tafi ya dauka tana biye da shi, ya mika mata handle din yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi ta amshi cart din, ya dau wani ya fara tafiya, bin bayansa tayi tana turawa a hankali, wajen turarruka ya nufa, yace "Pick" tace "Ni ina da turare da yawa" Bai kuma sauraronta ba ya dinga debar mata turaren, ta dinga bin sa da kallo tana mamaki, bayan ya gama ya tafi gun mayukan shafawa da sabulu da shower gel, su ma ya dibar mata, ita dai bin sa kawai take da cart din hannunta, duk wasu kananun abu na bukatar yau da kullum sai da ya dibar mata, har ta fara gajiya da binsa, don sun siya kaya da yawa, wajen sanitary pads taga ya nufa, ganin uban pads din da ya debo bata san lkcn da tace "Ai basu kare ba na gida" Yana juyowa ta sunkuyar da kanta, yace "Meye basu kare ba" Kasa cewa komai tayi, ya xuba pads din a cart ya bar wajen, ta bi bayansa tana tafiya a hankali, sai da yaga cart din ya cika sannan suka tafi wajen kayan ciye ciye, nan ma bai jira yace ta dau komai ba, ya dinga debar mata duk wani abu da shi yake ci yana xubawa a cart din da take turawa, har kayan shayi duk sai da ya daukar mata, Jiddah dai sai kallon wani chocolate dake side dinta take ta yi don Ahmad na kawo masu irinsa daga Abuja, chocolate din kuma ba dai dadi ba, ta d'an kallesa taga yayi backing dinta yana duba wani tsadadden biscuit, kwasan chocolate din tayi kusan biyar ta juyo da sauri xata xuba su a cart din dai dai nan shi ma ya juyo rike da biscuits din da yake kallo suka kusa cin karo, juya masa baya tayi da sauri taji kamar ta nutse ta rufe ido, xata maida chocolates din taji ya fixgota, tayi narai narai da ido tana kallonsa da manyan idonta, ya amsa ya xuba su a cart din yana kallonta shi ma, ita ta fara sauke idonta, sauran siyayyan duk tana gefe har ya gama, suka tafi wajen biyan kudi, a booth duk aka xuba ledojin kayan siyayyan, eatry din mall din ya shiga ya siyi ice cream da pizza with shawarma sannan ya fito, ita dai tana tsaye bakin motarsa tana jiransa, bayan ya shiga ita ma shiga motar, cikin minti ashirin da biyar suka iso kofar gidan Ramlah. Jinginar da kansa yayi da kujeran motar ita dai jira kawai take taji ya bude lock din motar ta sauka, amma sai taga yaki budewa, bayan five minutes, taji muryarsa calmly yace "Xan mu fita Dubai gobe in sha Allah, from there xa mu tafi Uk..." Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya kalleta.... ta sunkuyar da kanta tace "Allah ya kiyaye" ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Xan yi few months a can" Bata ce komai ba, yace "Kina da bukatar wani abu ne??" Ta girgixa masa kai tace "Wani abu kamar me bayan su Umma na yi min komai ni" Ya dinga kallonta yace "Wannan ne amsan tambayar da na maki?" Kin cewa komai tayi, yace "Bude baki kiyi min magana" Tace "Bana bukatar komai" shiru duk suka yi, ita dai wata magana ce ke cinta amma ta rasa ta ina xata fara masa, ji tayi yace "Do u have anything to say to me?" Ta kallesa da sauri, sai kuma tace "Ehh.." yace "Ina jin ki" cikin sanyin murya tace "Ranan Hajja tace wai kunje hayi an rusa gidanmu, ba kowa yanxu" Ya dinga kallonta yace "Sai aka yi yaya?" Ta fashe da kuka tace "Baabarmu da Bibalo fa?" Yace "Kina son xuwa wajensu ne yanxu??" Hawaye na sauka ido ta ta kallesa tace "Ehh ina so don Allah" Yace "Me xaki yi masu idan kinje" Cikin rawan murya tace "Ina son in gansu mana, saboda nayi kewarsu... Ban taso na gan ni da kowa ba sai su, and it's been long... Nayi kewarsu sosai" Tada motar yayi bai kuma ce mata komai ba yayi reverse suka bar layin. The journey was so silent, bayan tafiyar kusan minti talatin suka iso titin hayin rigasa, tunda suka shigo hayi Jiddah ta dinga bin anguwar tasu da kallo, ta rasa wani irin farin ciki xata yi a moment din, farin cikin nata bai bayyana a fili ba sai da ta gansu kan layin gidan Babaarta, ta kallesa da farin ciki amma ta rasa abinda xata ce masa, she looks so happy... shiga layin yyi da motarsa xuciyarta na bugawa tace "Don Allah ko xaka tsaya in fara shiga gidan Iyah in gaisheta???" Ya kalleta sannan yayi parking kofar gidan Iyah, sauka tayi daga motar da sauri ta shige gidan a guje, ya sauka ya jingina da motar tasa ya bi ta da kallo, Iyah na xaune tsakar gida da rediyonta a hannu, tana ma jikokinta dake kwance saman tabarma fifita sun yi bacci, Jiddah ta wara ido cike da murna tace "Iyah!!!" Fadawa jikinta tayi ta rungumeta, Iyah ta matsar da ita tana mata wani kallo daga sama har kasa, sai kuma tace "Jiddah????" Rungumeta Jiddahh ta kara yi lokaci daya hawaye ya kawo idonta tace "Nice Iyah, nayi kewarku wllh" Iyah ma ta fashe da kuka tace "Ashe rai kan ga rai Jiddah, ashe xan sake ganin ki a rayuwar nan?" Jiddah ta share idonta tana murmushi tace "Gashi kin gan ni Iyah" Iyah ta mike tsaye tana sake kare mata kallo don tabbatar da ita din ce kuwa, sai ta saki salati tace "Daga ina kike haka Jiddah?? Kece kika dawo haka kamar balarabiya Jiddah??" Jiddah tayi murmushi ta kasa ce mata komai tana kallonta, Iyah tace "Ke da waye yanxu haka? Daga ina kike?" Jiddah tace "Yana kofar gida, ince ya shigo?" Bata jira me Iyah xata ce ba ta tafi da sauri kofar gidan, har sannan Abuturrab na tsaye ya rungume hannunsa, tace "Wai tace ka shigo" kallonta ya dinga yi ta juya ta koma ciki da sauri, shafa kansa yyi ya bi bayanta... Har kasa Iyah ta durkusa tana gaishesa bayan ya shigo gidan, hakan yasa ya xauna saman darduma yana d'an murmushi calmly yace "Ina yini??" Iyah ta rushe da kuka tace "Wllh da kasan irin taimakon da Allah ya baka ikon yi da ladan da Allah xai baka da ba haka ba bawan Allah, ka taimaki rayuwar Jiddah a sanda take tsananin bukatar taimakon, ka cece Jiddah a dai dai lkcn da take bukatar ceto, Allah ubangiji ya sa ka samu me maka abinda kayi ma marainiyar Allahn nan duniya da lahira, Allah ya biyaka da aljanna, ya yalwata maka arxikin ka, Allah ya baka ikon ci gaba da riketa da amana, Allah kuma ya baku xaman lafiya tare na har abada ya bada xuri'a dayyaba" Kuka kawai Iyah take kamar jininta ce Jiddah, Jiddah dai duk jikinta yyi sanyi ta sunkuyar da kanta jin maganganun Iyah, shi ma kawai murmushin karfin hali yake yana kallon tsohuwar a hankali ya ce "Ameen nagode Mama" Iyah na kwalla tace "Wllh ki rikesa Jiddah, kaf duniya a yanxu dai baki da kamarsa, shine uwarki shine ubanki, ya maki abinda a cikin kashi dari na mutane baxa ki samu kashi biyu da xa su iya maki ba, ya fidda rayuwarki cikin kunci, maraici, tsanani, da bakar wahala, yayi maki duk wannan abun a lokacin da kike tsananin bukatarsu, to me xai janyo maki butulce masa a rayuwar nan, kiyi masa halacci yanda ya maki Jiddah, ga shi wai yau kece sai da na maki kallo kusan uku sannan na gane ki, ba don muryarki ba wlh baxan yarda ke din ce ba" Sosai jikin Jiddah yayi sanyi wanda bata san lkcn da hawaye ya dinga sauka idonta ba tana kallon Iyah, kallonta kawai Abuturrab yake babu ko kiftawa, Iyah tace "Ki rikesa, kiyi masa biyayya, ki rike yan uwansa da duk wani nasa Jiddah, da abinda xaki iya biyansa kadai kenan ki ji in gaya maki, nace kiyi masa biyayya, wllh kiyi masa biyayya, Allah kadai yasan sadaukarwan da yayi sabida ke, Allah kuma ya baku xaman lafiya na har abada, nasan baku ma kai ga shiga gidan Hansai ba, amma idan xa ku ji ta nawa ba sai kun shiga ba kuyi tafiyarku kawai, Hansai bata canxa ba dai daga yanda kika santa... Sai ma dai abinda ya faru" Jiddah sai goge hawayen da yaki tsaya mata take, Abuturrab ya ciro kudi aljihunsa ya ajiye ma Iyah yace "Kiyi hakuri Mama babu yawa wannan, in sha Allah xan sake dawowa gaisheki, sannan xan daukeki in kai ki inda mu ke" Iyah tace "Wllh gaisuwan da kuka xo min ma ya isa ya wadatar ba sai ka bani kudi ba Yarona" mikewa yayi yana kallon jiddah da ta kasa daina kuka, a haka dai Iyah ta rakasu kofar gida tana cewa "Ba sai kun je gun Hansai ba, kuyi tafiyarku Allah yayi maku albarka ya baku xuri'a dayyaba..." Cikin sanyi Jiddah tace "Iyah baxan iya tafiya ban shiga na gaisheta ba" Iyah tace "Toh shkkn Jiddah, Allah ubangiji ya kareki daga duk sharrinta ku shiga kawai, akwai Allah" Abuturrab ma bai hana Jiddah ba suka karasa kofar gidan nasu da kafa, gabanta na faduwa ta shiga gidan ta ma kasa ko sallama saboda fargaba, Hansai na xaune tsakar gida tana fiffita ga kwanon abinci a gabanta tana cewa "Yo ba gwara ma ya mutun ba ko xa a rage mugun iri, duk fa da hadin bakinsa da uban kudi da aka dinga lafta masa aka siyar min da 'ya ban ji ba ban gani ba, yau wata dai dai kusan biyar kenan, kuma wllh gaya maki ne kawai banyi ba amma so nake na hada yan kudaden wankauna, na kai gidan malam Hamisu a sake danne tsinanne kada Allah ya mikar da shi, kaf bani da makiyi irinsa a duniya yanxu kam..." Zulai dake kwance tsakar gidan da daurin kirji tace "Ai ko dai ance yana can shika rai a hannun Allah baya gane duk wa enda ke kansa, aiki ma xa a masa sai kuma jikin ya dada sususcewa kinga bbu xancen aikin ai sai ya farfado kuma" Jiddah ta kasa shiga gidan gabanta sai faduwa yake ta dinga karanto addu'o'i a ranta, Zulai ce ta hango shadow tace "Waye tsaye nan, ko Bibalo ce" Hansai tace "Bibalo ai sai karfe sha biyu kila, wani shegen ne ya tsaya min bakin kofa yana min la6e?" Jiddah ta runtse ido ta karasa shiga tsakar gidan, duk suka tsaya kallonta don akwai hasken wata sosai tsakar gidan, Hansai ta ajiye maficin hannunta tana kallonta daga sama har kasa tace "Waye wannan?" Da kyar Jiddah tace "Ni ce Baabarmu" Zulai ta mike a gigice tana sake gyara daurin zanin kirjinta tace "Ke wa??" Hansai dai hangame baki tayi tana kallon Jiddah daga sama har kasa, can ita ma ta mike ta nufeta tana sake kare mata kallo kamar taga aljanna, Hawaye ya shiga sauka idon Jiddah ta durkusa kasa cikin sanyin murya tace "Baabarmu" Hansai ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Toh Alhamdulillahi, yanxu saura in kai ma Badalan kan dutse cikon kudinsa, aiki kam ya ci Alhmdlh... Allah ya maido min ita gida da kafafuwanta" wani shewa Zulai ta saki da karfi tana gode ma Allah ita ma, Jiddah dai sai kallonsu take, Hansai na sharban majina tace "Tashi mu shiga ciki, tashi" Jiddah tayi karfin halin cewa "Ba ni kadai ba ce Baabarmu" Hansai ta kalli soro da sauri tace "Ke da uban waye??" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Ni da shi ne" Dai dai nan Abuturrab ya shigo cikin compound din don gaba daya hankalinsa ya ki nutsuwa shigan Jiddah gidan ita kadai, Hansai taji mugun faduwan gaba ganinsa tace "Ya xaka afko ma mutane gida haka kanka tsaye, kai waye??" Yana kallon Jiddah yace "Idan kun gama gaisawan taso mu tafi... It's getting late" Hansai ta gwalo ido tace "Ku tafi ina?? To wllh wllh karyarka ya sha karya Malam, babu inda 'ya ta xata daga tsakar gidan nan, ko taku daya baxata yi daga nan ba wllh, ku je ina?? Lallai sannunka...." tana huci ta kare maganar ta dago Jiddah da xumar shigar da ita daki tana cewa "Tashi don ubanki, idan kin sake fita ko nan da kofar gida Allah ya tsine min albarkan da yayi min...." Daga kasa har sama Abuturrab ke kallon Hansai da wani expression, can yace "Kin manta ita din matar aure ce?" Hansai ta mulmulo wani uban xagi tace "Fadi duk uban da ka kashe ni me iya siyar da gidan nan ne in biyaka, a gidan ubanwa ta xama matar aure?? Ka dau min ya ka tafi ka lalatata kace min matar aure ce??" Abuturrab na kallon Jiddah yace "Zo mu tafi" Jiddah hawaye na sauka idonta ta kallesa sannan ta kalli Hansai dake kokarin janta xuwa cikin daki, cikin kuka tace "Baabarmu...." Hansai bata saurari me xata ce ba ta wanka mata wani mummunan mari da yasa taji diff, ta kuma kai mata wani tana huci tace "Rufe min baki don ubanki" bai san lkcn da ya karasa compound din ya fincike Jiddah a hannunta ba yace "Kinyi na farko kinyi na karshe, kin kuma ci albarkacin ki na matar babanta da wllh sai na rama mata" Daga haka ya nufi soro da Jiddah, Hansai ta lafta wani uban ihu ta bi bayansu tana kunduma xagi tace "Idan Jiddah ta sake barin gidan nan shegiya aka haifeni, wllh babu inda xata je kuma ka cika min 'ya ta" Ganin ta yo kansu Abuturrab ya kwasheta da kafa sai gata wanwas a kasa, ya bude front seat ya saka Jiddah dake ta kuka a ciki sannan ya kulle ya xaga ya shiga driver seat, Xulai ce ta fito da katon tabarya tana ihu wai jama'a su kawo masu dauki, Hansai ta mike a rikice ta amshe tabaryan, da duk karfinta ta buga glass din bangaren da Jiddah take, ihu Jiddan ta fasa a tsorace ya fixgota jikinsa tayi lamo, don sai da glass din yyi tsawa, Hansai ta shige gaban motar kamar mahaukaciya tana cewa "Da dai ka tafi da Jiddah gwara ka kasheni, ka kasheni nace d'an banxa... xan ga ta inda xaka bi ai, sai dai ka takeni, babu inda xaka kai min ya ta d'an yankan kai..." Abuturrab yyi reverse sosai sannan ya taho a guje, wani uban tsalle Hansai tayi ta kauce sai gata da Zulai kwance a kasa, ya ja motarsa a guje ya bar layin, kuka kawai Jiddah take kamar ranta xai fita, har suka fita titin hayi bai ce mata komai ba.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Kofar gidan Ramlah Abuturrab yyi parking, tun barin su Hayi sai a lokacin ya juya ya kalleta, a hankali ta kai hannu a sanyaye xata bude motar taji a kulle, duk da haka ta ki kallonsa har sannan hawaye na idonta, yace "To kukan me kike, bayan abinda kika ce kina so nayi maki, gun Baabarki fa kika ce in kai ki kuma na kai ki" Hade rai tayi taki ce masa komai, hakan da tayi ya basa dariya amma bai yi ba ya jinginar da kansa da kujeran da yake xaune yace "Laifi na ne kenan?" Kamar jira take ta fashe masa da matsanancin kuka har da shessheka, kallonta ya tsaya yi, bude motar yyi ya sauka, ta hade kanta da gwiwa tana rera kuka tana jin xuciyarta na mata xafi, Booth ya tafi ya fito da duk kayan shopping din, ya nufi gate din gidan, dai dai mai gadi xai fito, ya mika masa yace "Ka ajiye su a bakin kofa" komawa yayi booth din motar, a haka duk ya kwashe kayan yana ajiye su cikin compound din mai gadi kuma na kai wa bakin kofar entrance din shiga gidan yana ajiyewa, Bayan kayan sun kare Abuturrab ya koma cikin motar ya kulle yana kallonta, jin shigowarsa ta dago kanta ta kai hannu xata bude side dinta taji ya kulle motar gaba daya, calmly yace "I'm asking u whose fault it is now? Mine?" Tana goge idonta a hankali tace "Nima ban sani ba ka bude min mota in fita dare yayi" ya dinga kallonta, sai a sannan ta kallesa tace "Ka bude min xan sauka" yace "Yeah!! You did good by wanting to go meet ur stepmom after so many months, that clearly shows u missed her no matter her maltreatment toward u... u had good intentions but, stepmum dinki bata canxa daga yanda kika santa ba, she is still the stepmom u knew her to be, don haka idan ma tana ranki ne har yanxu ki cireta na har abada, take her off ur mind totally and face reality, ki mance kin ta6a rayuwa da ita, ki kulle babinta a rayuwarki, face ur new life, bata sonki kuma baxata ta6a sonki ba...." Jiddah ta fashe da kuka cikin sanyin murya tace "Shikenan ni kuma bani da kowa kenan?" Kallonta ya dinga yi, a hankali yace "Baki da kowa??" Kuka kawai take ta ki ce masa komai, ya kamo hannunta yace "Baki da kowa kika ce?" Still bata basa amsa ba amma yanda take kuka kasan she is hurt, bude motar yayi ya sauka, ya xaga ta inda take ya bude side din, saukowa tayi xata wuce gate ya riko hannunta ya bude back seat yace "Shiga ki goge idonki da kyau before going.." ta kalli motar, sai kuma ta fara goge idon nata, ya d'an hade rai yace "Shiga nace, u can't go in with those eyes" a hankali tace "Ni na goge ai" Calmly yace "Get inside" Wani hawayen ya taru idonta ta shiga bayan motar, ya dau handkerchief dinsa ya mika mata, amsa tayi tana goge idonta amma da ta tuna abinda Baabarsu tayi mata sai wasu hawayen su xubo mata, shikenan ita ba warce xata nuna tace baabarta ce kenan, a wajenta ta taso fa ta ga kanta, kowa yana da wanda xai nuna yace yau ga d'an uwansa na jini amma ita banda ita, bata san kowa nata na jini ba, hade kai tayi da gwiwa crying sadly, shi dai kallonta kawai yake, can ya bi layin da kallo, babu kowa a layin don goma ma yayi, mai gadi ma tuni ya koma cikin compound din, shiga cikin motar yayi ya kulle, ta daga kai tana kallonsa tana kuka, yace "Kika ce ke baki da kowa??" a hankali ta fara matsawa taki ce masa komai, ya kamo hannunta yace "Tell me?" Ta girgixa masa kai kawai, yace "Kin manta kina da Umma, kina da Ummi, kina da Ahmad? Maimoon, Ramlah... Ain't they all there for u always?" Sunkuyar da kai tayi wasu hawayen na xubo mata bata iya ta basa amsa ba, yyi kasa da murya yace "Answer me" ta gyada masa kai a hankali tace "They are...." yace "Idan ni ban ta6a maki komai ba ae su sun maki kuma suna kan maki ko?" Ganin kamar tunxurata yake dada yi, ya lumshe ido ya jawota jikinsa, lkci daya ta hadiye kukan da take ta fara turasa a hankali tana komawa baya, ya rungumeta sosai murya can kasa yace "I know i am gonna..." Bai karasa ba kawai ya shiga kissing dinta passionately, tun tana kokarin kwace kanta a rikice har dai ta kasa kwakkwaran motsi ta tsaya cak kamar warce ruwa ya cinye, Tun dai ana kiss har abu ya fara wuce level din kiss, iyakar tsorata ta tsorata a lkcn, bata kuma san sanda ta fara rokansa cikin rawar murya tana cewa ya rufa mata asiri, sae da ya dawo mata kamar ba shi din da ta sani ba, bakinta na rawa tace "Don Allah Aliyu kayi hakuri ka rufa min asiri, don Allah ka bari, don girman Allah nace maka...." Gaba daya ya gigitata, Ya kai bakinsa kunnenta cikin muryar da bata san sa da shi ba yace "Me ya sa baki saka brassiere ba?" Cikin rawar murya bakinta na rawa tace "Bacci xan yi dama" bai kuma ce mata komai ba, ta kankamesa tana kara basa hakuri da sauran strength dinta, Sae da Abuturrab ya ga he is getting out of the little control he is trying to maintain sannan ya saketa ba shiri, da ta samu ta figi hijab dinta ko gama sawa bata yi ba ta bude motar ta fice fittt, ko kulle masa motar bata yi ba cikin sakwanni kadan ta shige cikin gate din gida, gaba daya ya hargitsa ta iyakar hargitsawa, Ramlah na xaune parlor ta xabga uban tagumi bayan ta gaji da tsayuwa Jiddah ta shigo parlon, Ramlah ta mike tace "Haba Jiddah ina kika je haka bayan kin san karfe nawa, kin fa san halin da nake ciki kuma kika sa na shiga damuwa sosai haka?" Jiddah ta kasa tsayawa parlon, bakinta har rawa yake tace "Wllh siyayya yayi yace a kawo maki gasu can a balcony, i.. i want to go ease my self now" Daga haka ta shige daki ta kulle tana sauke numfashi, fadawa tayi kan gado ta shige cikin bargo ta rufe har kanta.. Ramlah dai na ta tsaye parlon deep in her thought, tunda Jiddah ta shigo taji kamshin turaren Abuturrab... komawa tayi ta xauna ta kuma rafka tagumi tunani iri iri a ranta... Abuturrab ya fi minti talatin a mota bayan ya isa gida idonsa a kulle ya jingina da kujeran motar, he is just hoping Allah yasa Aneesah tayi bacci, wajen karfe sha daya ya sauka motar ya shiga ciki, ga mamakinsa sai ya ganta xaune parlor tana kallon tv, da alamar film din ya tafi da ita shi yasa ma bata fito ba da ta ji sa shiru shiru bai shigo ba, stairs ya nufa da sauri, ta juyo tace "Captain ka ga agogo kuwa kaje ka dade haka?? kuma me kake yi cikin mota tun daxu baka shigo ba?" Ya ki tsayawa yana haurawa stairs yace "Toh ai baki fito kin ga abinda nake yi ba" Ita dai ta ci gaba da kallonta tana washe baki don a xo dai dai scene din da take so a film din, yana isa bangarensa bandaki ya shiga yayi wanka ya fito ya saka pajamas dinsa ya kashe wutan dakin sannan ya kwanta yayi rub da ciki ya runtse ido, bayan kusan thirty minutes Aneesah ta shigo dakin don an gama film din, yana jin ta amma yayi kamar bacci yake, kwanciya tayi gefensa tana shafa fuskarsa tana kiransa a hankali cike da shagwaba, he just don't have Choice in dai yana son bacci a ranan, haka nan ya biyeta kamar jira yake dama, har hakan ya 6ata mamaki... Sha biyu saura Jiddah ta cire bargon da ta rufe jikinta da shi ta mike xaune a hankali, har lokacin kirjinta bai daina bugawa ba, da ta tuna abinda ya faru sae gabanta ya fadi sosai, bata ta6a jin tsoron Abuturrab irin na daxu ba, gaba daya ta tsorata da shi da lamarinsa, da kyar ta cire Hijab dinta ta sauka daga kan gadon ta wuce bandakin, ta shiga bandaki da kusan minti sha biyar Ramlah ta bude kofar dakin a hankali, shigowa dakin tayi ta dau hijab din Jiddah ta kai hancinta, imagine ta fara yi to ko dai fesa mata turaren yayi ne?? Kallon kofar bandakin tayi jin kamar wanka take yi, can dai ta ajiye Hijab din a hankali ta nufi kofa ta fita ta kulle dakin ta koma nata dakin ta xauna gefen gado, ita fa duk ta rasa takamaiman tunanin da xata yi, ta rasa ma'anar abinda ta gani. Washegari da safe ganin har kusan takwas Jiddah bata fito ba Ramlah ta tafi dakinta, kwance ta ganta tana bacci, Ramlah ta karasa ta kai hannu kafarta, bude ido Jiddah tayi ta mike xaune da sauri, Ramlah tace "Baxa ki Islamiyya bane yau Jiddah? Karfe takwas fa yanxu" Jiddah dai ta kasa barin ta hada ido da ita, a hankali tace "Um ciwon kai nake, sai gobe" Ramlah tace "Toh Allah ya kai mu" juyawa tayi ta nufi kofa Jiddah ta bi ta da kallo, komawa tayi a hankali ta kwanta ta lumshe ido. Sanin Ahmad na hanya Ramlah tayi duk ayyukan gidan don taga alamar Jiddah ba fitowa xata yi ba, kwashe duk shopping din da Abuturrab yayi ma Jiddah tayi ta kai wani spare room ta ajiye don bata san wanda xata ce ya kawo ba idan Ahmad ya tambaya. Karfe goma saura Ahmad ya shigo gidan daga Abuja, bayan Ramlah tayi welcoming dinsa ta kawo masa breakfast suna xaune parlor yace "Jiddah ta je weekend gidan Umma halan?" Ramlah tace "Aa tana daki yanxu ma haka" Yace "Islamiyyar fa?" Tace "She said she is having headache, bari in ce mata ka dawo" Daga haka ta mike ta wuce dakin Jiddah, kwance ta ganta kan gado duk da tayi wanka ta shirya, Ramlah sae kallonta take ganin kamar duk a tsorace take, Ramlah tace "Na xata bacci ma kike ai, baki karya ba fa, kuma Doctor ya dawo" Jiddah ta mike xaune taki yarda suyi eye contact da Ramlah tace "Xan fito yanxu" Ramlah ta juya ta fita, Jiddah ta sauka kan gadon ta dau Hijab dinta, sai da gabanta ya fadi jin kamshin da yake, ta ajiye ta bude press ta dau wani sannan ta nufi kofa ta fita, xaunawa kasan carpet tayi ta gaishe da Ahmad ya amsa yace "Ya ciwon kan?" Ta d'an yi murmushi tace "Yayi sauki yanxu, na sha magani" Yace "Maa sha Allah, kun gama exams din?" Ta girgixa kai tace "Aa ranan Wednesday in sha Allah" Yace "Toh Allah ya taimaka" ta amsa da Ameen, sannan ta mike ta wuce kitchen, Ramlah dae sae bin ta da ido take, tea kawai Jiddah ta hada ta koma daki. Karfe sha biyu saura Ramlah ta shigo dakin Jiddah, Jiddah na xaune saman darduma tana karatun qur'ani, Ta kai ayan karshe ta rufe Qur'anin ta d'an kalli Ramlah, ganin ta da mayafi tace "Fita xa ku yi?" Ramlah tace "Ehh yana kiranki, kayayyakin ki Kuma na daya dakin fa na ajiye maki a ciki" Jiddah tace "Aa ai ba nawa bane ni kadai" Mikewa tayi tunda dama da akwai Hijab a jikinta ta bi bayan Ramlah, Ahmad na xaune parlor rike da car key dinsa yana kallonta yace "Are you going out with us now Jiddah? Xan kai Captain airport" Jin sunan da ya kira sai da gaban Jiddah ya fadi sosai without thinking twice tace "Aa karatu nake" Ramlah dai na tsaye bayan kujera tana kallonta, Ahmad yace "Tafiya xai yi fa, kuma xai dau watanni bai dawo ba, kawai airport xa mu kai sa muyi sallama da shi mu dawo" Shiru tayi jin abinda Ahmad yace, yana ci gaba da kallonta yace "Kije ki shirya mu tafi, ba komai ai, beside we are not staying long" Bata kuma masa musu ba ta juya a hankali ta koma daki, Ramlah ta bi ta da kallo, Ahmad yana murmushi yace "Why are u looking at her that way Baby?" Ramlah ta d'an yi murmushi bata ce masa komai ba, Hijab kawai Jiddah ta canxa ta dau nikab dinta dake a goge ta saka hakan kadai ne xai iya sa ta bi su kai Abuturrab airport, jakarta ta dauka ta rataye a shoulder sannan ta fito parlor, Dariya Ahmad yyi ganinta yace "Tohh yau kuma nikab xa a sa kenan" Jiddah dai bata ce masa komai ba tayi murmushi daga cikin nikab din, a haka duk suka fita gidan, back seat ta shiga... hira Ahmad da Ramlah ke yi har suka iso kofar gidan Abuturrab, Ahmad ya dau wayarsa ya shiga kiransa, ba a dau lkci ba ya daga, Ahmad yace "I am outside ka fito...." Abuturrab yace "Sai karfe biyu jirgin xai tashi xuwa lagos, I can't sit all day at the airport, ka gane?" Ahmad yace "Ohk wai sai kun fara xuwa lagos dama?" Abuturrab yace "Yeaa, amma ba mu xa mu yi piloting xuwa lagos din ba ai" Ahmad yace "But u should have told me that since" Abuturrab yace "Is there anything wrong idan kun shigo kun jira for just few hours?" Ahmad yace "Alright then" Daga haka ya katse wayar ya kalli Ramlah yace "Mu shiga ciki" Ramlah ta bude motar ta sauka, tuni mood din jiddah ya canxa, amma bata jira ace ta sauka ba, kuma bata nuna hakan a fuskarta ba, ta bude motar ita ma ta sauka ta rufe, Kalle kallen layin ta fara yi, ganin karamin kiosk can farkon shigowa layin ta kalli Ahmad tace "Yaya xan d'an siyo abu a kantin can" Ya kalli inda ta nuna masa yace "Me xa ki siya" Tace "Yanxu xan amso in dawo yaya" daga haka ta nufi kantin da sauri, su kuma suka shiga gidan, Aneesah tayi welcoming din Ramlah kamar xata hadiyeta don fara'a, tuni ta cikasu da lemo da kayan ciye ciye irinsu cake, cin cin, da alkaki da Chef Salma ke mata ta ajiye a gida sbda bak'i, Shi dai Abuturrab na xaune parlon yana danna wayarsa, bayan few minutes Ramlah ta kalli Ahmad tace "Bata shigo ba har yanxu fa Yaya" sae a sannan Abuturrab ya daga kansa, Ahmad ya mike ya nufi kofa, Abuturrab na kallon Ramlah yace "Who?" Ramlah tace "Jiddah, tare muke, tace xata siya abu a kanti kuma har yanxu shiru" Bai kuma cewa komai ba, Aneesah ta wani ta6e baki ta koma kitchen tana kas kas da chewing gum a ranta kuwa cewa tayi gwara dai kam da bata shigo din ba don xata yi danasanin shigowa, abinci ta fiddo a deep freezer don dumama masu, Bayan some minutes Ahmad ya dawo yace "Har gun mai kantin naje, ba abinda ta siya wajensa, kila tafiyarta tayi" Ramlah ta dinga kallonsa, sae kuma tace "Toh ba waya kuma balle a kirata" Shi dai Abuturrab danna wayarsa kawai yake amma duk yana jin su, Ahmad yace "Da akwai makulli wajenta ne?" Ramlah tace "Eh akwai spare key, tun ranan da na bata da xan je gida" Ahmad yace "Ohk better" Aneesah ta fito daga kitchen tana washe baki tace "Na daura girki bari yayi sai in xubo maku Sis Ramlah" Ramlah tace "Ayya da ma baki yi bothering kanki ba Aunty, mun ci abinci daga gida kafin mu fito" Aneesah ta 6ata fuska tace "Aa wllh, ke da ko girkina baki ta6a ci ba, yau dai kam sae kin ci" Ramlah tayi murmushi tace "Toh shkkn Anty" Hira suke ta yi a parlon banda Abuturrab dake danne dannen waya, bayan kusan minti ashirin da xuwansu Ahmad ya kalli Aneesah yace "Dauko min car key xanje laundry in amso kayana ynxu" Tana kallonsa da mamaki tace "Amma kace delivery xa ayi maka ai, and babu wani kayan da xaka bukata a ciki, ko ka manta ne" yace "Noo na tuna akwai wani rigan sanyi da xan dauka a ciki" Tace "Toh ka kira su kawo maka mana dole sai kayi wahalan driving kuma" Mikewa yyi ya wuce sama, shi dai Ahmad idonsa na kan tv yana kallon wani program da ake yi, sai ga Abuturrab ya sakko da makullin motarsa, Ahmad yace "Mu je can din tare" Abuturrab ya kallesa yace "No, ba sai ka wani wahala ba kai da xaka kai ni airport, i will be back soon" mikewa Ahmad yyi yace "Mu je can din, babu damuwa" Ta gefen ido Abuturrab ya kallesa, Aneesah tace "Haba doctor ga abinci can nace ya kusa nuna kuma kace xaka fita, don Allah ka tsaya ka ci, don Allah Dr" Abuturrab yace "Kaga dama kai ma baka ta6a cin abincin amarya ba, kawai ka tsaya ka ci... So u can rate her" Yana fadin haka ya amshe makullin motar Ahmad yace "Ba sai na tsaya warming mota ba, i will go with ur car, and i will be back in d next 20 mins" daga haka ya fice daga parlon, Aneesah kuwa sai lallaba Ahmad take ya tsaya ya ci girkinta yau daya dai... Abuturrab na fita kofar gida ya shiga motar Ahmad ya bar layin, tafiyar minti kusan talatin yayi ya iso layin.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Parking yayi ya sauka yana kallon mai gadi dake xaune a waje, wanda har ya mike xai bude gate a tunaninsa Ahmad ne sai ya ga akasin haka, suka gaisa Abuturrab ya shafa kansa yace "Suna ciki?" Yace "Aa gaskiya basu jima da fita ba" Yace "Ba kowa a ciki yanxu?" Mai gadin yace "Babu kowa, ko awa daya basu yi da fita ba Yallabai" Abuturrab ya tsaya kallonsa, Mai gadin na washe baki yace "Da na ga motar ma na xata su ne ai" Abuturrab yace "Ohk, shkkn ba ma sai kace masu na xo ba... Sai anjima" Daga haka ya koma motarsa ya shiga, a hankali yake driving din... Parking yayi ya jinginar da kansa da kujera, bayan few seconds ya dau jotter a cikin motarsa da biro, ya cire pieces daya a ciki, kan steering ya ajiye takardan ya fara rubutu a jiki, bayan some minutes ya gama rubuta abinda xai rubuta ya maida biron sannan ya linke takardan gently, ya kashe motar ya sauka ya shiga cikin gidan, knocking yyi jin kofar a kulle, cikin minti kadan Maimoon ta bude kofar, matsawa tayi tana kallonsa daga sama har kasa, lkci daya ya daure fuska, ta xaro ido tace "Au, sannu da xuwa yaya" Da sauri ta juya ta koma parlon, Umma dake xaune Jiddah ma na xaune kasa daga kusa da ita ta daga kai tana kallonsa, tunda Jiddah ta kallesa sau daya ta sunkuyar da kanta, Ya karasa parlon ya xauna yana kallon Umma yace "Ina yini Umma" Tace "Lafiya lau, aka ce yau xaka yi tafiyar?" Yace "Ehh in sha Allah..." Sai kuma ya shafa kansa yace "Naga ban xo mun yi sallama bane" Umma tace "Bayan wanda mu ka yi a gidan Yaya?" Ya sunkuyar da kansa, Maimoon dai na tsaye sai kallonsa take, idan ta kallesa sai ta kalli Jiddah da taki dago kanta sai wasa da fingers dinta take, Umma tace "Toh ki kawo masa ruwa Maimoon" Maimoon tace "To Umma..." Har ta kai bakin kofar kitchen din ta tsaya tana kallon Jiddah tace "Jiddoh xan xuba moringa din yanxu, ki xo ki gani" Jiddah ta d'an kalleta, Umma tace "Ba kince kina son koya ba, ki tashi ki je" Mikewa Jiddah tayi ta wuce kitchen din, da gefen ido ya bi ta da kallo a sace yanda Umma ma baxata sani ba, Umma tace "Amma daxu mun yi waya da Ahmad yace xai je kai ka airport..." yace "Ehh Umma, xan koma yanxu.. nan da awa daya da rabi ne flight din" Umma tace "Toh Allah ubangiji ya tsare, ya kai ku lafiya ya dawo da ku lfya" Yace "Ameen" Jiddah na shigowa kitchen Maimoon ta kulle tana kallonta tace "Kawai sai naga yaya Aliyu, alhalin for almost 2 weeks bai xo gidan nan ba" Jiddah ta hade rai tace "Toh me yasa kike gaya min?" Dariya Maimoon tayi har da tafe hannu tace "Aa ni fa kawai hira nake maki wllh..." Jiddah ta juya xata fita Maimoon ta rikota tana dariya tace "Ke wllh ni kawai jajantawa nake son mu yi da ke" Jiddah tace "Ki sakeni fita xan yi" Maimoon tace "Dallah ki tsaya in hada miyan tukunna, to meye don nace kawai sai ga yaya Aliyu, au ni na ma xata Safiyya ce nake maki wannan maganan, abinda mun saba gulman mu haka, amma ke kina so ki min wata fassara" Jiddah dai bata ce komai ba sai kallon miyan dake saman gas take, Maimoon ta tafi ta dau ruwa da coke ta daura kan tray ta dawo tana kallon Jiddah ta mika mata tace "Don Allah ki kai masa kar miyan ya kone" Da sauri Jiddah ta matsa ta tafi gun miyan tace "Bar min miyan xan dinga dubawa kije ki dawo" Maimoon ta hade rai tace "Kika san me xan ma miyan to?? Ni wllh wani lokacin kina bani mamaki, meye a ciki kawai dai kije ki dungurar masa da tray din a gabansa ki taho, wllh ba don miyan ba ni da kaina xan kai, ai ni aka sa ba ke ba" Maimoon ta d'an yi tsaki ta ajiye tray din tace "Haba, sai kace warce nace ki kai ma wani dodo ruwan sha" Gun miyan ta tafi tana juyawa, sai kuma ta nufi kofa a tunanin Jiddah daukan ruwan xata yi ta kai masa, sai taga bata dauka ba, Maimoon na fita parlor ta kullo kofar kitchen din tana kallon Umma tace "Umma wai Aunty Malika na ta kiranki, kamar wayarki na daki koh?" Umma tace "Ta kira ki ne?" Maimoon na d'an rawan baki tace "Haka dai tace min" Mikewa Umma tayi ta nufi hanyar dakinta tana cewa "To ai wayar na daki" Maimoon ta koma kitchen da sauri tana ci gaba da juye juyen miya bayan gas din ma a kashe yake tace "Kawai minti nawa kin kai ruwa kin dawo, idan ba dai da akwai wani abu a ranki da kike boye ma mutane ba" Jiddah dai bata ce komai ba sai kallon tray din take, Maimoon banda satan kallonta babu abinda take, daukan tray din Jiddah tayi daga karshe ta nufi kofa tana tafiya kamar bata son yi, ta bude ta fita, sai da ta shigo parlor taga Umma bata nan, ta fara kalle kalle, yana ganin haka ya mike, ta dungurar da ruwan kamar yanda Maimoon tace, xata juya yyi saurin kamo hannunta, ta juya ta marairaice masa murya kasa kasa tace "Wllh xan maka ihu ka sakeni, ka daina min abun nn da kake yi bana so" jan hancinta yayi har sai da ta ji xafi sannan ya saka mata takardan hannunsa a tafin hannunta yana kallon kwayar idonta, fixge hannunta tayi daga rikon da yayi mata kusan a guje tayi hanyar dakin amma takardan da ya bata na hannunta har sannan, ya bi ta da kallo kafin ya juya, ido hudu suka yi da Maimoon da ta d'an bude kofar kitchen din tana lekosu, ai da sauri ta yi jamming kofar bayan sun hada ido, yayi hanyar kitchen din, saura kadan ta tunkude miyan kan gas din bayan ya shigo kitchen din, sai xare katon idonta take tace "Xa a xubo maka abincin ne Yaya?" Janyo hannunta yayi yace "Ba dai kin iya munafurci ba??" a gigice tace "Don girman Allah kayi hakuri yaya, naje kulle kofa ne sai ka gan ni..." Bai saurareta ba ya bude kofar kitchen din ya fita yana rike da hannunta.... Umma ce ta fito parlor tace "Au, tafiya yayi shashashan?" Babu kowa parlon balle a bata amsa, Ta wuce dakinsu Jiddah taga Jiddah kadai a dakin tace "Aliyun ya tafi ne?" Jiddah tace "Ina daki ban sani ba" Umma tace "Toh ga shi ki amso min kati na dubu daya a waje" Jiddah ta d'an xaro ido amma bata ce komai ba ta amshi kudin gabanta na faduwa, Umma na fita dakin ta saka hijab dinta ta fita ita ma, duk jikinta a sanyaye ta fita compound, tana isa gate ta leka waje ta ga motar Ahmad instead, amma Abuturrab ne a ciki Maimoon na tsaye daga window din kusa da shi ta daddage tana cewa "Ni dai wllh ka tura yanxu kafin ka tafi yaya, haka kawai idan ka je ka manta bayan na sanka da mantuwa, kawai bari in kira maka account number din ai yana kai na" Ko kallonsu Jiddah bata sake yi ba ta nufi kantin da xata amso kati, Abuturrab na danna wayarsa yace "Call the account number" tana washe baki ta shiga kira masa account number dinta har ta gama, snn ta fara kallon wayarta dake hannunta tana murmushi, cikin few seconds sai ga alert, ta duba da sauri taga dubu hamsin, wani tsalle ta doka tana tafe hannu sannan tayi masa blow din kisses tace "Nagode sosai yayana, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara maka budi, Allah ya kai mana kai lafiya ya dawo da kai lafiya" Komawa baya tayi ganin ya tada motarsa tana daga masa hannu har ya bar layin, baki har kunne ta shige cikin gida, Jiddah ma ta shiga gidan don duk tana kallon abinda Maimoon take a titi.... Dakin Umma jiddah ta tafi ta kai mata katin sannan ta fito ta shiga nasu dakin, gaban madubi ta tafi ta dau takardan da ta ajiye bayan ta shigo dakin daxu, daukan takardan tayi ta shiga warwarewa, haka kawai ta ji gabanta na faduwa, ganin ta kusa gama budesa ta rufe idonta, sai da ta warware gaba daya sannan ta bude idonta a hankali tana kallon content din takardan gabanta na faduwa, "Ni ba matarsa ba, ni ba muharramarsa ba... amma yake min wasu abubuwa da bai dace ba a addininmu, bayan duk wani da yasan karatun addinin nan namu yasan haramcin yin abinda yake yi, ya kuma san hukuncin wanda ya aikata hakan, kullum tunanina wanda xan kai ma kararsa... ya takura ni, ya takura ma rayuwata bayan kuma ya sakeni kowa kuma ya shaida ya sakeni....." Boldly daga kasan rubutun aka rubuta "Ur mentality Jidderh!!! And I know u might be questioning my fate, amma ki saka a ranki ba dai dai kike da sauran yan matan da ke gaban iyayensu ba yanxu, you ain't of the same level with them... abu kadan xa ki yi Allah yayi fushi da ke! ... no doubt na fi ki sanin addininmu, limit ur interaction with MALE, limit ur going out, and by so doing, u are respecting ur religion" Jiddah ta karanta content din takardan nan yayi sau biyar amma ba abinda ta gane, da ta dauko hanyar ganewa sai abun ya ruguje kan ta kai karshe, a hankali ta linke takardan ta yaga, sai da tayi masa pieces sannan ta tafi ta bude window ta watsar, Maimoon ta shigo dakin ta ajiye wayarta gaban mirror tace "Ke bikin kawar nan tawa fa sati me xuwa ne, ina ta son in kira Aunty Ramlah ince ta baki waya in gaya maki muna da biki, kuma ba karamin casu xa ayi ba, hope kun gama exams before then?" Jiddah ta tafi ta xauna gefen gado tana duba farcenta tace "Ban gama ba" Ta gefen ido Maimoon ta kalleta ta d'an ta6e baki ta nufi kofa tana cewa "Ko da yake ke ai sai da izini, mu din dai" Daga haka ta fice, Jiddah ta bi ta da kallo. Bayan sati daya Jiddah suka gama exams suka yi hutu ta dawo gidan Umma yin hutu... Ranan friday ita da Maimoon da Safiyya suka shirya xa su gaida Ummi, Da yake driver baya nan, Umma ta basu kudin adaidaita tana sake jaddada masu kar su kwana saboda Islamiyya gobe, Maimoon tace "Haba Umma karfe biyar na yi xa mu juyo, har sun nufi kofa Maimoon ta kalli Jiddah tace "Anya baxa ki sa Hijab ba Jiddah?" Safiyya tace "Saboda me?" Maimoon tace "A'a ba saboda komai ba, gani nayi ya fi mutunci" Daga sama har kasa Safiyya ta kalleta tace "Shi yasa naga kin sa Hijab din ke ai" Jiddah tayi ficewarta bata sake sauraron Maimoon ba, Safiyya tace "Duk wani harka na iyayi kin fi kowa iyawa" Maimoon tace "Aa daga magana sai cibi ya xama Kari, ni dai ba kawai suggestion na kawo ba" Safiyya tace "Why didn't u suggest that for ur self??" Maimoon tayi ficewarta tayi banxa da ita. Suna isa gidan direct bangaren Ummi suka wuce, Aneesah na xaune parlon da kanwar mamarta Safara'u da ta tare a gidanta tun bayan da Aliyu ya bar kasar, Ummi ma na parlon alamar dai su ma xuwansu kenan, Maimoon na ganin Aneesah ta hade rai tana kallon Ummi tace "Ummi ina yini?" Ummi tace "Lafiya lau Maimuna, daga gida ku ke haka?" Maimoon tace "Ehh wllh Ummi, Hajja na nan?" Ummi tace "Hajja ai tana Bauchi" Maimoon tace "Ohk" daga haka ta wuce dakin Ummi, Aneesah ta bi ta da kallo, Jiddah ma ta durkusa ta gaida Ummi, Ummi ta amsa da fara'a, wani kallo Aneesah ta dinga yi ma Jiddah kamar ta ga kashi, Jiddah ta kasa kin gaida Safara'u ganin babba ce, Aneesah na jin ta gaida Safara'u tayi ma Safara'un alamar kar ta amsa ta hanyar ta6a ta da sauri, ai ko Safara'u taki amsawa, Safiyya ta gaida Ummi sannan ta gaida Aneesah da Safara'u ta mike ta wuce dakin Ummi, Ummi na kallon jiddah tace "Tashi ki bi su ko" Mikewa jiddah tayi ta bi bayansu, Aneesah dai sai kallonta ta gefen ido take, ta rasa dalilin da yasa da taga Jiddah sai hankalinta ya d'an tashi, Safiya ce tsaye tana kallon Maimoon tace "Me yasa baki gaida Aunty Aneesah ba?" Maimoon da ke kwance kan gadon Ummi ta mike tace "Wacece kuma Anty Aneesah? Me na hada da ita da xan gaisheta?" Safiyya tace "Matar Yaya Aliyun??" Maimoon tayi wani dariya tace "Ta jira dai taga matar tasa ta ainahi... Wannan matar me yi ma mutane kallon rainin hankali da walakanci ne xan gaishe da, ji fa ranan da muka je gidanta abinda ta mana har xaki ce in gaisheta, a da nayi vow har in mutu baxan sake komawa gidan yaya Aliyu ba, amma dai nayi istigifari kwanan nan don can ne ma dabar mu idan Allah ya so nan ba da dadewa ba, sai ta raina kanta wllh, don ni tattara kayana ma xanyi in koma gidan sai dai in Umma ce ta hanani ko shi ya korani" Daga Safiyya har Jiddah dai kallonta kawai suke, ta murguda baki ta mike ta fice daga dakin yanda xata sake bin gaban Aneesah ba tare da ta gaisheta ba, ai ko Aneesah ta bi ta da kallo kasa kasa xuciyarta na tafarfasa har ta fita parlon. Kamar yanda suka sanar ma Umma karfe biyar suka fara shirin komawa gida, Ummi ta basu kudin mota sannan tace "Amma fa ku shiga ku sallami Aunty duk da bata dade da dawowa ba" Sallama suka mata suka fita, Jiddah tayi pretend kamar xata je ta sha ruwa, Maimoon da Safiyya suka shiga part din Aunty, Tana xaune parlonta da Aneesah da Safara'u, suna gaisheta ta mike rai bace tace "Wato ke Maimoon don baki da kunya baki gaji kunya ba ita Aneesar xa ki gani ki ki gaisarwa ki wuce don Ubanki??" Maimoon ta tsaya tana mata kallon tara saura amma taki cewa komai, Aunty na tafe hannu tace "Maxa fitar min daga parlor kada in rotsa maki kai, shegiya fitsararriya kawai" Aneesah tace "Ae kawai da kin kyaleni da ita Aunty, ita karamar alhaki ma?? Wllh so nayi watarana Allah ya kawota gidana in mata koran kare, uwar me gaisuwarta xai kare ni da shi dama?" Maimoon tayi wani dariya tace "A gidan yayan nawa xa ki yi min koran kare??" Aneesah ta mike tana huci tace "Kya dai je ki nemi yayanki amma ba Aliyu ba, idan kuma da akwai abinda ya fi koran kare wllh sai na aiwatar gareki in har rashin hankalinki ya ja ki xuwa gidana, don wannan gidan a yanxu ko shi Aliyun ba shi da wani say a kansa, yau da Ramlah ko Nafisah ko Aisha ce suka ki gaisheni shine xan ji takaici amma banda ke karere gayyar tsiya" Maimoon tayi wani shewa tace "To mu xuba dake shege ka fasa, kuma wannan gidan da kike takama da shi sai ya gagareki xama kwanan nan ba da wani dadewa ba wllh, abota xa ki kulla da sleepless night very soon..." Da gudu Maimoon ta fice daga parlon tana murguda baki ganin Aunty ta yo kanta tana kunduma mata wasu axababben xagi kamar bamagujiya, ita dai Safiyya na tsaye kamar shashasha, Safara'u kuwa sai dannan xuciyarta take tunda Aunty da Aneesah nayi ita bai kamata ta sa baki ba, Aunty tayi mata tsawa tace "Fita kema, gantalallu gayyar tsiya kawai...." Safiyya bata ce komai ba ta fita daga parlon, tuni Maimoon ta ja Jiddah suka fice daga gidan ranta fess ta fesa masu rashin kunya iya rashin kunya, sai da suka nufi titi Safiyya ke cewa "Wllh baki ji Maimoon, baki jin magana, Umma ta hanaki wannan halin kin ki, idan ma sun xageki meye na biyesu bayan kin san ba sa'anninki bane su??" Maimoon tana tafe hannu tace "Ba ruwana da tsufansu, ai ance respect begets respect, Respect should only be given to he who deserves ita, wato dai he who respect his or her self, basu yi respecting din kansu ba balle inyi respecting dinsu, haka kawai a xagi ubana dake kabari a kan wata banxa jaka can kaxama da ita kike expecting inyi shiru kamar ban san ciwon kai na ba?? To wllh ban rama yanda nake so ba ma, sai ranan da muka fara bata sleepless night a gidanta sannan xata gane ni ba kanwar lasa bace..." Wani shewa Maimoon tayi cike da farin ciki, Safiyya tace "Ke da wa xaki bata sleepless night din" Maimoon ta bude hannu tace "Ohoo a xuba ido a gani, shi sa Jiddah asirinta a rufe taki shiga nima da na sani wllh kawai ce ma Ummi xanyi to amma inyi wucewata, uwata ce ita da dole sai na gaisheta??" Safiyya tace "Ni dai ba ruwana ki daina wnn halin da kike...." Maimoon tayi gaba ta ki sauraran Safiyya kuma, Jiddah dai tafiyarta kawai take bata ce masu komai ba, a ranta kuwa taji dadin dubaran da tayi na shigewa kitchen da yau har da ita xa a hada a xage ubanta dake kabari. Bayan kwana biyu Jiddah na xaune kan darduma ta idar da isha Maimoon ta shigo rike da wayarta dake kare kunnenta, ta nufeta ta mika mata wayar tace "Kema ku gaisa, Safiyya ma sun gaisa, har da Umma ma sun gaisa" Jiddah na kallonta ta amshi wayar, screen din ta fara kalla ta ga "Yaya A" ta kai wayar kunne tayi shiru, Maimoon tace "Toh kiyi magana mana ai bai katse ba fa" daga daya bangaren taji yace "Shiru kika yi?" Lokaci daya ta dau muryarsa wanda hakan ya ja mata faduwar gaba, ta d'an hade rai a hnkli tace "Ina yini" Yace "How are you?" Tace "Lafiya" juyawa Maimoon tayi ta lallaba ta fita dakin.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Kallon screen din wayar Jiddah tayi jin shirun yyi yawa, taga har sannan bai katse ba, ta d'an turo baki tace "Ina jin ka" Yace "Ohk... Ae ban san kina ji ba" mikewa tayi ta nufi kofa ta fita, ganin Maimoon a xaune parlor ta tafi ta dungurar mata da wayarta ta juya ta koma daki... Umma ce xaune parlor tare da Maimoon, Jiddah kuma na xaune dinning area rike da littafi a hannunta tana dubawa, Umma na kallon Maimoon tace "Ke a ina ku ka yi magana da shi kika san bashi da lafiya?" Maimoon tace "Ba muna chatting ba Umma, wani lokacin ma har video call muna yi" Umma ta kyabe baki tace "Toh Allah ya basa lafiya" Maimoon tace "Ameen, Umma har fa ya je asibiti yace min" Umma tace "Ikon Allah, kila change of weather ne, barin yanda ya dade bai fita waje ba, Allah ya basa lafiya" Maimoon tace "Dama nima nace change of weather gashi he still have some months kafin ya dawo" Umma tace "To kuma wannan shirin gulman da ku ka tsiri yi da shi na meye?" Dariya Maimoon tayi har da kwanciya, tace "Toh ba ya ga ya tafi inda baxae dinga ganin mu ba Umma, gashi bashi da kowa a can, kinga yanxu da a kasar nan ne bashi da lafiya ae da duk mun je duba sa har da abinci... To amma yanxu babu me kula da shi" Umma dai tayi dariya kawai, can tace "Dama yaje da matar tasa ne da sauki, to bai je ba, kuma ranan da Ummi tayi masa magana cewa yyi kawai bai da niyyar xuwa da ita ne but he is allowed to go with his wife" Maimoon ta rike ha6a tace "Toh ba sonta yake ba Umma, don dai kawai baxai yiwu ya tafi da warce yake son bane amma ni nasan da ya tafi da ita" Umma tace "Wacece ita warce yake son?" Maimoon ta d'an rufe baki tace "Aa wai imagining kawai nake" Umma ta tabe baki tace "Haka yace maki baya son matar tasa? Da baya sonta ai baxai aureta ba" Maimoon dai bata sake cewa komai ba sai murmushi take, Safiyya ta fito daga daki rike da wayar Maimoon dake ring ta mika mata sannan ta koma dakin, mikewa Maimoon tayi bayan ta saci kallon Umma ta wuce dakin da sauri, tsaye tayi bakin kofa dai dai nn wayar ya katse, tabe baki tayi sai gashi an sake kira ta daga ta kai kunne tare da sallama, cikin faram faram tace "Lafiya lau wllh Engineer, amma kuma bata dawo ba har yau fa...." ta d'an yi shiru sai kuma ta kyabe baki tace "Toh gaskiya nima ban sani ba dai, amma babu rana kam, kasan nace maka ta bar nan sbda karatu, mu ma sai season season muke ganinta..." Da sauri tace "Toh ae ita ma matar Ya Ahmad din ba wayar gareta ba ya fada cikin ruwa..." Ta d'an sosa kai tace "Toh ina jin dai nan da sati biyu ne xan je can gidan sbda kaga baxa mu je mu tarar ma yaya Ahmad a gidansa ba, amma dai idan naje din xan bata in sha Allah" Ta kara da cewa "Toh shkkn bye" katse wayar tayi ta juya xata fita Safiyya tace "Wacece bata nan?" Maimoon ta juyo ta kalleta bata amsata ba ta fita dakin Safiyya ta bi ta da kallo... Tunda Maimoon ta fito Jiddah ke kallonta, Umma da ta bi ta da kallo tace "Waye ya kiraki don munafurci kika shiga daki Maimoon?" Maimoon ta sosa kai tana er dariya tace "Aa Umma kawata ce ta kirani tace akwai gist daxu ina aiki ban samu mun yi waya ba sai yanxu ta sake kira" Wani kallo Umma ta dinga yi mata ta wuce kitchen da sauri tana dariya... Da daddare Jiddah na kwance amma ba bacci take ba, tana son yin baccin amma ta rasa abinda yasa ta kasa, sannan tana jin abu da ita kanta bata san meye ba ya tsaya mata a rai yana damunta, Maimoon ce ta shigo dakin bayan ta gama kallon da take a parlor, ajiye wayarta tayi gefen gado ta shiga bandaki, Jiddah ta bi ta da kallo, sae da taga ta kulle kofar bandakin sannan ta mike xaune ta jawo wayar a hankali don bai shiga lock ba, call logs ta fara shiga ta d'an yi scrolling sae kuma ta fita da sauri ta shiga application din WhatsApp, second to the last chat din da ta ga an sa Yaya A... Ta shiga tana sake kallon kofar bandakin, dai dai nan taji an bude kofar saboda rudewa kawai ta kashe wayar tana kan What'sapp din ta mayar da sauri ta ajiye ta kwanta ta rufe ido, Maimoon ta fito ta dau wayarta ta bude lock din, mamaki ne ya cikata tana kallon wayar ganin chat dinta da Abuturrab ne gaban screen din bayan ita ba kan WhatsApp take ba, ta kalli Jiddah da ta ki bude ido, kofa kawai ta nufa ta tafi parlor ta xauna kan kujera sannan ta fara kyalkyale dariya har da kyakyatawa, Safiyya tace "Meye haka??" Dariya kawai Maimoon take, Safiyya tayi tsaki ta mike ta wuce daki, Sae da Maimoon tayi dariyar me isarta sannan ta tashi ta koma dakin, Jiddah dai ta rufe har kanta ko da Maimoon ta koma dakin. Da safe Jiddah taki amincewa su hada ido da Maimoon, Maimoon dai sai harkan gabanta take, karfe goma Umma da Safiyya suka fita xuwa kasuwa, Bayan fitarsu Maimoon ta shigo daki ta dinga jan Jiddah da hira don sun gama aikinsu tun safe, tun Jiddah na kin tanka mata har dai ta sake, labarin wata kawarta da tayi aure mijin ke gallaza mata Maimoon ke yi mata, Jiddah tace "uHum! To ko dai ita ma akwai abinda take masa ne kawai fada maku ne baxa tayi ba" Maimoon ta takarkare tace "Aa wllh, babu wani abu da take masa, d'an iska ne kawai ta aura, ke kinga soyayya kamar xa su cinye kansu kafin ayi auren?? Wllh soyayya kamar indiyawa har suna intimidating dinmu, to yau dai ga shi sun koma enemies din juna, abun da mamaki" Jiddah tace "Ke dai kawai kiyi shiru tunda ba a gidan nasu kike ba balle kiyi siding dinta, ba dole sai ta fada maku gaskiya ba" Maimoon tace "Ji wani magana da kike, to ke duk xamanki gidan yaya Aliyu kullum ne yake kula da kin ci abinci ko baki ci ba? Ba wahala ya dinga baki ba duk kika rame kika kanjale har kika gwammace bai dauko ki daga gidanku ba" Kallonta kawai Jiddah ke yi, sai kuma ta dauke kai tace "Aa ni bai ta6a bani wahala ko ya bar ni da yunwa ba, in ji waye yace maku haka..." Maimoon tace "Aa fa xancen gaskiya muke yi a nan Jiddah kar ki wani rufa masa asiri, kuma kinsan a yanda take bamu labarin mijin nan nata wllh kamar halinsu daya da Yaya Aliyu, ai ke kin xauna gidansa kinsan wanene shi" Jiddah dake kallonta tace "Wani irin hali ne irin nasa?" Maimoon ta gyara xama tace "Kin ga Zainab bata da wani freedom tun da ta shiga gidan nan, sannan kullum a hantare take wajensa, gashi babu wani kulawa, ga masifa ga fada, ga yunwa, ga shi yayi ta depriving dinta of so many things, to mention but a few..." Katse ta Jiddah tayi tace "Aa ni dai ban tuna sanda ya hantareni ba, sannan ni yana kula da ni... freedom kuma dama xaka auri mace ne ka saketa tayi ta yawo a gari? Sannan ni dai ban ta6a xama da yunwa a gidansa ba, and he never deprived me of anything all through my stay in his house, in dai Aliyun da na sani kike magana a kai to ba halinsu daya da mijin kawarki ba" Maimoon ta rike ha6a tace "Ohh har kin manta duk abinda kika yi facing lokacin kina gidansa kenan Jiddah?" Jiddah tace "Ban yi facing komai ba, ni dai nasan ko baya nan nace ga abinda xan ci yana kawo min, ba fa wai sae yana within kaduna ba, A'a ko daga kano ne yana kawo min, sannan xan iya kirga sau nawa nayi girki a gidan sa, kullum sai yayi min take away din abinci ko xan ci ko baxan ci ba" Maimoon tace "Tabb da gaske haka yake da caring? Ni wllh irin mijin da nake so kenan" Sau daya Jiddah ta kalleta ta dauke kai, Maimoon tayi tagumi tace "Toh ai kuwa in haka ne koma meye bai cancanci ki watsar da shi ko me xai faru ba, Toh Allah dai ya kyauta, na manta ma ban kirasa naji ya jikinsa ba" Daga haka ta jawo wayarta ta shiga kiransa, har ya katse bai dauka ba ta ajiye wayar tayi tagumi tace "To ko dai jikin nasa ne" Jiddah bata ce komai ba, sai gashi ya kira, da sauri Maimoon ta daga cike da damuwa tace "Hello Yaya A, ya jikin naka?" Kusan minti uku suna magana, Jiddah dai na wajen bata ko kara kallonta ba, can Maimoon tace "Yaya A, ga Jiddah xata yi maka ya jiki" daga haka ta kamo hannunta ta saka wayar, Jiddah dai kallon wayar kawai take, Maimoon ta mike ta dau cup din da ta sha shayi ta fita, Jiddah ta kai wayar kunne, jin yyi shiru tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau" Tana wasa da edge din xanin gado tace "Ya jikin?" Yace "Wa yace maki bani da lafiya" Shiru tayi, yace "Ina jin ki" Ta d'an turo baki tace "Maimoon" yace "Amma baki min ya jikin tun jiya ba ai" Bata ce komai ba, yace "Da sauki" tace "Allah ya kara lafiya" yace "Ameen... Me Awara" dago kai tayi da sauri ta d'an wara ido, sai kuma ta rufe fuskarta da pillow din dake kusa da ita tana murmushi, yyi kasa da murya yace "Ko ba ita bace?" Ta turo baki tace "Ni ai ba awara nake yi ba yanxu" Yace "Ohkk... Ko xaki fara ne?" Ta d'an yi murmushi taki ce masa komai, yace "Har yanxu ae kina da burin fara awara a bakin titin gida na...." Murmushi take yi sosai, a hankali tace "Toh ai ba a unguwar nake ba yanxu..." Yace "Toh idan kika dawo anguwan fa?' ta xaro ido tace "Me xai maida ni?" Yace "Ni xan maida ki duk sanda kika shirya" Tayi wani murmushin bata ce komai ba, yace "Ko baki son komawa?" Tace "Wai in koma inyi mene??" Yace "Ki koma kiyi ibada" Ta xaro ido tace "Wani irin ibada?" Yace "Irin warce baki samu daman yi ba" Tayi shiru kamar me son fahimtar abinda yake nufi, can tace "Ni ban gane ba" Yace "Irin warce Allah yace ayi" Tace "Ban san shi ba" Yace "Xaki san shi kwanan nan" Bata kuma cewa komai ba shi ma yayi shiru, a hankali tace "Allah ya kara lafiya" yace "Ameen, sai dai ban ta6a cin awaranki ba tun da can ma" Tayi murmushi bata ce komai ba, yace "Yeahh" tace "Sai ayi maka" Yace "Irin na Baabarku?" Shiru tayi, ya shafa kansa yace "Sai anjima" daga haka ya katse wayar ta kalli screen din sannan ta ajiye a hankali... Abba ne xaune parlor da Hajja sae Aunty, Hajja na gyara daurin dankwalinta tace "Ae kaga saboda xuciyata me kyau ce bana riko duk da rashin kunyar da yarinyar nan ta min hakan bai hanani tsayawa har sae da na tika uwar Bashir da kasa ba, don da cewa tayi inaaa d'an ta baxae ta6a auran mara asali ba, to duk duniya banda shege waye bai da asali, da yake kabiru na jin maganata yana min biyayya don har ma ya fi ka, ba shiri ya taka mata birki ya dau maganata da muhimmancin gaske, to ba gashi komai na tafiya dai dai ba" Abba dai sae kallonta yake, Aunty dake ta boiling from inside sai kallon Hajja take amma ba daman cewa komai, kasa hakura tayi daga karshe ta dake tace "Toh shi Bashir din me yace Hajja?" Hajja tace "Aa baya ma kasar, yo shi Ina ruwansa, galallawa ne fa yaron nan da kuke gani, duk yanda nayi yace dai dai ne yasan baxan masa xa6in da xai cucesa ba, toh ni abinda yasa na makale ma yarinyar saboda tsaftarta ne baxan biye rashin kunyan da tayi min ba, duk da nasan wannan narkekiyar matar Ramlah ce xata koya mata ta min haka, amma da baxa ta min haka ba... Yanxu dai Kabiru yace kai sai ka xama madaurin aurenta wato waliyyinta, so nake kafin Bashir ya dawo an daura sai dai kawai a wanketa a kai masa dakinsa, uban ma ya amince da hakan...." Abba yace "Toh Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi" Hajja tace "Cewa xaka yi Allah ya baki ladan wannan jihadi Hajja, ka ga ai da ni tsohuwar banxa ce baxan so in hada Jiddah da jinina ba don wllh gidan da Aliyu ya kai ni a hayin rigasa yace nasu ne, duk da a rushe gidan yake amma kana ganin gidan kasan na fakirai ne, su talaucin ma ba karamin kamu yyi masu ba, da kyar ake samun masu talauci irinsu, mu dai ba saboda Allah kawai muke abun mu ba dama, Allah dai kawai ya bamu lada" Mikewa Aunty tayi ta nufi kofa ta fice Hajja ta bi ta da wani kallo tace "Ae kaga da yake ta kaina nake, ni ko da wasa ban ta6a kawo d'an ta Salem a rai ba balle wataran ta zageni ko shi ya xageni, amma yanxu haka da xaka shiga xuciyarta xaka san hadin nan bai mata ba, na rasa abinda jiddah tayi mata da wannan tsana haka" Abba yace "Xan d'an fita Hajja, sae na dawo anjima" Tace "Toh Allah ya tsare, cikin satin nan Kabiru yace xa a kawo komai kilan har sadaki, wato shi ma xaman yaron a haka ya ishesa ashe, magana ce kawai baya yi, gashi sae yyi ta fita kasar waje an rasa uban me yake xuwa yi a can" Daga haka ta mike tace "To ba ruwana, ita warcan narkekiyar sae ka tafi har can gidanta ka yi mata bayanin komai don kar ta xo ta min rashin albarka ta cuce ku, ba karamin aikinta bane, don duk tayi bake bake kan lamarin yarinyar" shi dae bai ce mata komai ba har ta fita, girgixa kai kawai yake yana mamakin Hajja, ya dau wayarsa ya shiga kiran Ummi, tana shigowa ya tsara mata duk yanda suka yi da Hajja, Ummi ta rike ha6a tace "Ikon Allah, Haka dama auren yake da sauki Yallabai, ina laifin ma ta kare secondary din tunda ta dauko hanya? Ita fa Hajja idan ta shirya abu a ranta babu me canxa ta, sannan tana ta nuna Bashir din ma yace ba ruwansa, tayi duk yanda tayi.. to an ta6a aure haka babu fahimtar juna tsakanin mata da mijin? Ko magana fa basu ta6a yi ba a waya" Abba yace "Ba dai tace shi Kabir ya amince ba ya bata goyon baya? To Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi, ita ma yarinyar Allah ya sa hakan babban alkhairi ne a gareta" Ummi dai tayi shiru, can tace "Ba fa a tambayi yarinyar nan ko tayi na'am da hakan ba, it's more or less like auren dole xa ayi mata, gwara a fara jin ta bakinta Yallabai, kar a ga kamar don ba mu muka haifeta ba shi yasa ake juyata yanda ake so, hakan ba dai dai bane wllh" Abba yace "Wannan kuma ai aikin ke da Hajiya Ramlah ne, xuwa anjima sai kije can gidan kiyi mata bayani sannan a ji ta bakin ita yarinyar, don a yanda Hajja ta axalxali batun nan sai ta iya cewa cikin sati biyu ma take son ayi bikin" Ummi tace "Toh Allah ya kyauta, amma ya dace ka kira shi mai martaban kaji ta bakinsa, kilan ma shirinta ne ita kadai wa ya sani?" Abba yace "Ehh ina jiran nan da d'an anjima ne xan kirasa in sha Allah" Ummi tace "Toh Allah yayi mana me kyau" Abba ya amsa da "Ameen" mikewa tayi ta fita daga parlon. Umma ce xaune bedroom dinta tare da Ummi, ta jira har Ummi ta kai aya sannan tace "Kinga yanda baxan so ayi ma Maimoon ko Safiyya ko Siyama auren dole ba, to haka ita ma Jiddah baxan yarda da hakan ba Yaya, a ajiye batun ai ko bani na haifeta ba, wllh yanda xanyi ma 'ya yan cikina ita ma haka xan mata, ku yaya Hajja sai tayi ta wasu abubuwa kamar dai notiran kanta sun kwance amma ku dinga biye mata a rasa me gaya mata gaskiya? Meye amfanin hakan fisabilillah? Ni fa na xata tunda nace aa an bar xancen ne ashe abinda ya kai ta bauchi kenan ma? To ni dai sai dai a fadi duk abinda xa a fada amma Jiddah is too young for that marriage, sannan har take ikirarin uwar Bashir din bata so amma tayi ruwa da tsaki a kan lamarin har sai da ta sa kowa ya amince, wani xaman aure take son yarinyar taje tayi a wannan babban gidan Ummi, shikenan saboda bata da iyaye ita marainiya ce sai aka ce bata da gata? Aa wllh tana da gata don yanda na dau su Maimoon haka na dauketa, Hajja taje can ta samar ba Bashir wata matar amma ba Jiddah da ko secondary din ma bata kare ba" Ummi tace "Toh ina ga xai fi ki tashi kije ki samu Hajja kiyi mata duk bayanin nan, ke wani lkcn kina magana kamar baki san Hajja ba, kin gan ni nan duk fa abinda xai dameni ko ya bata min rai bana so yanxu, ta kaina kawai nake babu ruwana, In dai Bashir din da bakinsa yayi admitting yana son Jiddah kuma xai xauna da ita i see nothing wrong with that, domin kuwa shi din ba wani xama yake a kasar ba, bini bini ya fita, to ba sai ya tafi da matarsa ba, ina Jiddah xata ga uwarsa idan ba dawowa kasar suka yi ba, kinga wllh yanda kike hakikancewa a batun nan tsaf Hajja xata ce Hassada kike tunda ba er ki bace, don haka ina baki shawara ki bi komai saisa saisa babu ruwanki..." Umma tace "Aa kiyi hakuri yaya a gaskiya da ruwana, Hajja kuma ba tun yau na saba da tijararta ba, kuma ni kema kin san raga mata nake kawai sabida ke, banda haka ni baxan yi tolerating haka ba, kuma a gaskiya idan haka abubuwa xa su ci gaba da faruwa gwara ki tafi da Jiddah can gidan don ma kada taga kamar ban tsaya mata ba tunda ni ba uwarta bace.. ki tafi da ita kawai ku yi yanda ku ka ga ya dace da ita, dama ai Hajjar ta sha fada min ba don Aliyu ba a ina xa a santa, don haka ki tafi da ita ku yi mata bayani a can amma ba a nan ba" Ummi dai kallonta kawai take, Umma ta mike tace "Haka kawai ga gaskiya a dinga takesa kiri kiri, ita Hajjar Allah ce da dole sai an bi abinda tace mata gigin tsufa duk ya rikitata kuma ayi ta bin ta a haka, ba ga jikokinta sa'annin jiddar ba, tayi masu auren mana idan haka ne, kiyi hakuri fa kar kice rashin kunya nake maki Yaya, aa gaskiyata nake fadi, kawai don Jiddah bata da gata a duniya sai a tauyeta?? To dauketa ku tafi kuyi yanda ya dace da ita, babu ruwana" Mikewa Ummi tayi ta fita daga dakin tayi wucewarta... Bayan tafiyar Ummi da kusan awa daya su Maimoon suka dawo Islamiyya, bayan sun gaida Umma dake xaune parlor xa su wuce dakinsu Umma tace "Da wani number kike waya da Aliyu Maimuna?" Maimoon ta dawo, Jiddah ta d'an saci kallon Umma sannan ta wuce ciki, Maimoon tace "Da numbersa ne yana shiga" Umma tace "Toh" daga haka ta mike ta wuce dakinta ta hau kiran Abuturrab wayar bai yi connecting ba hakan yasa ta ajiye ta fito... Sai can da daddare Umma ta sake kiransa sai ya shiga, yana dagawa bayan sun gaisa tace "Kana ji na Aliyu?" Yace "Ina ji Umma" Tace "Ka dai ji abinda iyayenka ke shirin aikatawa ai ko?" Ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Na me fa?" Tace "Ohh duk baka sani ba, to Hajja ta dage ita dole sai tayi ma Jiddah aure da Bashir, na kiraka ne kuma saboda naga kamar tana jin maganarka, i want u to put a stop to that, ko secondary bana fatan Jiddah ta gama ace xa a aurar da ita, don haka talk sense into Hajja" Abuturrab dai yyi shiru, ta hade rai tace "Ko baka ji na ne?" Yace "Ina ji Umma, xan kirata in sha Allah, nobody told me about it, tace to wa xai gaya maka dama tunda cutar yarinyar ake son yi" a hankali Abuturrab yace "Shkkn, i will call her in sha Allah" Tace "Do so immediately" Daga haka ta katse wayar ta ajiye lamarin na kara kona mata rai, wai aure kamar xa a aurar da wata mara makabuli, to su yi ta gani. Hajja ta gama sauraron Abuturrab tsaff sannan tace "Toh ko ubanka Usman wanda shine lallai dole ne bai isa yace xai dakatar da ni kan abinda nayi niyya ba, kai kuma a wa Allah na tuba? Kai da ka walakanta yarinya ka cuceta ka mayar da ita baxawarar karfi da yaji sannan ka saketa? Kai fa ba wani abu ke damunka ba banda kishi, kuma sai dai ka hadiyesa don tayi maka nisa wllh, idan ma sa ka aka yi ka kirana ka koma ka fada ma wanda ya sa ka ai ba Hajjar da bace yanxu, bana nufin er yarinyar nan da sharri banda alkhairi, yanda ta taso cikin bakar talauci da rashin ga ta so nake ita ma ta ci arxiki ta bar sa a inda ta gansa, so nake ita ma ta shiga babban gida a dama da ita, to na meye kowa sai bakin ciki abinda ni Allah bai daura min ba kenan, to kowa dai ya ci kansa ya kurkure da bakin ruwa, kai kuma ina baka shawaran ka kauda idonka a kan duk wani abu da ya shafi yarinyar kayi mana me wuyar tunda ka kawota cikinmu" Tana kai wa nan ta katse wayar, Abuturrab murmushi kawai yake yi... Kawai bayan sati daya sai ga shi Aunty ta kira Umma wai an kawo kudin Jiddah daga masarautan bauchi... Ummi ta fi minti talatin rike da wayarta bayan aunty ta katse, Allah kadai yasan yanda take ji a xuciyarta a lkcn.... Sai yamma ta shirya ta tafi gidan don bata son xuwa ta tadda mutane, ai ko duk yan kawo kudin sun watse, parlon Abba ta shiga direct, yana xaune shi da duk brothers dinsa, Umma ta xauna bayan sun gaisa gaba daya tace "Alhaji Usman dama wajenka na xo" Abba na kallonta ya dau wayarsa yace "Toh Allah ya sa lafiya, in taso ne?" Tace "Ehh" tana fadin haka ta tashi ta fita, Abba ya mike ya bi bayanta, can kofar gida suka fita tana kallonsa tace "Yanxu Alhaji an xaunar da ita yarinyar an tambayeta ko tana son auren nan da ake shirin kulla mata? Domin bata da kowa ba yana nufin bata da gata Alhaji, this is wrong wllh" Abba yace "Domin bata da kowa mu ma ba yana nufin xa mu cutar da ita bane, did you know this is a great privilege to her also? Ki duba fa wanda ake son hadata aure da? Wa kike tunanin Hajja xata yi ma hakan banda ita din??" Umma tayi wani murmushi tace "Wato privilege? But she never begged for that privilege Alhaji, idan kuma xa ayi adalci kamata yyi a ji ta bakinta don a fita hakkinta, an ta6a yi ma mutum dole a aure? Shkkn sai aka ce ita bata da choice da dream dinta?" Abba ya duba wayarsa jin shigowar message yana dubawa yaga message din Abuturrab, and the content goes as thus "Kada ya kasance ana neman Aure ne a kan Aure Abba, that is highly prohibited in islam.... We plan but Allah plans best in sha Allah" Abba ya karanta text din ya fi sau uku, can ya mika ma Umma dake kallonsa, Umma ta amsa tana dubawa ita ma dai sau ukun ta karanta tana sake duba sender din, a ranta tace Aliyu?? A fili kuwa tana kallon Abba tace "Shashasha, to me yake nufi da text din? Wa ake nema ma aure a kan aure?" Abba yace "I am still trying to understand that too" Umma tace "Ka kirasa" Ba shiri Abba ya hau kiransa amma ya ji layin a kashe, ya kira sau uku duk a kashe, Umma tace "Wai wa yake nufi ne?? Wa ake nema ma aure kan aure?" Abba yace "Tare mu ka karanta text din nan yanxu Hajiya Ramlah" Umma tace "Toh ina jin shaye shaye ya fara a can din ko" Abba dai bai ce komai ba, Umma tace "Ni dai na gama magana, idan xa ayi mata adalci ayi mata, a tunaninku gata xa ayi mata tunda xa a aura mata d'an sarki, to amma kwanciyar hankalin xaman gidan auren fa, tunda naji ance uwar tasa ma ba so take ba, kuyi ma Allah a duba lamarin nan idan kuma shakkar yi ma Hajja magana ake ni sai inyi mata wllh" daga haka tayi ma Abba sai anjima ko gidan bata sake shiga ba ta bude motarta ta shiga, driving take amma tunanin solution da xata samar ma Jiddah take don in dai kuwa aka yi auren nan kilan bata doron kasa ne, samm baxata ta amince da auren ba, baxata ta6a bari a shiga hakkin yarinya ba. Abba na komawa cikin compound ya sa a kira masa Ummi, tana fitowa ya mika mata wayarsa yace "Ko xaki iya fahimtar wani abu a message din nan kiyi min bayani??" Ummi sai karanta message din take da surprise barin da ta ga cewar Aliyu ne sender din, can ta kalli mai gidan nata tace "What's the meaning of this?" Yace "Shine nake son ki min bayani" tace "Jiddar matar aure ce da xai ce kar a nemi aure kan aure?" Abba yace "Shine nake son fahimta Hauwa" Ummi tace "Ikon Allah, to ka kirasa" Abba na kokarin sake kiransa yace "A kashe wayar" sai gashi ance wayar a kashe, Ummi tace "Ji d'an rainin wayo, aurar da ita yayi ne ba a sani ba, ko ko?" Abba dai bai ce komai ba yayi shigewar sa ciki, Ummi ta bi sa da kallo, gaba daya ta ma rasa wani tunanin xata yi, anya kuwa Abuturrab na da kai? Menene manufar wnn text din wai kar a nemi aure kan aure, to ko aure yake nemar ma Jiddar basu sani ba ne. Abba na komawa gun brothers dinsa su ma ya basu wayar su duba message din, bayan sun duba da daddaya da daddaya, suka dinga kallon Abba, Alhaji Salmanu yace "Neman aure kan aure kuma? To ko dai bai saketa ba ne dama Alhaji Usman?" Abba yayi dariya yace "Ya fara hauka kenan, ai har yanxu takardan na nan bai je ko ina ba" Abba na fadin haka ya mike ya wuce daki sai gashi ya fito da takardan ya mika ma Alhaji Salmanu ya amsa ya karanta sannan ya ba duk sauran ma suka duba, Alhaji Salmanu yace "Ikon Allah, to me yake nufi da hakan? Is he even in his right senses?" Abba ya daga kafada yace "I thought as much" naxari duk suka yi shiru suna yi, Alhaji Umar yace "Try his line ko xai yi connecting" Abba ya sake kira yaji a kashe, Alhaji Lawal yace "Toh ko dai komawa yayi aka sake daura masa aure da yarinyar?" Kallonsa Abba yayi da sauri almost with shock, sai kuma yayi wani dariya yace "Aa he must be joking ashe, har ya isa ya sake yin hakan? Da kuwa nayi disowning dinsa wllh... Allah kuwa da ya ga the other side of me, wato ga yan iska ya ajiye, wllh in har hakan ne ya kasance Aliyu xai yi mamakina ainun" Alhaji Umar yace "Ikon Allah, that just dawn on me bayan Lawal ya fadi haka, in dai kuwa ba shi ya koma ya aureta ba to wani ya kai ya aureta, don babu yanda xai turo wannan message din idan ba dayan biyun abinda na fada ya kasance ba, but that's bad... Who does that, ya maida mutane kananun mutane kenan yake nufi ko me?" Abba dai da alama ransa idan yayi dubu ya baci, daukar wayarsa yayi ya tura ma Abuturrab text kamar haka, "call me immediately after switching on ur phone, i said immediately!!!" Alhaji Lawal yace "Lallai kuwa tunda har ya turo message din nan Komawa yaron nan yayi aka daura masa aure da yarinyar ba tare da sanin kowa ba, tunda ya san waliyanta sannan tun farko shi dama babu wanda yayi masa waliyyanci a cikinmu, don haka abu ne me sauki garesa" Abba dai baya cewa komai a parlon... Har bayan sati da text din nan wayar Abuturrab a kashe yake, Jiddah na xaune daki tare da Maimoon da daddare tana son mata magana amma ta kasa, don bata ma san ta ina xata fara maganar ba, tun 3 days ago maganar ke cin ta amma ta kasa yi mata shi, can dai ta dake a hankali tace "Maimoon ya jikin Ya Aliyu?" Maimoon ta kalleta tace "Wllh I don't know, I can't reach him for a week now" Jiddah tace "Both Whatsapp?" Maimoon tace "Baya hawa...." Jiddah bata kuma cewa komai, Maimoon dai sai kallonta take, mikewa tayi ta koma side din da take kwanciya tayi kwanciyarta.... Ranan Friday bayan an sauko sallan Juma'ah, Jiddah na xaune xaune bakin tap din compound din gidan tana wanke hijabs dinta biyu don Safiyya na wanki a washing machine aka bude gate din gidan, daga kai tayi a tunaninta Ahmad ne don in dai ya shigo kd ya kan fara xuwa ya gaida Umma kafin ya tafi gidansa, tun da ya shigo take kallonsa kamar yanda shi ma yake kallonta, saukarsa kasar kenan kuma babu inda ya fara nufowa sai gidan Umma...... My strength ends here wllh... Thank you!! *Wa enda nake bi dari biyar su ji tsoron Allah su xo su biya bashi su sauke nauyi ko ince hakki!! alfarman wannan ranaku da muke ciki, domin fatan yin ibada amsasshe... Allah ya amshi ibadunmu ya sa muyi sallah lafiya Ameen* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Jiddah ce ta fara dauke idonta ta ci gaba da wankin da take a hankali, har ya wuceta sannan ta bi sa da kallo ta durkusa tana ci gaba da daurayan hijabs dinta, bayan minti goma ta gama ta shanya su sannan ta dauraye hannunta ta wuce cikin gidan, Xaune ta gansa a parlon yana danna wayarsa, su Maimoon na daki Umma ma na bedroom dinta, Huraira kuma na kitchen tana girkin lunch, ta karasa cikin parlon tana kallonsa a hankali tace "Sannu da xuwa..." Kallonta shi ma yake yace "Kema sannu" Xata tafi dakin Umma taji yace "I will be back later" Ta juya tana kallonsa, mikewa yayi ya nufi kofa ita dai tana tsaye har ya fita parlon. A hankali ta nufi dakin Umma ta yi sallama sannan ta bude, Umma na xaune tana waya, Jiddah ta xauna saman carpet ta jira har ta gama ta ajiye wayar, Umma na kallonta tace "Ya aka yi Jiddah?" Tace "Aa dama xan tambayeki sanda xa ayi awaran da kika ce ne" Umma tace "Au kinga ma na mance ni, duk sanda kika shirya ba matsala ki xo ki amshi kudin ingredients din, ke da Huraira ko Maimoon ku tafi kasuwa" Jiddah tace "Toh Umma" Daga haka ta mike ta fita daga dakin. Abuturrab na isa gidansa ya sauka daga d'an sahun da ya kawo sa, sai a sannan ya tuna ba shi da currency din kasar a tare da shi, ya nufi gun Mai gadinsa da ya taso yana welcoming dinsa da fara'a, yace "Ka basa dari biyar idan kana da shi" Mai gadin ya taho gun Mai adaidaitan da sauri xai basa kudin Abuturrab ya shiga cikin gidan, the compound looks so neat saboda yayi employing masu shara da gyaran flowers da ba su ruwa, yana isa entrance din shiga parlon ya murda kofar gently ya shiga ciki, kida ne ke tashi an kure sa har kusan karshe a parlon, ya dinga bin parlon that looks very untidy and unkept da kallo, ga plates sun fi kala biyar a kan carpet da duk ya baci da shinkafa da kwallin lemo, kayan kallon da suka yi uban k'ura ya dinga kallo, ya kalli dining area can ma duk plates da cups ne da breads ko kulle ledan ba ayi ba, calmly yake tafiya ya nufi stairs, shi ma duk yana jin yana taka k'ura kasan tiles din, bangarensa ya tafi ya bude kofa, sun fi su bakwai xaune parlonsa nan din ma dai plates ne da kwalaye na ciye ciyen da aka yi, suna ta labari ga kida na tashi a parlon ma amma bai kai na parlor ba, Duk suka juya jin an bude kofa, Aneesah dake xaune kan carpet sanye da zani da ves a jikinta ta mike da mugun mamaki tana kallonsa tace "My Captain saukan yaushe babu notice? Mun fa yi waya jiya baka ce min kana tasowa ba" Bai sake kallonta ba balle ta sa ran amsa ya bude kofar bedroom dinsa, Safara'u dake parlon ita ma da daurin kirjin ta mike da sauri tana cewa "In ji dai bai gan ni ba??" Bata jira an bata amsa ba ta fice da sauri daga parlon, Kawayen Aneesah duk biyar din su ma suka mike suka bi bayanta suka bar Aneesah tana xaxxare ido tana bin parlon da yayi kaca kaca da kallo, gashi takasa bin sa cikin bedroom din, Abuturrab ya fi minti biyu tsaye yana bin bedroom din nasa da kallo, kaya ne ta ko ina a xube tun daga kan gado har kasan tiles da carpet, bayan kaya har da takalma, ga farin bedsheet din saman gadon har ya fara fita hayyacinsa duk ya yamutse, sababbin jakunkuna na kayan sa wa har uku ya gani jere a dakin su ma duk a wangale, tun da yake bai ta6a sanin bedroom na iya xama haka ba sai ranan, wannan ya wuce untidy ko unkept, har wani tsami tsami mara dadi yaji bedroom din ke yi, ga kofar bandaki a hangame, ya lumshe ido ya juya ya bude kofar ya fita, har sannan Aneesah na tsaye sai wuwwurga idanuwa take, bai kalli direction dinta ba ya fice, wani dakin daban ya tafi ya bude ya ga Safara'u xaune saman gado wanda shi ma din duk a yamutse yake, har lkcn daurin kirji tayi, ganin sun hada ido ya gaisheta, bai jira amsa dogon gaisuwan da take jere masa ba bayan ta jawo zanin gado ta yafa, yace "Alhmdlh mun gode Allah" Daga haka ya fice ya kulle mata kofa, wani dakin ya bude ya ga kawayen Aneesah sun yi dai dai a dakin ya kullo kofar ba tare da ya amsa gaisuwansu ba, bai sake bude wani dakin ba ya sauka downstairs ya fice daga gidan gaba daya, Abuturrab ya fi minti goma tsaye a kofar gida gashi babu cash a jikinsa babu Atm card, luggages dinsa kuma bai dauko daga airport ba, wayarsa ya ciro daga karshe ya shiga kiran layin Maimoon, tana dagawa bayan sun gaisa yace "Give the phone to ur frnd" Maimoon ta mika ma Jiddah dake gefenta waya, Jiddah ta amsa tana duba me kiran kafin ta kai kunne, Maimoon ta fita daga dakin, Jiddah tace "Ina ji" Yace "Did u tell them i am back?" Ta girgixa kai tace "Aa" Yace "Ohk, kina da cash wajen ki?" Ta d'an yi shiru, sai kuma tace "Aa sai a account, wanda Ya Ahmad ke sa min saboda makaranta" Calmly yace "Ohk ki bar wayar a wajenki..." Bai jira tace komai ba ya katse wayar ya karasa bakin titi, ya samu adaidaita ya koma gidan Umma, bai bari ya shiga can cikin layin ba ya sake kiran Number Maimoon, Jiddah ta daga, yace "Ki kawo min Atm card dinki waje yanxu" A hankali tace "Toh" ya katse wayar, ta mike ta dau jakarta ta cire atm card din ta mayar ta ajiye sannan ta dau gogaggen Hijab dinta ta saka ta bude kofa a hankali ta leka parlor bata ga kowa a parlon ba hakan ya sa ta fito da sauri ta nufi kofar fita, har ta isa gate tana waigen entrance din gidan, tana fitowa kofar gida ta dinga kalle kallen inda xata gansa, daga nesan ya hangota ya sauka daga kan adaidaitan, hakan ya sa ta gansa, ta karasa inda yake tana tafiya a hankali, idonsa na kanta har ta iso, ya sauke idonsa ya amshi Atm card din yace "Pin?" Ta gaya masa, yace "Thank you" daga haka ya shiga adaidaitan yace su tafi, ita kuma ta juya ta koma cikin gida. Abuturrab na cire kudin ya tafi yyi lodge a hotel, yana shiga dakin da aka bass ya kashe wayarsa, bayan ya huta yayi ordering abinci, Ana la'asar kuma ya fita xuwa airport don daukan luggages dinsa ya dawo hotel din a taxi, ya shiga da kayan ciki, bai sake fitowa hotel din ba sai da aka kira magrib ya fito yin sallah, bayan sun idar ya siya fruits ya koma cikin hotel din.... Washegari Asabar karfe tara ya kunna wayarsa ya shiga kiran Ramlah, tana dagawa da fara'arta tace "Yaya ka dawo ne?" Yace "Ahmad na gari?" Tace "Aa bai shigo ba satin nan, yace sai next week" yace "Ohk xan xo in amshi makullin motarsa yanxu" tace "Toh yaya sae ka xo" katse wayar yayi da yake ya shirya ya dau cash din da ya ciro jiya ya sa a aljihunsa sannan ya fita ya kulle dakin, a adaidaita ya isa gidan Ramlah, bayan ya sallamesa ya shiga ciki yana amsa gaisuwan mai gadi, ya wuce parking space, yana tsaye a nan ya shiga kiran Ramlah, bayan ta daga yace "Ki fito min da makullin parking space" tace "Yaya baxa ka shigo ba?" Yace "Ehh" tace "To bari in fito" ba a dau lkci ba ta fito rike da makullin motar, tana murmushi ta nufi parking space din ta risina ta basa tace "Ya hanya yaya?" Yace "Alhmdlh, ba sae kin ce masa na dawo ba" tace "Toh Yaya" bude motar yyi ya shiga yyi warming dinsa ita dai tana tsaye tana kallon sa, har daga karshe ta daga masa hannu ya fita da motar ita kuma ta koma cikin gida... Abuturrab ne xaune kansa a kasa yana sauraron uncle dinsa, Alhaji Lawal dake ta kallonsa da kyau yace "To ko dai kana shan wani abu ne wanda mu bamu sani ba Aliyu?" Shi dai bai ce komai ba, Alhaji Lawal yace "Dago ka kalleni ina maka magana" Ba musu Abuturrab ya dago kansa yana kallon Uncle din nasa, Alhaji Lawal yace "Tell me what exactly is wrong with u? Do we deserve being taking for granted Aliyu?" Abuturrab ya girgixa kai yace "Aa Abba ku yi hakuri, kuskure ne..." Alhaji Lawal ya dakatar da shi yace "You called this mistake also Aliyu?? Baka tsoron Allah ne da xaka kara kiran wannan ma da mistake??" Sake baki Alhaji Lawal yayi yana kallonsa, Abuturrab bai iya yace komai ba, Alhaji Lawal na jinjina kai yace "Lallai baka da hankali baka da manners, ka kuma mugun raina mutane ka daukemu for granted, ashe dama kai ka haifa kanka bamu sani ba?" Abuturrab yyi kasa da murya with remorse yace "Don Allah ku yi hakuri Abba, i know i wronged u all, but this the only way out for me, Abba baxai saurareni ba, so is Ummi... No one will give me a listening ear" Alhaji Lawal yace "Ohk ni kuma sbda ka yi shegen raina ni yanxu kake tunanin xan baka listening ear?? No... I am not giving u dat, and i am sorry babu wani abu da xan iya yi" Abuturrab ya kasa ce masa komai, Alhaji Lawal yace "I can't do anything about this... ina ce ita wannan yarinya idan ban mance ba babu irin hakuri da ban bakin da bamu baka ba a kan ka xauna da ita, ashe ka maida mu shashashai ne a lkcn ka je ka saketa kuna ta xama tare duk don sbda kana ganin ita ba class dinka bace or whatever, bugu da kari kuma u bluntly admitted baka sonta, to yanxun da ka koma ka aikata shirmen da ka aikata son nata ka fara yi kenan???" Nan ma dai Abuturrab bai ce komai ba, Alhaji Lawal ya daka masa tsawa yace "Bude baki ka bani amsa my frnd.. i am talking to u" A hankali yace "Ina son xama da ita yanxu Abba" Alhaji Lawal yace "U are very stupid, ae ba tambayar da nayi maka ba kenan.." Kasa basa amsa Abuturrab yayi nan ma, Ganin yanda Uncle din nasa ke kallonsa ya sunkuyar da kai, Alhaji Lawal yace "Toh ka saka a ranka cewar kamar yanda muka xaunar da kai kwanaki muka baka takarda da biro ka datse auren naku wannan karon ma hakan ne xai faru, mu ba 'yan banxa bane da xaka dinga controlling dinmu yanda ka so, kana aikata duk abinda ya xo kanka without our consent, we birth u..." Abuturrab ya marairaice masa yace "Abba don girman Allah ku yi hakuri, wllh ban koma na aureta da nufin in cuceta bane wannan karan, wancan lokacin ma kuskure aka samu, don Allah Abba kayi hakuri, i mean no harm to her..." Alhaji Lawal yace "Da nufin me ka koma ka aureta yanxu? Bani amsar tambayar nan" Abuturrab yace "Ina son xama da ita ne na har abada" Alhaji Lawal ya girgixa kai yace "Kamar dai yanda na fada you are very stupid, kawai ka koma ka aurota saboda kana son ku xauna tare har abada, wait!! are u mad??" Abuturrab yace "Abba ni dama fa ban ta6a buda baki nace bana sonta ba, kawai sharrin shaidan ne da kuma yanda kowa baya son auren shi yasa na aikata abinda na aikata, amma wllh ban ta6a cewa bana sonta ba" on a serious note Alhaji Lawal yace "Daga Hajja a rashin alkibla sai kai, anyway... I am so dedicated today, don haka idan Allah ya amince mana gobe xan shiga kadunan, xaka iya tafiyar ka sae na xo goben..." A hankali Abuturrab yace "Xan jira mu tafi tare goben in sha Allah" Alhaji Lawal yace "Allah ya kai mu" Godiya Abuturrab yayi ma uncle din nasa sanan ya mike ya nufi kofa hoping this will be the only challenge he is to face till end, Alhaji Lawal ya bi sa da kallo har ya fita yana mamakin karfin hali da taurin xuciya irin na Abuturrab, kiri kiri yayi ta abu ba tsoro. Abuturrab ya fi minti daya tsaye kofar parlon Abbansa ya kasa bude kofan, bai ta6a jin mugun shakkan Abbansa irin na lkcn ba, bai san me ya sa wnn karan ko Aunty baya jin ta kamar yanda yake jin Abbansa, ga bugun xuciyarsa da ya tsananta, it's been long da ya shiga yanayin nan da yake ciki yanxu, muryan Umma yaji a bayansa ta rike ha6a tace "Kai kuma yaushe a gari??" Ya juya da sauri, yyi feigning smile yace "Good evening Umma" tace "Saukan yaushe?" Ya d'an fara kame kame kafin yace "Jiya" tace "Ikon Allah, to sannu da dawowa..." Bude kofar parlon tayi, lkci daya fara'ar da ke fuskarta ya bace, ta wani sha kunu ta shiga parlon, tunda aka kirata aka ce ta xo gidan tayi tunanin xancen baxai wuce na auren da suke shirin laka6a ma Jiddah ba, kuma ta sha alwashin yau kam sae inda strength dinta ya kare, dai dai take da kowa, ganin Hajja xaune parlon ta wani kara daure fuska ta nemi waje ta xauna, Abuturrab ya shiga parlon kansa a kasa gabansa na mugun faduwa, xaunawa yyi saman carpet ya kasa kallon kowa, a hankali ya fara gaida Hajja kafin sauran occupant din parlon, Hajja dae fuskar nan nata babu ya6o bbu fallasa, Umma ma babu yabo babu fallasan tace "Ina yini Hajja" Hajja ta rike kanta tace "huhuhu wllh tun da naje Masar na samu saukin gaishe gaishen jaraban nan, yo kowa na ta kansa ina batun wani gaisuwa, su basa haka a can wllh, duk wayayyu ne, a kasar nan kowa sae yace sae ya gaisheka alhalin wani gaisuwar ma bai kai ciki ba, to ni dai na yafe, ko Usman ma ban amsa gaisuwarsa ba balle wani...." Ko kallonta Umma bata sake yi ba tana jan counter dinta... Alhaji Umar ne ya bude wajen da addu'a, sannan bbu 6ata lkci kuma babu boye boye in Brief Alhaji Lawal ya maimaita masu duk abinda Abuturrab ya sanar masa jiya a Zaria, Babu wanda bai girgixa ba a parlon, Abba dai kallon ceiling kawai yake, gaba daya sauran mutanan parlon kallon Abuturrab suke irin kallon tsoro, babu ko kiftawa, shi ko kansa na sunkuye xuciyarsa na bugawa, Hajja dae sae wani murmushi take me sauti irin na bosawa tana girgixa kafa da kai, Bayan shirun kusan minti biyu da ya ziyarci parlon, Aunty ta mike duk ta hada xufa daga sama har kasa tana girgixa kai tayi wani murmushin takaici tana nuna Abuturrab tace "Wllh karya kake Aliyu, karya kake baka isa ka kunyata ni ka toxarta ni, ka walakanta ni a idon duniya ba wllh... Karyanka ta sha karya wllh" kofa ta nufa ta fice daga parlon da sauri, Umma da Ummi har sannan hangame baki suka yi suna kallon Abuturrab, Hajja na kallon Abba a hankali tace "Yau da ace a Masar ne idan ba a garkame d'an ka a kurkuku ba shegiya nake Usman, ae wannan shine ta'addanci mafi muni da mutum xai yi a hukuntasa a kasar Masar, kai ba a ma ta6a haka a can ba wllh, Aliyu dai ya fita sahun mutanen kwarai, Aliyu mutumin banxa ne... Kiri kiri ya nuna ma d'an uwansa na jini bakin ciki, da hassada, ba fa son yarinyar yake ba kawai bakin ciki ya mayar da shi gun danginta ya sake aurota a gantale, su ma dai dangin nata matsiyata ne, kawai sun mayar da 'ya kaza don yaje yyi masu fafan yana tukin jirgin sama, to meye kuma tukin jirgin sama Allah na tuba abinda matsayinsa da d'an acaba da d'an taxi daya a idon duniya, wato sbda hassada sai ya ga ta yanda yarima zai aureta ko??" Cije yatsa Hajja tayi sae kuma ta rushe da kuka tace "Wllh mun fi awa biyu da mutumin nan muna garari a hayin rigasa, katon ya gilla min karya wai an rushe gidansu Jiddah daga karshe ma gaya maka ne kawai ban yi ba Usman wllh a tsakiyar titi ya yasar dani yyi wucewarsa kamar mara galihu duk na hada xufa, har ya kai ya kawo mutane suka xata almajira ce idan an xo wucewa sae a mika min ashirin, goma...." Sosai Hajja take kuka tace "Ni a tarihin duniya ma ban ta6a jin an haifi me hali irin na Aliyu ba, kuma a bisa dokan Masar duk wanda xai iya aikata abinda ya aikata to xae iya kashe rai babu ko darrr, shi yasa ma ake garkamesa a gidan gyaran hali, ni dae xan xuba ido kawai in ga hukuncin da xaka dauka a kan wannan d'a naka Usman, dalilin abun nan da Aliyu ya aikata sae zumunci ya tarwatse ya daidaice ya lalace wllh, don ba Yarima kadai ba.. hatta mutan Bauchi sae sun kullaci Aliyu, daga nan kuma sae a fara gaba tsakanin Bauchi da kaduna, to wa xai so haka??" Ta kara fashewa da matsanancin kuka tana kwance ha6ar xaninta tana salallami, ta mike ta fice daga parlon tace "Tirrrrrr" A karo na farko Abba ya kalli Abuturrab da har sannan ya ki raising kansa, Abba ya gyara xama speaking calmly yace "Yanxu kai ka tabbatar ka koma an sake daura maku aure da yarinyar nan Aliyu? Are u very sure about this" Sai a sannan Abuturrab ya daga kansa ya kalli Abbansa amma ya kasa cewa komai, Abba yace "I'm asking you...." A hankali yace "Ehh Abba" Abba yace "To da yaushe kaje aka mayar da auren?" Cikin sanyin murya Abuturrab yace "Before i got married to my recent wife..." Abba ya gyada kai yace "Ohkk that's good, wani sadakin ka kai kenan?" Abuturrab ya sunkuyar da kansa yace "Ehh" Abba yace "Nawa ka kai?" Abuturrab ya share xufar forehead dinsa yace "150k" Abba ya gyada kai cike da gamsuwa yace "Ohkk that's fine" Ummi ta rike ha6a tana kallon Aliyu da abinda ya fi mamaki, Umma kam dariya ma abun ya fara bata sai taji kamar film, hakan yasa bata san sanda ta dinga murmushi ba tana gyada kai, Mikewa Abba yayi Abuturrab ya bi sa da kallo kamar idanuwansa xa su fito ganin ya nufi bedroom dinsa, kallon Ummi yayi ya marairaice mata amma ya kasa cewa komai, gaba daya hankalinsa ya tashi sosai, ita kuwa sai kallonsa take har sannan tana rike da ha6a, Abba ya fito daga dakinsa rike da paper and pen, Alhaji Lawal ya dakatar da shi yace "Let's talk first Alhaji Usman" Abba ya ajiye takardan hannunsa gaban Abuturrab kafin yace komai Abuturrab ya hade hannayensa cikin breaking voice yace "I am sorry Abba, wllh i can't, i can't plsss...." Ai bai jira mai Abba xai kuma cewa ba ya mike ya fice daga parlon, duk suka bi sa da kallo. Babu yanda Alhaji Lawal bai yi kokarin ganin yayi convincing Abba yayi hakuri da abinda Abuturrab ya aikata ba, he should calm down before making any decision... but all his effort prove abortive, har Alhaji Umar ya sa baki don ganin Abba ya janye wannan kudirin da ya dauka amma Abba ya ki sauraron kowa, kana ganinsa kasan ya hau sama sosai, Ummi dai sai kallonsa take haka ma Umma dake parlon har sannan, Alhaji Umar yace "Ka fahimce ni Alhaji Usman ba don muna tsoronsa ya sa xa mu saurara masa ba, akwai abubuwan dubawa da yawa...." Abba ya dakatar dashi yana girgixa kai yace "Kasan Allah Umar?? Wllh wllh sai ya saketa, wllh baxai xauna da ita ba, xan nuna masa i birth him...." Yana kai wa nan ya mike ya fice daga parlon...... *Masu neman littafin Jiddatul Khair complete sae ku yi payment ku xo ku sameni da evidence* 👇🏻 Wa.me/+2347087865788 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Allah ubangiji ya maimaita mana😇[7/15, 1:54 PM] Ummuanwar🥰: Abuturrab na bedroom din Umminsa ta shigo, tun da ta gansa ta dauke kai ta tafi gaban mirror tana cire jewelries dinta, bayan ta gama ta nufi kofa xata fita yyi karfin halin cewa "Ummi" juyowa tayi ta kallesa, ya sauka kasa on his knees ya hade hannayensa pleadingly yace "Ummi don Allah ki ma Abba magana, interpose pls, nasan ke baxa ki juya min baya ba, pls don't say no to me Ummi, don girman Allah don't let him force me do wat will ruin me, baxan iya ba..." Ummi dake ta kallonsa tace "Ikon Allah!! Aliyu lkcn da kake abubuwan ka kana shawara da ni ne?" Yace "Ummi i don't know how to open up to you about this, i don't know where to start from, and I don't know how u will take it, idan ban yi hakan da nayi ba i might ruin my self, don girman Allah kiyi hakuri ki yafe min Ummi, i only did what will favor me till end" Ummi tayi wani murmushi ta girgixa kai tace "Aliyu kenan, but i am sorry i can't nd won't do anything about this, wannan batun ya fi karfina coz Abbanka ya dauka da xafi kuma ko na minti daya ban ga laifinsa ba duk abinda ya aiwatar dai dai ne, he is doing what is right, i see no reason we will birth a child dat will keep on controlling us" tana kai wa nan ta fice daga dakin, ya bi ta da kallo xuciyarsa na bugawa yana jin wasu xufan na keto masa a forehead, dafe kansa yyi na kusan minti goma, daga karshe ya mike ko minti daya bai kara a gidan ba ya fice... Tun da Umma ta koma gida take xaune dakinta ta ma rasa takamaiman tunanin da xata yi, ita wllh sai take ga kamar a mafarki duk abubuwan nan suke faruwa, lkci lkci take bude baki ta rike ha6a tana sake imagining da jinjina halin Abuturrab, yanxu komawa yayi ya sake auran yarinyar nan duk ya maida su shashashai gantalallu, ta ma rasa ko takaici take ji, haushi take ji, ko bakin cikin abinda Abuturrab ya aikata take, ko a tarihi bata ta6a jin shigen abinda Abuturrab yayi ba, wato yaron nan yayi mugun rainasu bai daukesu bakin komai ba, baya kuma tsoro ko shakkan kowa, tafe hannu tayi tana salati. Bayan magrib tana xaune kan darduma hannunta rike da carbi tayi nisa tunanin da take tana kallon Jiddah dake jera mata goggagun kayanta da me wanki da guga ya kawo a press, to meye manufarsa a kan marainiyar nan kuma yanxu?? Me yake nufi da su for the second time, wato idan ba a dau kwakkwaran mataki kan wnn abinda yaje yyi ba sun xama shashashan da gaske kawai, Ko kadan bata ji haushin reaction din Abba ba this time around kuma she is supporting him 100%, Aliyu xai gane ba shi da wayo.... bude kofar bedroom din aka yi amma ba duka ba, kuma ba a shigo ba, daga Umma har Jiddah kallon kofar suke, sai kuma aka yi sallama kasa kasa, still not coming inside the room, Lkci daya Jiddah ta dau muryarsa, kamar yanda Umma ma ta dau muryan amma sai ta hade rai tace "Waye wannan?" Shigowa dakin yayi kansa a kasa bayan yyi pushing door din slowly, Umma har ta mance rabon da ya shigo mata daki, Jiddah dai bata yarda ta kalli kofar ba don kamar kuwa ta san kallonta yake, Umma ta buda hannu da sauri tace "Ya aka yi xaka shigo min daki babu sallama?" Ya sauke idonsa daga kallon Jiddah ya karasa cikin dakin yana tafiya a hankali ya xauna nan saman carpet, yyi kasa da murya yace "Ina yini Umma?" As if in a hurry tace "Lafiya lau, ya aka yi?" Shiru yayi ya sunkuyar da kansa, Jiddah ta bar gyaran da take ta rufe press din ta nufi kofa ta fita, sannan ta kullo masu kofar. Cikin sanyin murya Abuturrab yace "Umma i know i wronged u all, kuma ni bani da bakin da xan baku hakuri, coz i don't deserve being forgiven, But Umma i want u all to get this... A Mistake repeated more than once is a DECISION, No mistake is repeated twice because the second time it's not longer a mistake but a CHOICE, this is my Decision and my Choice Umma" Ya hade Palm dinsa gathering much courage yace "This shouldn't be used against me plss, ku yi hakuri ku sassauta min, I don't have the strength to bear being denied my Choice, kuyi hakuri don Allah Umma..." Umma da ke ta masa kallon mamaki ta dakatar da shi tace "Ur Decision and Choice?? Lokacin da kayi watsi da namu decision din mun hakura ko bamu hakura ba Aliyu?? Kai don baka da kunya da tsoron Allah har xaka iya sake komawa a aura maka Jiddah?? Yarinyar da kafi karfinta? Yarinyar da ba class dinka ba? Yarinyar da ka dinga kunyan nuna ma duniya cewar ita ce matarka? Yarinyar da kayi ma sakin walakanci ka toxartata? Tsakaninka da ita fa abinci da suturan sakawa shi ma duk don kada Allah ya tambayeka ne... Get out from my sight plss Aliyu " Abuturrab ya girgixa mata kai ya marairaice yace "Noo plss Umma, kar ki min haka ke ma, i have no back up" Cikin tsawa Umma "Ohk so kake ince ka dau Jiddah ku tafi ko me? Haka kake son ji??" Ya girgixa kai cikin sanyin murya yace "Aa Umma, so nake kawai ki taimaka ki sa baki Ummi da Abba su sassauta min, don nasan baxan iya tsallake hukunci daga garesu ba, su yi min komai amma kada su ce in sake sakinta don girman Allah" Umma tace "Kaga ka xo kawai ka sa min ciwon kai Malam, ba don halina ba tashi kaje sae da safe i need rest, kuma kada ka sake xuwa min gida da batun Jiddah, ko me kake son fada kaje ka samu ubanka ko Ummi, but don't come to my house again, get out pls..." kallonta ya dinga yi, ta mike ta cire hijab dinta ta linke ta xauna gefen gado tana ci gaba da jan carbinta fuskarta a daure, a sanyaye ya mike ya yi mata sae da safe ya nufi kofa ya fita. A kofar gida Abuturrab yyi parking ya shiga cikin gida, wani kamshin bala'i ne ke tashi tun daga balcony har cikin gidan, ya bude kofar parlon ya shiga, ko ina na parlon sae walkiya yake don neatness, ya xauna saman kujera ya jinginar da kansa dake sara masa ya runtse ido xuciyarsa na bugawa, ya fi minti talatin a haka, sae ga Aneesah xata tafi kitchen da cup din hade hadenta na Maman Farida me kayan yan gayu da ta gama sha🙄, ta xaro ido ganinsa ta ajiye cup din a kasan parlon ta nufesa da sauri tace "My captain? Yaushe ka shigo?" K'in bude ido yyi, ta xube gefensa giving him a hug tace "Oyoyo my husband nayi missing dinka sosai wllh, amma dai yanxu daga kano kake ko? Don da naji ka shiru kuma I can't reach u tun shekaranjiya nace to kilan kano kaje..." Bude idonsa da ya canxa kamanni yyi ya mike, lkci daya yace "I want to be left alone Aneesah" daga haka ya wuce sama ta bi sa da kallo ganin kamar xai tashi sama, sai kuma ta tashi ta bi bayansa da sauri, bangarensa ya nufa yana shiga dakinsa ya sa makulli duk da xanin gadon dakin a gyare yake haka ya yaye ya bude press ya dau wani xanin gadon ya shimfida sannan ya dau duvet ya kwanta ya rufe har kansa. Har kusan asuba Abuturrab bai yi bacci ba, gashi ya ji gaba daya bai da strength din tashi yayi sallah, har alwala sae da ya daure ya je yyi duk da he is cold amma daga karshe kwanciya yayi without praying, sallan asuban ma a daki ya samu yayi, he wished all this wasn't happening, he wish all this will turn out to be a dream, his heart is to weal for all this... Ya kalli wayarsa jin shigowan message, mikewa yyi ya dau wayar ya xauna gefen gado, ganin message din na Abbansa ne ya ki budewa ya ajiye wayar xuciyarsa na bugawa, yana nn xaune har rana ta fito, kwanciya yyi jin kansa yyi masa nauyi sosai yana kuma sara masa, lkci daya bacci me nauyi ya daukesa... Hannu ya ji a forehead dinsa ya bude ido da sauri, Aneesah ce xaune gefensa tana kallonsa da damuwa tace "Are u okay captain? U are restless even in sleep, and it seems u are developing fever, ko dai duk stress din tafiyar ne?" Yayi kokari ya mike xaune ya cire hannunta a kansa yace "Hey i am okay" ta daure fuska tace "How will u tell me u are okay ga temperature dinka is saying it all, dubi fa yanda jikinka ya fara xafi" Ya hade rai yace "I said i am okay Aneesah, me yasa ma zaki tasheni ina bacci tukun?" Tace "Aa wnn ba bacci kake ba, bacci babu nutsuwa duk ka wani firgice kamar wanda yyi ma sarki karya?" Sauka yyi daga kan gadon ya fita dakin ta bi sa da kallo baki bude. Ummi ce xaune bedroom din Umma tayi tagumi kana ganinta kasan abun duniya ya dameta, Umma na kallonta tace "Toh ke sae kika yi masu shiru Yaya?" A hankali Ummi tace "Toh me xance? I was speechless Ramlah... I was mute all through, har yana cewa i should provide him in less den 24hrs or we both face the consequence" Umma ta mike cikin daga murya tace "Toh aje a hakan, kin san komai din ko da yanda xa ayi da ke?? Tabbas da goyon bayanki Aliyu yake duk abinda yake yi, sai aka yi yaya? Da akwai yanda xa ayi da ke ne? Ko wani ya haifar maki Aliyun?? Kuma ina ce dae ba kashe mutum yaje yayi ba auren sunna yaje aka daura masa da shaidu ya dawo gida, to wanda bai fasa ce wa ke kike xugasa ba... tunda munafuka annamimiyar matarsa ta daga hankali ta rikice kamar ita aka yi ma kishiya ba dole shi ma ya birkice ba, ita kuma Hajja tunda babu abinda ta iya sai son kai da son abun duniya da rashin alkibla ba dole ta gigice ba ita ma, ae tun ba yau nake nuna maki irin bambancin da take nunawa kiri kiri a kan 'ya ya ba, to wllh a da ina jin babu wanda ya kai ni bakin ciki da takaicin abun nan da Aliyu ya koma ya aikata ba, amma yanxu kuwa sae in da karfina ya kare, ae auren sunna yaje aka daura masa, in dai a kan Hajja da makira shegiyar matar nan Hafsah ne sae iya inda karfina ya kare, aure kuma ya riga da ya je yyi babu yanda aka iya da shi, shi kansa Abban sae yayi hakuri tunda dae ba sata yaje yayi ba ko wani mugun abu" Ummi dae kallonta kawai take bata ce komai ba, Umma na huci tace "Ba kallona xaki yi haka ba Yaya, fitowa xaki yi kanki tsaye ki goyi bayan d'an ki tunda abun haka ne, ki nuna masu ae fa shirun da kike yi ba tsoro bane, kuma kina da iko a kan Aliyu ba Ubansa kadai ba" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "I am not against him dama Ramlah, kawai dae nayi shiru ne don kada uban da baabarsa suce ae goyon bayansa nake, amma kinga a hakan ma ban fita ba sunce da sani na yake komai har auren farkon ma, kuma wllh for months now yana ta son yyi min magana duk ina lura da shi amma ya kasa sae yyi kamar xae yi sae kuma ya wayance, ke akwai ranan da har daki sae da na shiga da shi kamar xae fada kuma ya fasa, sae dai yace in taya sa da addu'a kuma no matter how everything will turn out kar inyi fushi da shi, kin kuma san sa da xurfin ciki, ni dae nasan duk sallolina biyar bana masa fashin addu'a kuma ina masa fatan alkhairi a duk lamarinsa, duk wani abu da xai cucesa ina addu'an Allah ya nisanta sa da shi, don haka ni i am not against him going back to marry Jiddah, bayan ya saketa da watanni ni kaina nayi masa takaicin hakan barin ma idan aka duba halin da yake ciki tun bayan auren nasa na biyu, kwata kwata bai yi dacen mace ba, tafiyar nan da yayi kusan duk bayan kwana biyu sai ta xo gidanmu amma ko sau daya bata shigowa bangarena da sunan gaisheni, duk sanda Allah yyi muka hadu a main parlor sai ta gaisheni a can bbu wani ladabi, ga uban kazanta da yake complain a gidan nasa...." Umma tayi wani dariya tace "Ai kadan ya gani, sannan ni abinda ya fi tsaya min a rai ita Hafsah da ta xakalkale har tana ikirarin ba dai ya kunyatata ba me take nufi? Ita ta isa ta hanasa karin aure ko yin abinda yake ra'ayi ne? To wllh tana ji tana gani xan wanke Jiddah tsaf in kai ta gidan Aliyu da kai na, sai in ga ko xuwa gidan xata yi ta fito da ita, duk da dai xai ci ubansa kafin hakan ma ya faru" Ummi dai tayi murmushi bata ce komai ba, Umma tace "Ina baki shawara da kakkausan murya yaya, kar ki raga ma duk wanda ya gaya maki babu dadi a kan case din nan, ko Hajja ban cire ba wllh, shi kuwa ki barbade toka a idonki ki wankesa wankin babban bargo shi Abban idan ya sake attacking dinki, ai shiru ba hauka bane, me yasa sai da aka bari na bar gidan aka maki ca?? Toh in sha Allah har su gama duk abinda xa su yi a kan case din nan a can xan dinga yini" Tana kai wa nan ta nufi kofa tana cewa "Bari in kawo maki abinci" Ummi tayi tagumi can kasan ranta tana jin tausayin d'an ta, karfin hali tayi ta gaya masa maganganun da ta gaya masa jiya a daki, ta rasa dalilin da yasa ko kadan bata ji haushinsa ba, ta dai yi mamaki ainun amma ba wai haushin sa ba, daukar wayarta tayi ta sake kiransa still ta ji a kashe, tun ma da suke tare da Jiddah bata ta6a xuwa gidansa ba balle yanxu, banda haka da sai ita taje can gidan nasa, Jiddah ce ta shigo dakin da sallama rike da Tray me dauke da cooler din abinci da spoon, Ummi tana ta kallonta har ta ajiye tray din ta daga kai ta kalli Ummi tana d'an murmushi tace "In debar maki Ummi?" Ummi ta girgixa kai tace "Aa sai anjima, nagode" Jiddah tace "Toh" Sannan ta mike ta nufi kofa Ummi ta bi ta da kallo. Aneesah ce xaune daki tare da Safara'u, Safara'u ta kyabe baki tace "Ni ban ma ta6a jin haka ba wllh, ae kamata yayi idan wani abun ne ke samunsa sai ya sanar maki a matsayin ki na matarsa, amma ba wai yayi ta abu kamar ke 6are ce, ni na ma rasa gane alkiblan mijin nan naki kamar me tambotsai, ni da sai ince ki fita harkansa kawai ki kama kanki tunda shi d'an iska ne, idan kuma don gidansa da na xo ne yake ta wannan halayyan na basarwa yana ciccin magani sai in tattara inyi tafiyata ni bai isa ya walakanta ni ba, ance masa mu fakirai ne? Ko bai je gidanmu ya gani bane?" Aneesah da ta d'an hade rai jin ta xagi Aliyu tace "Kai Aunty Safuu, wllh ke dai da fassara kike, to ina ruwansa da xamanki? Ae shi ba haka yake ba, snn fa shi haka halinsa yake na Basarwa suna fa da jimi da jinin sarauta Aunty, yayan Babansa fa shine sarkin Bauchi kin sani, kuma ina jin ma kamar bashi da lafiya don yanayinsa ma ya nuna karfin hali kawai yake, kawayena ma ba ruwansa da xuwansu gidana balle ke kanwar uwata, yanxu Ahmad xan kira, kilan stress ne daga dawowan da yayi tafiya" Safara'u ta kara kyabe baki tace "Atoh ai da sai ince ki ba banxa ajiyarsa kawai, kowa ma na da jinin sarautar ae, mutumi ba shi da aiki sae ji da kai da nuna shi wani ne, to ta ina? kawai ki fita harkansa kema ki koyi d'an jan ajin nan na mata mana" Aneesah ta rike ha6a tace "Ina xan iya haka Aunty? Uhum lallai baki san yanda nake son mijina bane, in ja masa aji fa kika ce? Aa baxan iya ba wllh, baki ga ba duk na ma kasa cin abinci saboda wannan yanayin da yake ciki, Aa wllh duk wani abu da xai dami mijina bana so gaskiya" Safara'u ta dau ayaba daya ta 6are tana ci tace "Tsoron da nake jiye maki shine kada ya kyallara ido ya hango wata a tafiye tafiyansa tunda suna yawon kasashe ma, duk da dai mu bama sakankancewa balle har a mana kishiyar, a tsaye muke ta ko ina, ba gashi ba har mijina ya mutu ni daya ce tal sai uban tarin dukiya da 'ya ya biyu da ya bar ni da shi" Aneesah tace "Ni baxai mutun ba in Allah ya yrda, amma dukiyarsa kam nawa ne da 'ya yan da xan haifa in sha Allah, Babu wata shegiyar mace da ta isa ta ra6ar min miji in dai ina numfashi, don ni na gwammace ma in kasheta wllh, kuma yarana uku sun isheni xaman duniya" Safara'u ta jefar da 6awon hannunta tace "Toh dai kiyi kokari ki gama amfani da maganin nan, idan ma baki sani ba duk danginsa sun xura maki ido ne a ga ciki amma shiru ake ji, barin wnn kanwar uwar nan tasa da na ga alamar bata da mutunci, dama ni duk na tsaneta tun encounter dinmu a lkcn bikinku" Aneesah ta yi tsaki tace "Umma suke ce mata ko wa, ae ina ga baki tsaneta irin ynda ni na tsaneta ba, ko hanyar gidanta ma ban sani ba har yau, na lura ta fiye shisshigi kan lamarin Aliyu, ko da yake ita wnn ae karamar alhaki ce" Safara'u tace "Atoh dae, duk ta karkashin kasa xa a bi masu bakinmu alekum" Aneesah ta marairaice tace "In sha Allahu nan ba da dadewa ba Allah xae bani ciki, kinga Mummy ma duk ta damu inyi ciki, ko daxu ta kirani ko na gama amfani da wanda aka kawo last week nace eh, wllh na kagu ace yau ga d'a na haifa ma Aliyu" Safara'u tace "In sha Allahu kuwa kamar anyi an gama, nan da wata tara xaki sullubo masa d'a ko 'ya" Aneesah ta washe baki tace "Allah ya tabbatar Small mum" Da daddare Aneesah na parlor suna kallon wani movie da small mum dinta wayarta ya fara ring, dauka tayi ganin Abuturrab ke kiranta, ta d'an buda ido tace "Ina xuwa Aunty yana kirana, ya tashi kenan" daga haka ta wuce sama da sauri.... Tana shiga bedroom din nasa ta samesa kwance har sannan da duvet a jikinsa, ta karasa kusa da shi ta xauna gefensa da damuwa tace "Ka tashi Captain? I still can't reach Ahmad ni kuma bani da number Ramlah" Tana magana ta kai hannu goshinsa, xaro ido tayi ta dauke hannun da sauri tace "Subhanallah, Ur temperature is very high Captain, plss ka samu ka tashi mu tafi hospital, this is getting out of hand" Sai kuma ta washe masa baki tace "U need not worry about the driving, ur wife can now drive expertly, na koya sanda baka nan, babu inda bana shiga da mota yanxu" Ya mike xaune da kyar yace "With whose car kika koya?" Ta fara kas kas da cingam tace "Whose car kuwa banda naka? D'an kurkurjewa ne kawai yayi kafin hannuna ya fada, har by pass naje da mota na xagayo har Mando, baka ga yanda na kware ba yanxu nake gudu" Shi dai kallonta kawai yake can yace "Sai kuma wa ya koya maki?" Tace "Ehh to da farko da Aunty Safara'u muka fara naga dai ba abun arxiki shine nayi ma wani frnd dina Auwal da muka yi makaranta tare magana, shi dai yake ta koya min muna yawo a gari har hannuna ya fada" Kallonta yake bbu ko kiftawa, ta mike tana cewa "Bari in fito maka da kaya mu tafi asibiti gaskiya, tun jiya kana kwance baka da lafiya ka ki yarda baka da lafiya, ai ba wai ance wani abu na damunka bane, kowa ya san stress ne from ur long journey, journey din nan kuma har da kai aka dinga piloting jirgin, body no be firewood ae..." komawa yayi ya kwanta don idan ya fiye magana yana jin xuciyarsa babu dadi, ganin tana kokarin dauko masa kaya ya ajiye mata wayarsa yace "Akwai layin Ahmad ki kirasa" Ta jefa masa wani kallo tace "Sau nawa xan ce maka na kirasa bai shiga ba" Abuturrab yyi kasa da murya yace "His other line, Dr Ahmad" Daukar wayar tayi ta shiga contact ta duba number sannan tayi dialing, yana fara ring ta kallesa tace "Ashe yana da wata number dama nake ta trying na cikin wayata" Shi dai bai ce mata komai ba, Ahmad na daga wayar ta marairaice tace "Hello Dr, it's Aneesah wllh i am telling u for the pass 2 days now Captain ba shi da lafiya sosai kuma ya ki xuwa asibiti, ko masallaci baya fita wllh balle a xo ga cin abinci...." Shiru tayi sai kuma tayi saurin cewa "Toh shkkn, sai ka xo, na gode" Daga haka ta katse wayar tana kallon Abuturrab tace "Kaji wai yana can gidanku ma, he is on his way coming right away" Shi dai bai ce mata komai ba tace "Let me make a cup of tea for u sai ka daure ka sha ko kadan ne kafin ya iso" Daga haka ta fice daga dakin.... *In kinsan kin samu full document na Jiddatul Khair, kar ki fitar min da shi i am begging in the name of God* 🥹 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 [7/16, 5:35 PM] Ummuanwar🥰: Tun da Ahmad ya shigo yake kallon Abuturrab dake xaune with a cup of tea a hannunsa, can ya karasa jikin window ya tsaya ya rungume hannunsa still looking at him yace "So what's wrong with you now?" Abuturrab ya d'an hade rai jin tambayar da yake masa, ya ajiye cup din hannunsa yace "Kawai ka rubuta min magani xa a amso min a pharmacy" Ahmad ya d'an yi murmushi yace "Ana rubuta magani without knowing d cause of a sickness?" Abuturrab yyi kasa da murya yace "Headache, dizziness, loss of appetite, Nausea, and... yawan faduwan gaba" Ahmad ya kuma yin wani murmushin kamar baxai ce komai ba, sai kuma yana kallonsa yace "And all this while Jiddah matarka ce kake fooling each and everyone of us Aliyu...." Abuturrab ya dauke idonsa daga kallonsa as if the question came unexpected, Ahmad bai kuma cewa komai ba, ya ciro biro a aljihunsa ya nufi gaban mirror ya dau takardan da ya gani a ajiye, ya d'an yi rubuce rubucensa snn ya dawo ya mika ma Abuturrab yana kallonsa yace "I think this drugs will do, Allah ya kara lafiya" Daga haka ya juya ya nufi kofa Abuturrab ya bi sa da kallo kafin ya fita cike da karfin hali yace "Ahmad" Ahmad ya tsaya sannan ya juyo, Abuturrab ya sauke idonsa kasa yace "U are not saying anything about the topic u brought up just now?" Ahmad ya girgixa kai yace "Nahh!! I have nothing to say, and i am wishing u nothing but d best" Yana fadin haka ya fice daga dakin, Abuturrab ya dinga kallon kofar sae kuma ya dafe kansa ya lumshe ido... Washegari da safe Abuturrab ya gama shiryawa with so many restless thought in mind, he wish this is all but a dream, ji yake xuciyarsa is getting weaker day by day and he really need to go to the hospital, Amma kuma idan ba yanayinsa ka duba da kyau ba baxa kace ba shi da lafiya ba, sbda taurin halin da yake yi, ya kalli agogo dake nuna karfe tara snn ya kalli Aneesah dake baje saman gado tana ta baccinta, buga gadon yyi gently amma ko motsawa bata yi ba, ya tafi daya side din ya janye pillow din da take kwance kai a hankali, bude ido tayi sai kuma ta mike xaune da sauri tace "Haba Captain kai komai naka baka yin sa romantically or in a romantic manner? yanxu haka ake tashin mutum fisabilillahi?" Speaking calmly yace "Ina makullin motata?" Ta dauke kai hade da jan tsaki kasa kasa, sai kuma tace "Saboda makullin mota xaka min irin wnn tashin walakanci?" Yace "Kinyi sallah ne da xa a maki tashin da ya kamata? Kullum sai karfe goma bbu tsoron Allah xaki shiga bathroom kiyi alwala ki fito ki shimfida darduma kice xa ki yi sallah, who does that Aneesah?? Not even a 10 year old child" a fusace tace "Toh a je a banyi sallahn ba sae me? Ae ba kai ake ma sallan ba naga, balle ma ni nasan nayi sallata, kuma wllh ba laifinka bane nice na fita tsakar dare naje pharmacy na samo maka magani ka sha har ka samu karfi da bakin yi min walakancin da baka min ba tunda ka dawo kasar, for the pass 2 days da baka da lafiya waye ya ji kanmu, sae yau don ka samu kanka?" A hankali yace "Bani makullin motata malama" Tace "Ai kana ganinsa gaban madubi" Tafiya yyi gun mirror din ya dauka ya fice daga dakin feeling so irritated at her. Ramlah ce ta bude kofar parlon ganinsa ta koma gefe da murmushi fuskarta tace "Sannu da xuwa Yaya" Yace "Yauwa" tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya... Ahmad?" Tace "Ehh yana ciki ka shigo yaya" shiga parlon yayi ya xauna, ta wuce daki, Abuturrab na xaune ya jinginar da kansa da kujera bayan minti biyar Ahmad ya shigo parlon, ya xauna kujeran dake facing din nasa yace "Good morning" Abuturrab ya d'an yi shiru, sae kuma yace "Ina ce idan kowa xai yi misperceiving dina kai baxa kayi ba, no not you Ahmad... and i was hoping u will understand me better then anyone, but do u mean i am mistaken?" Ahmad yace "U never wanted me to understand u, kana tunanin ni xan ki abinda kake so ne Captain?" Sai kuma yyi murmushi ya girgixa kai yace "Ka bani mamaki sosai, har gida na bi ka na sameka kan maganan Jiddah not long ago, kilan a lkcn ma ka koma kaje ka aureta ban sani ba, amma u almost blasted me telling me u have nothing to do with her, and u are leaving happily with ur wife, kana ganin ni xan maka bakin ciki idan ka kasance tare da Jiddah a matsayin mai dakin ka? Kana ganin i will also be against that bayan nasan komai tun daga farko har karshe? Da kuwa baka min adalci ba, coz i tried my very best tun farkon aurenka da Jiddah ka xauna da ita as ur wife, though i know u never bargained for that... amma nace ka dauka kaddarar ka ce a haka, kayi hakuri ku xauna, Aliyu sbda haka ka maida ni makiyinka, daga karshe kuma ka munafurce ni, Yes ka munafurceni, and you made me feel as if i am not trustworthy of, ban yi tunanin idan xaka boye ma kowa nima xaka boye min ba..." Abuturrab ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya, looking so confuse yace "U misperceived me instead Ahmad, i never knew xan iya gathering courage lkci daya in fadi abinda ke raina kwana kusa, ban san xan iya ba, and abinda yasa bana involving dinka I don't want to look foolish after everything, ban san ta ina xan fara ba bayan abubuwa da yawa da suka faru, plss I don't want to go deep into this coz i am not okay Ahmad, but i am here to just say to u that.... i am sorry about everything, nasan a ko da yaushe kana sona da alkhairi fiye da kowa, kuma da na dau shawaranka tun farko abubuwan dake faruwa yanxu baxa su faru ba, i will accept all this in good faith in sha Allah" Ahmad dai bai ce komai ba yana sake mamakin Abuturrab, his pretence is just something else, ba a ta6a predicting dinsa, can yace "Allah ya tabbatar da alkhairi, ya Kuma kawo sassauci cikin lamarin" Abuturrab yace "Ameen, But i need a favour from u plss" Kallonsa Ahmad yake yana jiran jin favor din, a hankali Abuturrab yace "I want u to help me convince Umma" Ahmad ya girgixa kansa yace "I am sorry i can't involve my self in this because naga yanda suka dau issue din too personally, most especially Abba nd Hajja, sannan idan nace xan sa baki Umma cewa xata yi da sanina kayi komai kaga nima ka ja min kenan" Abuturrab bai kuma ce masa komai ba ya mike, har ya nufi kofa sai kuma ya tsaya ya juyo yace "Thank you" sannan ya fita Ahmad dai ya bi sa da ido cike da tausayinsa, fuskarsa kawai xaka kalla kasan yana cikin damuwa sosai, jinginar da kai Ahmad yyi da kujera wishing he can help. Abuturrab na xaune parlonsa a sama yana rubutu saman wani plain sheet aka bude kofar parlon, juye takardan yyi upside down ya maida idonsa saman laptop din gabansa dake a kunne saman center table din kamar dai yana operating dinsa, Ta gefen ido ya kalli wanda ya shigo parlon ganin Ahmad ne ya ci gaba da rubutunsa a hankali, Ahmad ya karaso cikin parlon walking calmly yana kallonsa har ya iso ya tsaya gabansa yace "How are you feeling now?" Abuturrab bai ce komai ba idonsa na kan takardan da yake rubutu, Ahmad ya duka ya dauke takardan, Abuturrab xai kwace amma tuni ya koma baya yana kallonsa, Abuturrab ya mika masa hannu yace "Pass it to me..." Ahmad bai tankasa ba sai da ya gama karance abinda takardan ke dauke da shi tsaf, ya kalli Abuturrab da wani irin mamaki yace "What the heck... kana da hankali kuwa Captain?? Are u okay? what is this u are trying to do, are you even okay?" Bai jira me Abuturrab xai ce ba ya dauke har laptop din nasa, Abuturrab ya mike kafin yace komai Ahmad ya fita daga parlon... Aneesah dake downstairs tare da wasu kawayenta biyu da suka xo ta bi Ahmad da kallo ganin laptop din Abuturrab a hannunsa, sai bayan da ya fita kawarta Suhaila tayi kasa da murya tace "Ni dai ina son gayen nan wllh, sau biyu kenan nake ganinsa a gidan nan, d'an uwan captain ne??" Aneesah tace "Mijin kanwarsa ce fa" Suhaila ta hade rai tace "Toh ina ruwana, ni dai har raina naji ina sonsa wllh" Aneesah tayi kasa da murya tace "Toh xan tura maki numbersa" Rungumeta Suhaila tayi tace "Ko ke fa sweety" Gida Ahmad ya tafi direct, bayan yyi parking kofar gidan ya sauka ya shiga ciki, Umma ta fito daga dakinta kenan ta shirya xata fita ya shigo, Umma na kallonsa tace "Mu je ka ajiyeni gidan Yaya yanxu" Ahmad ya ajiye laptop din hannunsa ya mika mata takardan ta amsa tana cewa "Meye wannan din?" Har ta kai karshen content din sannan ta kalli Ahmad da mamaki tace "Did he send this?" Ahmad yace "Shi yasa na taho da laptop din, ni ban sani ba" Umma ta ma rasa abinda xata ce, haka ta bude baku, can tace "Toh ko bashi da hankali ne dai??" Bata jira abinda Ahmad xai ce ba ta bude jakarta ta nemi waje ta xauna ta shiga dialing numbersa amma ta ji a kashe, ta kalli Ahmad tace "Kana da number Aneesah ne?" Ahmad ya ciro wayarsa yace "Eh" Umma tace "Kira min ita kace mata ta kai masa wayar yanxu" Dialing kiran yyi Aneesah na dagawa yace "Pls ki d'an kai ma Captain waya, his phone isn't going through" Aneesah ta mike tace "Toh" bayan kusan minti biyar Aneesah ta kira Ahmad tace "Gashi nan Dr" Ahmad ya mika ma Umma wayarsa, Umma na amsa ta kai kunne da sauri tace "Aliyu??" Abuturrab yyi shiru jin muryan Umma, tace "Baka ji na ne?" Ya sauke kansa kasa yace "Ina ji" tace "Ka taho gida yanxun nan ka sameni" jin yyi shiru still tace "Ka ji abinda nace maka??" Yace "Toh" tace "Ba To ba, don't keep me waiting ina jiranka in 30mins time" A hankali yace "Ohk" daga haka ta katse wayar, buda baki tayi ta rike ha6a tace "Lallai ina ga ya fara xarewa ne yaron nan" Ahmad ya girgixa kai kawai ya xauna, yana ta tunanin ta ina xai fara yi ma Umma magana sai kuma yayi kasa da murya yana kallonta yace "Umma da banyi niyyar cewa komai a kan issue din nan ba don Aliyu really failed u all, ko kadan bai kyauta ba, amma yanxu ina rokon ayi masa afuwa don Allah Umma, he is really frustrated now, i know it's not going to be easy amma ki sa baki a sassauta masa Umma, kuma wllh Allah yana son Jiddah fiye da yanda ku ke tunani" Umma tace "Dama ina ta jiran wnn lokacin sai gashi Allah ya kawo, munafakai algungumai kawai, waye bai san bakin ku daya ba?? xaka ce kai baka san ya koma ya daura aurensa da Jiddah ba?? Ai duk iskancin da Aliyu yayi kana sane kuma kai ke mara masa baya, banda haka dubi yanda ka dinga watsi da batun yusuf a wancan lokacin, sbda baka ma son yana xuwa gidan nan yana ganin Jiddah ka dauketa ka mayar gidan ka, ashe da abinda ku ka kullala da shi, toh baxan sa bakin a sassauta masa ba, sae ya raina kansa wllh, kuma duk abinda iyayensa suka ga daman yi masa dai dai ne, yanda in his next life baxai sake daukanmu for granted ba, munafukai kawai" Ahmad dai yyi shiru yana kallonta ya ma kasa cewa komai, ta ina xai fara ce mata shi bai da masaniya a kan duk abinda Aliyu ke yi?? Sanin waste of time ne hakan don ba yarda xata yi ba ya sa yyi shiru, dama abinda yake gudu kenan ya ki cewa komai tun shekaranjiya sai gashi still bai fita ba... Kamar yanda Umma ta umarce Aliyu cikin 30mins din ya iso gidanta amma fa da karfin hali gashi driving yyi, he just saw his self a gidan, sae yanxu ya sake yarda ba shi da lafiya don har jiri yake ji sama sama, Umma ta dinga kallonsa har ya xauna yana kallonta a hankali yace "Ina yini" tace "Uban wa ka tura ma letter din nan da ka rubuta??" Yayi mata shiru breathing slowly, tace "Tambayarka nake malam" ya girgixa kai yace "Xan tura, amma ban tura ba tukun" Tace "Ohk wani aikin ka nema ka samu wanda mu bamu sani ba tunda dama baka maida mu a bakin komai ba?" Ya mata shiru, sai kuma ya jinginar da kansa da kujera, Umma tace "Ikon Allah, yanxu abinda ka fara sha ne ke gaya maka karya haka Aliyu? Ko dai hauka ka fara yi?" Ya dago yana kallonta yace "I don't want to risk my life and the life of more than 100 Umma... Hakan da nake son yi shine mafi alkhairi, my job isn't a anyhow job, nd i don't think i can continue with the situation i am in now, ni baxan iya ba, i just..." Shiru yyi ya sunkuyar da kansa, mikewa Ahmad yyi ya fice daga parlon ya bar su. Ahmad bai samu kowa cikin main parlor din gidan ba, direct ya nufi dakin Hajja, sallama yayi ya bude kofar ya shiga, Hajja na ganinsa tace "Toh kinga algungumin na biyu, tare suke komai in gaya maki.. shi ke xugasa kuma shi ya lalatasa, ya gantalar masa da rayuwa, wllh sanda na bar Aliyu xan je Masar ba haka yake ba, ba ruwansa da kowa ta kansa yake, bayan na tafi wannan mutumi duk ya lalatasa ya koya masa mugayen halayya" Aunty dake xaune dakin ta hade rai ta dauke kai ganin Ahmad, shi ma tun da ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba, Hajja tace "Ai wllh ina nan ina xuba ido inga hukuncin Usman a kan Aliyu, kuma duk mun yarda mu xama gantalallun... Allah sai ya sake sakinta, ai dai wnn karan idan ya saketa babu kuma aure tsakaninsu har abada, sai kuma yaje can ya ci kansa ya koma hayin rigasa ya nemo wata me siyar da awaran..." Aunty dai ta dauke kai saboda Ahmad dake tsaye, Hajja tace "Kinga ai ita narkekiyar can da yake sun san me suka tafka ita da yayarta ai har yau bata sake xuwa gidan nn ba, duk su suke xuga sa fa, kuma shawaran da kika bani na cewa a mayar da Jiddar Bauchi haka xa ayi wllh, ni ban ta6a sanin kin iya kawo shawara me kyau irin yau ba" Aunty dai tayi shiru, Ahmad yace "Ina yini Hajja?" Tace "Aa ni na yafe wllh, meye kuma ina wuni?" Yace "Ashe kuma dai abinda Aliyu ya aikata kenan?" Ta kallesa sannan ta kalli Aunty tace "Kinji munafuki koh? A gaskiya ya fitar min a daki kar ni in bar gidan, duk wani abu da ya shafi Hauwa ba son ganinsa nake ba gashi ta dalilinta da abinda ta haifa xa a fara tashin hankali tsakanin Bauchi da Kaduna" Aunty ta mike ta nufi kofa ta fice daga dakin, Ahmad yace "Wannan dai abinda ake ko kashe mutum Aliyu yayi sai haka, kuma da ba don shi din ba akwai wani da xai san Jiddah a cikin ku? Ya aureta domin ya ceci rayuwarta aka dinga samun me xugasa cikin gidan nan sbda tana da wani mugun kuduri a kansa har ya saketa ba don ransa ya so ba, ba wani ya xauna masa da Jiddah kafin su rabu ba, a xaunar da Jiddar a tambayeta ko ya ta6a cutarta dai dai da kwana daya duk xamansu har suka rabu?" Hajja tace "Ji algungumi Uban wa ke xugasa katon mutumi balagagge kace ana xugasa?" Yace "Aunty Hafsah ke xugasa sbda tana son aura masa er aminiyarta wanda gashi can ta hadasa da abinda ke cutarsa yanxu" Hajja tace "Aa bawan Allah na samu labari da kansa ya ga Nanisa yace yana so babu ruwan Hafsah, yau kwana uku kenan banda mutunci da girmamawa babu abinda ke hadani da Hafsah ko ita ce da girki ko ba ita ba nan take xuwa ta durkusa ta ajiye min abinci idan da akwai wani abu ta min kafin ta fita, da yake ni nace kada Hauwa ta sake shigo min daki babu ruwana da ita, toh ni ban ta6a sanin Hafsah na da hankali da mutunci ba sai a yan kwanakin nan, komai yi min take har wanki da wankin bandaki, yanxu idan xan kai Jiddah bauchin ma tace tare da ita xa mu kai ta, kuma ita ta kawo wnn shawarar me kyau" kallonta Ahmad yake ko kiftawa babu, Hajja tace "Ba ruwana xan nuna ma kowa ni er banxa ce har sai naji Aliyu ya saki yarinyar nan Jiddah, ita kuma Nanisa da kake cewa na fa je gidanta ranan tare da jiddan har muka kwana, baka ga kazanta ba kamar a fursin, gidan duk wari duk ya ru6e, ni dai da na dawo gida sai da na kwanta aka kara min ruwa wllh, ga gudawa da na dinga yi in gaya maka, ai ina jinjina kokarin Aliyu duk tsaftarsa har yake iya xama da ita har su kwanta, inaaaa shima kawai dai ya lalace da kazantar ne ba wani abu ba" Ahmad yace "Hajja kar ku tilasta Aliyu ya saki Jiddah wani abun yaje ya samesa, don a yanxu haka yana kwance tun shekaranjiya ba shi da lafiya, yau kuma ya rubuta resignation letter xai ajiye aikinsa" Hajja ta kallesa da sauri tace "Xai ajiye wani aikin? tukin jirgin saman??" Ahmad yace "Kwarai" Hajja tace "Ya ajiye a kan me bayan duk na fesa ma kawayena Larabawan Masar cewar jikana tukin jirgin sama yake, ba fa karamin aiki bane don ba kowa Allah ke ba ma ba sai turawa..." Hajja ta mike tace "Toh ya ajiye a kan wani dalili ana dai xaune qlau ba komai? Sannan wani rashin lafiya ce tun shekaranjiya kamar mara gata banga wani da ya shirya daga gidan nan yace xai je dubasa ba, kai ni wllh babu wanda ma yace bashi da lafiya banda kai yanxu, to uban me ya masu haka kamar wanda ya kashe d'an mutum? Kai tun fa fil'azal Usman ya fi son wancan shegen yaron Salim, gashi ya sallama ma en benue shi, Mu je ka kai ni gidan Aliyun yanxu ai ban ga ta xama ba, amma Allah wadaran Hauwa dai, d'an ki na fari baxa ki dinga jan sa jiki ki ji damuwarsa ba, wata uwar kirki ce d'anta ba lafiya xata yi shiru da bakinta kamar yaron banxa, wllh na gaji da wahalan matan Usman, duk en iska ne wllh" Daga haka ta suri katon jakarta ta fice daga dakin tana cewa "Mu je Ahmad, ai Allah yayi maka albarka kai da ka xo ka sanar min, wa ya sani ko asiri aka masa xai ajiye wannan aikin gwal din da yake yi, wllh ba kowa ake ba ma aikin ba sai turawa, to idan ba ikon Allah ba ta ya mutum xai iya daga ringimemen jirgi har sararin samaniya, ai sai irin su Aliyun da Allah ya ba" A haka har ta fita dakin, Ahmad ya xauna gefen gado ya rike kansa yayi dariya sannan ya mike ya bi bayanta, har ta kai compound ya sameta tana tafiya kamar xata tashi sama, wayarsa ya ciro a aljihu yyi dialing number Umma bayan ta daga yace "Abuturrab din na nan ne ko ya koma?" Umma tace "Kai da kaje gidan jiya dama baka dubasa ba kayi tafiyarka Ahmad?" Yace "No na basa magani ai" Umma tace "Toh ka same mu a hospital" Da mamaki yace "Hospital kuma? But he was fine da ya xo ai ko" Umma ta katse wayarta, sake kira yyi bayan ta dauka yace "Wani hospital din?" Ta gaya masa ta katse wayarta, Hajja ta leko daga kofar gida cikin daga murya tace "Yau na shiga uku, baxa ka fito ka kai ni in ga halin da jikana ke ciki ba Ahmad??" Ahmad ya karasa kofar gidan, Ya bude mata back seat, tace "Yanxu yana can gidan nasa ne?" Ahmad yace "Yana asibiti" Buda baki Hajja tayi da shock tace "Asibiti??" ta ciro wayarta da sauri tace "Kira min Usman din" Ahmad ya amshi wayar ya shiga kira mata layin Abba, Abba na dagawa ya mika mata..... *Allah maku albarka my trustworthy fans, ina yin ku 100%* 🥰😘 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank youHajja ta gyara xama a motar tace "Usman dama akwai wani laifin da Aliyu yayi maka ne da ban sani ba bayan komawa da yayi ya karasa abinda ya fara?" Abba dake sauraranta yace "Ban fahimta ba Hajiya" a fusace Hajja tace "Naga bala'i, Meye baka fahimta ba Usman?? Tambayarka fa nake ko bayan auren nan da yaje yayi akwai kuma wani laifin da ya tafka maka wanda mu bamu sani ba?" Abba yace "Ance maki ya min wani laifin ne bayan wannan Hajiya?" Hajja ta kalli Ahmad tace "Ka ji gantallale ina tambayarsa yana tambayata, abinda kabiru baya yi kenan..." Abba yace "Hajiya me yasa idan xa ki yi magana baki yi kanki tsaye yanda xa a fahimce ki, sai kiyi ta kauce kauce kuma idan ance maki ba a gane ba ki kama fada, ni ban san kan me kike magana ba wllh" a nutse Hajja tace "Toh ni dai dama kawai ce maka xanyi idan wani abu ya samu jikana to ka nemi wata uwar ba ni ba gaskiya, ba fa kisan kai Aliyu yayi da xa a saka sa a bakin duniya ba har yana neman ajiye aikin gwal dinsa da sai wanda Allah ya so yake ba, sannan ga shi can ance yana kwance rai a hannun Allah, ba fa wani abun tashin hankali na a xo a gani Aliyu ya aikata ba da xa saka sa a bakin duniya a sa shi gaba, toh wllh idan wani abu ya samesa Masar xan kai karar nan, don Najeriya baxata iya mana shari'a da ku ba, takardar da aka min na Masar din kawai xan kai in nuna a maka min ku a kotunsu" Tana kai wa nan ta katse wayar tana kallon Ahmad tace "Mu je Ahmad" Ya tada motar ya nufi asibitin da Umma tace, har suka isa asibitin kuma Hajja tsigale Abba da Ummi take, Bayan Ahmad yayi parking yace "Toh ita Aunty fa bayan da na shigo ma na tarar da ita xaune dakin ki tana ta xuga ki" Hajja tace "Ta dai xuga uwarta dake kabari, ita har ta isa ta xuga ni... Snn me yasa xan sakota a batun nan bayan nasan babu abinda ta hada da Aliyun idan ba cutarsa da ta dinga yi da tana cinye masa kudi ba" Ahmad dai ya ta6e baki ya sauka motar ita ma ta fito tana sharce xufar goshinta tace "A kai ni inda Aliyun yake, wllh xa a sha mamaki na idan wani abu ya samu Aliyu, tunda nake ko tari bai ta6a min ba da nufin fitsara ko rashin kunya, to yaushe ma yayi magana balle har ya raina babba, shi da magana ke masa wuya" Ahmad dai tafiya yake har suka shiga reception din asibitin, Hajja ta nufi nurse da sauri a rude tace "Ke yarinya an kawo wani matukin jirgin sama nan? Shi kadai ne matukin jirgi bahaushe a duk Najeriya" juyawa Ahmad yyi da sauri ya ji kamar da baya wajen Hajja tayi wannan maganan, Nurse din sai kallon Hajja take, sai kuma ta d'an yi dariya tace "Ya sunansa Mama?" Hajja tace "Sunansa Aliyu Usman, jikana ne, amma Abuntural naji suna ce masa" Kujera Ahmad ya nema ya xauna trying his very best not to laugh, nurse din ta shiga duba files din admitted patient dinsu na ranan, daga bisanni ta kalli Hajja tace "Xa ki hau sama daki na biyu, dake kallon hagunki nan xa ki shiga Mama" Hajja ta nufi stairs da sauri, Ahmad ya bi ta da kallo yana murmushi, can ya mike ya gaida nurses din ya wuce sama shi ma, Tsaye ya tadda Hajja tsakiyar ward din bayan ta shiga, cikin rawan murya tana kallon Umma take cewa "Me likitocin suka ce ke damun jikan nawa Ramlah?" Umma ta ajiye wayar hannunta tace "Toh gashi nan dai Ahmad xai je ya sami likitan yanxu" Ahmad ya karasa saman gadon yana kallon Abuturrab dake bacci, kamar dama don yayi baccin aka kawosa asibitin, bacci yake tsakaninsa da Allah, amma kuma ga drip a hannunsa, Hajja ta rushe da kuka xata nufi saman gadon Umma da ta bi da wani kallo tace "Hajja don Allah sun ce a bar sa ya huta sosai baya samun bacci dama, kuma wannan kururuwan naki ai sai ya tashe sa" Hajja ta dawo da sauri tana share hawayenta tace "Toh nayi shiru" Umma ta kalli Ahmad tace "Kaje likitan na office dinsa, sai kaji bayanin da xai maka" Ahmad ya nufi kofa ya fita, ganin kujera daya ne a ward din Umma ta mike tace "Ga kujera Hajja" Hajja na matsar kwalla tace "In xauna inyi me jikana na kwance ba lafiya, aa barni a tsaye Ramlah, amma Allah shi kadai yasan yanda xai yi da Hauwa, ki haifi yaro ki maida sa banxa, ai kuwa Aliyu ba d'an banxa bane, wato ita dai kawai duniya ta haifar ma shi yayi ta jigila da mutan duniyar a jirgin sama" Umma tace "Toh Hajja da kike wnn maganan kina da tabbacin ta xo ko bata xo ba??" Da sauri Hajja tace "Wllh bata xo ba Ramlah, ta xo tayi me bayan ba sonsa take ba, sai kace ba gida daya muka kwana da ita ba xaki ce min ta xo, ina ganinta ai da safe tana ta share share kamar tababbiya a cikin gidan, ashe d'an ta na nan kwance asibiti rai a hannun Allah, kuma banda Ahmad babu wanda yaje ya gaya min, kai ai ni kawai ina rayuwa da yan iska ne a gida daya, daga Usman din har matansa kuwa, kuma in wani abu ya samu Aliyu wllh sai na dauresu duka a Masar" Umma tace "To ko awa daya ba ayi da na kawosa asibitin ba ai, don daga gida na ya ke, kuma ko minti sha biyar banyi da kiran ita yayan na sanar mata ba" Hajja tace "Allah???" Banxa Umma tayi mata, Hajja tace "Toh ni dai fatana Allah ya farfado min da shi inji meye damuwarsa ba shkkn ba, dama ba uban wani ya renan min shi ba har ya kai haka" tana kai wa nan ta ciro wayarta ta mika ma Umma tace "Kira min Hafsah" Umma ta d'an kalleta, sai kuma ta amshi wayar ta gama danne dannenta ta mayar mata tace "Bai shiga ba" Hajja tace "Kira Usman to" Sai a nan Umma ta kira mata Abba ta mika mata wayar, Abba na dagawa babu yabo babu fallasa Hajja tace "Ka kira matarka Hafsah yanxu yanxu kace ta kirani, ni an kira min ita ban sameta ba... Bani da wata magana da kai bayan wannan" Daga haka ta katse wayarta, bayan kusan minti biyar sai ga Aunty ta kira Hajja, Hajja na dagawa tace "Hafsah ki ba su Aisha pillow da bargo hade da tabarma su kawo min asibiti, ga Aliyu nan dai an kwantar rai a hannun Allah da kyar likitoci suka samo kansa" Aunty tace "Subhanallahi wani asibitin me kuma ya samesa?" Hajja tace "Ban sani ba, ki bada sakon da nace a kawo min" Daga haka Hajja ta katse wayar tace "Munafuka kawai har tana cewa in dauki Jiddah in kai Bauchi kamar ubanta ne ya halitto Jiddar, ai duk sai na ci kaza kazan kowa in dai abu ya samu Aliyu" Umma dai bata sake bin ta kan Hajja ba. Hajja na katse wayar Aunty ta shiga kiran Aneesah, Aneesah na dagawa tace "Ke dama mijinki na asibiti shine baki gaya min ba, kuma me ya samesa?" Aneesah ta mike xaune daga kwancen da take ta dafe kirji da sauri tace "Asibiti? Ke wa ya gaya maki Aunty??" Aunty tace "Ban gane wa ya gaya min ba, ina Aliyun toh?" Aneesah ta mike tsaye cike da confusion tace "Wllh ina bacci ya tasheni na basa makullin mota ya fita daxu da safe kuma bai ma ce min ga inda xai je ba... auu ya kuma dawowa gida ai wajajen karfe sha daya, to shine ya sake fita bayan azahar, ke a ina kika ji yana asibiti?" Aunty tace "Yanxu tsinanniyar tsohuwar can ta kirani take fada min a kai mata bargo da pillow" Aneesah tace "Bai fa ce min asibiti xai je ba, bari xan kira Ahmad yanxu" Aunty tace "Ki kirani idan kin tambayesa" Aneesah tace "Toh" daga haka ta katse wayar, Ahmad ta shiga kira nan kuma ya gaya mata asibitin da suke, iyakar tashin hankali ta shiga a lokacin, abun har ya kai ga admitting, da sauri ta kuma kiran Aunty tace "Wllh da gaske ne Aunty har an kwantar da shi wai..." Aunty tace "Wani asibitin ne?" Aneesah ta gaya mata, Aunty tace "Toh ki biyo mu tafi tare kawai" Aneesah tace "Ai na koma baya Aunty, mu hadu a asibitin kawai xai fi, sai mu tafi da Aunty Safara'u" Aunty tace "Aa nafi son mu je dukanmu tare xai fi, xan jira ku a bakin hanya" Aneesah tace "Toh ai shkkn" daga haka ta katse wayar, da sauri ta wuce sama ta sanar ma Aunty Safara'u, cikin minti goma duk suka shirya suka fito, Safara'u tace "Wannan dai ba girmanmu bane a ganmu cikin adaidaita sahu kamar wasu en iska, katon gida haka ace mota daya ne kacal kamar rai, duk kudinsa shi baxai siya maki karamar mota ki dinga tukawa kije duk inda xa ki ba" Aneesah ta hade rai tace "Toh wai aunty duka duka yaushe na koyi motar, ni dai mu daga kafa kinga kafin a fita bakin titin nan da tafiya, wllh duk hankalina ya tashi" Safara'u ta ta6e baki tana ci gaba da bin ta. Ana kiran la'asar su Aneesah suka shiga asibitin, nurses suka masu kwatancen ward din sannan suka wuce sama, Aneesah ce ta bude kofar ward din, Umma na dakin har lkcn da Hajja dake xaune kan kujera daga kusa da Abuturrab dake ta bacci har lkcn, Ramlah ma na ward din a xaune kan daya daga kujeru hudun da aka kawo, Daga sama har kasa Hajja ta dinga kallon Aneesah da ta iso gun gadon da sauri cike da damuwa tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Hajja ta kare gadon ta bubbuda hannunta tace "Ance kada wanda ya matso kusa da shi inji likitocin...." Tsayawa Aneesah tayi tana kallonta irin kallon rainin wayo, Hajja ta kalli su Safara'u da suka yi cirko cirko bakin kofa tace "Oh oh Allah, likitocin fa sunce mutum uku kadai ke iya shigowa dakin saboda yanayinsa, sunce kuma a gaskiya idan ba mu bi doka ba xa su kora mu tunda ba Asibitin ubanmu bane, da a Masar ne ma yaushe xa su bar mutane ukun? Ai sai ni kadai ko Ramlah uwarsa, amma kun wani kwaso jiki kun shigo daki me window biyu kacal ta ina xa a ja numfashi saboda Allah??" Juyawa Safara'u tayi ta fice daga ward din, Aunty dai na tsaye sai kallon kasa kasa take ma Hajja, Hajja tace "In kuma ni in fita ne to sai in fita in bar dakin, ai likitocin ne suka bani umarnin in xauna kusa da shi" Aunty ta d'an kalli Umma tace "Sannu" Umma tace "Au ashe kece" Ko kallonta Aunty bata sake yi ba ta juya xata fita, Hajja tace "Ina bargo da pillon da nace maki Hafsah?" Tuni Aunty ta fice daga ward din without answering her, Hajja ta kalli Umma tace "Kinga er iska ko?? To ni nasan me ta shigo da shi da xan bar ta ta matso kusa da jikana, Aa wllh ba ruwana kowa yayi takansa, ke Ramlah karama fita ki kira mijinki ku koma gida ki taho min da pillow da Bargo daga gidanki" Ramlah tace "Toh" sannan ta fita daga ward din, ita dai Aneesah na tsaye Hajja taki barin ta karasa kusa da Abuturrab kuma ta ki fita, Hajja ta kalli Aneesah tace "Toh kinga ai mun cika uku cif cif a dakin yanxu, ga kujera can ki tafi ki xauna sunce kada a xo kusa da shi saboda halin rayuwa" Aneesah ta kalli Umma ta gefen ido kamar ana tilastata tace "Ina yini?" A dakile Umma tace "Lafiya" Juyawa Aneesah tayi ta nufi kofa ta fita, a reception ta tarar da Aunty da Safara'u suna xagin Hajja, Safara'u na hangota ta mike tace "Bani makullin gida inyi wucewata, ba dani xa a ci gaba a haka ba, idan xuciya ta debeni xan iya dura ma Tsohuwar can Ashar babu ruwana, ba kuma dangin iya balle na baba, ina dalili mata ta tijarani haka" Aneesah tace "Haba Aunty, mijina ne fa ba lafiya, saboda me zaki ce xaki tafi kamar saboda ita kika xo" Safara'u tace "Wllh baxan xauna ba ni ba er iska bace, toh lafiyar ni xan basa idan na tsaya kina ganin walakancin da aka mana yanxu, ke kanki gashi kin fito ward din" Aneesah tace "Toh wai Aunty sai ki biye mayyar can? Mayya ce fa, ni dai kiyi hakuri ki tsaya, duk xan rama maki wllh tllh" Safara'u tace "Anjima dai xan dawo amma baxan zauna yanxu ba tana nan" Aunty da duk hankalinta ya ki kwanciya don tana tsoron kada a tada batun auren Abuturrab a asibitin su Aneesah su ji don har sannan basu da labari, tace "Aneesah kawai ku tafi tunda tijararriyar can na nan, ga kuma wancan munafukar Ramlan a xaune, kinga sunyi bake bake a dakin suna nuna isa da iko gwara kawai mu tafi" Aneesah tayi wani shewa tace "Wllh wllh ba inda xanje ina nan wajen mijina, yanxu a cikinsu akwai warce xata iya masa wanka ko wani abun banda ni da nake matarsa?? Ai duk sai dai su gama kame kamensu a nan amma nice nan dolensa kuma babu inda xanje al-qur'an, xa su sha mamaki yau" Aunty ta hadiye abu da kyar tace "Toh kuwa xaki sha walakanci iri iri wllh" Aneesah tace "Sai kace baki san ni ba Aunty, wllh babu xancen respect tsakanina da su, xa su ga rashin kunya ganin idonsu" Daga haka ta bude jakarta ta ciro makulli ta ajiye ma Safara'u a gefenta ta wuce sama. Aneesah na komawa ward din ko kallon Hajja bata yi ba ta tafi gefen gadon ta xauna tana kallon Abuturrab dake bacci tana gyara masa kwanciya cike da kissa, buda baki Hajja tayi tana kallonta, sai tayi tagumi tace "Yau naga jaraba, ke matar nan bance maki ance kada warce ta je kusa da shi ba ko wata cutar kike son goga masa mu shiga uku?" Aneesah ta kalleta tace "Cuta kuma Hajja, mutumin da muke kwana gida daya, daki daya kan gado daya, wuri daya kice xan goga masa cuta?" Hajja ta mike tace "Toh ai nan ba gidanku bane shegiya, xo ki fita kar in tara maki likitoci yanxu, ko kazantar ki bai isa ya kwantar min da jika ba er banxa kawai" Tun Umma na danne dariyarta tana dakewa har ta kasa, ta mike ta fita daga ward din, Aneesah ta sake baki tana kallon Hajja ko kiftawa babu, Hajja tace "Mata kawai duk kin cika turare a jiki xaki xo ki kawo ma mutane raini a asibiti shashasha kawai" Aneesah tace "Shegiya fa kika ce min?" Hajja na nunata da yatsa tace "Ance maki shegiyar ko ramawa xa ki yi?" Aneesah ta bar wajen fuuu ta koma can jikin window a fusace tace "Wllh ni ba shegiya bace, da uwata da ubana kam" Hajja ta ja kujera ta xauna kusa da gadon tace "Oho dai, ni dai ba kin matsa daga kusa da shi ba" Aneesah kallonta kawai take xuciyarta na tafarfasa, Bude ward din aka yi Ummi ta shigo tare da Umma da Nafisah, kallo daya Hajja ta ma Ummi ta dauke kai, Ummi ta karaso ciki ta ajiye basket din abincin hannunta, with respect ta kalli Hajja tace "Ina wuni Hajja?" Hajja tace "In dai kika kashe Aliyu nima ki kasheni kawai Hauwa" sai kuma ta fashe da kuka tace "Mata ki haifi yaro ki fi kowa k'in sa?" Umma tace "Ya xa ayi ta k'i sa Hajja, ranan da ku ka yi masa caaa a kai so kike ta bude baki ta ce wani abun kice tana goyon bayansa, ko kice ta maki rashin da'a?" Hajja ta mike tace "Aa wllh baxan ce ba ai nasan xafin Haihuwa, idan nice ita ai sai inda karfina ya kare, kaca kaca xan ma duk wanda yace xai sa d'a na a bakin duniya, amma sai tayi shiru kamar jira take a walakanta Aliyun, to wllh Allah xai maku hisabi da shi ba ruwana" Ummi dai bata ce komai ba, Hajja ta fyace majina ta koma ta xauna, Aneesah ta kalli Ummi bbu yabo bbu fallasa tace "Sannu da xuwa" Ummi tace "Sannu" Umma ta kawo ma Ummi kujera ta xauna tana kallon Hajja tace "Toh ayi hakuri Hajja, xa a gyara in sha Allah" Hajja tace "Aa gwara ki gyara kam, yanxu ni da nake dolensa ba gani xaune a gefensa ba tun daxu, kema banda kina uwarsa baxan bari ki xo kusa da shi ba ma wllh, likitocin sun ce yana bukatar hutu sosai" Ba a dade ba Ramlah ta shigo da bargon da pillow hade da tabarma, Hajja tace "Yauwa er albarka, ajiye min can gefe da daddare a shimfida min inyi kwanciyata" Ramlah ta tafi ta ajiye inda Hajja tace.... Tun lokacin da Hajja ke ma Aneesah ihu Abuturrab ya farka don har tsakiyar kansa dake masa ciwo sosai yake jin surutun Hajja, amma ya ki bude ido ko nuna ya tashi, jin muryan Umminsa yanxu yasa shi bude idonsa ya mike xaune... Hajja tace "Alhamdulillah sannu Aliyu, ya jikin yanxu, amma inji dai ba surutunsu ya tashe ka ba duk su fita kawai, don ance a bari ka huta" Ya girgixa mata kai kawai, ya kalli Ummi a hankali yace "Ina wuni" Ummi tace "Lafiya lau, how are u feeling now?" Yace "Alhmdlh" Aneesah dai na tsaye sai kallonsa take tana tsoron xuwa kusa da shi Hajja ta koreta kuma, Kallonta yayi ai suna hada ido bata san lkcn da ta nufesa da sauri ba tace "How are u feeling now?" Hajja ta dinga mata wani kallo daga sama har kasa tana yamutse fuska, Umma ta tafi gun abincin da Ummi ta kawo ta dau plate ta shiga xuba masa har ta gama Hajja ta amshe ta kai masa tace "Ka daure ka ci ko kadan ne ka ji Aliyu?" Ya dinga kallon white rice din kafin yace "Ba shi nake so ba" Hajja tace "Me kake so Aliyu, fada min ko meye shi kaji" Ya d'an yi shiru, Hajja ta shiga lallabasa tace "Daure ka fada ko meye shi kaji Aliyu" Yace "Awara xan ci" Daga sama har kasa Umma take kallonsa, Aneesah tace "Toh Baby bari in koma gida yanxu inyi, i know it wont take long" Da sauri Hajja ta kalleta tace "Ba fa indomie yace xai ci ba Nanisa, Awara yace..." Umma tace "Xan kira can gida xa a soya yanxu a kawo, muna da shi ajiye a freezer dama" Hajja tace "Yauwa to maza kirasu, ko Jiddah ce sai a sa tayi tunda naga ta iya duk abun gargajiyan nan, dubi dambun da tayi ranan nan me shegen dadi wllh, sannan uwa uba tsafta, a tsaftace xata yi masa ta kawo tunda shi sarkin son tsafta ne" Aneesah da lokaci da mood dinta ya canxa ta hade rai tace "Nima ina da shi a freezer din, kuma cikin minti kadan xanyi in kawo..." Hajja ta kalli Umma tace "Yi min kiran Jiddah" Umma ta shiga dialing number Maimoon tana dagawa tace "Ba Jiddah wayar" Maimoon na ba Jiddah Umma tace "Kina ji na Jiddah" Jiddah tace "Ina ji Umma" Umma tace "Ku soya awara yanxu kuyi sauce xa ku kawo asibiti, xan kira driver ya je ya dauko ku" Jiddah tace "Toh Umma" Umma ta katse wayar, Hajja tace "Allah ya maki albarka Ramlah, yanda kika tsaya kan Aliyu kamar d'an da kika haifa Allah ya tsaya maki haka ke ma, uwarsa kuma Allah ya shiryeta..." Ummi ta mike tace "Toh Allah ya kara lafiya, Xan dawo anjima Hajja" Hajja tace "Je ki, tunda dai ga mu, idan da kara ma bai kamata ki biyo mu rigirigi asibiti ba sai kace ba d'an ki na fari ba, ai kara ma wani abu ne, duk sai naji kunya da na ganki wllh" Ummi dai bata ce komai ba ta nufi kofa ta fita Ramlah ta bi bayanta don Ahmad na jiranta tun daxu a waje, Umma dai ta tabe baki tana girgixa kai tana jinjina lamarin Hajja. Aneesah kam abun duniya ya isheta gashi har ga Allah bata iya awaran ba, to ko dai ta koma gida tayi order kawai yanxu yanxu, kallon agogo dake nuna shidda saura tayi, sai kuma ta nufi kofa ta fice daga ward din, bayan ta sauka downstairs ta shiga kiran Chef Salma, tana dagawa tace "Salma don Allah ina xan samu Awara yanxun nan na order...." Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulu mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd guess what😍munyi upgrading kayanmu gbdy domin jindadinku🥰bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida 💯 Natural/organic maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki komai da komai Akwai soap 3k Student package 7k Beauty kit 11k Bridal kit 18k Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏Ko gida Aneesah bata koma ba bayan ta amshi awarar a bakin hanya ta hau adaidaita ta koma asibitin, tana isa bayan ta sauka tana kokarin ba mai adaidaitan kudi sai ga Jiddah tare da Maimoon driver ya ajiyesu sun sauka motar, Hijab har kasa ne jikin Jiddah, Aneesah na ganinta bata jira amsan canjinta ba ta shige gate din asibitin kamar ana tunkudata ciki, Maimoon ta kalli Jiddah da sauri, ta rike ha6a tace "Saurin me wancan matar kuma take daga ganinmu? Ko dai sleepless night din ne tun yanxu" Jiddah dai bata ce komai ba, suka shiga gate din asibitin tare. Suna kallon Aneesah na ta xabga uban sauri, Maimoon bata san lkcn da ta kyalkyale da dariya ba tana tafe hannu tace "Ke wllh kamar tsoron mu take, saurin da take fa hade yake da guduwa" Aneesah na shiga ward din bata bi ta kan kowa ba tana kallon Aliyu dake kwance ta nufesa da sauri tace "Baby gashi nan har na yi" Tana fadin haka ta tafi gun basket din da Ummi ta kawo ta duka ta dau plate da sauri tayi backing dinsu don kar su ga tambarin inda tayi order din awaran ta juyesa a plate har da katon part na naman kaza ta sa spoon snn ta mike tana murmushi xata nufi gadon da Abuturrab yake Hajja tayi saurin mikewa ta dakatar da ita tace "Aa Nanisa... Ba xancen baby gashi har nayi bane, bani in ga irin awaran, wa xai ci abinda xae cucesa?" Aunty da shigowarta kenan kafin Aneesah ita ma da d'an coolern farfesunta ta dinga hararan Hajja kamar ta shaketa, Dai dai nan Jiddah suka shigo ward din da Maimoon, kallonta Abuturrab ya dinga yi without blinking, ita ko tun da suka hada ido sau daya ta sunkuyar da kanta, ta karasa gun Hajja ta durkusa ta gaisheta, Hajja tace "Tashi tashi, maza xuba masa ya ci tun daxu yake jira" Jiddah ta gaida Umma, sannan Aunty da ta ki amsawa, bayan nan ta mike, daga sama har kasa Aneesah dake rike da plate din awaranta take kallon Jiddah haka nan kawai taji gabanta na bugawa, Jiddah ta dau plate din da suka xo da shi ta bude warmer din awaran, Aneesah na ganin haka ta karasa gadon da Abuturrab yake tana mika masa awaran fuskar nan nata a tamke tace "Gashi nan na maka awaran Baby, eat it now" Ya amshi plate din ya ajiye gefensa yace "Thank you" Hajja ta bude hannu tace "Atoh dai" Mikewa Jiddah tayi tana mika ma Hajja awaran da ta xuba Hajja tace "Ya kike abu sanyi sanyi kamar kina shakkan wani, ki tafi kanki tsaye ki mika masa awaran tun daxu yake ta jira wllh, ko ke baki ga ya gantalar da wanda ta mika masa a gefe ba tunda ya san me xai ci ma kansa, atoh wa xai ci gaibu, maxa karasa ki basa, ae shi sa ake son duk runtsi ka xamo mai tsafta, Maimoon fita ki amso masa ruwan gora me sanyi, naga wa ennan duk ba sanyi...." Maimoon bata so ba, amma haka ta dau kudi da sauri ta fita taje ta siyo ruwan, Umma dai sai kallon ikon Allah take a cikin ward din nan yau, Aunty kuwa lkci daya ta ji xufa na keto mata daga inda take tsaye, a hankali Jiddah ta daga kai ta kalli Abuturrab suka hada ido cause bin ta kawai yake da kallo as if his life depends on that, kawai ta sauke idonta ta nufesa ta tsaya opposite side din da Aneesah ke tsaye ta kafeta da ido xuciyarta na ci gaba da bugawa babu sassauci, Jiddah tayi kasa da murya tana mika masa awaran tace "Ya jikin?" And he felt he was melting, kallon cikin idonta kawai yake, wanda hakan ya sa ta dawo uncomfortable ta sauke idonta da sauri tace "Is this enough??" basu ankara ba sai gani suka yi Aneesah ta kai hannu ta kwa6ar da plate din hannun Jiddah da karfi, har sae da awaran ya kife gaba dayansa a kasa, Jiddah ta ja baya da sauri tana kallon Aneesah gabanta na faduwa, tsalle Hajja tayi ta mike tana rafka uban salati ta kankance ido, Abuturrab yayi mata wani tsawa bayan ya fixge drip din hannunsa yace "Are you stupid Aneesah?? Are u mad???" Cikin daga murya Aneesah tace "Yes i am Aliyu, a gabana wata banxa yar talakawa xata wani kawo maka abincin ka ci bayan ni ma na kawo maka, ita a su wa? ko uban me ka hada da ita da xata wani xubo maka abinci ta taho simi simi kamar munafuka tana kallonka kallon cikin ido tana mika maka awara bata ji tsoron matarka na kusa da kai ba???" Ae tuni Aunty ta nufi Aneesah tana kokarin jan ta su fice daga ward din tana tutturjewa lkci daya kuma tana kunduma ma Jiddah wasu mugayen xagi jikinta na rawa, Hajja ta karasa kusa da su bakinta alekum ta dau plate din awaran Aneesan dake gefen Abuturrab ta kifa mata shi a kai cikin daga murya tace "Xo ki fita Shegiya uwar kazamai, ita Jiddar kike tambaya hadinta da Aliyu? to yanxu kuwa xa kiji hadinta da shi, Don kaza kazanki yanda kike matarsa ta sunna ita ma matarsa ce halaq malaq babu d'an kwal uban da ya isa ya canxa hakan, ko ke baki da labarin ya koma ya sake aure abarsa bai yi shawara da ko wani shege ba?" Sai da Aneesah ta dafa bango jin abinda Hajja ke cewa tana kallon Hajjar, ga jikinta duk awara tun daga saman kanta har kafarta, Ita kanta Jiddah jingina tayi da bango ta daya side din tana kallon Hajja babu ko kiftawa jin abinda take fadi, sae kuma ta juya ta kalli Umma... Aneesah ta nufi Abuturrab da sauri hankali tashe bakinta na rawa tace "What is she talking about Aliyu? What is she talking about i don't understand" Jin ya ki bata amsa kuma ya ki kallonta ta nufi Aunty ta riko hijab dinta kamar mahaukaciya tace "Aunty da gaske ne abinda matar can take fadi?? Is she for real" Hajja tace "Uwarki ce matar can ba ni ba, tsoron ki nake da xan ki fada maki gaskiya idan kowa ya ki?? ashe kwalo kwalo ake ta maki ba a sanar maki ba dama, to Jiddah dai matar Aliyu ce yau ni dai na fada maki kai na tsaye, kuma duk mun yi farin ciki da wannan abun arxikin, ae kowa na son nasa ya auri me tsafta...." Kaman daga sama suka ga Aneesah tayi kan Jiddah da tayi stiff a jikin bangon da take ita ma tana jin xancen Hajja kamar a mafarki, kafin Jiddah ta kauce tuni Aneesah ta cafkota ta hadeta da bango ta shakota iya karfinta, Abuturrab ya sauka saman gadon da yake yayi kansu da sauri, amma Umma ta rigasa yin kan nasu tana salati tana kokarin fixge Aneesah da ta kanainaiye Jiddah kamar macijiya tana kai mata duka ta ko ina, Hajja ta fasa wani ihu da karfi ta fice ward din a rude, cikin daga murya ta dinga cewa "Likitoci kuna ina ku kawo dauki, nas nas kuna ina ku kawo dauki, marasu lafiya kuna ina ku kawo dauki, an bar mahaukaciya ta shigo mana daki bamu san daga gidan uban wa ba, wayyoo xata kashe mana ita ku kawo dauki" Da yake da xuciya Aneesah ta rike Jiddah, duk karfin Abuturrab ya kasa kwace Jiddah daga rikon da ta mata, hakan ya sa shi ma ya shaketa da karfi amma inaaa taki cika Jiddah, Umma sai salati take tana kai ma Aneesah duka ita ma amma ko dar bata yi ba, sai cewa take wllh sai na kasheta nima a kasheni, wllh sai na kasheta, Allah sai na kasheta, Aunty taki ko motsawa daga inda take tana ta kallonsu, dai dai nan Maimoon ta shigo ward din tare da likitoci da Nurses, wani ihu Maimoon tayi tana bin dakin da kallo ta tafi da gudu ta dau cokalin diban miya ta nufi Aneesah wata nurse na kokarin riketa har sai da ta samu ta kwala mata da karfinta sau uku, hakan ne yasa Aneesah ta sassauta rikon da ta ma Jiddan sbda jiri da ya fara dibanta, Abuturrab ya turata baya da karfi without mind inda xata fadi, yayi saurin riko Jiddah da ta sulale kasa ya dauketa ya kwantar saman gado, Gaba daya likitocin where speechless a ward din... Is this movie they where acting or something of such here??? wani likita ne yayi kan Jiddah da sauri checking if she is fine sauran colleagues dinsa suka rufa masa baya, nurses din kuma suka dinga jan Aneesah da ta mike tsaye bayan ta fadi tana neman komawa kan Jiddah, don banda kundume kundumen xagi babu abinda take har dai suka fitar da ita ward din tana cewa su kyaleta ta kasheta, Abuturrab gaba daya ya gama rikicewa ya kuma ki barin kan Jiddah duk da instruction din doctors din, banda kuka babu abinda Jiddah take tana jin ko ina na jikinta na mata ciwo, Hajja bata tsaya iya kiran likitoci da nurses ba har masu gadi duk taje ta kira da passers by, Ta dinga ihu bayan ta ga an fito da Aneesah haraban asibitin tana cewa "Ku fita da ita can bakin titi kar a bar ta a nan, a fita da ita mahaukaciya ce, babu dawanau ne a kaduna? A taimake mu a mika ta can..." sbda yanda Hajja ta dage sai da aka fitar da Aneesah outside gate din asibitin, Hajja ta nemi gossip chair ta xauna ta rushe da kuka tana cewa "Yanxu xa ayi saki da wajewa ai ba sakin shirme da Usman ke son ayi da farko ba" Tuni Umma ta kira Ahmad ya taho ya fitar da su daga Asibitin, bayan ta katse wayar tana huci tace "Wllh sai ta san ta ta6a Jiddah, she must surely regret this..." Hajja ta gaji da kuka a waje ta dawo ward din bayan ta ta66atar an fitar da Aneesah, ta kuma rushewa da kuka tana kallon Umma tace "Ashe dama yar daba Aliyu ya aura duk bamu sani ba muke xaune da ita? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wllh bata doki banxa ba sai na shiga duk inda xan shiga an bi ma Jiddah hakkinta daga kaduna har Masar, xan nuna mata ni na fi ta dabanci, ni da nayi nawa dabancin a Masar" Abuturrab dai na tsaye kan Jiddah dake xaune saman gado likitoci sun bata pain reliever ta sha duk sun fita, ya ma kasa kallon su Umma ya kuma rasa abinda xai ce a ward din, ita dai Jiddah lokaci lokaci take share hawayen dake xubo mata ga kanta dake mata ciwo sosai har lkcn kuma gabanta bai daina faduwa ba, Abuturrab ya rasa ta yanda xai lallasheta saboda Umma dake ward din, Aunty dama tun da aka fitar da Aneesah ita ma ta fice sum sum sum, Maimoon da ke ta xaga ward din tana takaicin me yasa sai da aka aiketa hakan ya faru, wani kwafa tayi tace "Ai wllh bashi ta ci, kuma idan ban rama ma Jiddah wannan abinda ta mata ba ace ba ni bace" Umma dake ta boiling from inside sai jiran Ahmad dai take, yana xuwa kuma bata ko tsaya ta saurari kowa ba ta kama Jiddah suka nufi kofa Abuturrab ya bi su da kallo har suka fita... Ahmad da ke tsaye ward din bayan fitar Umma was so speechless sai kallon Abuturrab yake, sai kuma ya juya ya bi bayan su Umma, magunguna Umma ta sa ya siya ma Jiddah a pharmacy har da drip da xai kara mata wai, suna komawa gidan bayan ta sa ya saka ma Jiddah drip din, ta kuma sha magani ta kwanta ta mike a dakin tana saka hijab dinta kamar boss lady tace "Kai ni station Ahmad" Ahmad ya dinga kallonta ganin har ta nufi kofa ya bi bayanta yayi kasa da murya yace "Umma u need to calm down plss, wannan ai family issue ne, albarkacin Abuturrab da su Ummi kada ki kai ta police station, it won't make sense Umma" Umma ta juya a fusace ta kunduma masa wani xagi tace "A gidan uban wa wannan ya xama family issue?? Uban me Jiddah ta hada da ita da xai xama family issue? Wato ta doki banxa kenan kake nufi ko me?? Toh bari kaji ko Alhaji Usman bai isa ya hanani kai karar matsiyaciyar yarinyar nan police station ba yau, wllh sai na kulleta...." Jiddah dai sai kallon Umma take daga kwancen da take, Ahmad yace "Noo Umma plss listen to me..." Ficewa Umma tayi daga dakin kamar xata tashi sama, Ahmad ya bi bayanta da sauri, amma Umma bata sauraresa ko na second daya ba ta kama hanyar Police station ita kadai, ta kuma yi warning dinsa kar ma ya bi ta. Dole Abuturrab ya tilasta likita yayi discharging dinsa daga asibitin, ya kira Ahmad yayi driving dinsu gaba daya xuwa gida, Hajja har suka isa gida bakinta bai yi shiru ba, ba irin la'antar Aneesah da bata yi ba, tana shiga parlor ta fara kwala ma Abba kira kamar xata tsaga gidan, Ummi dake kitchen ta fito da sauri tace "Ai bai dawo ba Hajja..." Hajja tace "Toh ai duk gidan uban da yaje xai dawo ya sameni yanxu yanxun nan kuwa, ba shi dai babban burinsa ayi saki ba, to ya dawo ya sa ayi wannan da wajewa, don wllh ni dai idan Aliyu bai saki yarinyar nan ba xan iya mutuwa..." Ummi da gabanta ya dinga faduwa don a tunaninta Jiddah Hajja ke fadi tayi shiru tana kallon Hajja, Hajja tace "Wllh Hauwa da kyar likitoci da Nas suka kwace ta a hannunta, tana can duk ta mata jina jina an kai ta wani asibitin..." Sai kuma ta rushe da kuka, Ummi tace "Me ke faruwa Hajja?" Hajja tace "Meye kuwa baxai faru ba Hauwa, tsinanniyar Nanisa matar Aliyu ce ta saka Jiddah a hammata ta dinga duka kamar an aikota, daga wai Ramlah ta sa tayi ma Aliyu awara tun da ta iya ta kawo masa asibiti, ni dai can kofar gida na fita na samo mana agajin gaggawa aka xo aka fitar da ita daga Asibitin anyi dawanan Kaduna da ita" Abuturrab ya wuce dakinsa kawai, Ummi ta dinga salati tace "Ina Jiddar yanxu Hajja?" Hajja tace "Ramlah ta dauketa ta kai ta wani asibitin nace maki, baki ganta ba abun ba a cewa komai duk ta ji mata rauni ta ko ina" Sosai hankalin Ummi ya tashi ta koma parlonta da sauri ta dau waya ta shiga kiran Umma har ya katse bata dauka ba, Ahmad dai ya ma rasa bakin cewa komai a parlon, Hajja tace "Ina jin saki kala biyu ma xa ayi a gidan nan yau, wato Hafsah Allah ya tsine mata albarka, tana tsaye duk aka gama wnn tashin hankalin bata yi yunkurin yin komai ba, wannan ne kuma ya tabbatar min cewar da hadin bakinta Aneesah ta xo tayi abinda tayi, ai ita ta fara shigowa dakin asibitin da minti biyar sai ga Aneesah, to duk xan nuna masu ni er banxa ce, xan kuma nuna masu ni na haifi uban Aliyu sannan ya haifi Aliyun" Ummi ta fito rike da makullin mota tace "Bari xanje can gidan Hajja" Hajja tace "Wani gida bayan nace maki a asibiti aka kwantar da su, mu kanmu bamu san asibitin ba, yanxu mijinki xaki kira min duk gidan uban da yake ya dawo yanxu yanxun nan" Ummi tayi shiru tana kallon Hajja, Sai kuma ta koma parlonta kawai, bin bayanta Ahmad yayi ya kulle kofar yace "Ummi plss ki kira Umma ta tafi police station i tried stopping her but she isn't listening, wannan family issue ne bai kamata a kai station ba" Ummi tace "Police station kuma? I called but she isn't responding" Ahmad ya nemi waje ya xauna yace "Ki kara kira Ummi, bana son hakan ya faru wllh, su Abba baxa su ji dadi ba" Ummi ta shiga kiran Umma har ya katse still bata dauka ba, Ummi ta xauna ita ma cike da damuwa tace "Toh wai ya aka yi wnn abun? Babu kowa wajen ne har aka bari Aneesar ta doki Jiddah?" Ahmad yace "Ni bana nan na bar wajen Umma ce ta kirani after the incident" Ummi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Bayan kusan minti ashirin Abuturrab ya fito daga dakinsa ya nufi kofa, Hajja dake ta xaune tana jiran Abba ta bi sa da harara tace "To banda ta dalilinka a gidan uban wa Jiddah xata san axxalumar matarka? Wllh Allah ya isar mata... Xan ga abinda ubanka xai ce a kan wnn lamarin kuma ai" Shi dai bai ko kalleta ba ya fita.... Aunty na can bedroom dinta ta kulle da makulli kafin kowa ya kira Abba dama ta kirasa ta giggilla masa karya tana kuka, yace ta kwantar da hankalinta gashi nan dawowa... Kiran Safara'u ne ya sake shigowa wayarta for the 5th time, bayan na Aneesah kusan takwas da ta ki dagawa, ta dake dai ta dauka don ta ji abinda xa su ce mata, bayan ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren cikin tashin hankali Safara'u tace "Hafsah to ga motar yan sanda guda sun shigo gidan Aliyu sun xo tafiya da Aneesah don ma Allah ya rufa asiri kamar mun sani muka garkame kofa.... Banda bubbuga kofa bbu abinda suke yi yanxu haka" Aunty tace "Yan sanda kuma??" Safara'u tace "Wllh, da muka leka ta window muka ga wnn matar Ramlah ce tayi masu jagora" Aunty tace "Ina xuwa" daga haka ta katse wayar, ta shiga kiran Abba, yana dagawa ta sanar masa abinda Umma tayi, yyi shiru sai kuma ya katse wayar, Ummi ya shiga kira, tana dagawa yace "Ki kira yar uwarki ta sallami yan sandan nan da ta kwaso idan ba haka ba xan dau mummunan mataki a kan ke da ita wllh" Rasa ma abinda xata ce masa Ummi tayi.... Bai kuma jira me xata ce din ba ya katse wayarsa, Ummi dai ta dinga kallon Ahmad. Cikin minti ashirin Abuturrab ya isa gidan Umma... Direct dakinsu Maimoon ya nufa, yana bude kofar Jiddah dake kwance ta juya da sauri ta mike xaune don duk a tsorace take tana ganin kamar Aneesah xata ce xata xo gidan, Ya shigo dakin yana kallonta, mikewa Maimoon dake dakin tayi ta fice don ta ji har shi tana jin haushinsa, Jiddah ta ki kallonsa tana gyara duvet din jikinta gabanta na faduwa. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulu mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd guess what😍munyi upgrading kayanmu gbdy domin jindadinku🥰bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida 💯 Natural/organic maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki komai da komai Akwai soap 3k Student package 7k Beauty kit 11k Bridal kit 18k Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏Abuturrab ya xauna gefen gadon yana kallonta, still ta ki yarda ta kallesa, yayi kasa da murya yace "Look at me Jidderh..." Dauke kanta tayi ya kamo hannunta kamar jira take ta fashe masa da kuka ta rufe ido, a hankali ya daura kanta bisa shoulder dinsa cikin sanyin murya yana patting bayanta yace "Kiyi hakuri pls, i caused u all this... And ni nasan matakin da xan dauka a kanta" ita dai kuka kawai take, ya dago kanta yana kallonta a hankali ya kai hannu jikinta yace "Tell me where is hurting u now" Turasa tayi ta girgixa masa kai har sannan ta kasa daina hawaye, Bude kofar dakin aka yi Abuturrab ya juya da sauri tare da saketa, ita ma ta koma baya da sauri gabanta na faduwa, Umma ce ta shigo tana ganinsa a dakin ta wangale kofar tana nuna masa hanyar waje tace "Mu je ka bude masu gidanka a tafi da matsiyaciyar yarinyar nan yanxu...." ya mike amma ya rasa abinda xai ce mata, Cikin tsawa tace "Mu tafi nace ko baka ji na ne?" Yayi lowering voice dinsa yace "But Umma plss ba sai anje police station ba, i will personally deal with..." Wani tsawan Umma ta kuma yi masa tace "Ba sai anje police station ba?? Ohhh kana nufin ko bayan an kai ta police station din kenan kai babu wani hukuncin ma da kake da niyyar yi mata tunda kai ne dalilin da yasa ta kusa kashe yar mutane? Wait first who are u to question my order Aliyu?" Da sauri yace "Aa ba haka nake nufi ba Umma" Umma tace "Wato tun ba a kai ko ina ba kenan a titi wannan mummunan al'amarin ya faru babu kunya a kan idonmu, to in sha Allahu daga kai har matsiyaciyar nan bbu ajalin Jiddah a cikinku, babu inda xa ku ganta balle ku kasheta daga kai har matarka, police station kuwa ko uban da ya haifeka bai isa ya hanani kai ta ba balle kai..." Cikin tsawa tace "Fita mu je ka bude masu gida my frnd" kofa ya nufa ya fita Umma ta bi bayansa, a motarta suka koma station ta sake biya aka bata en sanda suka nufi gidan Abuturrab, a kofar gidan ta tsaya tare da en sandan tana kallonsa babu wasa tace "Go in and get her out" Ya d'an kalli yan sanda ya kasa ce mata komai, kawai dai ya nufi gate din cikin gidan ya shiga yana tafiya a hankali, mai gadi ya taso da sauri cike da damuwa yace "Yallabai ina fatan dai lafiya ko? Daxu ma sun xo suka dinga buga kofar shiga cikin gidan..." Abuturrab bai tsaya ba yace "Lafiya lau" har ya isa entrance din parlon yayi knocking, lkci daya kuma ya ciro wayarsa a aljihu ya kunna, dialing number din Aneesah yayi, kamar wayar na hannunta yana fara ringing ta daga da sauri, fashe masa da kuka tayi kafin ta ce komai yace "Zo ki bude min kofa" Tace "Honey yan sanda ne fa sun fi biyar suka shigo compound din nan daxu, suna ta knocking, kai kana ina yanxu don Allah?" Yace "Ina bakin kofa" kallon Safara'u tayi sai kuma ta mike da sauri ta sauka downstairs tana kallon kofar, tafiya tayi a hankali ta isa bakin kofar tayi kasa da murya tace "My captain?" Yace "Bude kofar" Wani ajiyar xuciya ta sauke ta bude kofar ya shigo parlon, ta rushe da wani sabon kukan tana kallonsa, Controlling temper dinsa kawai yake cause he felt like doing her exactly what she did to Jiddah at the hospital, wani haushinta yake ji har cikin ransa, ya dai dake yace "Tafi ki sako hijab din ki?" Ta dakatar da kukan da take tace "In je ina??" Yace "Inyi wucewata in bar ki ne?" Tace "Aa..." Da sauri ta wuce sama, ba a dau lkci ba ta sakko tare da Safara'u da ita ma ta xumbula Hijab din don xatonsu fitar da su xai yi daga gidan, yana ganinsu ya nufi kofa ya fita, Aneesah ta bi sa da sauri cike da wani farin ciki ashe Aliyu na sonta dama haka, wato dawowa yyi ya fitar da ita daga gidan tunda en sandan might likely come back, Safara'u dai sai bin su take da sauri ita ma, yana fitowa daga parlor ya ga en sanda biyu tsaye gefe da gefen balcony din, Umma kuma na tsaye daga kasa fuskar nan nata a murtuke, a hankali ya karasa sauka sai ga Aneesah ta fito, tana fitowa en sandan mata suka cafketa, daya dake rike da handcuff tace "U are under arrest" Xaro ido Aneesah ta dinga yi tana kallon Abuturrab tana bin en sandan da kallo cikinta ya duri ruwa sosai, Tuni Safara'u ta juya a guje ta koma cikin gidan, haka suka fitar da Aneesah daga gidan tana cewa "Captain da kai xa a hada baki a kai ni station?? Da kai captain??" Tsawa yar sandan tayi mata ta rufe ma mutane baki, sannan aka sa ta a mota aka wuce, Umma ko kallon Abuturrab bata yi ba ta shige motarta tayi reverse ta bi bayan motan en sanda Abuturrab ya bi ta da kallo kawai. Abba ne ya shigo parlor babu ko sallama yana kallon Ummi dake xaune tare da Hajja a parlon directly, yau kam Hajja ta bada labarin yanda incident din asibitin ya faru ya fi sau ashirin har da demonstration dinta, gashi ta ki yarda su tafi gidan Umma duba Jiddan wai ai dole Usman ake jira a je da shi ya gane ma idonsa abinda Hafsah ta sa Nanisa ta aikata ma Jiddah, don haka a hada hannu har shi a kwato ma Jiddah hakkinta tunda ba uwa ba uba, Shiru Ummi tayi ta sauke kanta tana sauraron Abba dake gaggaya mata magananganu ido rufe, ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, Hajja ta mike ta daka masa wani axababben tsawa tace "Shet up malam... A gabana kake wannan tijara babu tsoron Allah balle ni??? A gabana kake mata wannan cin mutuncin Usman??" Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tace "Ita Hauwar me ta maka kake jifanta da wa en nan axababben maganganun ba dadin ji?? Er banxa ka mayar da ita kenan Usman?? A gabana fa aka yi komai a asibitin nan ba wai labari na tsinta ba, ita Hafsar ce tayi maka duk wannan tsarin? to wllh wllh yau a gidan nan ko ni ko ita, Allah sai ka xaba ko ni ko Hafsah tunda babu wanda xai kiraka ya giggilla maka wannan karyan da ya sa ka dawo kake sababi sai ita, wllh idan baka xabi ko ni ko ita ba ka canxa uwa kawai kafin dare" Abba bai kuma kallon Hajja ba ya wuce bangarensa rai a bace, Hajja ta nemi waje tana kara rushewa da kuka ta ciro wayarta ta mika ma Nafisah dake xaune kasa gefenta tace "Kira min Kabiru" Nafisah ta amsa ta kira mata sannan ta mika ma Hajja, Yana dagawa ta sakar masa kuka tace "Duk abinda kake yi ka barosa don bai fi ni ba, ka biyo jirgi ka taho garin kaduna ta faru ta kare Usman babu xagi da cin mutuncin da bai min ba yau har korata yayi, ka taho kawai kabiru xuciyata xata fashe" daga haka ta katse wayar ta mika ma Nafisah tace "Kira min Umaru" Nafisah ta kira mata shi ma Hajja ta sanar masa, duk sai da ta bi ta kira 'ya yan mijinta gaba dayansu su bar duk abinda suke su taho kaduna Usman ya xageta ya koreta daga gidansa, Ummi dai na xaune tayi tagumi abun duniya ya dameta, banda radadi da xafi babu abinda xuciyarta yake mata and she is trying her best to hold back tears, duk wannan abun kuma Aunty na part dinta tare da er ta Aisha sun bama makulli.... Ko minti goma Abba bai yi da shigewa bangarensa ba Umma ta shigo gidan, tana shigowa ta kalli Nafisah tana huci tace "Abban naku ya dawo??" Nafisah ta gyada mata kai kawai, Umma tace "Toh ya fito gani nan na tako da kaina naxo ba sai yaje can gida ya sameni ba, ya fito ya sa a daureni har karshen igiya kamar yanda yace, gani gidansa ya fito" Hajja ta marairaice tace "Ya daure ki ko a dauresa??? Huhuhu ai da Masar ne yau xai san ya xagi mahaifiyar da ta tsugunna ta haifesa don wllh wllh baxai kwana kasar su ba ma, sai sun walakantasa sun masa dukan tsiya" Umma ta kalli Ummi tace "Ki tashi mu tafi Yaya, ya dade bai dau hukuncin da yace ba wllh, tashi muje babu shegen da ya isa ya sa maki hypertension, wllh dai dai nake da shi" Hajja ta mike tace "Babu inda xata je wllh, sai dai shi katon ya fito ya bar mata gidan, sannan in har ya kwana da auren Hafsah a kansa kowa xai girgixa da lamarina a gidan nan..." Tana huci ta kare maganar, sai kuma ta koma ta xauna tace "Kema koma ki xauna Ramlah yau kowa ya xuba ido akwai kallo" Nan Hajja ta kuma bi ta doddoka ma duk wa enda ta kira wani sabon kiran wai ga fa kayanta Usman ya watso bakin kofa.... Umma dai taki xama gidan tayi wucewarta ranta fess Aneesah xata yi kwanan cell, kuma ta ji dadin yanda Hajja ta tsaya ma Ummi, Ana idar da Magrib duk wa enda Hajja ta kira suka iso gidan, tana nan xaune ta hakikance a parlor taki motsawa ko nan da can, sallan ma a parlon tayi, duk suka xauna nan kasa suna gaisheta, ta amsa tana shessheka, babu yanda basu yi da ita a kan sun shiga parlon Abba ba ta ki, ta kalli Ummi da fitowarta daga part dinta kenan ta xo yi ma bakin sannu da xuwa tace "Kiyi kiran Aliyu da Ramlah su xo, a gabansu xa ayi komai" Ummi ta amsa mata da toh, sannan ta dau wayarta ta shiga kiran nasu, Abba ya fito daga bangarensa ya gaida brothers din nasa, shi dai Abban El-Basheer kallonsa kawai yake, Hajja ta wani dauke fuska kamar ta ga mugun abu, xaunawa yayi shi ma a parlon, Ummi bayan ta gama kiraye kirayenta ta taho ta xauna ita ma, Hajja ta kalli Kabiru tayi mici mici da ido tace "Dama ku gaya masa duk inda matarsa Hafsah take ta fito ta nemi waje ta xauna a nan ita ma" Abba dai bai ce komai ba, sai kuma ya mike ya tafi bangaren Aunty, ba a dau lkci ba suka fito tana biye da shi a baya, da hijab dinta me jan kasa, ta ki kallon kowa na parlon fuskar nan nata babu yabo babu fallasa ta nemi waje ta xauna ta gaida yan uwan mijin nata, duk suka amsa, ko kallon Hajja ita ma bata yi, ba a wani dau lkci ba Umma ta shigo gidan, ganin Aliyu bai iso ba, Alhaji Kabiru ya bude wajen da addu'a aka sake gaisawa sannan yana kallon Hajja yace "Hajiya lafiya me ke faruwa, kin kiramu duk hankali a tashi mun taho babu shiri" Hajja ta fashe da kuka tace "Baxan kiraku ba Kabiru, babu xagi da cin mutuncin da Usman bai min yau ba a gidan nan ni da uwar gidansa uwar 'ya yansa a kan wannan mata dai da ku ke gani Hafsah, kai ni har kayana yace in debe in bar masa gidansa baya son ganina" Bude baki Aunty tayi tana kallon Hajja, Abba kuwa kansa na kasa yana sauraronta, Hajja ta fyace majina tace "Don haka na kiraku ku xama shaida, in har Usman ya kwana da auren matar nan Hafsah to shegiya iyayena suka haifeni, wllh wllh sai ya saketa a gaban kowa ko kuwa ya canxa wata uwar a kasuwa" Abba ya daga kai yana kallon Hajja da sauri don maganan nata came unexpected, Aunty da ta fara jin xufa na keto mata ta dinga kallon Hajja xuciyarta na bugawa, Hajja tace "Shkkn na gama wannan babin, yanxu sai in koma maku babin abinda ya haddasa komai" Nan Hajja ta kwashe duk abinda ya faru a asibiti tana daga tsaye tana demonstrating har karshe... Tana huci tace "Yanxu duk xan kwasheku mu tafi gidan Ramlah ku ga yanda yarinyar ta mayar da Jiddan, to kuwa tunda yar daba ce har shi Aliyun wataran sai tayi masa jina jina ai, ni ko ina xa mu jira wannan ranan, oh oh ba matar xama bace wllh" Hajja ta kalli Ummi tace "Kema don haka Aliyu ya xo ki tisa shi gaba ya sallami yarinyar ko ya canxa uwa, duk nuna masu xa mu yi mu en banxa ne" cike da isa Umma tace "Kuma kin manta baki kara masu da cewa na kai ita matar Aliyun police station ba, yanxu haka tana can a kulle" Hajja ta kalleta da sauri tace "Auuu, kun ji abun arxiki, kai amma Allah ya maki albarka Ramlah, ka ga mace me kamar maza, yo ai da dani kika tafi gidan yan sandan in basu bayanin komai da yanda komai ya faru xa su fi daukar abun da muhimmanci" Gaba daya brothers din Abba kallon Umma kawai suke amma sun ki cewa komai sbda Hajja, Hajja ta koma ta xauna ta sharce xufar goshinta tace "Ko ni ko Hafsah yau" Aunty dai idan hankalinta yayi dubu ya tashi a lokacin, Alhaji Lawal ya d'an yi gyaran murya yace "Kina ji na Hajja" Hajja ta jefa masa wani kallo tace "Kai saurara Malam, ba na kiraku don ku kawo taku shawaran bane, ni fa umarni kawai na bada a nan ba wani abu ba, nayi kiranku ne don ku taho ku ba d'an uwanku shawaran yayi duk yanda xai yi kada in sakar masa bakina ya tagayyara, wllh wllh...." Sai kuma ta fashe da kuka sosai tace "Na fi shekara hamsin ban xubda hawaye ba sai gashi yau wai Usman xai sani inyi ta xubarwa kamar er banxa" Abba ya kalleta a karo na farko yace "Hajja kiyi hakuri, wannan abun wllh duk bai kai..." Wani tsawa tayi tace "Ya kai, har ya wuce... Wllh sai ka saketa" Duk aka kasa cewa komai a parlon Umma dai sai kallon tv da aka rage magana har karshe take bbu ko digon tausayin Aunty a ranta, Aunty taga fa da gaske Hajja take, ta mike ta isa gabanta ta fashe da kuka ta durkusa ta rike kafarta tace "Don Allah kiyi hakuri Hajja, idan ma wani laifin na maki kiyi hakuri kar ki kashe min aure...." Hajja ta janye kafarta tace "Kun ga muguwa wai inyi hakuri kar in kashe mata aure, halinki ne xai kashe maki aure ba ni ba, kuma ai Hauwa ya kamata ki tafi ki kama kafarta ki bata hakuri kafin ki bar gidan idan kuwa ba haka ba sai hakkinta ya kama ki wllh, wato kin cuceta ainun, kin shiga tsakaninta da mijinta kin raba su, walakancin da take hadiya ko kurma da bata jin magana baxa ta iya hadiyewa ba, duk wanda ya kalleta ya san cikin damuwa take babu kwanciyar hankalin xaman aure, hakan kuma bai isheki ba sai da kika nemo ma d'anta er dabar Habuja kika aura masa neman kashe masa uwar gidansa Jiddah, don kuwa duk ke kika koya mata abinda xata yi idan ta xo asibitin" Kuka kawai Aunty take cikin tashin hankali tana cewa "Hajja idan wani abun nayi ayi min hakuri don Allah" Hajja ta mike tana kallon Abba da kyau tace "Tashi ka dauko takardan da ka adana kake sa wa ayi sake sake ba tsoron Allah" Abba ya kalleta cikin kwantar da murya yace "Hajja..." Ta dakatar da shi a fusace tace "Wllh kar ka bari xuciya ta kwasheni in fada maka ba dai dai ba Usmanu" Ummi na son cewa ayi hakuri amma ta rasa ta ya don bata san yanda Hajja xata dau hakurin nata ba, ita dai duk jikinta yayi sanyi kuma har ranta bata son Abba yayi wnn sakin, mikewa Abba yayi ya tafi parlonsa, Alhaji Kabir ya mike ya bi bayansa, bayan sun shiga parlon yace "Hajja baxa ta saurari kowa ba a wannan lokacin Usman gudun matsala da kuma fushin uwa, ka rubuta ma Hafsah saki daya hakan shine kadai mafita" Abba dai bai ce komai ba ya dau takardan da biro suka fito parlon, Aunty na ganin takardan da biro ta kara rudewa tace "Usman yanxu sai ka iya saki na?? Takarda fa ka dauko Usman, yanxu baxa ka bata hakuri ba Usman" Hajja ta mike sai safa da marwa take fuskar nan nata a murtuke take cewa "Wllh baxan hakura ba kar ma a bani" Abba babu yanda ya iya haka ya rubuta takardan yana kallon Aunty xai ajiye a gabanta Hajja ta fixge ta kai ma Umma tace "Karanta min Ramlah" Umma ta amsa tana kallon takardan tace "Na sake ki saki daya" Sai da gaban Ummi ya fadi sosai ta dinga kallon Abba, Hajja tace "Shkkn haka ya sa?? To uban wa ya saka?" Umma tace "Haka aka sa" Hajja ta mayar masa tace "Rubuta Hafsah a gaba" Abba ya amsa ya rubuta sannan ya mika mata, kin amsa tayi tace "Aa bata da hannunka ba ruwana kar ta kai ni gaba tace ai ni na mika mata takardan ma" Abba ya ajiye ma Aunty takardan yana kallonta, ta dauka tana dubawa, wani murmushi tayi tana gyada kai ta goge idonta ta kalli Ummi da Umma sannan ta mike fuuu ta wuce bangarenta sunan Jiddah na mata yawo a kai...., Hajja tace "Sai a tafi a fara harhada kaya kuma a koma benue, Allah ubangiji ya saka ma Hauwa duk cutarta da kika yi" Mikewa Abba yayi xai bar parlon Hajja tace "Dawo malam" ya dawo kuwa, tana tafe hannu tana kallonsa da kyau tace "Aliyu kuma da ka sa a baki sai ya saki baiwar Allah har da rantse rantse to ka cire ido a kansa, rantsuwan da kayi kuma daga gobe ka fara daukan axumi don Aliyu ba shi da matar kirki da ta wuce Jiddah ita din alkhairinsa ce, yo kayi axumi sittin ma ranan da ka hallaka wani bawan Allah da mota a hanyar Abuja balle uku kacal? To tun wuri ka fara axuminka bakin ka alekum, ita kuma wannan mata ta Aliyu Nanisa take ko wa?? ni da Ramlah kadai muka san yanda xa ayi da ita wllh, yanxu ma police station din xan bi ta mu tafi" tana kai wa nan Abba ya mike ya bar parlon ta bi sa da wani shegen kallo, snn ta kalli su Alhaji Lawal tace "Duk na sallameku, a nemi me rufe mana taro ku koma garin ku" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Ina mata ma'abuta gyaran jiki kuzu ga supplement na gyaran jiki kala muna da supplement masu sa haske da laushin fata da gyaran jiki da maganin sanyi da masu kashe kuraje da tanbo ku Wani kalar supplement muna da cikin sauki da rahusa kadan Daga cikin su Lady capsule Royal jelly Sugar wanita Khusus Vitamin e Cantik ayyu Puspa ayyu Dara Rapit wanita Maca capsule Reload Papaya Collagen snail Flat tummy Sliming capsule Da sauran su domin neman Karin bayani atuntube wanna number 08066726866 mmn mujaheedUmma bata kara ko minti daya a gidan ba ta yi wucewarta gidanta ranta fess, bata ta6a jin Hajja ta burgeta irin yau ba, tana xaune parlonta bayan ta idar da magrib kenan Ahmad ya shigo tare da Abuturrab, tayi masu kallo daya ta ci gaba da jan carbinta, Ahmad ya xauna saman carpet yana shafa kansa, Abuturrab ya xauna saman kujera yana kallonta, Jin duk sun ki cewa komai ta kallesu tace "Wai ya aka yi ku ka xauna min jigum jigum a gabana? Lafiya" Ahmad ya sauke kansa a hankali yace "Umma don Allah kiyi hakuri ayi abinda ya kamata, Umma all this...." Umma ta katse sa tace "Inyi hakuri ayi me?" Ahmad yayi shiru, Abuturrab dai sai kallonta yake, ta girgixa kai tace "Kun ga ku fita harkata wllh, ku fita harkata kar in maku rashin mutunci, ku kun isa ku gaya min abinda ya kamata inyi?" Sallama aka yi bakin kofa, Ahmad ya juya, Nafisah ta shigo parlon ta karaso ta xauna ta gaida Umma sannan tace "Umma wai kawu Lawal xa su yi magana da ke a waje" Umma ta ta6e baki kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Toh sai su shigo" Nafisah ta mike ta fita, Bayan few minutes Alhaji Lawal da Alhaji Umar suka shigo parlon, xaunawa suka yi saman kujera Ahmad ya gaishesu, Abuturrab ma ya gaida su ya mike ya tafi bedroom din Ahmad, Ahmad ya mike ya bi bayansa, Hakuri Alhaji Lawal suka dinga ba Umma tayi hakuri ta janye case din da ta kai police station na Aneesah, Umma ta saki baki tace "Wato dai ana nufin banxa kawai ta doka kenan?" Alhaji Umar yace "Aa bata doki banxa ba, amma ta ci darajan masu daraja, sannan shi Aliyun dole xai dau matakin da ya kamata a kanta, ba ido xa a xuba mata ba...." Umma ta kasa ce masu komai don tana jin nauyinsu ainun, ita dai ta san da Abba ne bai isa ya sa ta janye case din nan ba, ganin ita suke saurara ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh a gaskiya sai ta xo har gidan nan ta ba Jiddah hakuri, sannan sai ta rubuta statement a station cewar ko kallon banxa baxai kara hadata da Jiddah ba" Alhaji Umar yace "Ai wannan ko baki fada ba doka ce, dole yan sanda sai sun sa ta rubuta statement din" Mikewa Umma tayi ta wuce dakinta ta dauko jaka da wayarta, ta fito ta shiga dakin Ahmad tana kallonsu tace "Ka fito ka wuce da mu station Aliyu" Ahmad ya kalleta yace "Umma kin manta patient ne shi?" Umma tace "Eh ban manta ba amma ya taso ya kama gabansa, kai kuma ka xo kayi driving dina" Daga haka ta juya ta fita, Ahmad ya d'an yi murmushi ya mike ya nufi kofa, Abuturrab ya tashi shi ma ya fita, Su Alhaji Lawal suka fara fita parlon Umma ma ta fita, Abuturrab dai na tsaye, Ahmad ya gane dakinsu Maimoon yake son shiga, shi dai bai ce masa komai ba ya nufi kofa, Abuturrab ya shafa kansa yana bin sa da kallo, Har Ahmad ya fita ya juyo da sauri ya kalli Abuturrab yace "Umma.. she is coming back" Ko rufe baki bai yi ba Abuturrab ya bi sa shi ma... A motar Umma suka tafi police station din, su Alhaji Umar kuma na tasu motar. Abuturrab ya kulle kofar parlon bayan ya shigo yana kallon Aneesah da ta wuce sama fuuuu kamar xata tashi sama, Calmly yace "Hey you, listen to me!!!" Kamar jira take ta dawo da sauri ta nufesa ta cakumo kwalarsa tana xaro ido tace "Me xaka ce min Aliyu?? Gaya min me xaka ce min?? Nace me xaka ce min??" Sai kuma tayi wani murmushin takaici tace "Ni kayi ma kishiya, kishiyar ma me tallan awara a hayin rigasa? Ni Aliyu? Hakan kuma bai isheka ba kai da iyayenka ku ka kulleni a cell a kan matsiyaciyar yar talakawa??" Sai kuma tayi wani dariya ta sake sa ta koma baya tana tafe hannu tace "Toh ni kuwa xan ga ta yanda xa ku yi xaman aure da ita, xan ga ta yanda xaka xauna da ita a matsayin matarka, xan ga ta yanda hakan xai faru...." Safara'u ce ta sakko kasa da saurinta jin shigowarsu da hayaniyar Aneesah, tana huci ta nufesa ta sauke masa mari me kyau cikin daga murya tace "Da hadin bakinka har xa a je a kulle 'ya ta a cell don ta doki wata banxa can mara galihu? A kan wata banxa ka amince aka ci mutunci matarka har gidan yan sanda? To wllh wlllh sai ka san ka mika Aneesah hannun hukuma sun tafi da ita police station, xaka san ka kai er mu station, wnn case din yanxu aka fara shi Aliyu..." Abuturrab ya dinga kallonta babu ko kiftawa trying hard to control his rising Temper, tafiyar da ya ji a stairs ya sa shi daga kai, ya ga Aunty ce ke saukowa cike da isa da gadara tana masa wani kallo, ita ma ya dinga kallonta har ta shigo parlon, tayi wani murmushi tana nuna sa da hannu tace "Aliyu xaka san ni Hafsah ka munafurta, i will mercilessly deal with u, xan nuna maku ku kananun kwari ne daga kai har uwarka da tsinanniyar kanwar uwarka, yanda uwarka da kanwarta suka sa na fita dakina na kwana daya kacal, yess na kwana daya ne kacal don babu uban da ya isa yyi terminating xamana a gidan nan don xuwa gobe matsayina still dai dai yake da na uwarka a cikin gidan nan, to haka ita ma xan sa ta fita gidan na har abada, sai xaman gidan ubanka ya gagareta wlh, kai kuma xan ga abinda xai sa kayi rayuwar aure da Jiddah a duniyar nan...." Sai kuma ta kalli Aneesah tace "Ki kwantar da hankalin ki Aneesah, Aliyu ya shigo da Jiddah gidan nan su xauna a sunan mata da miji mu ga, ta tare mu ga ta yaya" Safara'u tayi wani dariya kamar mahaukaciya tace "Ashe bashi da labarin ba a mana kishiya ne, ba shi da labarin mu daya muke rayuwa gidan miji har mutuwa, to kai da xama da mata biyu sai a lahira idan ana yi" Abuturrab na kallon Aneesah strictly yace "First thing tomorrow morning ki kwashi kayanki ki kama hanyar gidanku na sake ki Aneesah" Daga haka ya juya ya fice daga gidan without closing d door, xaro ido Aneesah tayi, tayi still a wajen kamar me son fahimtar kalman da ya furta, lkci daya ta dafe kirji jikinta ya dau rawa tace "Aunty ban gane me yake nufi ba, me yace ne wai?? Ku min bayani don Allah Aunty" Daga Safara'u har Aunty dama bude baki suka yi suka bi sa da ido ko wannensu with shock, Safara'u ta kalli Aunty da idanuwanta kamar xa su yi magana tace "Hafsah ashe dama d'an ta'adda kika hada aure da yar mu?? Hafsah kin san su waye familyn mu kuwa??" Wani kara Aneesah ta saki ta cakumo Aunty ta runtsa ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Aunty ji nayi kamar yace ya sakeni, ko ba haka yace ba??Ji nayi yace ya sakeni...." Ta kuma rusa wani ihu tace "Na shiga uku na lalace..." sai kuma ta sulale nan kasa a sume.... Bayan kwana uku, Umma na xaune dakin Ummi dake gefen gado a xaune, xuwanta gidan kenan amma bata ji dadin yanayin da ta tarda yayartata ba, ko bata fada mata ba ta san tana tare da damuwa da rashin kwanciyan hankali ne sosai, don har ta fada, Umma tace "Yaya na baki shawara na baki shawara kin ki dauka, wllh wllh yaya ki ajiye batun wannan mutumin a gefe, ki ajiye batunsa yaya, kar ki je wani cutar ya kama ki a bar ki da wahala, to wai sai me in Alhaji Usman ya fita harkanki? Abinci ne babu ko sutura ne babu? Sai me don Allah, nace maki ki debi kayanki mu tafi can gidan nawa ki huta na kwana biyu kin ki, idan ma baki son xaman gidana ne ki wuce Adamawa kawai mana, ga ki da yan uwa birjik dake marhaba dake kin tsaya takaicin namiji xai kashe ki yaya??" Ummi tayi murmushi tace "Kenan banyi appreciating duk kokarin Hajja a kai na ba, ai baxata ji dadi ba idan nace xan tafi tunda nasan har yau a bayana take kuma tana kan bakanta, ni damuwata Ramlah abinda mutanen gari suke fada a kan batun nan, Hafsah ta wuce tunaninki wllh, barin yanda take da shige shigen mutane kaf anguwar nan babu inda ba a santa ba, babu inda bata shiga, shi Usman Hajja ta sa ya saki Hafsah wai duk a kai na kamar yanda ake cewa, sannan shi kuma Aliyu kinga aika aikan da ya tafka, ance kuma ni na sa shi ya aikata hakan, to duka duka yaushe ya auri yarinyar da har xai saketa Ramlah? I am really confuse, na kirasa sai yace min ai ya koma aiki baya kaduna, to ya xan yi, har nan kanwar uwarta ta xo ta mana tijara da rashin mutunci har tana ikirarin xa mu gani ta kuma ci sa'an Hajja taje gidanki ranan, ni dai har ta gama ina xaune parlor bance mata komai ba, wato yanda na fitar da kishiyata shine na sa d'a na ya saki er su sbda mugun hali, kinga Ramlah duk wani abu na damuwa bana sonsa wllh kasa bacci nake, ni bani da wata matsala da Usman a yanxu, don da can din ma ai kusan a hakan muke xaune da shi, ai wnn ba sabon abu bane na saba, kawai yanxu abinda Aliyu yayi ma Aneesan ne ya tsaya min yake damuna" Umma ta kyabe baki without showing any concern tace "Ji yaya fa da wata magana, mutum xai yi ta rayuwa da abinda ke cutar da shi ne? Aliyu fa ya ga baxai iya xama da ita bane ya saketa to me yasa xa a ga laifinsa tunda ba wani ke xaunan masa da ita ba, sannan ya gaya min duk tijaran da kanwar uwarta da Hafsah suka je can gidan suka yi masa na kuma gaya maki, toh me yasa xaki damu kanki a kan yan iska? ba a farin ciki da saki amma wllh wllh nayi farin ciki da sakin wnn yarinya da yayi ko don Hafsah, Allah da ba don Hafsah dake cikin lamarin auren dumu dumu ba ni me tausansa ne ya maida matarsa amma duk wani abu da ya fito daga bangaren Hafsah bama fata mu kara kusancinsa in sha Allah, iyaka dai yanxu ya gama xagaye xagayensa ni kuma in gama gwara kansa idan Jiddah ta xana waec sai in basa ita ba don ya cancanta ba sai don bakin ciki da takaici ya kashe wasu" Ummi tace "Mu ma muna da 'ya ya matan nan fa Ramlah ki daina cewa haka..." Umma tace "Lallai yaya, ai mu ba mu watsar da tarbiyanmu ba, kuma in sha Allahu mun san mun ma ya yan mu tarbiyan da xa su iya shiga ko ina su xauna lafiya... Kin ga ni mu bar wannan xancen ba ruwana ni baxan tilasta Aliyu yayi abinda xai cucesa ba, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi, ita kuma taje can Allah ya bata wani" Ummi bata kuma ce mata komai ba amma ko kadan bata gamsu da bayanan Umma ba. Tun bayan da Abuturrab ya saki Aneesah ya samu relieve ya daina jin komai na damunsa a rayuwa, ji yayi kamar wani kaya dake piercing dinsa aka xare masa, kusan ko da yaushe a kashe xaka ji wayarsa sbda kira uku da yake ignoring, na farko kiran Aneesah da take masa babu kakkautawa da text messages iri iri wanda baya dubawa, na biyu kuma kiran Ummi don yasan dalilin kiran nata, sai kuma kiran Aunty da ita baya ma son sanin dalilin kiran nata, da suka sauke jirgi Abuja bai yarda ma yaje gidansa ba don kada Aneesah ta bi sa duk da bai san ko tana Abuja ko kadunan ba, ya gwammace yayi xamansa hotel har sanda xa su daga jirgi xuwa kano, ranan Friday ya shigo garin kaduna, direct gidansu ya nufa sanin Abbansa na gari, ganin motarsa a parking space ya sake tabbatar masa da Abban nasa na garin, bayan ya shiga main parlor din gidan ya tafi bangaren Ummi, Aisha dake parlor a xaune tace "Ummi bata nan" ya kalleta yace "Ina ta je?" Aisha tace "Nima ban sani ba sun fita ne tare da Hajja" Bai ce mata komai ba ya tafi parlon Abbansa, kallo daya Abba yayi masa ya ci gaba da danne dannen laptop dinsa, ya xauna kasa ya gaishesa, Abba ya amsa a takaice without looking at him, Abuturrab yayi shiru, bayan few minutes Abba ya juya ya kallesa yace "Any problem? Na ga ka xauna min" Abuturrab ya girgixa masa kai amma kuma bai tashi ba, Abba ya ajiye laptop dinsa yana kallonsa da kyau yace "Ita uwar taka ce ta sa ka saki matarka ko???" Abuturrab ya kallesa da sauri yace "Not at all Abba, wllh she knows nothing about it...." Abba yayi wani murmushi yace "Dama nasan xaka kareta ai, sbda kai ka maida saki abun banxa abun hofi, Sbda uwarka ta xugaka domin kuyi tarnishing din Image din Hafsah a gun iyayen yarinyar tunda kasan akwai alaka me karfi tsakaninta da iyayen yarinyar, to u are a liar Aliyu, i birth u...." Abuturrab ya sauke boyayyen ajiyar xuciya a hankali yace "Abba threatening dina suke yi ita da aunt dinta, i have no option a lkcn, the aunt even went ahead and slapped me...." Abba na kallonsa strictly yace "Toh ni ubanka nace ka koma yanxu ka maida matarka..." Abuturrab ya daga kai da sauri ya kalli Abba, Abba ya hade rai yace "Yes that is my instruction, and u have to do so immediately" Abuturrab ya kasa ce masa komai lkci daya duk jikinsa yayi sanyi, Abba yace "Get out, and i am giving you from now till d end of this week" Da kyar Abuturrab yace "Toh Abba" daga haka ya mike ya fita daga parlon yana jin xuciyarsa na tafarfasa, gidansa kawai ya wuce direct duk da yayi niyyar xuwa gidan Umma. Har aka kira Magrib yana kwance daki, daga karshe ya fita masallaci bayan an idar ya dawo yana xaune gefen gado ya kunna wayarsa don kiran Ahmad, yana kunnawa sai ga kiran Aneesah, jefa wayar yyi a gefensa har ya katse ta kuma kira, sai da ta kira yayi sau hudu sai kuma text suka biyo baya, daukan wayar yayi a karo na farko ya buda text dinta da suka fi 50, gaba daya text din ban hakuri ne da rokon baxata iya rayuwa babu shi ba ya yafe mata, duk text din are full of remorseful words, har da cewa ita ta yarda ta amince xata xauna da kishiya don Allah yayi mata rai ya maidata dakinta, tsaki ya ja yana jin xuciyarsa na tafarfasa, ya mike daga karshe ya dau car key dinsa ya fice daga gidan, kofar gidan Umma yayi parking ya shiga ciki, minti daya yayi tsaye bakin kofar parlon sannan ya bude ya shiga, Hajja ce xaune parlon tayi rashe rashe abunta ga kulolin abinci sun fi hudu, Jiddah na xaune kusa da ita tana yanka mata lemo, ta daga kai suka hada ido da shi, lkci daya ta sunkuyar da kanta, he don't know all of a sudden sai yaji duk ya nemi damuwar da ya addabi xuciyarsa ya rasa, walking slowly ya karasa cikin parlon ya xauna saman kujera Hajja dake ta kallonsa ta rike kai tace "Kaii Allah ya rabamu da duk wani abu dake cutarmu a rayuwa, jama'a ku dubi yanda Aliyu yayi kyau yayi fess da shi daga rabuwa da kazama, ku dubi Aliyu jama'a..." Kwafa tayi tace "Kaji tsoron Allah kaji tsoron kazanta, kazanta ba kyau, Allah ka ci gaba sa nisanta mu da kazami" Jiddah dai yanka lemon hannunta kawai take, Hajja ta washe baki tace "Sannu da xuwa Aliyu ina yini" Ya ajiye wayarsa da yake dubawa yace "Ina yini?" Tace "Lafiya lau wllh, yanxun nan Hauwa ta bar gidan nan tun safe muke nan tare da ita" Shi dai Jiddah kawai yake kallo, Hajja ta mike tace "Toh bari in je in kira maka Ramlan yanxu ita ma ta shiga ciki bayan yayar ta wuce, baka ga uban tuwon da ta narka ba a nan, ita ko tsoron kibanta bata yi, ni dai na gaji da magana na ja bakina nayi shiru, tunda ba ni xa a kai asibiti hankali tashe ba" Jiddah ta kalli Hajja da sauri tace "Hajja in kirata?" Hajja tace "Aa ba ruwana bari in je da kai na meye amfanina" Daga haka tayi hanyar dakin Umma, Jiddah ta ajiye wukar hannunta a hankali, shi dai kallonta kawai yake, tana jin Hajja ta bude kofar Umma ta mike xumbur kafin ta bar wajen yayi saurin tashi ya rikota, marairaice masa tayi tana kalle kalle kamar munafuka tayi kasa da murya tace "Don Allah ka bari, wllh yanxu Umma xata fito parlon..." Mayafin da ya gani a kan kujera ya dauka ya mika mata taki amsa, bai sake sauraronta ba yayi hanyar kofa da ita, ta xaro ido tace "Na shiga uku, meye haka don Allah ka sakeni" _Not edited_ *Sorry for the late update fans* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you Ina mata ma'abuta gyaran jiki kuzu ga supplement na gyaran jiki kala muna da supplement masu sa haske da laushin fata da gyaran jiki da maganin sanyi da masu kashe kuraje da tanbo ku Wani kalar supplement muna da cikin sauki da rahusa kadan Daga cikin su Lady capsule Royal jelly Sugar wanita Khusus Vitamin e Cantik ayyu Puspa ayyu Dara Rapit wanita Maca capsule Reload Papaya Collagen snail Flat tummy Sliming capsule Da sauran su domin neman Karin bayani atuntube wanna number 08066726866 mmn mujaheed Suna fitowa compound Abuturrab ya mika mata veil din hannunsa yace "Sa mayafin ki nace" ta marairaice masa tana xare manyan idanuwanta tace "Ina xan ce ma Umma na je yanxu, wllh tana dakinta plss ka sakeni in koma ciki don Allah" Bai sake jiran ta saka mayafin ba ya nufi gate da ita still holding her hands tana son kwacewa amma ta kasa, pleadingly tace "Na shiga uku, to don Allah ka jira in koma ciki in dauko takalmina wannan ba nawa bane..." Dariya ta basa, bai kuma tanka ta ba har suka isa gate, taji kamar ta nutse sbda mai gadi dake xaune bakin gate yana kallonsu, shi kam Abuturrab ko a jikinsa ya fita kofar gida da ita ya bude front seat yana kallonta yace "Get in..." Sai a snn ta fashe masa da kuka tace "Wai me yasa kake min haka ne don Allah, kaga fa karfe nawa kuma nace maka Umma na ciki...." Bata karasa ba ta shiga motar da sauri tana matsar kwalla ganin daukanta yake shirin yi ya sakata cikin motar da kansa, yayi wani murmushi ya kulle motar da lock don kamar ya san kafin ya karasa daya side din xata bude ta gudu, tana kokarin budewa da sauri kuwa taji motar a kulle, hakan yasa ta kuma rushewa da kuka tana kallonsa har ya shigo motar ya kulle, tada motar yayi ya bar layin, hankalin Jiddah ya tashi sosai a lkcn, babban damuwarta Umma, bata san me xata ce mata ba, bata ma san da wani idon xata kalleta ba yanxu, bayan sun hau saman titi ta kwantar da murya pleadingly tace "Don girman Allah kar ka min haka, ban san me xance ma Umma ba wllh, I don't know what to say to her, ina kake son ince mata naje da daddaren nan yanxu" yana kallon titin gabansa speaking calmly yace "Sai ki ce mata mijin ki ne ya daukeki, ko laifi ne idan miji ya tafi da matarsa??" Ta xaro ido tana kallonsa xuciyarta na bugawa, Jiddah ta rasa abinda xata ce masa, kawai sai ta hau goge hawayen da ya ki tsaya mata tana nanata abinda ya fada a ranta, wai mijinta, sai yanxu xae iya kiran kansa da mijinta??? horn yayi bakin gate din gidansa mai gadi na bude gate din ya shiga yayi parking a parking lot, duk da Jiddah tasan Aneesah bata gidan hakan bai sa gabanta ya dinga faduwa tana kallonsa hankali tashe ba, bayan ya kashe motar ya juya yana kallonta kasa kasa... cikin rawan murya ta hade hannunta tace "kar ka min haka don Allah nake rokon ka, ba don halina ba ka maida ni gida, ban san me su Umma xa su yi tunani ba da Hajja don Allah ka rufa min asiri ka kai ni gida plss" ya dauke kai ya bude motar yace "Ko ma me suka yi tunani dai dai ne, mijin ki ai kika bi ba wani ba..." wani irin kallo ta dinga masa don haushi kalmar yake bata, wai mijinta, bata san lkcn da ta dake fuska daure tace "Ta ina ka xama mijina?" Juyawa yayi ya kalleta kamar baxai ce komai ba, sai kuma yace "Mu je to in gaya maki ta ina" Yana fadin haka ya sauka sannan ya xaga ya bude side dinta yana kallonta, a hankali ta fara kuka ta rufe fuskarta da hannunta cikin sanyin murya tace "Don girman Allah ka maida ni gida Yaya" Ya dinga kallonta babu ko kiftawa, sai kuma yayi murmushi yace "Kin iya cewa yaya kenan, ni na xata Aliyu kadai kika iya fadi" Bai jira cewarta ba ya kama hannunta ya sauko da ita daga motar ya kulle motarsa, sai a sannan Jiddah ta fara kukan gaske tana biye da shi yana rike da hannunta har suka shiga parlorn gidan, ya kulle kofar ya sa makulli ya saketa yana kallonta, ta sunkuyar da kanta tana share hawayen dake xuba idonta, she looks so afraid, wucewa yayi sama ya bar ta a wajen, ta fi minti biyar a tsaye sannan ta karasa cikin parlon tana tafiya kamar me counting steps dinta, ta karasa tana kallon kujera ta xauna a hankali, tsadadden carpet din dake tsakar parlon duk yayi wani dusu dusu da shi, da ido ta dinga bin parlon da kallo, wani sai yace kayan parlon ya shekara biyu, ko kuma da akwai yara a gidan, Jiddah na ta xaune har karfe takwas da rabi ya gota, tagumi tayi xuciyarta cike fal da fargaban abinda su Umma da Hajja xa su ce, bata ma san da wani idon xata kallesu ba, furucin Hajja a hospital ne ranan ya fado mata da take gaya ma Aneesah, sai taji gabanta ya fadi sosai, saukowa yayi parlon sanye da jallabiya, ta daga kai da sauri tana kallonsa, kana ganinsa kasan wanka yayi, ya nufeta ya xauna gefenta, ta rike numfashinta sbda kamshin turarensa da ya cika wajen, xuciyarta na bugawa ta matsa a hankali ta bar space a tsakaninsu taki yarda ta kallesa, shi dai kallonta kawai yake, sai kuma yayi kasa da murya yace "Xa ki iya girki yanxu?" Ta d'an kallesa suka hada ido, sunkuyar da kanta tayi tace "Girkin me?" Yace "Something light, i haven't taken anything since afternoon" A hankali tace "Toh" yace "Ko in fita in siya?" Ta girgixa kai ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Xan yi, amma idan na gama xaka maida ni gida?" Ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Nan ba gida bane?" kamar xata fashe da kuka tace "Ba gida bane" Yana kallonta babu kiftawa yace "Toh xan maida ki" Ta kallesa ta marairaice tace "Kayi alkawari?" Ya dage girarsa sama yace "Sai kin gama girkin xan yi wannan alkawarin" tace "To akwai kayan miya?" Ya langwabar da kai yace "Sai dai mu je mu siya yanxu" Ta xaro ido tace "Lokaci xai wuce ai, ji karfe nawa fa" Yace "Aa... bakin hanya ne ai, ba nisa" Tayi shiru kamar me naxari, mikewa yayi ya nufi stairs ta bi sa da kallo babu ko kiftawa har ya haura sannan ta sunkuyar da kanta, ba a dau lkci ba ya dawo da makullin motarsa yace "Mu je" Ta mike ta dau gyalen da ya ajiye saman kujera sannan ta bi bayansa suka fita, kayan miya ya siyo har da Irish da crate din kwai, with beverages... Ita dai Jiddah kallonsa kawai take bata ce komai ba, ya shiga shopping mall ya siya yoghurt me tsada da bread, ita dai tana mota tana jiransa, yana fitowa ya shiga motar suka fita mall din, ya tsaya gun masu siyar da gasasshen kaza a hanya ya siya sannan suka wuce gida, suna isa bakin gate Jiddah ta kallesa innocently tace "Toh ka bar motar a waje ba sai ka sake fitowa da shi ba idan xaka maida ni" ya kalleta yace "So kike a sace min mota?" Tayi shiru tana kallonsa, horn yyi mai gadi ya bude gate din ya shiga ciki yayi parking, xata debi wasu daga kayan da ya siyo yace "Aa yi wucewarki ciki xan dauka" Tayi shiru tana kallonsa, ya dau wasu daga ledojin yace "Ki tafi nace" A hankali ta fara tafiya har suka shiga parlon, ya ajiye kayan ya koma ya dauko sauran, ledan kayan miyan ta dauka ta wuce kitchen din. Tsaye tayi tana tunanin light food da xata girka da baxai dau lkci ba, ta dinga bin kitchen din da ya d'an yi k'ura da kallo, a hankali ta shiga store ta duba me da meye a ciki, ledan cous cous guda daya ta dauko ta fito, tana kokarin diban kayan miya a bowl jikinta ya bata kamar ana kallonta, ta juya da sauri suka hada ido da shi, yana tsaye jikin kofar ya rungume hannunsa yana kallonta, a hankali yace "Ki dafa ruwan shayi kawai ki soya min kwai, i will take tea and bread..." Tace "Girkin fa?" Yace "Aa.. do not stress ur self, it's already almost late" tace "Ae xan iya, nan da 20mins" yayi kasa da murya yace "Sae kiyi min gobe da safe" Ta kallesa da sauri tace "A ina?" Yyi murmushi yace "Gidan Umma" Bata ce komai ba ta shiga daura ruwan shayin da yace a gas, juyawa yayi ya bar kitchen din, ta duba kitchen din bata ga ko alamar kayan kamshi, mamaki ta dinga yi ganin ko spices da kayan maggi babu, to da xata yi girkin ma da me xata yi amfani? Matar gidan bata girki kenan?? ta tabe baki ta tafasa ruwan Lipton din kadai, ta dau mug da plate, ta wankesu da cokali da tray duk ta tsane sosai, snn ta wanke fry pan ma, cikin mintuna kadan ta soya kwan ta juye a plate sannan ta xuba ruwan lipton dake tafasa a cikin mug din ta daura a kan tray din da cokali ta dauka ta fita, bata gansa a parlon ba ta ajiye tray din saman carpet ta tafi ta dauko kayan shayin da bread sannan ta dawo ta ajiye ta xauna kan kujera, bayan minti goma bata ga ya sauko ba, ga ruwan shayin dake a bude xai huce, kallon stairs tayi sai kuma ta mike tana tafiya a hankali har ta wuce sama, ta rasa me yasa in dai ya shigo gidan nan memories iri iri ke dawo mata, tana ta tsaye corridor din rooms din na kusan minti uku kafin ta nufi part dinsa kamar bata son tafiya, a hankali ta murda kofar parlon ta leka ciki ya daga kai ya kalleta ta sunkuyar da kai tace "Na gama tun daxu" ya ajiye remote din hannunsa yace "Me yasa baki kawo upstairs ba, I don't eat downstairs" tayi shiru tana kallonsa, yace "Or?? In sauko?" ta girgixa kai tace "Xan dauko" daga haka ta juya ta wuce, ta tafi kasa ta dauko masa abincin ta kawo ta durkusa ta ajiye gabansa sannan ta koma ta dauko kayan shayin da bread su ma ta ajiye, yana kallonta yace "Why just a cup?" Ta girgixa kai tace "Ni baxan sha ba ai" ya mike yace "Jirani" daga haka ya fita parlon, tana dai durkushe har ya dawo da wani cup da ya wanke with plate da ledan gasasshiyar kaza, ya raba ruwan shayin into equal two ya xuba madara da milo with sugar cubes, ya juya da cokali ya ajiye mata daya a gabanta yana kallon eyeballs dinta, ta kalli agogo kamar xata yi kuka tace "Karfe tara ya wuce fa yanxu" yace "Kuma kike bata ma kanki lkci" bai jira me xata ce ba ya juye kazan a plate ya ajiye mata gabanta yace "You had better start eating and stop wasting ur time don idan baki ci ba baxan maida ki gida ba..." ko rufe baki bai yi ba ta dau tsoka daya na nama ta fara ci a hankali, idan ta ci sae ta dau shayin ta sha kadan, duk yanda yayi da ita ta ki cin bread din da kwai wai ta koshi, lkci lkci take kallon agogo don duk hankalinta baya tare da ita, har dai ta shanye shayin ta jingina da kujera tana jiransa ya gama, kamar bai son ci abincin yake ci, sae yayi minti biyu xuwa uku yana kallon Tv kafin ya ci gaba da ci, tayi narai narai da ido a hankali tace "Kai fa nake jira, ko in sauka kasa in jira ka?" Ya kalleta yace "Kike jirana ayi me?" Ta xaro ido tana kallonsa tace "Toh wa xai maida ni gida?" Yace "Oh that?" Tayi shiru tana kallonsa xuciyarta na bugawa, yace "Toh bari in gama inyi wanka" hade kai tayi da gwiwa wani hawaye ya taho mata, mikewa yayi ya isa kofar ya sa makulli ya cire snn ya shiga bedroom, tun Jiddah na ta zaune tana jiransa har ta gaji ta mike tana kallon agogo dake nuna karfe goma da minti talatin, ta fashe da kuka ta nufi dakin ta tsaya bakin kofa ta bude a hankali tana kallon ciki, kwance ta gansa yayi rub da ciki idonsa lumshe, goge hawayen dake xuba idonta tayi ta juya ta koma parlor, gajiya tayi da xama ta kwanta saman kujera ta takure waje daya ta rufe idonta nan da nan kuma bacci ya dauketa don da gida ne ita tuni tayi bacci ma.... Karfe sha biyu Abuturrab ya tashi ya fita dakin ya dawo parlor, kallo daya yayi mata ya dauke plates din abin da suka ci ya nufi kofa ya bude ya sauka downstairs ya kai kitchen, kayan shayin da bread kawai ya bari a parlonsa, ya dawo ya shiga daki ya bude press ya dau bedsheet dinsa da duvet ba na Aneesah ba, har ya fita ya dawo ya dau hijab din Aneesah dake a goge, sannan ya tafi wani dakin ya shimfida xanin gadon bayan yayi dusting din ko ina ya dawo clean, fita yyi ya koma part dinsa, ya nufi Jiddah dake bacci, dukawa yayi yana kallonta, doguwar riga ne jikinta me sharashara amma ba sosai ba don ba a ganin jikinta, What a sleeping beauty, ya fi minti daya yana kallonta bbu ko kiftawa, bayan few seconds ya lumshe ido ya dauketa kamar Baby ya nufi kofa, a gigice ta bude ido tace "Na shiga uku, mene haka?" Bai tankata ba har ya fita dakin, bakinta na rawa tace "Don Allah ka ajiyeni ba bacci nake ba, i will walk with my feet, pls ka ajiyeni" har suka shiga dakin da ya gyara bai ce mata komai ba ya tafi ya kwantar da ita saman gadon a hankali yana kallonta, ta kasa kallonsa balle su hada ido, yyi kasa da murya yace "Kina son xa kiyi wanka?" Da sauri tace "Aa na yi a gida" yace "Toh ban ga kinyi sllhn isha ba, and u didn't wash ur teeth after eating..." Gaba daya a rikice take, tace "Nayi fa" yace "A ina?" Ta rasa abun cewa yace "Je kiyi alwala yanxu" sauka tayi kan gadon ta wuce bandaki da sauri, ya bi ta da kallo kamar yasan abinda xata yi ya mike da sauri ya bi bayanta tana kokarin saka makulli ya tura kofar ya shiga bandakin, ta fashe da kuka ta marairaice masa tace "Alwalan fa xan yi ka shigo" yace "Yi ina kallonki" ta rasa ma abinda xata ce masa, gaba daya a tsorace take da shi sae xare ido take, cikin rawan murya tace "But i want to ease my self" yana kallonta da kyau yace "Ai ban hanaki ba" Alwalan ta fara yi, gaba daya a rude take, shi dai yana kallonta har ta gama ya bata hanya ta fita sannan ya fita shi ma, hijab din ya dauka ya mika mata ya shimfida mata darduman, ta amsa ta saka hijab din, ya koma gefen gado ya xauna yana kallonta, sai kuma ya mike ya kulle kofar dakin, da bathroom duk ya cire keys din ya ajiye karkashin pillow, yana ganin ta idar da sllh ya kashe wutan dakin ya kwanta hade da lumshe ido, hawaye ne ya shiga sauka idonta tana xaune kan darduman, daga karshe ta kwanta ta takure waje daya, cikin bacci taji ya dauketa ya kwantar saman gado ya cire mata Hijab din jikinta ya rufa mata duvet, ya manna mata soft kiss a cheek dinta, ita dae runtse ido kawai tayi xuciyarta kamar xai fito kirjinta don tsoro, tana jin sa ya kwanta close to her ya cire mata hulan kanta ya xare ribbon din gashinta, a haka dae bata san lkcn da bacci ya sake dauketa ba.... Hajja ce rakube jikin kofar dakin Umma dake waya da Ummi inda take shiga ba ta nan take fita ba bayan ta sanar ma Ummi abinda Abuturrab yayi jiya, lkci daya Hajja ta tura kofar da karfi ta shiga tace "Huhuhu ke dai daga baxawara a fitina sae ke Ramlah, Ramlah ya xaki sa yaron mutane a bakin duniya haka tun jiya, daga dai ya xo ya dau matarsa, kika san aikin da yake so ta masa da ya tafi da ita tunda ita wancan ballagazar kazama ya saketa har saki uku? Matarsa ce fa ta sunna wa enda suka shaida kuma sun shaida, kai wannan mata da a Masar ne da an je an duba kwakwalwarki, mata tun jiya kin ishemu da mita ko baccin kirki baki bar mu mun yi ba wai Aliyu ya dauki Jiddah kaman wanda ya sace ta, Haba Ramlah!! Kawai daga tashi yau kin kama waya kin doka ma Hauwa kira, to me Hauwar xata yi? Ku dai wllh bakwa tsoron Allah ke da er uwarki, yaro dai da matarsa ta sunna ku bi ku sa masa ido kamar wanda yayi karuwanci, tirrrr da halinku wllh" Umma ta katse wayar hannunta fuskarta a murtuke tace "Don ubansa ni nace na basa Jiddah ne da xai dauketa ya tafi, ina ruwana da komawarsa da yayi aka sake masa aure?? Sannan kin xo kina wasu maganganu...." Da sauri Hajja ta katse ta tace "A'a... Ba tashin hankali bane Ramlah, kawai tunasar maki nake cewa matarsa ce ta sunnar ma'aiki ba wani abu ba, kilan yan gyare gyare xai sa ta gidan yayi k'ura tunda kinsan gidan ba kowa shi kuma yau ya dawo daga tukin jirginsa..." Umma ta ki tankata tana danna wayarta fuska daure, juyawa Hajja tayi ta nufi kofa murya can kasa tace "Ke dai ki rage fitina ko wannan kiba taki xai sa6e ki dawo mutum, fitina kadae ya isa ya dinga hura mutum ba sai abinci ba, amma ke kuwa fitinarki yayi yawa wllh, wannan ma nasan don kina jin kunyan idona ne da a gidan yan sanda asuba xai maki, to ni dae ba ruwana na sa halira take ko wa, ta yi masu kumallo Sapiya ta kai masu, sae ta dau kayan jiddah kala biyu ko uku ta kai mata" Daga haka Hajja ta juya ta fice daga dakin. karfe bakwai Jiddah ta bude kofar dakin da suka kwana a hankali ta fita ta bar Abuturrab dake bacci, sae kusan karfe shidda suka yi sllhn asuba sbda sun makara, wanda shi dai Abuturrab da wayonsa ya mance rabon yyi missing jam'i , kofar parlor ta nufa tana waige waige bayan ta sauko kasa tana isa kofar xata bude taji sa a kulle, ta 6ata fuska kamar xata yi kuka, babu yanda ta iya haka ta koma parlon ta xauna, sae kuma ta mike ta shiga bandakin dake downstairs xata yi wanka, bata ga sabulu ba haka yasa ta koma sama ta bude dakin a hankali ta shiga ta dau sabulu a bandaki ta dau hijab din da tayi sallah ta fita, bayan tayi wanka ta hau gyaran gidan da yayi k'ura which is so obvious ba kamar jiya da daddare ba. A hankali Abuturrab ya bude ido ta dalilin wayarsa dake vibrate, jawo wayar yayi ya ga Aneesah ke kiransa, yayi silencing wayar ya mike xaune yana kallon agogo dake nuna karfe tara, kiransa aka sake yi ya dau wayar yana kallon screen din, lkci daya ya hade rai, sai kuma ya daga ya sa handsfree yyi shiru, cikin rawan murya tace "Captain don Allah ka saurareni ba don halina ba, plss listen to me for God sake captain...." Sae kuma ta fashe da kuka sosai har da shessheka, babu yabo babu fallasa yace "Ina saurarenki" Pleadingly tace "Kayi min rai Captain, kayi min rai kayi hakuri, wllh kai ma ka san ina sonka, sonka da kishin ka ne ya ja min abinda na aikata ba da son raina ba, sharrin shaidan ne wannan abinda ya faru wllh, don Allah kayi hakuri ka gafarceni ka maida ni dakina captain, hakan baxai sake faruwa ba nayi maka alkawari, ka dubi girman Allah ka yafe min pls" yace "Kin yarda xaki xauna da abokiyar xama yanxu kenan?" Cikin kuka tace "Wllh na amince Captain, na yarda wllh" yace "Good, idan har kina son dawowa dakin ki kamar yanda kika ce to sai kin ba ita warce kika doka hakuri, xaki je har gida ki sameta ki bata hakuri yanda ya kamata sannan ki ba Umma da Ummi hakuri, u are coming back only on that condition Aneesah...." Shiru tayi taki cewa komai tana jin xuciyarta na mata wani xafi, yayarta Falmata tayi mata alama da tace masa tohhh, Aneesah ta galla mata wani harara, Abuturrab yace "U are not ready to come back then, don haka kada ki sake kirana baxan dauka ba" Cikin tashin hankali tace "Wllh i am ready captain, xan bata hakurin..." Yace "We will talk later then" Bai jira cewarta ba ya katse wayarsa ya mike l ya fita dakin ya tafi bangarensa, fess ya ga parlon ko ina sae walkiya yake, ya fi minti daya yana bin parlon da kallo, sai kuma ya karasa bedroom dinsa, nan ne kawai bata shiga ta gyara ba, wanka yayi ya shirya cikin kananun kaya ya sauko downstairs, dai dai nan aka yi ring din bell, Jiddah dake kitchen tana goge goge babu warce ta fado mata sai Aneesah, ta kasa motsi a inda take tsaye gabanta ya dinga faduwa, Abuturrab ya karasa ya bude kofar, Safiyya ce tsaye rike da breakfast ta gaishesa sannan ta mika masa basket din, yana kallonta yace "In ji wa?" Tace "Hajja" murmushi yyi ya kalli karamin jakar hannunta yace "Wannan fa?" Tace "Hajja tace a kawo ma Jiddah" ya amsa yace "Kina da kudin mota?" Tace "Driver ne ya kawo ni" yace "Sae anjima" kulle kofar yayi ya juya ya koma parlor ya ajiye abincin da jakar kayan ya nufi kitchen, ja baya Jiddah tayi da sauri da ya bude kofar, bayan sun hada ido ta juya masa baya har sannan xuciyarta bai dawo dai dai ba, ya karasa kusa da ita ya jawota kusa da shi yayi kasa da murya yace "Good morning...." Ganin taki cewa komai ya juyo da ita a hankali, suna hada ido ta sunkuyar da kai, ya lumshe ido ya daura lips dinsa a forehead dinta underneath his breathe yace "Good morning... other half" Juya masa baya tayi, tayi kasa da murya tace "Ka nemeta" ya bude ido yana kallonta sosai yace "Wace?" Ta juyo tace "Ur Other half, ko ka mance wacece ni?" Da farko shiru yyi yana kallonta, sae kuma yace "Wacece ke?" Tayi wani murmushi ta nufi gas ta kashe tace "Jiddah me Awara ta hayin rigasa, warce ba class dinka ba, warce ka aura kawai domin taimako ba don wani abu ba, warce kace ta saka a ranta kai din ba mijinta bane, snn kuma baxa ka ta6a xama mijinta ba, the jiddah that u were ashame to show as ur wife, the Jiddah u divorced without second thought, and the same Jiddah....." Wani tsawa ya daka mata, lkci daya tayi tsit ta juya tana kallonsa, daure fuska yayi sosai yace "Ni kike gaya ma haka?" Tace "Yes i was only reminding u" ya nufeta fuskarsa a tamke, haka nan taji gabanta na faduwa tayi still tana kallonsa, ya fixgota yana mata wani kallo yace "Ce maki aka yi na manta?" Tayi shiru, a d'an tsawace yace "Do u think u need to remind me of all this?" Sunkuyar da kanta tayi, ya saketa ya juya ya fice daga kitchen din... Ta fi minti biyar a tsaye kafin ta samu courage din fitowa parlor, xaune ta samesa a parlon, tana karasowa parlon ta kasa kallonsa, shi ma bai kalleta ba, lkci daya ya mike yace "Dauko gyalenki" bata ce komai ba ta wuce sama, ba a dau lkci ba ta sauko da mayafin tana kallonsa taga ya wuce sama, sae gashi ya sauko da car key dinsa, ba tare da ya kalleta ba ya nuna mata jakan da Safiyya ta kawo yace "Dauki kayanki ki sameni a mota" ta bi sa da kallo kafin ta dau jakar ta bi bayansa.... Har suka isa gidan Umma bai ce mata komai ba yayi parking bakin gate ya bude lock din motar, bude motar tayi ta bude back seat ta dau jakarta ta kulle masa motarsa ba tare da ta kallesa ba ta nufi gate, ya bi ta da kallo har ta shiga gate din sannan ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido xuciyarsa na bugawa... Jiddah tana ta tsaye bakin kofa ta kasa shiga ciki, ta rasa me ke mata dadi, haka kawai taji duk nauyin kowa na gidan ma ita take, gajiya tayi da tsayuwa daga karshe ta bude kofa a hankali ta shiga, bbu kowa parlon hakan ya sa ta nufi dakinsu da sauri ta bude ta shiga, Maimoon na ganinta ta kwashe da wani dariya tace "Aunty Jiddah da sassafe haka?" Lkci daya Jiddah ta hade rai ta ajiye jakarta ta tafi can karshen gado ta xauna, Maimoon dae sae murmushi take, Jiddah ta mike daga karshe ta nufi kofa da nufin ta tafi can bayan gidan tayi xamanta, Maimoon dae sae kallonta take kamar me son gano abu har ta fita, sae ta kuma kyalkyalewa da dariya... Jiddah taji kamar ta nutse bayan sun yi clashing da Umma da ta fito dakinta, ta sunkuyar da kanta ta risina a hankali tace "Ina kwana Umma" Umma da ta ki kallonta ita ma tace "Ina Aliyun?" Jiddah ta kasa cewa komai Umma ta wuce parlor kawai, ji tayi kamar ta koma dakin nasu kawai, muryar Hajja ta ji tace "Aa har kin dawo da sassafe haka kamar ana koranki? Ina Aliyun?" Jiddah ta risina ta gaisheta, Hajja tace "Ga dai kaya na bada a kai maki xaki bugo wannan uban sammako haka, ni dai ba ruwana wllh" daga haka tayi wucewarta tace "Toh ko bakin Ramlah ma bai isheku ba, mata kawai katuwar banxa" Throughout ranan Jiddah ta kasa sakewa gidan, bayan tafiyar Hajja gidan Ummi tsarguwan nata yyi yawa don dama Hajja ce kawai ke jan ta kamar ba abinda ya faru, jiddah kuwa gani take kamar kowa tunanin da yake daban a kan kwanan da bata yi a gida ba jiya, Ahmad ma da ya xo gidan duk hiran da ya dinga janta da shi ta ki sakewa, gani take kamar shi ma an gaya masa, she wished all this never happened, wani haushin Abuturrab take ji har cikin ranta, da yamma tana kwance a daki Safiyya ta shigo wai ana kiranta a parlor, ta mike da kyar ta sa hijab dinta ta fito, sosai gabanta ya fadi ganin Aneesah da yayarta Falmata xaune a parlon, Umma ma na xaune ta sha kunu, Jiddah ta xauna ba tare da ta sake kallonsu ba tace "Umma ga ni?" Umma ta kyabe baki tana nuna mata su Aneesah tace "Wai ke suke nema" Jiddah ta kallesu babu yabo babu fallasa tace "Ohk" Aneesah ta d'an kalleta after gathering much courage tace "Dama na xo ne in baki hakuri a kan abinda ya faru, sharrin shaidan ne ba wani abu ba" Jiddah na kallon Tv tace "No ya wuce ae" Aneesah ta dake tace "Toh nagode..." Falmata na kallon Umma tace "Sae ayi hakuri Umma, hakan baxae sake faruwa ba tayi nadama wllh" Umma taki cewa komai, bayan few minutes Aneesah tace "Toh mun gode Umma xa mu tafi can gidan gun Ummi Allah ya kara girma" har suka fita parlon Umma hararansu take. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you **DATA! DATA!! DATA!!!* **Assalamu Alaikum** *A.M.J DATA SERVICE* *Muna sayar da DATA bundle akan farashi mai sauki, tuntubemu domin yin subcription dinku* *📶MTN DATA🌕* *Ina kke customer's ganifa na garzayo muku da data Mai aminci* *mtn data plan*👇🏼👇🏼👇🏼 *500MB @₦200* *1GB @₦ 300* *2GB @ ₦600* *3GB @₦900* *4GB. @N1200* *5GB @₦1500* *6GB @₦1800* *10GB. @N3000* *15GB. @N4500* *20GB. @N6000* *30GB. @N9000* *(Valid for 30days)* Check your data Balance through, *461*4#* OR *131*4#* *AKWAI DATA NA SAURAN NETWORK* *CALL/SMS 09037037040 or WHATSAPP No 08183611133 👇👇👇 *MTN 1GB @ 300* *biyan kudi ta✔Bank ne* *ACCOUNT NUMBER:* *1500981702* *ACCOUNT NAME: AISHA MUHAMMED HERITAGE BANKAneesah ce tsaye bakin kofa tana kallon bedroom din Abuturrab da mamaki, shi dai yana kishingide saman kujera a parlon yana danna wayarsa ko kallon inda take bai yi ba, can ta dawo cikin parlon da sauri tace "Captain ina kayan dakina??" Sai a sannan ya ajiye wayarsa ya kalleta yace "Among the four rooms out there, though na kulle guda daya, so u can chose from the other 3" Kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa, ganin ya ci gaba da danna wayarsa tace "Meye dalilin ta6a min kaya ka fitar daga nan bangarenka ba tare da izinina ba Captain?" Ya kalleta yace "Saboda bangarena ne nan ba na matana ba, here is my comfort zone alone, amma a duk sanda na bukaci ku xa ku xo nan din ai...." Aneesah tace "Walakancin naka har ya kai haka Captain?? Ni xaka yi ma wannan walakancin?" Sai kuma tayi wani murmushi ta fice fuuu, dakunan dake corridor din after staircase ta shiga budewa taga furnitures dinta a ajiye ko jerawa ba ayi ba a daya daga dakunan, duk sai da ta bi sauran dakunan ta bude, amma banda guda daya wanda shi bathroom da toilet din dake ciki ba shi da banbanci da na bangaren Abuturrab, sannan the room is a bit bigger than the rest kuma a wannan dakin Safara'u take xama, shi kadai ne a kulle cikin rooms din, Aneesah ta juya fuuuu ta koma side din Abuturrab, tana huci tace "Toh shi kuma wancan dakin da ka kulle fa??" Ya gyara xamansa yace "Na uwar gidana ne" Still tayi tana kallonsa, sai kuma tace "Uwar gidanka???" Yace "Yeaa because i married her before u, kuma tace wannan dakin take so.. rashin adalci kike son inyi?" Aneesah ta girgixa kai cike da bacin rai tace "Wllh baxan yarda ba wannan dakin da ka kulle shi nake so sai dai duk tsiyar da xa ayi ayi, ni xaka raina ma wayo kace uwar gidanka?? Wllh baxan yarda ba Captain, yaushe ka koma ka aureta din da ta xama uwar gida??" Ya mike yace "Kafin in aureki na koma na aureta, look idan any of the room except d close one basu maki ba Aneesah, xaki iya kwasan kayanki ki kai downstairs ai akwai daki sannan duk ya fi na sama girma" Daga haka ya fice daga parlon ya bar ta tsaye, Aneesah ta bude baki ta bi sa da kallo xuciyarta na bugawa, murmushi kawai Abuturrab yake yana sauka downstairs, he never thought Aneesah will calm down so quickly, bai ta6a tunanin xata amince da cewar Jiddah matarsa ce babu wani gagarumin tashin hankali ba, duk bata yi abinda yayi tunanin xata yi ba, kuma yayi mugun mamakin da har ta amince taje ta ba Jiddah hakuri domin ta dawo gidansa, this is something he never expect from her, although yasan tana sonsa amma bai yi tunanin to this extent da xata yarda su xauna da Jiddah a matsayin kishiyarta duk kiyayyar da take mata. Aneesah ta shige dakinsa ta xauna kasan carpet ta fashe da wani matsanancin kuka kamar ranta xai fita, yanxu a hakan ma duk hakurin da tayi Jiddah ce uwar gida ba ita na? Anya xuciyarta xai iya daukan wnn takaicin da bakin ciki kuwa, handbag dinta ta jawo tana kuka sosai ta shiga kiran line din Aunty dake can gidansu a Abuja yanxu haka, banda ma tausan da ita Auntyn da Safara'u da Uwarta suka dinga mata ai ita ba kwana kusa ta so dawowa ba, amma duk sun addabeta ta dawo kar ta ji komai, sai da wayar Aunty ya kusa katsewa snn ta daga, Aneesah ta kuma rushe mata da matsanancin kuka tace "Aunty wllh baxan iya ba xuciyata xata fashe, Aunty wai fa ce min yake ai ita Jiddar ce uwar gida sannan duk ya kwashe kayan dakina daga bangarensa ya kai wani dakin, ita kuma ya kulle mata wannan babban dakin da Aunty Safara'u take ciki, ni dai wllh Aunty xan iya mutuwa idan na ci gaba da sauke kaina kasa kamar yanda ku ka ce, wayyo na shiga uku wllh baxan iya sharing captain da wata shegiya ba, wllh Aunty na tsaneta ban ki in kasheta ba Allah ya sani" Aunty dake ta sauraronta tace "Wai me yasa ke ba a isa a gaya maki magana ba Aneesah, ance maki haka nan muka turaki ki koma dakin ki?? Ba dai ni nace ki kwantar da hankalinki ba to me xai dameki? Nace maki duk abinda yace kice masa toh kawai babu musu, xai ci kaza kazansa ne wllh, ai yau Uban nasa xai xo wajena a Abuja, bayan abinda muke yi ta karkashin kasa shi ma da abinda xan gaya masa idan mun hadu, kuma duk a kan batun nan, ki kwantar da hankalin ki kawai Aneesah, ubansa ma ya kasa nutsuwa tun da na bar masa gida duk da ya maida ni balle wani Aliyu karamin alhaki, in sha Allah yau Abban nasa xai shigo wajena a nan Abuja nace maki, kar ki ji komai ki kwantar da hankalin ki xan yi duk abinda ya kamata" Kuka kawai Aneesah take tana kara regretting irin downgrading kanta da tayi wai taje har gida ta ba Jiddah hakuri, sai taji da ma hatsari tayi a hanya bata karasa gidan ba da dai hakurin nan da taje ta bata, she felt so downgraded, wato yanxu Jiddah will now feel belong and important tunda anje an bata hakuri, Aunty ta katse mata tunaninta tace "Kina ji na kuwa Aneesah?" Cikin shessheka tace "Ina ji" Aunty tace "Toh kiyi hakuri, ba cutarki muke ba da muka ce ki kwantar da kanki ai komai na da dalili, yanxu dai ki samu wa enda za su jera maki kayan gadonki a dakin da ya baki, lkcn da xai kwashi kayan naki ya maida bangaren nasa da uban wa xai yi shawara, ke dai sai anjima kawai muna nan muna maki shiri yar nan" daga haka Aunty ta katse wayar, Aneesah ta dinga kwalla tana jin mugun tsanar Jiddah har ranta, she hate her uncontrollably, wllh ita fa xata iya bindigeta idan an bata bindiga take ji.... Umma ce parlon Ummi tana ta danna wayarta tana jiran fitan Hajja tayi ma yar uwartata maganar da ya kawota ta wuce gida don akwai inda xa ta, tun da Hajja ta kyallara ido taga shigowarta gidan ta biyo ta parlon Ummi, kuma taki fita gashi har anyi awa daya, Hajja ta gyara xama tace "To shi Usman din yace maki xai yi tafiya kuwa ko bai ce maki ba Hauwa? Ni dai ya shigo wai yana da wani meeting a Habuja" Ummi tace "Ehh haka ni ma yace min jiya" Hajja ta kyabe baki tace "Toh shi har wani saninsa aka yi a Habuja da xai je wani meeting? Da su wa xai yi meeting din, wllh baku ga yanda ya dinga bani hakuri yana rokona gafara ba da ya shigo, ni dai nayi shiru abuna, kun dai ga ya je yayi kulle kullensa ya sa Aliyu ya maida aurensa da Nanisa, to har da hakurin nan ya dinga bani wai an sasanta lamarin kuma ita Nanisar taje har gida ta ba Jiddah hakuri, snn mu ma nan ta xo ta bamu, ni dai kar a kirani da fitinanniyar uwa shi sa nayi shiru ba ruwana, amma Nanisa ai ba matar xama bace, duk da dai abinda yasa na hakura bai wuce Jiddah da take matsayin matarsa ba ita ma yanxu, tsaf xata dinga masa duk abinda yake so, xata tsaftace masa muhalli da abinda xai ci babu ganda, kinga kuwa daga nan ai ta kwace miji a hannunta, mu ma duk haka muka yi muka tsira, tsaftar mu ce ta kwace mu wllh...." Babu dai wanda ya tankata a cikinsu, Hajja tace "Toh ni dai ba ruwana da duk wannan, damuwata yanxu kawai Aliyu da baki yayi ma yawa wllh, kowa ya bude bakinsa me tsamin gaske sai yace Aliyu kamar dai ya kashe d'an mutum, wllh wnn abun na hanani bacci, shi kuma idan ka basa hayaki sai ya ki yi, ba wai fa hayakin tsafi bane, ko su wannan garin habbatus saudan ai ana turarawa domin miyagu... balle ma wanda xan basa ba boka bane ya bani, ina ga dai da kaina xan dinga xuwa ina turarasa da hayakin, kafin nan Jiddah ma ta tare ita ma duk in hadasu in masu, don wllh wllh duniya ba gaskiya yanxu miyagu sun yi yawa ta ko ina, Ko Nanisar nan ban yarda da ita ba Allah" Ta gefen ido Umma ta kalli Hajja amma bata ce komai ba, Hajja ta rike kai tace "Huhuhu... Abun na damuna wllh, wani sai kaga ya ci ado ya yafo katon gyale ya sa kwaba suu, ya kona fetur dinsa ya fito tun daga gida duk don kawai a raya dumi da gurmi, shi dai Aliyun nan komai yayi dai dai ne wllh tunda ba sata yayi ko kisan kai ba, aure fa kawai yaje aka daura masa babu shawara da ko wani shege, amma duk an sa shi a bakin duniya kamar wanda yayi wani axababben laifi, wllh daxu da ya xo gaisheni baku ga kyan da yayi ya d'an murmure ba, dubu biyar ya ajiye min a dinga saka min kati ga alkawarin turare da yayi min, to wa xai min haka banda shi din dama? Shi Bashir dama yana can yana lalatansa da mata a kasan turawa shi sa ku ka ji na ja bakina nayi shiru da xancensa da Jiddah, Atoh ba ruwana ni kaina nasan iskanci yake yi, ni kuma ai baxan so abinda xai cuci er yarinyar ba, balle ma figaggiyar uwarsa tana nan da girman kai kamar dawisu ba son yarinyar take ba wllh, kowa na murmurewa ya dawo d'an duma duma da shi yayi kyau kamar Ramlah, amma ita tana can kamar sandan agwai taki gaba taki baya duk da uban dukiya da aka tara sbda mugun halayen da take a masarautan, to ba ruwana da xancen da bai shafeni ba ta kaina nake, amma gaskiya kowa ya cire baki da idonsa a kan Aliyu, Jiddan nan dai matarsa ce ba farkarsa ba, to meye wnn fitina da bala'i fisabilillah, har ana kona man fetur a xo ayi da shi, To ba ruwana gulma dai ajalin me shi ce" daga haka ta mike ta fice daga parlon ta wangale masu kofa. Murmushi kawai Ummi tayi don sarai tasan da Umma take, Umma da ta hade rai ta mike ta kulle kofar ta dawo tace "So take in biyeta ni kuma ba da ni ba wllh" Ummi tace "Ai kam sai hakuri Hajja, da ma ina son xan kiraki sai gashi ma kin xo..." Umma tace "Ehh kuma ba dadewa xan yi ba da akwai inda xa ni, gashi duk Hajja ta 6ata min lkci wllh" Ummi tace "Ki saurareni Ramlah, ina son don Allah kiyi hakuri ki bari Jiddah ta tare a dakinta, tunda har ya gano kuskurensa ya kuma yi nadama, main point a nan da Aliyu baya sonta babu abinda xai maida shi sake aurenta, don haka nake son komai ya wuce ta koma dakinta don Allah, ba wai ina magana on Behalf of Aliyu bane, Aa kawai ina magana ne sbda naga ya dace, mu ba kananun yara bane" Umma dake ta kallonta tace "Ummi yanxu Abuturrab har kin ga alamar ya gano kuskurensa yayi nadama? Kina nufin kawai a basa ita a banxa yaje ya ci gaba da walakantata daga inda ya tsaya yaya? mutumin da har yau bai fito direct ya fadi dalilin da ya sa ya koma ya sake auranta ba sai kame kamen rainin hankali da yake, komawa fa yayi ya aureta don yana son xama da ita ba don yana sonta ba?? Kawai don bata da gata sai a mata haka yaya? Ni wllh sai duk banji dadin da wannan ya fito daga gareki ba, Yarinyar da ko waec din bata xana ba?" Ummi tace "Toh yanxu ina amfanin xuwa da yayi ya dauketa ya kai ta gidansa ta kwana sannan ya maido maki ita?? haka kike son a ci gaba da yi ko ya?" Umma tace "Toh ai haduwarmu nake jira da shi yaya, wllh haduwarmu baxai yi kyau ba, sai na masa rashin mutuncin da xai dade bai manta ba, wnn shawara taki kuma bata gamsheni ba kwata kwata yaya, don har yanxu ban yarda Abuturrab ya saduda ba, yana nan a d'an iskan da muka sansa wllh" Ummi dai sai kallonta take, Umma tace "Ita wancan mara tarbiyar an sa ya maidata, to ana nufin ma gida daya xa su xauna tare da Jiddar su kasheta a banxa yarinya ba wani bakin kirki ba?? To kuwa sai dai aki tarewan har abada wllh in dai gida daya xa su xauna da mahaukaciyar matar nan tasa" Ummi tace "Toh wani gidan garesa a Kaduna da xai raba su Ramlah?" Umma tace "Wllh shi ya sani, Jiddah dai baxata xauna gida daya tare da matarsa ba, idan ma haya ce yaje ya nema mata amma sam babu xancen xamansu gida daya da Aneesah, yarinyar da babu Allah a ranta?? Aa wllh baxai yiwu ba, Jiddah baxata iya xama da ita ba" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh indai batun xama gida daya ne xan masa magana a san abun yi sai kar a hadasu din, amma batun wai Jiddah baxata tare ba yanxu ki janye wannan batun Ramlah, ai ana karatu a gidan miji, ke a ina kika yi karatun ki? Ni kaina a ina nayi furthering karatuna, don haka wnn ba hujja bace, tunda Hajja ma ta dage kan sai ta tare xuwa next week in sha Allah xa ayi ma Jiddah duk abinda ya kamata ta tare gidan mijinta, Allah ya basu xaman lafiya da xaman hakuri kuma, shkkn fatanmu" Umma ta bude baki tana kallon Ummi kafin tace komai Ummi ta girgixa kai tace "Bana son kina min musun nan Ramlah, ni xan cuci Jiddah ne, ko kuma xan yarda Aliyu ya cuceta? Yanda na fada haka xa ayi, batun xama gida daya ne kawai xai xo in shaida masa baxai yiwu ba... Idan ya so ko driver ne sai ya samar mata ya dinga ajiyeta a makaranta kullum, shkkn na gama maganata ni kam bana son wani maganan" Aunty ta gama kada ma Abba shayi a hotel room din da ya sauka tana kallonsa tace "Amma sai jibi dai zaka koma ko Yallabai" Abba dake duba laptop dinsa yace "Allah ya kai mu" Tayi wani murmushin kissa tace "Ameen, amma akwai wata muhimmin magana da nake son yi maka Yallabai a kan Aliyu" Abba ya daina abinda yake a laptop yace "Ina jin ki" Tace "Kaga dai wannan yaro kawai xuwa yayi yace mana ai ya koma ya daura aurensa da Jiddah, ba a san ko shiryawa yayi duk domin kada a rabasa da yarinyar ba, snn wa ya kai ma sadakin in har da gaske ne an sake wani auren, don haka Yallabai kamata yayi a tisa keyarsa a tafi hayin gun wanda ya daura masa auren don a tabbatar, daga nan ai yace kishiyar uwar yarinyar na raye sai ya kai ku a gana da ita ma, ba wai ayi ta xama haka kamar bamu da ilimi ba, kasan dai yaran yanxu ba wani tsoron mahaliccinmu suka cika ba, to gwara dai a tsananta bincike kada suje su yi xama na haramun da yarinya, mu ma sai laifin hakan ya shafemu tunda bamu xurfafa bincike ba" Abba na gyada kai cike da gamsuwa yace "This is true, ina komawa kadunan in sha Allah xai kai ni da Alhaji Lawal wajen shi wanda ya daura masu auren, wannan gaskiya ne Hafsah" Aunty tace "Atoh, don Aliyu kam ya xama abun tsoro wllh, abunsa yake kai tsaye babu shakkan kowa, ko wa ya koya masa haka oho kamar dai wanda ake xugawa" Abba yace "Wannan ba damuwa bane gwara da kika tunatar da ni, tun farko ma abinda ya kamata ayi kenan" Abba ya ci gaba da danna laptop dinsa, Aunty tayi murmushi tana ci gaba da juya shayin da cokali a hankali. Abuturrab na xaune parlon Umminsa bayan ta gama fadin abinda xata fada ya dago kansa yace "To Ummi, xan ajiye daya a nan kaduna daya kuma ta xauna a gidana na Abuja in sha Allah..." Ummi tace "Toh hakan dai ya fi, idan Allah ya yarda xuwa next week din sai Jiddah ta tare..." Abuturrab yayi shiru bai ce komai ba, bai ta6a xaton haka da wuri ba, bai ta6a tunanin it will be this easy ba, sai kuma ya kalleta a hankali yace "Toh Ummi ai Umma ce...." Ummi tace "Aa Umma ba matsala bace na kirata nan munyi magana, ya rage naka kuma ka xama me tsoron Allah kayi adalci tsakaninsu Aliyu...." Farin cikinsa ya kasa boyuwa, cikin sanyi yace "Toh nagode Ummi, Allah ya saka da alkhairi Allah ya kara girma, nagode Ummi" Ummi tace "Ameen, sadakin nata fa??" Abuturrab ya sauke kansa yace "Mai anguwan ya bani in taho mata da shi tun a lkcn yana wajena, i bought her gold" Ummi tace "Toh maa sha Allah, hakan yayi kyau sosai, amma fa ga wata er shawara, ka rike Ahmad d'an uwanka da kyau, coz he made everything easy as it seems to u, he made sure he convince each and everyone... barin dai Hajja, a da na dau alwashin cire hannuna a lamarinka tunda kai baka shawara da mutane kanka tsaye kake aikata abinda ya xo maka, worst of all baka daukeni matsayin uwa ba, amma kuma babu yanda na iya hannunka baya rubewa ka yanke ka yar, Idan ma ni baxa kayi shawara da ni ba kanwata na da ranta Aliyu kuma baxata ta6a cutarka ba ko bayan babu ni" Abuturrab da ya sunkuyar da kansa a hankali yace "Kuyi hakuri Ummi, in sha Allah xan gyara, nagode sosai... Allah ya kara girma" Ummi na kallon agogon dake nuna karfe takwas da rabi na dare tace "Toh a gaida Aneesah" yace "In sha Allah, sai da safe Ummi" daga haka ya mike ya fita parlonta, sai da ya tafi yayi ma Hajja sai da safe sannan ya bar gidan. Har wajen karfe sha daya Aneesah bata shigo bangarensa ba duk da ta ji shigowarsa gidan, tana can dakin da ya maidata takaici na neman hallaka ta, tuni ta sa aka kafa mata furnitures dinta tana ta tausan kanta dai, sosai dakin yayi kyau don shima din yana da girma enough, wanda ya rufe ma Jiddah ne kawai ya fi su girma gaba daya, Abuturrab ya fito bangarensa sanye da Pajamas dinsa ya nufi dakin nata, tana xaune tsakiyar gado sanye da wani kayan bacci shara shara tana chatting da wayarta, yana shigowa ta daure fuska kamar ta ga enemy dinta, yayi mata kallo daya ya xauna gefen gadon yace "Baki ji shigowata bane Aneesah?" A takaice babu yabo babu fallasa tace "Ban ji ba" Tana fadin hakan kuma sai ta tuna warning dinsu Aunty da Safara'u, sai kuma ta sake fuska tace "Da yake yanxu na cire air piece ban ji ba" shi dai yana lura da ita, kawai ya d'an yi murmushi yana bin dakin nata da kallo, sai kuma ya kalleta yace "Make me a cup of tea pls" Tace "Babu gas, nima har yanxu ban ci abincin ba" kallonta kawai yake don sarai yasan akwai gas da shi kuma Jiddah tayi amfani jiya, yace "Ohk, ina son maki wata tambaya" Tace "Ina ji" Yace "Gidan nan da gidana da Abuja which will u prefer staying?" Ta kallesa tace "Kamar yaya???" Yace "Ki xabi inda kika fi son xama a ciki" Tayi shiru tana kallonsa, sai kuma tace "Ban gane in xabi wanda na fi so ba" Yace "Ohk, ko da yake ba ma ke ya kamata in fara tambaya ba, uwar gidan ya kamata a fara tambaya ta xaba, duk wanda ta bar maki kuma sai ki xauna a ciki" Aneesah ta sauka daga saman gadon da sauri tana huci tace "Kana nufin raba mana gida xa kayi?" Yace "Eh" Wani shewa tayi tana tafe hannu tace "Toh wllh baxai yiwu ba, duk mu taru mu xauna a nan din, babu xancen raba gida, duk girman gidan nan kace xaka raba mana gida, to wllh baxai yiwu ba, ta xauna nan nima in xauna nan, ai ba kanta xan xauna ba ita ma ba kaina xata xauna ba, wato ka raba mana gida don kuji dadin cutata ku dinga shiga hakkina to ban amince yau ba ban amince gobe ba...." Abuturrab kallonta ya dinga yi da mamaki cause he thought she will welcome the idea na raba masu gida da Jiddah, sai da ya jira ta gama tijaranta sannan ya mike yace "Baki isa ki gaya min abinda xanyi a gidana ba, idan na kai Jiddah Abuja sai ki bi ta can din ku xauna in gani" Daga haka ya fice mata daga daki ya kulle kofar, ta fashe da kuka tace "Wllh duk a gidan nan xa mu xauna duk abinda xai faru ya faru, babu xancen raba mana gida..." Sai kuma ta dau wayarta da sauri ta shiga kiran Aunty, Aunty dake kwance hotel room, Abba kuma yana bandaki ta daga kiran Aneesah tace "Lafiya??" Aneesah ta fashe da kuka tace "Kin ji wai raba mana gida xai yi Aunty" Aunty ta mike xaune da wani expression tace "Ya raba maku gida? A saboda me xai raba maku gida?? Shi har ya isa ya raba maku gida" Aneesah tace "Wlh he just finished telling me now and he is very serious about it...." Aunty tayi er dariya tace "Shine kike kuka kamar wata wawuya Aneesah, to sha kuruminki, battun dai gani ga ubansa kuma dama sai yanda nace, yi shiru ki saurari ikon Allah, gida daya kamar kun xauna, babu xancen raba gida" Abba na fitowa bandaki Aunty ta katse wayarta. *pls wa enda na tura ma doc din Jiddatul Khair banyi saving digit dinsu ba, so I can't add dem to any group, pls su sake min magana so that i can do so, thank you* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari,_ Location Lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *Tested and trusted* *if interested contact* 👇🏻 08052466875 Via WhatsAppRanan Friday as usual Abuturrab na shigowa garin kaduna da yamma ya nufi gidansu direct ta dalilin kiran da Abbansa ya masa jiya, babu kowa parlon ya fara shiga bangaren Abban nasa ganin motarsa da yayi a parking space, waya ya samesa yana yi, ya nemi waje ya xauna ya jira har ya gama sannan ya daga kai yace "Ina yini Abba" Abba yace "Sae yau ka shigo garin?" Yace "Ehh" Abba yace "Good, na samu labarin abinda kake son aikatawa na raba ma matanka gida isn't it?" Abuturrab ya daga kai yana kallonsa bai ce komai ba, Abba yace "Ko ba haka bane?" Abuturrab yace "Haka ne" Abba na kallonsa da kyau yace "Saboda haka kaga nima nayi ko??" Shiru Abuturrab yayi, Abba yace "At the first place wa ya baka wannan gurguwar shawaran?" Abuturrab yace "Aa kawai naga hakan xai fi xama alkhairi ne a tunanina" Abba yace "Toh ba me yiwuwa bane hakan, it's either ka ajiye su a Abuja gaba daya, ko Kaduna, amma u dare not separate der home, ba haka ka taso ka ga nayi a gidana ba, ni nasan wannan ba shawaran kowa bane banda Hauwa da Er uwarta don sune basu son xaman lafiya, ba kuma sa son wani ya xauna lafiya, to ni da nake mahaifinka nace ka hade matanka duk gida daya, final say din kenan, kuma in har xaka ci gaba a haka baka da decision din kanka sae wanda wasu can suka xartar maka to kuwa baxa ka dinga ganin dai dai lamarin ka ba, wannan a rubuce ma yake, tashi ka bani waje" Abuturrab ya kasa cewa komai ya kuma kasa tashi, bayan few seconds ya dago a hankali ya ga irin kallon da Abban nasa ke jefa masa, a hankali yace "Toh shkkn Abba, in sha Allah baxa a raba su ba" Abba yace "Tashi ka ban waje nace Malam...." Mikewa yayi ya fita parlon, ya tafi parlon Umminsa ya xauna, Ummi na fitowa daki ta gansa xaune, da mamaki tace "A'a, yaushe ka shigo?" Yace "Ban jima ba, ina yini" Ummi tace "Lafiya lau, ya aikin" yace "Alhmdlh" karasowa tayi ta xauna tace "What's wrong?" Yayi kasa da kai kamar baxai ce komai ba, sai kuma dai yace "Jiya Abba ya kirani ina wajen aiki.... Ummi ke kika masa magana a kan raba gidan da xa ayi?" Ummi tayi shiru da mamaki can ta girgixa kai tace "A ina na gansa xan gaya masa, jiya shi ma ya dawo ai... Hajja kuma na can gidan Ramlah balle ince ko ita ta gaya masa, balle ma bata san da xancen ba wllh" Abuturrab yace "Ce min yayi kar in kuskura in raba masu gida" Ummi tayi shiru tana kallonsa, can tace "Ikon Allah, ya fada maka dalilin nasa na cewa kar ka raba masu gidan?" Abuturrab yace "Kawai umarni ya bani without any reason" Ummi tace "Toh Allah ya sa hakan yafi xama alkhairi, bana son kayi disrespecting mahaifinka ka ki yin abinda yace, adhere to his instructions nd obey, sai kaga komai naka ya tafi dai dai da amincewan Allah, su kuma Allah ya hade kansu ya basu xaman lafiya, balle Jiddah naga bata da fitina ko kadan, baxa ta biye matarka ba idan Allah ya yrda" Abuturrab dai kansa na kasa, jin Ummi tayi shiru ya daga kai yace "Ummi goben xata koma can gidan?" Ummi tace "Xan kira Ramlan in ji, rabonmu da waya da ita tun jiya, bari ma dai in kirata yanxu" tashi tayi ta tafi daki ta dauko wayarta ta dawo ta xauna sannan ta shiga kiran Umma, Umma na dagawa bayan sun gaisa Ummi tace "Ramlah ya batun tarewan Jiddah gobe?" Umma tace "Ya raba gidan ne Yaya?" Ummi tace "Abbansa ya hanasa yin hakan...." Umma tace "Atoh kuma ae ba a so Jiddah ta tare ba kenan, ana nufin ta tare gida daya matsiyaciyar yarinyar nan warce bamu san xuciyarta ba? Gaskiya da sake yaya" Ummi tace "So kike ya tsallake umarnin mahaifinsa kenan ko me Ramlah?" Umma tace "Atoh Allah na tuba shi yana da wani umarnin da yake son abi bayan bai bi na tasa mahaifiyar ba, kiyi hakuri fa yaya ba rashin kunya nake maki ba, amma ke tunaninki bai baki cewar gun matarsa ya tafi kwana biyar din nan da yayi baya gida ba, to kuma wani umarni nasa yake son abi ga na mahaifiyarsa da yayi fatali da shi" Ummi tace "Kece wannan ya xama matsalarki ba ni ba, don ko kadan ban kawo a kai ba balle ya dameni, abinda na sani kawai gobe da safe aje ma Jiddah da furnitures dinta dakinta, da yamma kuma ta shirya mijinta ya je ya dauketa, that's all.... Sai anjima" daga haka ta katse wayarta, Abuturrab dai kansa na sunkuye, bayan few seconds ya dago yace "Nagode Ummi, Allah ya kara girma" Ummi tace "Ameen, amma kana ji na?" Yace "Ina ji Ummi" Tace "Xuwa yaushe xaka hada mata lefenta kamar yanda kayi ma daya matarka?" Ya sauke kansa yace "Sae dai in tura ma Umma kudi ta hada lefen" Ummi tace "Sae ka tura mata kamar nawa?" A hankali yace "1.5 yayi?" Ummi tace "Bai yi ba" Yace "Toh xan tura mata 2M" Ummi tace "Better" yace "I will send her in sha Allah, ana bukatan wani abun daban that i can assist with na kayan daki?" Ummi tace "Aa bama bukatar komai tunda ba maula muke ba, lefen dai da ya xame maka dole shi xaka yi, sauran duk dolenmu ne mu ya kamata mu yi mata don gudun gori wataran" Ya d'an yi murmushi ya mike yace "Xan karasa gida Ummi, daga kano nake yanxu" Ummi tace "Toh sae anjima" daga haka ya fita parlonta feeling much relieved. Kusan rabi da quarter din kudin lafiyayyun furnitures da aka yi ma Jiddah Ahmad ne ya bada kudin ba tare da yayi shawara da kowa ba, Umma ta cika sauran kudin, sannan ta hada mata lafiyayyun turarurrukan wuta da kwalabensu, Humra da Kulaccam... kai kace Maimoon xata kai gidan Miji sbda qualities din abubuwan da ta siya, Ummi kuma ta siyi komai na kitchen wares da ya mace xata bukata masu tsadan gaske, basu raga jiddah da komai ba na gatan da ake ma 'ya mace idan xa a kai ta gidan miji.... Aneesah na kwance dakinta da safe tana ta baccin da ta saba, wajajen karfe tara ta dinga jin kamar ana haurowa sama da kaya, hayaniyar ya sa ta mikewa ta saka Hijab dinta ta fito daga dakinta da sauri, tsaye tayi corridor tana xare ido, sai da xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin ubansun kayan gadon da ake shigowa da su dakin da Abuturrab ya kulle madadin na Jiddah, Masu haurowa da kayan suka gaisheta, maimakon ta amsa masu cikin daga murya tace "Da izinin ubanwa xa ku dinga shigo ma mutane da kaya babu notice cikin gida? Uban wa ya aiko ku?" Tsayawa duk suka yi suna kallonta, cikin tsawa tace "Ba magana nake maku ba kun tsaya min kamar kurame? Daga ina wannan rubabbun kayan haka?" Daya daga matasan masu shigo da kayan yace "Easy Hajiya, babu wanda dai xai shigo wannan gida babu izini, mai gidan ma na kasa muke shigowa da kayan" Ta nufesa tana huci tace "Ni xaka yi ma rashin kunya ka gaya min maganar banxa?? Ni xaka daga ma murya?" Yace "Aa ba ni na kar xoman ba Hajiya, nima rataya aka bani..." Daga haka ya ci gaba da shigar da kayan da yake cikin empty room din, sai a sannan Aneesah ta lura da cewar an fitar da former furnitures din ciki babu komai a dakin, downstairs ta nufa kamar mahaukaciya, tana sauka taga Abuturrab xaune parlor, kallo daya yayi mata ya dauke kai, cikin rawar murya ta nufesa tace "Amma ai ina da hakkin a sanar da ni xa a shigo min gida ayi wani abu Captain, ba wai in ga katti a sama suna kokuwa da wasu tsinannun kayan gado can ba" Ya kalleta yace "Kina baccin asaran xa a sanar maki xa a kawo kaya, na xata har su gama abinda ya kawosu ma baxa ki tashi ba don lokacin tashin ki bai yi ba" Xata yi magana ya mike ya dakatar da ita fuska daure yace "Look Aneesah, bana son ki sa min ciwon kai da safen nan, gidanki ne nan din da xan sanar maki xa a kawo kaya? Ko kuma a kanki aka je xa a ajiye kayan? Do not provoke me Aneesah!!! Naga alamar ke baki son xaman lafiya a rayuwarki" Yana fadin haka ya koma balcony ya xauna ya bar mata parlon, wasu hawaye masu xafi suka shiga sauka idonta tana jin xuciyarta kamar xai fashe don bakin ciki, sai taji tsaf xata iya cinna ma gidan ashana duk ya kone da dai wannan kayan da ake shigowa da su, goge fuskarta tayi ta koma sama da sauri ta shige dakinta ta kulle ta dau wayarta tayi dialing number Aunty, bayan ta daga ta rushe mata da matsanancin kuka ta xauna a kasan dakin... Abuturrab na saukowa downstairs xai je masallaci yin Sallan azahar, har lkcn kuma masu aikin dake dakin Jiddah basu gama ba amma sun kusa, don ma su kusan shidda ne, yana stairs din karshe aka bude kofar parlon, kallonsu ya dinga yi har suka shigo, Aunty ce da Safara'u da Falmata, ya karasa shiga cikin parlon, Aunty ko kallonsa bata yi ba xata wuce sama, calmly yace "Sannu da xuwa, ina yini" kamar jiransa take dama, ta nufesa fuska a murtuke tace "Pardon??? Ka sha giyan wake ne kake gaisheni Aliyu? Or are u stupid? Ni xaka kalla kace ma sannu da xuwa?" Kallonta kawai yake, tayi wani kwafa ta nufi stairs kamar xata tashi sama, bai ko kalli su Safara'u ba ya fice daga parlon, Safara'u tayi wani murmushi ta bi bayan Aunty, Falmata ta rike ha6a tana biye da ita a baya tace "Ji fa tafiyarsa yayi bai gaishemu ba Aunty, dama d'an iska ne mijin Aneesan nan? In ni baxai gaisheni ba a matsayina na yayar Aneesah ke da kike matsayin kanwar uwarta sai ya ki gaisheki?" Safara'u ta juya ta kalleta tace "Meye abun damuwa Falmata, ai mutumin nan da kike ganin karshen d'an rainin wayo ne, ke dai mu je kawai xai shigo hannu ai, banda ma Aneesar da ta makale masa uban waye shi da xai min wnn walakanci da kimata da martabata" kwafa tayi ita ma, a haka suka haura sama tana ci gaba da bambaminta. Karfe hudu da yan mintuna motoci biyu suka shigo compound din gidan, Maimoon ce ta bude gaban mota ta sauka, Nafisah da Siyama da Safiyya, sai kanwar Yousuf Salima duk suka sauka bayan motar, Umma ce ta sauka daga cikin daya motar tare da mahaifiyar Yousuf Hajiya Rukayya, da wata kawarsu Hajiya Fatima, Su Maimoon suka bude booth din motocin suka dinga shiga da well packaged kayan turarrukan cikin gidan, da wasu kayan suna ajiyewa a main parlor, Umma na shigowa parlon da frnds dinta tace "Toh meye amfanin ajiyesu a nan, ba makullin na wajenku ba ku kai mun su can sama mana" Xaunawa su Umma suka yi a parlor har sai da su Maimoon suka gama haurawa da kayan sama xuwa dakin da aka jera ma Jiddah furnitures, Maimoon sai murmushi take don ba karamin haduwa dakin yayi ba kamar dakin gimbiya, Duk wannan abun Aneesah da falmata na kitchen suna girka indomie, su Aunty kuma ana can sama dakin Aneesah tare da Safara'u, tun da Aneesah ta leko taga su Maimoon ne ke shigo da kaya, wanda lkci daya kamshi ya gauraye parlon ta koma kitchen din da sauri xuciyarta na bugawa, takaici da bakin ciki kamar ya kar ta, Falmata dai sai cewa take "Ma ga ta yanda xa ayi xaman dai" kasa daurewa Aneesah tayi daga karshe jin ana ta shigowa da kaya anki gamawa, ta bar yayarta ta fito parlon tana tafiya cike da kasaita, ido hudu tayi da su Umma dake xaxxaune kan kujera suna hira, ta daure fuska ta dauke kai tayi wucewarta sama without greeting any of them, Hajiya Fatima da ta bi ta da kallon mamaki tace "Kar dai wannan fitsararriyar ce matar gidan?" Umma tayi wani murmushi tana girgixa kafa, sai kawai ta mike tace "Ku mu tafi mu yi abinda ya kawo mu yamma na yi" Tashi suka yi xuwa sama gaba dayansu... sai kusan karfe shidda da rabi suka gama jera turarrukan gaban madubi suka shimfida wani ubansun carpet a tsakiyar dakin, Maimoon ta shimfida tsadadden bedsheet saman gadon sannan aka cika ma dakin turaren wuta a burner aka sauke curtains, daki ya dawo sak na sabuwar amarya, kafin a kira sallah suka fito dakin bayan Umma kashe burner din, ta kulle dakin da makulli ta saka a handbag dinta, har lkcn Safara'u da Aunty suna makale daki babu wanda yasan suna gidan, su Umma na kokarin shiga motarsu Abuturrab ya shigo gidan da motarsa, can gefe ya tsayar da motar ya sauka ya karaso don gaida su Umma, kawayenta ne kawai suka amsa, ita kuwa tuni tayi shigewarta mota ko kallonsa bata yi ba, a haka har suka bar gidan. Bayan magrib su Maimoon suka shigo gida da Umma, a nan parlor duk suka yi sallah, Huraira ta kawo masu abinci ganin Jiddah bata fito ba Umma ta kalli Maimoon tace "Jiddah bata ji shigowar mu bane?" Mikewa Maimoon tayi tace "Bari in duba ta" Dakinsu ta nufa ta bude kofar, kwance ta tadda Jiddah cikin blanket ta rufe har kanta, ta karasa kusa da ita tace "Bacci kike Jiddah, an fa yi sallah.." Xaunawa tayi kusa da ita jin bata amsa ba ta cire blanket din jikinta tana kallonta, Jiddah ta ki bude idonta amma kana ganinta kasan ba bacci take ba, Maimoon tace "Toh meye haka, kukan me kike haka?" Rufe fuskarta tayi da pillow ta ki cewa komai, Maimoon ta dinga kallonta, tun jiya da Umma ta sanar mata xata tare gidan Abuturrab taki bacci da daddare, yanda taga safiya haka taga daren, yau kuma ta tashi da ciwon kai tun safe, ga abinci ta kasa ci, sae take jin kamar xata yi xaxxabi, da ta tuna wai gidan Umma xata bari ta sake komawa gidan Abuturrab da xama this time around ba su biyu kadai xa su xauna ba har da Aneesah sai taji hawaye ya taho mata, duk wannan damuwan da take ciki bata bari kowa ya lura ba, duk da tun safe Umma ta shiga kasuwa da Maimoon, ko da suka dawo kasuwan kuma frnds dinta kawai ta jira suka iso suka kama hanyar gidan Abuturrab gaba dayansu, tun kuma da suka tafi take kuka har shigowar su yanxu, Mikewa Maimoon tayi ta nufi kofa, Jiddah na ganin haka ta mike xaune tana goge kwallar dake makale idonta kafin tace mata komai har ta fita, Komawa tayi ta kwanta wasu hawayen masu xafi na xuba idonta, kawai tausayin rayuwarta take kuma yanxu, shi kansa Abuturrab din taji tana tsoronsa ta rasa dalili, ko don sbda abubuwan da ya tsiri yi mata yanxu wanda baya mata a lkcn da suke su biyu kadai a gidansa ne oho, yanxu kam ko ganinsa ta ji bata son yi, yana bata tsoro ba na wasa ba, ko sunansa taji an kira sae gabanta ya fadi, sannan kuma ga Aneesah, ai bata san lkcn da ta fashe da kuka ta kife kanta da pillow ba tana shessheka tana tausayin kanta, Maimoon na komawa parlor ta duka kusa da Umma dake xaune kan darduma tace "Umma kuka fa take ta yi a daki" Umma ta kalleta tace "Kuka kuma? To kukan uban me?" Maimoon dai tayi shiru don ita ma har ta fara jin tausayin Jiddah, yanxu gobe haka xa a kai ta gidan Abuturrab a barota ita kadai ga Aneesah da yan uwanta a gidan, mikewa Umma tayi ta tafi dakin nasu, kulle kofa tayi bayan ta shiga ta nufi kan gadon ta xauna kusa da ita tace "Jiddah" Jiddah ta mike xaune amma bata yarda ta kalleta ba tana share hawayen da ya ki tsaya mata, Umma ta kamo hannunta cikin sigar lallashi tace "Gaya min kukan me kike Jiddah, tell me what it is my daughter" Jiddah ta girgixa mata kai wasu sabbin hawayen na kai komo a fuskarta, Umma tace "Kina da warce xa ki gaya ma damuwarki bayan ni Jiddah?" Jiddah ta fada jikinta cikin rawan murya tace "Umma me yasa baxa a bar ni a gidan nan ba" Umma tayi shiru ta ma rasa abinda xata ce mata, can tayi kasa da murya tace "Ke matar aure ce yanxu Jiddah, ba don kuma bama sonki ba xa ki tafi gidan mijinki" Tana kuka sosai tace "Umma wllh na fi son nan, don Allah a bar ni in xauna a nan" Umma tace "Da nan din da can duk daya ne Jiddah, kuma duk sanda kike son xuwa nan Aliyu baxai hanaki ba" Ta girgixa kai da sauri tace "Aa Umma ni bana son in xauna a gidansa wllh" Umma tace "Saboda me?" A hankali tace "Ni tsoronsa nake ji" Dariya ta ba Umma amma bata yi ba tace "Tsoronsa kamar wani dodo Jiddah" Cikin kuka tace "Allah Umma ina tsoronsa" Umma tace "Watanninku kusan hudu tare a gida daya Jiddah duk baki ji tsoronsa ba sae yanxu?" Jiddah tayi shiru tana tuna lkcn da suke tare gida dayan, to amma a lkcn bata ta6a tsoronsa ba sai yanxu, Umma ta dago kanta tana share mata idonta tace "Don't worry my dear... Da gidan Aliyu da nan duk daya ne kin ji" Jiddah tayi shiru tana kallonta, Umma tace "Kin yi sallah?" Sunkuyar da kanta tayi a hankali tace "Aa" Umma tace "Tashi ki je kiyi" Mikewa tayi a sanyaye ta nufi bathroom, Umma ta bi ta da kallo cike da tausayinta.... Babu wani abu da Umma ta ba Jiddah ta sha na mata don tana ganin at this her age bata bukatansa, iyaka dai turaren tsugunno da ta sa take yi, yanda Jiddah ta ga daren jiya haka taga na yau ma, da ta tuna xata bar gidan Umma ta koma gidan Aliyu sai taji gabanta ya fadi, hawaye ya taho mata, da safe shayi kawai ta iya sha bayan tayi wanka ta kwanta, nan da nan kuma bacci ya dauketa amma ba me dadi ba, karfe tara Umma ta fita xuwa gidan Ummi da frnds dinta don kwasan kayan kitchen din Jiddah a kai can gidan Abuturrab, A hanya Hajiya Rukayya tace "Toh yanxu ya xa ayi da jeran kayan Kitchen din tunda dai ita warcan naga kayanta ne ko ina na cikin kitchen din, jiya na shiga da naje daukan ruwa" Umma na gyara xama a motar tace "Ki sa ido ki gani ke dai, don ma ba yanda Hajja tace ayi xanyi ba, Hajjan fa cewa tayi duk a fitar da kayan kitchen din sun kaxance a ajiye ma me su a backyard a jera sababbi na Jiddah, to amma baxa mu yi haka ba ai, ni nasan yanda xan yi" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp Karfe goma Maimoon ta tashi Jiddah daga baccin da take, Jiddah ta mike xaune tana kallonta da kyar saboda kanta da yayi mata nauyi, Maimoon tace "Driver din ya xo yana jiranmu a waje" Jiddah ta marairaice tace "Gashina fa a gyara yake Maimoon, last week fa mun je saloon" Maimoon ta buda hannu tace "Oho go ai nima bani nace mu je ba, kina dai ji Umma ta fada da asuba ai da kince mata a gyara gashin ki yake" Jiddah bata ce mata komai ba ta mike tsaye ba don ranta ya so ba ta fara shiryawa, Maimoon tace "Ina jiranki a parlor" Daga haka ta dau hijab dinta ta fita, Jiddah ta gama shiryawa ita ma ta saka hijab din ta fito sannan suka wuce saloon din, har suka isa jikinta a sanyaye yake tayi nisa tunanin da take, Lkci lkci Maimoon ke kallonta amma dai bata ce mata komai ba. Bayan an gana gyara mata gashin da kyar da lallami Maimoon tayi convincing dinta aka yi zanzara mata henna a hannu, sosai lallin yayi kyau don expert ce tayi mata, Maimoon sai kallonta take tana murmushi, karfe biyu da yan mintuna suka koma gida, Umma dake parlor da frnds dinta sun dawo daga jeran kayan kitchen ta bi su da kallo har suka wuce daki, Jiddah ta xauna can karshen gado ta jinginar da kanta, she looks so sad, Maimoon ta je ta debo masu abincin don sun yi sallah a saloon din, da farko kin cin abincin Jiddah tayi sai da ta ga da gaske Maimoon xata je ta gaya ma Umma sannan ta sauko ta debi abincin ta kai baki, daurewa kawai take wajen cin abincin don jin sa take kamar magani... Throughout ranan Abuturrab a bedroom din Umminsa ya yini sai dai ya fita masallaci, Ummi dai na lura da shi kamar he isn't happy amma kuma bai ce mata komai ba, bayan la'asar tace "Wai baxa ka ci abincin bane, abincin tun karfe daya a ajiye? Ko a fita kitchen da shi ne?" Yayi pausing movie din da yake kallo a wayarsa yace "Xan ci Ummi" kallon abincin nasa dake ajiye kawai yake, Ummi tace "Tell me what is wrong Aliyu!!" Ya kalleta sai kuma yayi shiru ya sauke kansa ya ki ce mata komai, jin Ummi bata sake ce masa komai ba ita ma, ya daga kai ya kalleta yace "Ummi ni kawai na rasa gane amfanin aurena da Aneesah, can u imagine all 2 of her family members suna gidana yanxu haka... sannan Aunty ma na gidan tun jiya" Da mamaki Ummi tace "Wacce Auntyn?" Ya shafa kansa bai ce komai ba yana jin xuciyarsa na tafarfasa tuna abinda Aunty tayi masa da safe har da xagin Umminsa, Ummi tace "Wai Hafsah kake nufi ko wa?" Yace "Ita... Ummi gaba daya fa suna gidan yanxu haka" Ummi ta kasa ce masa komai sai kallonsa take da mamaki, Ya dafe kansa sounding so fed up yace "I'm really fed up with this Ummi, shkkn mutum ba shi da kwanciyar hankali a rayuwa, i regret marrying Aneesah, i regret ever making this mistake" Ummi ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya tace "Toh Allah ya kyauta, amma ban san me xance ba gaskiya, i think it's better kaje yanxu ka sanar ma Hajja, ita xata fi daukan Action, ko kace xaka gaya ma Abbanka ba wai sauraranka xai yi ba yanxu" Shi dai bai ce komai ba, Ummi tace "Haka Allah ya kaddaro maka sai kayi hakuri, kowa ma hakurin yake, kuma babu hakurin da yake tashi in vain, there is always a reward for that, Allah yayi mana maganin duk abinda ya dame mu" shirun dai Abuturrab yayi but he looks so worried, Ummi tace "Yanxu jiran tarewan Jiddah suke kenan da suka rigata tarewa a gidan? Toh me yayi xafi sai ka bari next week idan sun gama xaman nasu koh" Ya kalli Ummi da sauri, sai kuma ya sunkuyar da kansa yace "Aa nothing is going to change because of them Ummi" Ummi tace "Amma gaskiya kaje ka sanar ma Hajja, amma kar ka gaya ma Ramlah don bana son tashin hankali" Ya amsa mata da toh kawai. Ana kiran isha Abuturrab ya isa gidan Umma, sai da ya gama waya da Ahmad da ya kirasa for almost 10min sannan ya shiga masallacin dake layin yayi sallah ya fito, ya fi minti daya tsaye bakin kofar parlon Umma don shi ko kadan bai son matsalan Umma, a hankali ya bude kofar daga karshe ya shiga ciki da sallama, su Safiyya ne a parlon ya karasa ya xauna duk suka gaishesa, ya amsa without looking at them yana danna wayarsa, Umma na bedroom dinta tare da Jiddah dake xaune saman darduma a gabanta ta sunkuyar da kanta, lafiyayyen lace me tsada ne jikinta wanda yayi mugun amsan fatar jikinta, ko ba a fada maka ba xaka san kuka take duk da mayafin da ya rufe har fuskarta, nasiha sosai Umma ke mata kamar yanda uwa xata ma 'yar ta, Maimoon ta shigo dakin da sallama ta duka kusa da gadon jin Umma na magana bata ce komai ba, Umma ta kalleta tace "Ya aka yi?" Tace "Yaya ne ya xo yana parlor" Umma ta ci gaba da yi ma Jiddah maganar da take har ta kai aya sannan tace "Toh shkkn abinda xance maki kenan daughter, and i hope u won't disappoint me by taking all my words for granted, Allah ubangiji ya bada xaman lafiya... Sai da safe" Jiddah ta kasa tashi ta fara rera mata kuka, Umma da taji tausayin har ranta ta kalli Maimoon a hankali tace "Kama hannunta ku tafi" Maimoon taji kamar ta fara kukan ita ma, ta mike a sanyaye ta daga Jiddah suka nufi kofa, Umma ta bi Jiddah da kallo cike da tausayinta, babu yanda ta iya da yayarta ne amma banda haka in dai ta Hajja ne ko yakin duniya xa ayi baxata bar Jiddah ta koma gidan Aliyu ynxu ba, kawai duk abinda xai faru ya faru, but babu yanda ta iya da Ummi.... Tun da Maimoon suka fito parlor Abuturrab ke kallon Jiddah babu ko kiftawa, sosai kayan jikinta da mayafin suka mata kyau, ya mike yana kallon Maimoon yace "Umma fa?" Maimoon tace "Tana daki" Bai ce komai ba ya tafi dakin Umma, kasa shiga yayi yana ta tsaye kamar mara gaskiya can dai yayi shahada daga karshe ya tura kofar da sallama kasa kasa ya shiga ciki, Umma dake linkin Hijab dinta tayi kamar bata gansa ba ta hade rai, ya xauna saman carpet murya can kasa yace "Ina yini Umma" Ba tare da ta kallesa ba tace "Lafiya lau" Shiru yayi bayan few minutes ya mike yace "Toh sai da safe Umma nagode, Allah ya kara girma" Umma ta juyo tace "Ba ka gode ba Aliyu, wllh ko k'uda ka bari ya cuci wannan er marainiyar Allahn, Allah ya isa ban yafe ba, ba wai an ce sai ka ajiyesu gida daya ba dole.. Wllh duk abinda ya samu Jiddah ina me tabbatar maka xan mance relationship din meye tsakaninmu in ma rashin mutunci in dau matakin da ya dace, matarka kuwa ka ja mata kunne kar tace xata yi crossing part din 'ya ta, ta tsaya iya lane dinta, she should take her eyes off my daughter don wllh bani da mutunci, a al'adanmu na fulani kusan abun kunya ne ace uwa na sintirin xuwa gidan 'ya babu dalili to kuwa sai dai a kirani da mara kunya in this case" Shi dai Abuturrab bai ce komai ba yana sauraronta kansa a kasa, Umma tayi kwafa ta ci gaba da abinda take tace "Allah dai ya ba kowa sa'a..." Jin bata sake cewa komai ba, a hankali yace "Toh in sha Allah Umma, sai da safe" Fita yayi dakin, Maimoon dake xaune kusa da Jiddah kan kujera ta mike ta kama hannun Jiddah suka fita parlon safiyya da Huraira suka rakasu har bakin motarsa, shi dai yana biye da su a baya, Maimoon ta bude ma Jiddah front seat taki shiga sai kuka take tana rike da hannun Maimoon gam, Abuturrab na kallonsu gaba daya yace "Sai da safe" Babu wanda yace komai duk suka juya, Maimoon ta kwace hannunta cikin na jiddah ta nufi gate tana goge guntun hawayen idonta, yana kallon Jiddah calmly yace "Shiga" taki shiga taji kamar ta bi su Maimoon ciki da gudu, bin kofar gidan yayi da kallo tana ganin xae dagata tayi saurin shiga motar tana kuka sosai, ya kulle motar sannan ya xaga ya bude driver seat ya shiga... Har suka isa gida kuka Jiddah take, shi dai bai ce mata komai ba yayi horn driver ya bude gate ya shiga yyi parking ya kashe motar, sae a sannan ya jinginar da kansa jikin kujeran motar yana jin yanda take shessheka, juyawa yyi ya kalleta, Lowering his voice yace "Jidderh..." Kukanta kawai take, ya kamo hannunta a hankali yace "Gaya min kukan me kike" Ta xame hannunta taki cewa komai wani sabon kukan na taho mata, bude motar yayi ya sauka ya xaga ya bude side dinta ya sauko da ita, ya kulle motar yana rike da hannunta ya nufi cikin gidan da ita, sosai take jin gabanta na faduwa tana fatan ace mafarki take yau, tsaye yayi balcony yana kallonta ganin kamar ana dada tunxurata da kukan, ya dage mayafin kanta yana kallon kyakkyawan face dinta da ya baci da hawaye, side hug yyi mata murya can kasa yace "Ohk then! Next week in sha Allah xan maida ki gidan Umma amma sai kin daina kukan nan, stop the cry now..." cikin kuka sosai tace "Next week is too far, don girman Allah kayi hakuri ka maida ni yau, wllh bana son gidan nan, don Allah nace maka...." rungumeta yayi ta dinga rera masa kuka kamar ranta xai fita tana shessheka, ya lumshe ido yana jin yanda xuciyarta ke bugawa, ga kamshinta da ya cika hancinsa, bayan few seconds ya bude idonsa a hankali yace "Gobe xan maida ki, but sae kin daina kukan..." Cikin rawar murya tace "Kace wllh" yayi kasa da murya ya daura goshinsa a nata yace "Na ce" ta dauke kanta da sauri tace "Aa wllh xaka ce" ya juyo da ita yayi kissing lips dinta lightly, underneath his breathe yace "Ga shi nace" bai jira me xata ce ba ya manna mata wani kiss din a cheeks dinta yana rike da hannunta ya bude kofar parlon suka shiga, ba ita ba har shi sae da gabansa ya fadi ganin Aunty, Safara'u, Falmata da Aneesah duk xaxxaune a parlon, lkci daya ya dauke kansa yana ci gaba da tafiyarsa fuskarsa a daure, Jiddah kuwa tunda ta hada ido da Aunty da Aneesah ta dinga bobboyewa gefensa kamar xata shige jikinsa, hakan da tayi ya sa shi rungumeta ta side dinsa har suka wuce sama su Aunty duk suka bi su da kallo, A hankali Aneesah ta fara kuka tana jin xuciyarta na mata xafi, Safara'u tace "Meye haka? Kun ga wani shashanci ko, ke kam wllh dole ma miji ya rainaki... Haka aka koya maki kiyi? To kukan uban me kike masu yanxu don uwarki??" Falmata dake hararanta ita ma tace "Wlh ke kam baki yo halinmu ba Aneesah, ga dai yanda aka shirya abu da ke, kawai ki kama yi ma mutane kuka kamar wata mara class" Aunty dau takaicin yanda Abuturrab ya wuce bai ce mata kala ba ya cikata, tun dai da wnn yarinya Jiddah ta shigo rayuwarsa ya daina mata biyayya, ya daina ganinta da girma, sai kuma ga raini yanxu, to kuwa ai babu wanda ya kamata yaji haushin Jiddah fiye da ita tunda ita ce silar rabata da Abuturrab, Sosai xuciyarta ke k'una, can ta ja tsaki tana kallon Aneesah tace "Toh kukan uban meye haka? Shi kike ma kukan ko ita?" Aneesah dae bata ce masu komai ba kuka kawai take tana jin dama duk mafarki take yi wnn bakar rana da take witnessing, yanxu kishiyarta a ka kawo mata gida tana ji tana gani, a d'an tsawace Falmata tace "Baxa ki tashi kije ba, ni fa wllh sai in tattara kayana gobe in bar gidan nan idan baxa ki bi abubuwan da aka daura ki a kai ba don xaman lafiyan ki, wannan wacce irin yarinya ce haka don Allah" Aneesah ta goge idonta ta dake ta mike da kyar ta wuce saman duk suka bi ta da wani kallo, Aunty ta ja tsaki tace "Ni abinda ke min takaici da ita trusting dinmu da ta kasa yi har yanxu, shekarana ashirin da shidda tare da mahaifinsa sai yanda nace a gidan wllh, ko uwarsa da ta kusa shekara talatin da takwas bata isa bane, idan nace eh toh eh ne, Aa kuma Aa, to kuma waye Aliyu karamin alhaki?" Wani dariya Aunty tayi tace "Toh ko abinda ya faru kwanan nan da yanda ubansa ya birkice ma ya isa a san ba da wasa nake xama gidan ba, kwanansa biyar a Abuja shi ma sai da na dinga lallabasa ya tafi sabida aiki, to kuma waye Aliyu" Safara'u tace "Dalla rabu da ita har mijina ya mutu wllh ko kallon wata Mace bai yi da sha'awan aure, ita Aneesah ta cika hanzari ne sannan ga uban son da ta dauka ta daura masa duk shi ke cutanta" Aneesah na haurawa sama ta goge idonta sosai, tsaye tayi kofar dakin Jiddah dake ta xuba kamshi don tun daga bakin stairs ake jin kamshin, ta dake, ta danna xuciyarta ta kwankwasa kofar ta koma gefe, bayan wani lkci jin ba a amsa ba ta sake kwankwasawa sai kuma ta murda kofar ta ji a kulle, Abuturrab dake duke gaban Jiddah da ta ki daina kukan da take don ganin mutanen da tayi a parlor ya kara tsoratata, ya daga kai yana kallon kofar, lkci daya tayi tsit ita ma tana kallon kofar, gaba daya a tsorace take, mikewa yayi ya nufi kofar babu yabo babu fallasa yace "Waye?" Aneesah ta dake tace "It's me Captain" bude kofar yayi yana kallonta, tun da Jiddah ta kalleta sau daya ta dauke kai, Abuturrab ya juya ya koma ya xauna gefen gado, ta bi bayansa tana tafiya a hankali tace "Sorry for the interruption..." Ba dai wanda ya tanka ta, tana murmushi tace "Sannu da xuwa amarya" Jiddah ta hade rai ta d'an ja mayafinta ta rufe fuskarta, Aneesah ta xauna saman kujera daya dake cikin dakin, tana kirkiran murmushin karfin hali a hankali tace "Welcome to our home Jiddah, Allah ubangiji ya hade kanmu ya bamu xaman lafiya, ya kauda fitina tsakaninmu..." Ko dagowa Jiddah bata yi ba balle ta amsa mata, Aneesah tayi karfin halin cewa "Kin yi shiru... I only came to welcome u for being part of us, and i thought u will also welcome...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka ba tare da ta shirya hakan ba, shi dai Abuturrab kallonta kawai yake, ta tashi ta nufi kofa da sauri ta fita daga dakin, Abuturrab ya kalli Jiddah kamar baxai tashi ba sai kuma ya mike ya bi bayan Aneesah, sai a sannan Jiddah ta daga kanta ta bi sa da wani kallo, yana fita dakin ta tashi ta karasa tayi locking kofar da makulli. Aneesah ta shige dakinta hakan ya sa ya bi ta cikin dakin, kuka take kamar ranta xai fita, ya tsaya bakin kofa yana kallonta yace "What's the meaning of that?" Girgixa masa kai kawai tayi, ganin yanda take kukan ya karasa cikin dakin, ta hade kanta da gado cikin kuka sosai tace "Captain baka ce min xaka min kishiya ba, baka ce min xa mu xauna tare ba, u once told me baka da burin mata biyu a rayuwanka, kullum cikin nuna min kake babu komai tsakaninka da Jiddah tun aurenku na farko, you deceived me all this while, me yasa baka gaya min gaskiya ba tun a farko in cire ran cewar ni kadai ce, me yasa tun sannan baka gaya min ba in hakura da tunanin ni kadai ce Captain, ka bar ni na sakankance, sannan ka dawo ka min haka? this is too painful to bear..." Yayi shiru yana kallonta, sai kuma ya xauna gefen gadon yana kallonta a hankali yace "We plan... But God plans best Aneesah, we were together before i met Jiddah, and i am sorry i never bargained for this, kaddara ta ce a haka, Allah ya rubuto min dole xan auri Jiddah kuma xan yi rayuwa da ita, and i am sorry to let u know that i can't live without her, babu yanda xanyi ita matata ce kamar yanda kike matata kema..." kuka kawai take kamar ranta xai fita, ya dagota ya jawota jikinsa yace "I am sorry all this happened Aneesah, ke ma kuma ba wai bana sonki bane, da bana sonki baxan aureki har in kai warhaka dake ba, i married u because i love u too" Ita dai kuka kawai take, ya rungumeta yace "Is that okay now?" Girgixa masa kai kawai take hawaye masu xafi na xuba idonta tace "Kasan ina sonka so me tsanani Captain..." yace "Yea na sani, kuma sai ki so abinda nima nake so ku xauna lafiya" Kai kawai ta gyada masa bata iya tace komai ba, yace "Kuma in sha Allah xan kwatanta adalci a tsakaninku" Sai da Abuturrab ya tabbatar ta daina kukan sannan ya mike yace "Yaushe su Aunty xa su bar gidan nan?" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, shiru yayi na wani d'an lokaci sai kuma yace "Sai da safe" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo wasu sabbin hawayen na sauka idonta har ya fita ya kulle kofar, dakin Jiddah ya nufa yana murda kofar ya ji a kulle, ya kwankwasa Jiddah dake kwance taki motsawa balle ta tashi ta bude, kwankwasawa ya sake yi gently amma taki budewa. Juyawa yayi ya tafi bangarensa, wanka yayi ya sauya xuwa Pajamas sannan ya xauna yana danna laptop dinsa, yana son shan shayi but come to think of the set of people sitting down at the parlor ya sa shi kin fita yayi making tea din, kuma bai son ya sa Aneesah tayi masa, ma'anar abinda Jiddah tayi ne ya kasa ganewa har lkcn, ya dai ci gaba da operating laptop dinsa kawai, he doesn't even know if he is angry or not... Sai kusan karfe sha daya da rabi su Aunty suka hauro sama jin Aneesah shiru shiru kamar an aiki bawa garinsu, Aunty ta gama kare ma kofar dakin Jiddah kallo sai kuma tayi wani murmushi ta nufi dakin Aneesah, su Safara'u na biye da ita a baya suka bude kofar, kwance suka sameta tayi bacci da hawaye a fuskarta, Safara'u ta rike ha6a tace "Toh Allah ubangiji ya sa dai ba xubda mutuncinta da kimarta taje tayi a gabansu ba, kai wannan yarinya dai bata yo mu ba wllh yanda kika san ba jinin mu ba, ko kadan bata da xuciya sai hauka da shashanci" Aunty ta tada Aneesah tace "Shine kika shanya mu a parlor kamar yan iska, ya ake ciki?" Ta murxa ido a hankali, agogo ta kalla taga karfe sha biyu saura da sauri ta dira daga kan gadon ta fita dakin hawaye na taruwa idonta, duk suka bi ta da kallo Falmata tace "Toh wajen ubanwa xata, idan kun bibiya wllh bata yi abinda ku ka ce ba, xuwa tayi ta sha kukanta ta koshi ta kwanta, wnn fitina har ina ni falmata, anya xa ayi abun arxiki da er nan kuwa?" Aneesah na fita ta dinga kallon dakin Jiddah wasu hawaye na xuba idonta, she just can't imagine this, yanxu Aliyu na dakin kenan a nan xai kwana, jingina tayi da bango ta dinga rera kuka a hankali tana jin xuciyarta na mata xafi, kamar ance ta kalli part dinsa taga hasken wutan parlor na reflecting don an kashe fitilar corridor din wajen, da sauri ta karasa xuciyarta na bugawa, tura kofar tayi ta gansa xaune parlon ya daga kai yana kallonta, ta karasa ta xauna kasan carpet ta marairaice masa tace "I am not feeling okay captain, wllh ji nake kamar xaxxabi xai rufeni" yace "Toh sai ki sha paracetamol ai" Tayi shiru bata ce komai ba, amma tana son gano ko Jiddah na dakin ko bata nan, bayan few seconds a hankali tace "paracetamol dake gidan nan na bedroom din ka ai" bai ce komai ba ya mike ya nufi dakin ya shiga, da sauri ta tashi ta tafi tana leka cikin dakin taga babu jiddah, alamar dai tana can dakinta, ji tayi hankalinta ya d'an kwanta, to kenan ba a dakinta xai kwana ba? ta koma ta xauna tayi jigum xuciyarta babu dadi, fitowa yayi daga dakin rike da paracetamol din da wani spare key, ta dinga kallonsa ya mika mata paracetamol din ta amsa yace "Idan kin sha sai ki tafi ki kwanta, sai da safe" bata iya ta ce masa komai ba ya kashe laptop dinsa ya ajiye sannan ya nufi kofa, ji tayi kamar xuciyarta xai daina aiki kwata kwata at that moment, har sai da ya fita parlon sannan ta fashe da kuka sai kuma ta mike da gudu ta nufi kofar tana lekansa taga hanyar dakin Jiddah ya nufa, tana ta lekensa har ya bude kofar da makullin hannunsa sannan ya shiga ya kulle.[7/26, 9:00 AM] Ummuanwar🥰: Abuturrab ya bi ta da kallo ganin da speed din da tayi use ta shige bandaki ta kulle kofar, ya karasa cikin dakin ya tsaya kusa da window ya rungume hannunsa, lkci lkci kuma yake kallon kofar bandakin, at first he pretend he isn't angry at all, yayi iya kokarin ganin bai ji haushin hakan da tayi ba, but he realize he was only deceiving himself cause he was jet angry, few days ago tayi masa rashin kunya, daxu kuma ya fita kafin ya shigo ta kulle kofa da makulli another rashin kunya, yanxu kuma ya shigo ta shige bandaki ta kulle... kallon kofar bandakin yayi for almost 3 minutes, kawai ya ji dole ma sae yayi maganinta yau, kofar ya nufa ya murda duk da ya san ta sa makulli, Jiddah dake tsaye jikin washing machine din bandakin ta wani harari kofar ta juya masa baya kamar irin yana ganinta din nan, calmly yace "Xo ki bude kofar nan right away" K'in cewa komai tayi, yace "Ba ki ji na ne?" Tayi masa shiru still, yace "Don't allow me to get that door open my self" Tace "Toh ni me xan maka idan na bude kofar, ka tafi wajen matarka mana, ai na xata a can ya kamata ka kwana tunda ka bi ta..." Shiru yayi na kusan one minute abinda ta fada na rotating a kansa, can yace "Ohk fine" Tana jin ya bude kofar dakin ya kulle, tayi ta tunanin to fita yayi? ita dai tana ta tsaye bandakin ta gaji da tsayuwa daga karshe ta durkusa, tana nan a haka har bacci ya fara damunta, xaro ido tayi ganin duhu ya gauraye bandakin lkci daya, hasken wata kadai ke reflecting ta window, mikewa tayi ta karasa kofar bandakin gabanta na faduwa ta murda makullin a hankali ta bude, without making any sound ta fito cikin dakin, ji tayi an fixgota da karfi, sbda rudewa da yanda ta gigice bata san sanda ta tsala wani ihu da karfi ba jikinta na rawa ta fara basa hakuri, da sauri ya rufe bakinta don bai ta6a xaton xata yi wannan ihun ba yace "Baki da hankali ne, baki san dare ne ba" Kuka ta fara yi tana son kwace kanta amma ya ki saketa, ba Aneesah da Falmata dake daki daya ba, har su Aunty da Safara'u dake room din karshe sae da suka ji wannan ihu na Jiddah duk da sun fara bacci ma, ita dama Aneesah ba baccin take ba falmata ce ke bacci, tun bayan da taga Abuturrab ya shiga dakin Jiddah ya kulle almost an hour ago ta wuce dakinta hawaye na xuba idonta kamar famfo, shine tun sannan take ta juye juye kan gado abin duniya yabi ya dameta, taji kamar da gaske xaxxabin karyan da ta ce masa na neman rufeta, sae kuma ga wannan ihun Jiddah da ya kara gigitata, sauka tayi daga kan gadonta ta xauna kasa tana jin kamar mashi ake soka mata a kirji ta dinga rera kuka tana imagining ihun meye Jiddah tayi, Falmata dae na kwance tana jin ta, ita ma dai takaicin ne ya cikata ta dinga jin kamar ita aka ma wannan kishiya... Ganin yanda Jiddah ta tsorata ya sa Abuturrab ya ji gwara ya kara tsoratata ya fidda rainin tsakaninsu ko xata shiga hankalinta da shi, don ya ga wani tashe raini take ji, ai kam Jiddah ta tsorata iya tsorata don taga sababbin al'amarin da kanta ya kasa iya dauka daga Abuturrab, taga abinda ya fi karfin tunaninta, bata ta6a sanin haka Abuturrab yake ba, gashi ya ki bata daman ko tari, roko ne fal bakinta da take son yi masa ko xai tausaya mata ya kyaleta amma yaki bata chance din hakan, Bai yi tunanin tsoronta ya kai haka ba, duk da babu abinda yayi niyyar mata without her consent amma sai yaga yana neman crossing boundaries dinsa shima, he was finding it hard to control himself anymore, ba karamin namijin kokari yayi ba na ganin ya kyaleta ya koma can end din gadon yayi kwanciyar upside down, ai tana samun wannan opportunity din saketa da yayi ta dira daga saman gadon ta kwala wani ihun ta fashe da kuka tana kiran Umma, ta kira Umma yayi sau biyar, gaba daya tayi mugun tsorata, bata ta6a xaton abinda ya mata ba, shi kam ina ya ga strength din hanata kukan nata da kiraye kirayen sunan Umma, kyaleta kawai yayi tayi me isarta, daga karshe ma tashi yayi ya shige bandaki ya kulle, wannan dare dai daga Aneesah har su Aunty kusan kwanan xaune suka yi, Aneesah ta ji dama ta mutu kafin safiya da wannan mugun abinda taji ma kunnenta, Falmata kuwa sae cewa take da gangan Jiddah ta dinga wannan abun duk karya ce, abu ne da aka kissa mata tun daga gida, Abuturrab ya fi awa daya a bandakin kafin ya fito wajajen karfe uku saura, switch din dakin ya kunna ya ganta kwance kasan tiles ta takure waje daya tana bacci, bai san lkcn da yayi murmushi ba ya kashe wutan ya nufeta ya duka a hankali ya kai hannu xae dauketa, wani ihun ta sakar masa a raxane, ya rufe bakinta da sauri murya can kasa yace "Ba abinda xan maki..." Daukanta yayi ya kwantar da ita saman gadon ya lullubeta da blanket, ita dai jikinta banda bari babu abinda yake, ta gama tsorata da lamarin Abuturrab, don ma ta saki jiki tayi bacci without fear, far end of the bed ya tafi ya kwanta ya juya mata baya, kasa bacci yayi gaba daya daren nan, tunaninsa kawai ya ranan da xae san jiddah xai kasance, gaba daya ya gama gano cewar raguwa ce kuma matsoraciya, ba ma wannan ba he couldn't find any way duk kokarinsa, unlike Aneesah... which the case is different on that very day... Da asuba a kan kunnen Aneesah ya bude kofa ya tafi masallaci, bai kuma tafi masallacin ba sae da ya sa ma kofar dakin Jiddah key, bayan ya gama azkar dinsa a masallaci ya shigo gidan, bude kofar dakin yayi ya ga har sannan Jiddah bata tashi ba duk da ya tasheta tayi sallah kafin ya fita, karasawa yayi ya xauna gefen gadon yana kallonta ya kai hannu fuskarta yana shafawa gently, sae kuma ya ta6a forehead dinta ya ji da dumi, a firgice ta mike xaune ta koma baya yace "Are you okay?" Ta kasa kallonsa xata sauka saman gadon ya jawota, ji yayi jikinta da xafi ta marairaice masa tace "Xan je in yi sallah" yana kallon duk jikinta yace "Are u feeling pain anywhere?" Girgixa masa kai tayi bata yarda sun hada ido ba ta wuce bandaki da sauri, gaba daya she looks afraid, ya bi ta da kallo, toh ae shi kuma ba irin wannan tsoron nasa yake son ta dinga yi ba, yana ta xaune har ta fito bandaki ta tada sallah... Bayan ta idar ta ki daga kai ta kallesa, a hankali yace "Jidderh" Kamar jira take ta fashe masa da kuka taki yarda ta kallesa, yayi kasa da murya yace "Ki je kiyi wanka ki shirya" ita dai bata ce komai ba, ya mike ya fita dakin sannan ya kulle da makulli ya tafi da makullin bangarensa, wanka yayi ya shirya cikin kananun kaya ya dau jakar laptop dinsa da makullin mota sannan ya fito, yana xaune dakin nata ya jira har ta gama shiryawa, ko da wasa bata yarda ta shirya a gabansa ba, a bandaki tayi komai, shi dai kawai murmushi yake yana danna wayarsa, bayan ta fito ya sa ta hada kayanta kala uku a karamin jaka ya amshi jakar sannan suka fito dakin, kulle kofa yayi ya sauka downstairs tana biye da shi, babu kowa a parlon infact kamar ba mutane gidan ma gaba daya, Jiddah dai ta xauna kan kujera har sannan taki yarda su hada ido da shi, shi kam sai kallonta yake don hakan da take dariya yake basa, Wayarsa ya ciro ya shiga kiran Aneesah, Aneesah dake xaune dakin da su Aunty suka kwana idonta yayi bulu bulu ta kalli wayarta dake hannunta, sai kuma ta jefar da wayar gefen gado fuskarta daure, Safara'u ta dauka ganin me kiran wayar ita ma ta ajiye a gefe, Aunty ta kallesu tace "Wa ke kiran nata?" Safara'u ta kyabe baki tace "Shi yake kiranta, to uban me xata masa? Ki ita xata gasa masa amaryar" Aneesah ta matse kwallar idonta, Aunty tace "Je ki kiji kiran meye yake maki, tashi ki je" Aneesah dai bata ce komai ba, Safara'u tace "Tabbb!! Lallai ni naga abinda ban ta6a ji ba jiya, a cikin surkanka sbda baka daukesu da mutunci da kima ba? Muna gidan xai yi wannan ta6arar?" Ba dai wanda ya amsa mata, ta kalli Aunty tace "To idan mu ya maida mu banxa ke kuma fa? Yana fa sane kina gidan nan ba tafiya kika yi ba yayi abinda yayi, idan uwarsa ce ke gidan xai yi haka?" Aunty dai takaici, bakin ciki, da bacin rai duk ya baibayeta, yanda take ji iyakar haka Aneesahn ma xata ji, Aneesah ta sakar masu kuka tace "Ce min fa ku ka yi har xamansu ya kare ance baxai kusanceta ba, haka fa ku ka ce min, kuma duk kun ji abinda aka yi a gidan nan jiya, shkkn sai ya ji dadin min kallon gantalalliya kenan? Shkkn sai yaji dadin fara min gori kenan" Kuka sosai take cike da takaici, Aunty tace "Haka aka ce maki ya kusanceta? Ke baki san makircin mace bane, wllh wllh baxan yi kaffara ba babu abinda ya wakana tsakaninsu, an fa gaya min komai, to meye na daga hankali, ashe ma abu me sauki ne kusantar nata, tsabar makirci ne kawai irin na mata fa" Mikewa Aneesah tayi ta dau wayarta ta fita dakin ganin yana sake kiranta, sai da ta shiga dakinta ta dau hijab har kasa ta saka ta jawo hijab din ya kusa rufe rabin fuskarta sannan ta daga kiransa kafin tace komai yace "Ki sauko downstairs yanxu" Bai jira me xata ce ba ya katse wayar, saukowa kasa tayi ta gansu xaune a parlon, bata yarda ta kalli inda Jiddah take ba, kamar yanda Jiddah ma ta ki kallon inda take, ta tsaya bayan kujera babu yabo babu fallasa tace "Good morning" yace "Morning, dama xan ce maki xan koma aiki, hope ba ki bukatar wani abu?" Aneesah ta d'an saci kallon Jiddah dake sanye da Hijab har kasa ta sunkuyar da kai, sai kuma tace "Toh fa!! aiki kuma captain? Har an gama cin amarcin kenan? Ni da na xata hutu xaka dauka" Bai bata amsa ba kuma bai kalleta ba, tayi murmushi tace "Toh shkkn Allah ya tsare hanya, amma baxa kayi breakfast ba?" Yace "Xan yi a jirgi" tana ci gaba da murmushi tace "Toh shkkn, in Allah ya yarda babu wata matsala har kaje ka dawo, hope ka gaya mata ta saki jikinta da ni, ni kam kai ma kasan bani da matsala, xa kuma mu xauna lafiya xan dauketa tamkar kanuwata... Babu wani damuwa" Sai a sannan Abuturrab ya daga kai ya kalli Aneesah, tayi murmushi irin tana assuring dinsa din nan kar ya ji komai, bai ce mata komai ba, sai tace "Amma baxa ka shiga ka gaisa da su Aunty ba kafin ka tafi? sun tashi fa" Yace "Xa mu yi hakan ta waya, Jiddah kuma da ita xan tafi..." Sosai gaban Aneesah ya fadi tana kallonsa don duk a tunaninta barin Jiddah xai yi tunda dai ba xama xai je yayi a waje daya ba, A hankali tace "Da ita kuma? Naga ai ba xama kake a gari daya ba" Yace "Ehh" yana fadin haka ya mike ya dau jakar kusa da shi yace "If there is anything sai ki kirani" yana kallon Jiddah yace "Tashi mu je" a hankali ta mike ta nufi kofa tana tafiya kamar bata son yi, Aneesah ta bi ta da wani irin kallon tsana, ya bi bayanta har suka fita parlon, da gudu ta koma sama taje sanar ma su Aunty ai da Jiddah xai tafi.... Karfe biyar Abuturrab ya shigo gidansa na Abuja bayan sun sauke jirgi a garin Abujan, Jiddah ta xauna parlon da babu abinda ya canxa daga yanda ta san shi months back, har a lkcn taki sakewa da Abuturrab har xuciyarta taji tsoronsa take, bayan wani lkci ta saci kallonsa suka hada ido don kallonta yake, dauke kanta tayi da sauri, yyi lowering voice dinsa yace "Since u are uncomfortable staying with me here, sai ki shiga daki ko?" Ko rufe baki bai yi ba ta mike ta wuce daki tana rike da handbag dinta ta rufe kofar, ya bi ta da kallo yayi murmushi a ransa yace "Xaki ji tsoro me dalili soon yarinya" Da yake sun ci abinci a garin lagos kwanciya kawai yayi kan 3 seater yana kallon movie da ake yi a Tv, shidda da yan mintuna aka danna bell din parlon ya mike ya isa kofar sanin wanene, ya bude kofar, Ahmad na murmushi ya shigo yace "Latest ango in town, irin wannan fresh din haka Captain... Uhnnn" Abuturrab ya shafa kansa yace "Xan dai yi fresh din" Xaunawa suka yi kan kujera Ahmad yace "Toh ina Jiddar? Kace min kuna tare" Abuturrab ya kalli hanyar bedroom kafin yace komai Ahmad yace "Ohh shigewa ciki kace tayi don na xo??" Abuturrab yace "Not at all, i think bacci take yi, she is been inside since" Ahmad yace "Better!! Hope ka dau shawaran da na baka?" Abuturrab yace "Wanne a ciki?" Ahmad ya hararesa, a hankali Abuturrab yace "I want to ask u Ahmad" Ahmad yace "I am all ears" Abuturrab ya d'an yi shiru sai kuma ya shafa beard dinsa alamar dai ya rasa ta inda xai fara tambayar, Ahmad yace "Akan me kake son min tambayar?" Abuturrab yace "Marital Bed" Dariya Ahmad yayi yace "Then we should chat..." a hankali Abuturrab yace "That will be better" Ahmad yace "Hope no intimate relationship took place between u and...." Abuturrab ya kallesa yace "I couldn't find the way" Wani dariya Ahmad ya fasa ya jinginar da kansa jikin kujera, Abuturrab ya hade rai yana kallonsa, Ahmad yace "We really need to chat about that then, so bak'in naka sun bar gidan ko suna nan har yanxu" Abuturrab yace "Suna nan" da mamaki Ahmad ke kallonsa, can yace "Ohk haka xa ka xuba masu ido kenan, na gaya maka they have a mission to accomplish ka ki taking dina serious Captain, tun da can me ya sa basu xauna gidan naka ba gaba dayansu sai yanxu?" Abuturrab dai bai ce komai ba. Ana kiran magrib Abuturrab ya shiga dakin da Jiddah ke ciki ya sameta tana bacci, ya rasa me yasa ta dawo so silent, ya tasheta tayi sallah, sannan suka fita masallaci tare da Ahmad, bayan sun dawo masallacin Ahmad yace "Baxa mu je can gidana ku ci abinci ba" Abuturrab yace "Is ur wife around?" Ahmad yace "Yea tun da Jiddah ta koma gun Umma kawai na dawo da ita Abuja, baka yi mamakin me yasa na rage xuwa weekend kd ba" Abuturrab yace "Ohk ban sani ba" Daki Abuturrab ya shiga ya sa Jiddah ta shirya su tafi gidan Ahmad, hijab dinta kawai ta sa ta fito, ta gaida Ahmad tana sunkuyar da kanta ya amsa da murmushin sa, Ahmad hira kawai yake da Captain, amma da ta daga kai sai sun hada ido da Abuturrab dake kallonta, daga karshe ta koma can end din a hankali ta xauna har suka isa gidan. Sosai Ramlah tayi farin cikin ganin Jiddah a gidanta don Ahmad bai gaya mata suna xuwa ba, Jiddah ma taji dadin ganinta sosai. Abinci ta kawo masu nan parlon, Ahmad ya dibar masa shi da Abuturrab, ita dai Jiddah na xaune kan kujera idonta na kan tv dake aiki, Ramlah ta xuba masu a plate ita da Jiddah tana kallonta da murmushi fuskarta tace "Sauko Aunty Jiddah" Jiddah dai tayi murmushin karfin hali amma bata sauko ba, Ramlah tace "To tashi mu shiga ciki" Ba musu Jiddah ta mike ta bi ta suka wuce bedroom dinta, Ahmad dake kallon Abuturrab da ya bi Jiddah da kallo yace "Uhnn wannan kallo haka Captain?" Abuturrab ya shafa kansa ya ci gaba da cin abincin gabansu... Ba laifi Jiddah ta ci abincin don a lagos ta ki sakewa ta ci sbda Abuturrab da ya sa ta gaba, hira suka dinga yi da Ramlah har aka yi isha, karfe takwas da rabi Ahmad ya shigo dakin da sallama yana kallon Jiddah yace "Captain na jiran ki Jiddah" Marairaice masa tayi tace "Ya Ahmad don Allah kace masa ya bar ni in kwana a nan" Tana fadin haka sai hawaye ya cika idonta, shi dai Ahmad dariya ta basa, Jiddah ta kalli Ramlah tace "Don Allah ki masa magana ya bar ni a gidan nan" Ramlah tayi dariya tace "Aa wnn sai dai Dr yayi masa magana" Ahmad na kallon Jiddah yace "Ki je ki gaya masa xai bar ki ma sani" Gaba daya a tsorace take, Ramlah dai sai kallonta take, Ahmad yace "Yea kije ki gaya masa xai bar ki" A sanyaye ta mike ta fita, Ramlah ta wara ido tace "Toh ko tsoron Yayan take?" Ahmad yayi murmushi ya xauna gefen gado, Jiddah na fitowa parlor suka hada ido da Captain dake xaune, karasawa tayi kanta a kasa ta durkusa d'an nesa da shi a hankali tace "Dama don Allah ka bar ni in kwana a nan plsss" Kallonta ya dinga yi, ta daga kai ta kallesa jin yayi shiru, lkci daya hawaye har ya kawo idonta, yace "Tsorona kike ji Jiddah?" Girgixa masa kai tayi da sauri, yace "Toh shkkn, sai da safe" Mikewa yayi ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, sai kuma jikinta yayi sanyi, amma dai wata xuciyar tace mata gwara haka, da dai abinda Allah ya nuna mata jiya gwara kawai ta kwana gidan Ramlah. Washegari Abuturrab yayi piloting xuwa Kano leaving Jiddah behind in Abuja shi kansa ya ga hakan ya fi tunda ya lura bata son hawa jirgi, a kwanaki hudun nan duk abinda Ramlah ke amfani da shi na mata wanda Umma ta hana Jiddah haka ta dinga bata, to tunda ita bata san meye shi ba haka xata amsa ta sha, all this while kuma Aunty da su Safara'u na gidan Aneesah suna jiran dawowar Abuturrab da Jiddah gidan, Ranan Thursday Ramlah na parlor tare da Jiddah aka danna bell, mikewa Ramlah tayi ta nufi kofar ta bude tana tambayar waye, Abuturrab ta gani tsaye bakin kofar, ta washe baki tace "Sannu da xuwa yaya" sai kuma ta basa hanya ya shigo parlon, sai da gaban Jiddah ya fadi da ta hada ido da shi, ya karaso ya xauna parlon yana kallonta yace "Tashi ki dauko kayanki" Ramlah dai na tsaye gefe sai murmushi take, Jiddah taki motsawa a inda take, Ramlah tace "Mu je ai kayan a hade suke" Daga haka ta nufi dakin da jakar kayan Jiddah wanda Ahmad ya taho mata da shi yake, mikewa Jiddah tayi ta bi bayan Ramlah tana tafiya kamar xata yi kuka ya bi ta da kallo, Ramlah ta rufe kofar bayan Jiddah ta shigo tana kallonta tace "Me yasa kike haka Jiddah yana maki magana kin yi shiru" Jiddah ta fashe da kuka ta xauna gefen gado, Ramlah ta xauna kusa da ita da mamaki tace "Gaya min meye damuwarki?" Cikin kuka tace "Wallahi ni tsoronsa nake ji" Sake baki tayi tana kallonta, can tace "Tsoronsa kuma Jiddah? To saboda me" Jiddah tayi shiru tana share idonta xuciyarta na bugawa, Ramlah tayi shiru sai kuma tayi murmushi tace "Kin ta6a jin inda mata ke tsoron mijinta? Look Jiddah ki ajiye duk wani kuruciya aside babu wannan a aure sannan kishiya gareki, kishiyar kuma ba mai tsoron Allah ba, ko so kike ta kwace maki miji?" Kallonta Jiddah ta dinga yi, Ramlah tace "Wllh idan kina masa haka fita harkanki kawai xai yi ya kama kishiyarki tunda ita ai bata tsoronsa, dubi ranan fa kiri kiri kika ki binsa sai shi kadai yayi wucewarsa, so kike ya daina kulaki ya barki da tsoronsa da kike?" A hankali Jiddah ta girgixa mata kai, Ramlah tace "To kar ki sake yarda ki sa ma ranki kina tsoron mijin ki, kuma kar ki xama raguwar mace... It's something that happens just once in lifetime, you get me" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Ramlah ta mike ta dauko jakarta ta mika mata tace "Tashi ki je yana jiranki, sai da safe, xan kira wayarsa gobe sai ya baki mu yi magana" Jiddah ta goge idonta ta amshi jakarta. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp [7/26, 9:10 PM] Ummuanwar🥰: Har suka isa gida Abuturrab bai ce ma Jiddah komai ba, ita ma dama ko hada ido bata yarda ta yi da shi ba, ya kunna switch din parlon sannan ya kulle gidan ya nufi daki, a hankali ta xauna saman kujera ta ajiye jakarta a kusa da ita, tana ta xaune parlon ita kadai har karfe tara, mikewa tayi daga karshe ta tafi saman 3 seater ta kwanta, har ta fara bacci ta ji ana jan hancinta, ta bude ido da sauri, ganinsa durkushe gabanta ta mike xaune, yace "Tashi ki je ki kwanta" Ta make kafada tace "Ni nafi son kwanciya kan kujera" Duk da dariyan da ta basa sai ya dake yace "Ni ke kwanciya kan kujeran ai shi yasa na tashe ki, go inside the room now" Tayi shiru sai kuma ta mike daga kan kujeran ta nufi dakin tana waigensa, kwanciya ta ga yayi kan kujeran ya lumshe ido, ta shige daya daga 3 room din tana kallon kofar ganin babu makulli a makale, a hankali ta lallabo ta fito ta shiga wani dakin nan ma babu makulli, wani dakin ta shiga shi ma dai door din ba makulli, ta 6ata fuska kamar xata yi kuka ta fito parlor ta tsaya tana kallonsa tace "Ban ga key a doors din ba" Bude ido yayi ya kalleta yace "Me xa kiyi da key?" A hankali tace "Ni nafi son in kulle kofa idan xan yi bacci" Yace "Toh haka doors din suka xo babu key" daga haka ya kulle idonsa, tana ta tsaye tana kallonsa kafin ta juya ta koma dakin ya d'an bude ido ganin ta tafi yayi murmushi, ta fi minti goma xaune gefen gado daga karshe ta kwanta ta takure waje daya tunda dama bacci take ji, babu bata lkci baccin ya dauketa, can cikin bacci ta ji ta a jikinsa, ya rufe bakinsa da hannunsa kafin ta kwala ihun da tayi niyya, yayi lowering voice dinsa yace "Tell me why u are afraid of me?" Shessheka ta fara yi masa, ya cire hannunsa a bakinta ya juyo da ita a hankali yace "Tell me plss, ko na ta6a yi maki wani abu da baki so ne?" Cikin rawar murya tace "Ehh" yace "Toh me na maki?" Tayi shiru, yace "Gaya min ina jin ki" A hankali tace "Kawai dai ni bana son kana ta6a ni" yace "Toh wa kike son in ta6a?" Nan ma tayi shiru, yace "Aneesah?" Daga kai tayi ta kallesa, sai kuma ta turo baki xata juya masa ba, ya ki barin tayi haka yace "Yanxu wajenta kike son in koma" a takaice tace "Toh ai dama a wajenta kake" Yace "Aa dake na fara xama ai kafin in xauna da ita" tace "Da ka zauna da ni ai ka ce ni ba matarka bace" Murmushi yayi, murya can kasa yace "Wasa nake maki a lkcn ai" Tace "Da gaske kake, tunda har ka rubuta ka bani" shiru yayi bai sake cewa komai ba, ta rufe idonta tana jin kamshinsa da ya cikata, a hankali ya kai bakinsa kunnenta yace "Amma duk abinda kike so ai ina maki, baki rasa komai a lkcn ba sai abinda nake maki baki so yanxu" Ya fadi hakan yana sake rungumeta closely, ta marairaice tace "Toh bana son hakan, kawai mu xauna yanda muka xauna wancan lokacin ya fi" Ya girgixa kai underneath his breathe yace "Baxan iya ba, wancan lokacin ma...." sai kuma yayi shiru, ta kallesa tace "Me?" Yace "Ba komai, yanxu dai kince baki son in dinga ta6a ki, gaya min wanda xan dinga ta6awa? Wajen Aneesah kike son in dinga xuwa? Kinga ita bata min haka" Ta ki cewa komai ta wani hade rai, yace "Tell me plss" a takaice tace "Toh ba sai ka je ba" Saketa yayi a hankali yace "Ohk fine" daga haka ya juya mata baya, kallonsa ta dinga yi sai kuma ta cusa kanta cikin pillow ta fara kuka a hankali, duk yana jin ta, bayan few minutes ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "ke fa kika ce baki son in dinga ta6abki" Cikin kuka tace "Toh ba kai ne sai ka dinga bani tsoro ba" yace "Gaya min ranan da na baki tsoro" a hankali tace "Ranan a can gida mana" Yayi shiru, sai kuma yace "Toh baxan sake irin wannan da ke baki tsoro ba, amma kuma idan kina min gardama sai in koma gun Aneesah don ita bata min...." ta kallesa tace "Gardaman me?" Yace "Xan nuna maki yanxu, amma ki sani kina gardaman wajenta xan koma da gaske tunda ni ina so" Ita dai tayi shiru gabanta na faduwa sosai, ya kashe wutan dakin tana kokarin guduwa ya rikota gam ya kai bakinsa kunnenta yace "Pls" very light love affair ya shiga yi mata wanda baxai tsoratata ba sai dai ma ya dimautar da ita, sosai yayi mamakin yanda tayi masa lamo idonta a rufe babu gardama, he don't know if she's relishing what he is doing to her or she just doesn't want him to go back to Aneesah kamar yanda ya fada mata, Ganin he is becoming uncontrollable ya saketa babu shiri don baxai so ta ci gaba da tsoronsa da take cewa ba, da kyar ya rada mata good night a kunne sannan yayi kwanciyarsa, ita dai har lkcn bata bude idonta ba, yana jin sanda ta fara bacci jin saukan breathing dinta a hankali, amma shi ya kasa baccin sai juye juye yake, daga karshe ma ya sauka kan gadon ya fita dakin ko xai samu relieve.... Da asuba bayan ya dawo masallaci ya shiga dakin ya ganta xaune kan darduma duk da bai tasheta ba, abinda bai ta6a ganin Aneesah tayi ba duk xamansu, kasa kallonsa Jiddah tayi, ya xauna gefen gado a hankali yace "Good morning...." tana wasa da fingers dinta a hankali ita ma tace "Ina kwana" yayi kasa da murya yace "How was ur night?" Kin ce masa komai tayi, ya shafa kansa yace "Ki shirya xa mu tafi kano anjima" Yana fadin haka ya mike ya fita dakin. Karfe sha daya saura suka nufi airport a Uber, kamo hannunta yayi jin tayi shiru, yayi kasa da murya yace "Tell me what you are thinking now... Yesternight?" Ai bata san lkcn da ta daga kai ta kallesa da sauri ba, ya kashe mata ido yace "You like it?" Dauke kai tayi ta turo baki, shi dai murmushi kawai yake yana kallonta yana murxa hannunta har suka isa airport. Kafin 12 suka sauka airport din kano, ita dai Jiddah kallon Abuturrab kawai take yana gaisawa da ma'aikatan airport din, duk inda ya bi xaka ji an kirasa da Captain, inda yake parking din motarsa a airport din suka tafi, bayan ya ajiye kayansu a bayan motar ya bude mata front seat ya wara manyan idanuwansa yana kallonta, ita dai bata yarda ta kallesa ba ta karaso ta shiga ya kulle sannan ya xaga ya shiga motar, bayan yayi warming dinsa suka fita airport din, muryarta ya ji tace "Me yasa ake kiranka Captain?" Ya d'an kalleta sai kuma yayi murmushi yace "Kema ki fara kirana da hakan mana" ta ta6e baki tace "Baxan kira ba" Yace "Saboda me?" Tace "Haka nan" Yace "Toh kinga ai Aneesah ma haka take kirana" ta kallesa da kyau tace "Dalilin da yasa baxan kiraka haka ba kenan ai, na fi ka sanin haka take kiranka" Sosai ta basa dariya jin how serious she was, yace "Ohh really" confidently tace "Ehh, kuma ka daina min magananta bana so, komai sai ka wani kira min ita as if i have anything to do with her, meye hadina da ita?? To ni bana so, ka daina min haka" a hankali yace "Toh ya hakuri, na daina" Hade rai tayi ta dauke kai tana kallon wajen glass, haka nan kawai yaji reaction din da tayi displaying ya masa dadi, murmushi kawai yake yana tukinsa, can ya kamo hannunta a hankali yace "Na fa ce kiyi hakuri na daina tunda baki so, why are u sulking? Why the pout now" Hade kai tayi da gwiwa xata fara kuka tace "Komai sai ka wani ce min Aneesah ni meye ruwana da ita to?" Cikin sanyin murya "Toh ai nace kiyi hakuri baxan sake ba koh?" Ta dago kanta tana matsar kwallan da ya kawo idonta, yayi kasa da voice dinsa yace "i am sorry dear" Ita dai bata ce komai ba, suna fara nisa a tafiyar ta jinginar da kanta da kujera ta lumshe ido, yana ganin alamar bacci xata yi, yayi parking ya d'an kwantar mata kujeran motar sannan ya ci gaba da tafiya. Suna shigowa garin kaduna Abuturrab ya dau wayarsa yayi dialing number Aneesah, har ya katse bata dauka ba, ya sake kira nan ma sai da ya kusa katsewa sannan ta daga tayi shiru, ajiye wayar yayi bayan ya sa a handsfree yace "Baki ga miss calls dina bane jiya da daddare da yau da safe?" Jiddah ta d'an sace kallonsa sai kuma ta dauke kanta, A takaice Aneesah tace "Ehh" yace "Ohk good, ya gida?" Tace "Yana nan yanda ka bar sa" Yace "Bak'in ki sun tafi?" Tace "Su tafi ina? Dama ashe a kanka suke xaune ban sani ba, dama sun tare maka wani abu kenan? kuma ai naga bak'in nawa guda biyu ne a ciki, kuma su kadai nake da ikon ce ma su tafi, Daya bakuwar kuwa kai ke da hurumin ce mata ta tafi ba ni ba ai" Shiru yayi na few seconds sai kuma yace "Kina son xaman lafiya da ni kuwa Aneesah?" Tace "Inaaa sai xaman tashin hankali, xaman lafiya kam ai sai da uwar gida kamar yanda ka taso kaga ake yi a house, to meye abun mamaki don ka bi footstep din? ai ba abun mamaki bane wannan" Yace "What???" Tace "Ya uwargida? Fatan ana cin amarci yanda ya kamata..." katse wayarsa yayi, Jiddah ta kallesa tace "Kaga ka ja mata kunne ta cire bakinta da idonta a kaina babu abinda na hadata da ita, ba ruwana da ita..." Abuturrab da xuciyarsa ke tafarfasa jin maganan da Aneesah tayi masa ya nufi gidansu kawai, a compound yayi parking ya kalli Jiddah da ta wani hade rai tun bayan tambayarta da Aneesah tayi, bude motar yayi ya sauka, ta bude ita ma ta sauka, xagayowa yayi yana kallonta, a hankali yace "Toh xan ja mata kunne Ummi" banxa tayi masa, yayi murmushi suka shiga gidan a tare, parlon Ummi suka shiga bayan ya gaida Umminsa ya fita ya bar su ya shiga dakin Hajja, Nafisah na xaune dakin sai dariya take kasa kasa, Hajja kuma na xaune saman darduma ta maka wani uban glass a idonta ta sa wani lafiyayyen leshi ta yafa mayafi, ga dankunnenta da sarka kai kace anguwa xata amma wayar Nafisah ne a hannunta suna gaisawa da wasu makotansu na Masar bakinta har kunne, duk ta cika dakin da muryarta tana jagwalgwala larabci da Hausa, Tun Nafisa na dariya kan kujera har ta sauko kasa, ko bin ta kan Abuturrab dake tsaye yana kallonta Hajja bata yi ba, da sauri ta mika ma Nafisah wayar tace "Ke taho ki duba sun daina motsi ko notwork din ne ya dauke" Abuturrab ya amshe wayar ya kashe data sannan yace "Daga can network dinsu ya dauke sai xuwa dare xaku iya sake magana da su" rai bace Hajja tace "Toh Allah ya tsine wnn notwork din, don rashin tsoron Allah baxai bari ayi xumuncin da Allah yace ayi ba?? Ni naga bala'i amma lefin wanda suka dauke shi notwork din ne, to ya wuce arnaye da basu san meye xumunci ba..." Abuturrab dai bai tanka ta ba ya mika ma Nafisah wayarta, Hajja tace "Kawai ina xaune fa Nafisah ta shigo wai ai gashi takwararta daga can Masar ta kira tace ta kawo min waya xamu gaisa da mokatanmu da aka yi xaman mutunci na can Masar din, baka ga yanda suke ji da ni suke sona ba wllh, ashe duk sun yi kewata ni ina nan ban sani ba, kasan fa duk safiya ina fitowa in xaga titin anguwan su Nafisah ba irin rubabbun titunan Najeriya ba da idan baka yi hankali ba idan ka afka wani ramin da kyar xa a fiddoka idan ma ba shi ne ajalinka ba, makociyar tata ma tare suke da uwarta shine muke kawance da uwar amma uwar duk ta kwararrabe, kasan tsufansu fa bashi da kyau, wllh yamushewa kawai suke kamar fanken da ya huce, to Nafisah na gaya min na yi maza maza na bude akwati na ciro tsadadden leshi na da mayafi wanda na sa da bikinka da yar iskar can, na ciro dankunne da sarkata na saka, sannan nayi maxa na ciro gilashina na saka shi ma, na shimfida darduma na xauna, to ai dai gwara haka ko?" Abuturrab yace "Gaskiya" Hajja tace "Atoh, kawai sai su ganni su xata wahala nake sha a Najeriyan duk da dai wahalan nake sha don babu komai xama gidan Usman sai wahala, kawai saboda Hauwa nake xaune in ga ta yanda xai dawo da wancan bokanniyar da na ya saka...." Xaunawa Abuturrab yayi yana kallon Nafisah yace "Ba an gama wayar ba?" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita, Hajja tayi kasa da murya tace "Ina Jiddar??" Yace "Tana parlon Ummi, na xo mu yi magana da ke ne" Hajja ta gyara xama ta cire gilashinta ta ajiye tace "Ina sauraronka, ai gwara da ka korata don bakinta baya haila" Yace "Dama tun ana gobe xa a kai Jiddah can gidana Aunty da yan uwan Aneesah guda biyu ke gidan, kuma har yanxu sun ki tafiya ban san xaman me suke ba" Hajja tace "Wacece kuma Aunty?" Kallonta kawai yake, ganin da gaske bata gane wace Auntyn ba yace "Auntyn nan gidan" Hajja ta gwalo ido tace "Hafsah???" Yace "Ehh" Salati Hajja ta rafka ta rike kai tace "Huhuhu dama Hafsah na kaduna ban sani ba, sannan kadunan ma gidanka? Me ya kai ta gidanka ni 'ya su?" Abuturrab yace "Nima ban sani ba" Buda baki Hajja tayi tace "Yaushe ta tare gidan naka bani da labari?" Yace "Fin sati daya kenan" Mikewa Hajja tayi tana gyara yafin gyalenta tace "Mu tafi gidan, tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin inda matar uba ta tare gidan d'an kishiyarta ba bayan miji ya saketa, ai shkkn kuma ta kashe maka gida don Allah kadai yasan karatun da ta dinga xuba ma Aneesah na makirci da kuma gun bokaye nawa ta kai ta, Amma Allah ya tsine ma Hafsah albarka, Allah yayi daya daya da ita, mu tafi gidan yanxu duk xa su ci kuturin ubansu, ni da nake er banxa kuma, ae ba canxawa nayi ba" daga haka ta fice daga dakin, murmushi Abuturrab yayi ya mike ya bi bayanta, parlon Ummi ya fara shiga ya tarda ita tana yi ma Jiddah dake xaune kasa ta sunkuyar da kanta Nasiha, Ummi na ganinsa tace "Toh tashi ki je ki gaida Hajjan" Abuturrab yace "Xa mu je can gidan tare da ita yanxu" Ummi tace "Hajjan?" Yace "Ehh" tace "Toh Allah ya tsare, baxa ku tafi da abinci ba?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Toh ki bata ta taho da shi, xan je mota Hajja na waje" Ummi tace "Toh shkkn" Juyawa Abuturrab yyi ya fita, Bayan Ummi ta xuba ma Jiddah abincin a warmer biyu ta ba Nafisah ta kai mota Jiddah na biye da ita a baya suka fita kofar gida, a bayan motar Jiddah ta xauna bayan ta gaida Hajja, sannan ta ajiye warmer din abincin gefenta, Hajja na kallon Abuturrab tace "Ya naga ta xabge haka daga tarewa Aliyu? A cikinsu ka bar ta ka tafi tukin jirgin naka ne?" Yana kallonta ta madubi yace "Daga kano muke yanxu haka" Hajja tace "Atoh dole ta rame, maxa kai ni gidan, tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin wannan tabargaxan ba sai yanxu da xanje in gane ma idona, matar ubanka ta tare gidanka bayan an saketa matar da ba shiri take da uwarka ba ta rasa yanda xata yi da ita ne kawai? Mu je kawai in fatattaki yan iska, Allah da a Masar ne har kai da ka bar su na sati dayan a gidanka sai an hukunta ka don cewa xa ayi kai ne babban d'an iskan, ai duk wanda bai xauna a Masar ya ga yanda suke rayuwa ba yayi asara a duniya, Allah yayi ma kasar Masar da mutanen cikinta albarka sun koya min abubuwan rayuwa iri iri wllh, ba gashi ba daxu sbda xaman mutuncin da muka yi da su kirana suka yi ta wayar salulan Nafisah muka gaisa muna ta xabga larabci da su" Babu wanda ya tanka Hajja a motar har suka isa gidan Abuturrab, parking yayi a parking space sannan ya sauka motar, Jiddah ma ta sauka ta dau warmers din biyu, tuni Hajja ta bude daya side din motar ta sauka tayi cikin gidan, Abuturrab ya kalli Jiddah ya xaga ya amshi warmer daya a hannunta yayi kasa da murya yace "Kin gaji ko?" Bata ce komai ba ya dau makullin dakinta a mota ya mika mata yana kallonta yace "Mu je" Ta fara tafiya yana biye da ita, tuni Hajja ta shige parlon gidan ta ci sa'ar ganin Aunty, Safara'u, da Falmata xaune a parlon, Aneesah kuma na kitchen tana dafa masu indomie don dawowarsu daga wani waje kenan, Duk suka juya suna kallon Hajja, Hajja ta rafka wani uban salati tace "Wacece wannan nake gani kamar Hafsah tsohuwar matar Usman??" Tun da Aunty ta kalleta sau daya ta dauke kai tana ci gaba da danna wayarta tana taunar chewing gum, Hajja ta karasa tsakar parlon tana kallon su Safara'u tace "Su kuma masu k'iran samudawan nan fa??" Hajja ta rike kai tace "Huhuhu gidan Aliyu ya xama dandalin zawarawa, an shiga uku an lalace, to wllh baxai sa6u ba ko wacce ta tashi ta tafi gidan ubanta, idan ya kama ku tafi har da Nanisar ce to ku tafi don ai sbda ita ku ka xo dama...." Aneesah ta fito daga kitchen da sauri jin hayaniya, Safara'u na kallon Aneesah cike da izgilanci tace "Ke... wacece wannan kuma ta shigo mana haka ba control?" A fusace Hajja tayi mata dakuwa tace "Uwaki ce ta shigo.... shegiya kawai 'ya yan banxa gayyar tsiya, har ni xaki kalli tsabagen idona kice baki san ni ba, to uwar uban Aliyun ce, kuma tun muna imu imu ba a jiyo kanmu a titin anguwan nan ba ko wacce ta tashi ta dau jakanta ta kama gabanta, gidan jikana ba dandalin karuwai bane, mu ba arnaye bane..." Falmata ta mike tana mata wani kallo tace "Ai kuwa mu ba karuwai bane wllh... Mun fi karfin a kira mu da haka..." Tuni Hajja tayi hanyar stairs bayan ta jefa mayafinta saman kujera xata je watso duk jakunkunan da ta gani a sama, Dai dai nan Abuturrab ya shigo parlon, Safara'u ta mike ta nufesa tana huci ya ki tsayawa har yaje ya ajiye abincin hannunsa saman dining table, ita kuwa bata fasa bin sa ba tana cewa "Ashe dama kai ka gayyato mana tsohuwar can ta xo ta mana tijara tayi mana rashin mutunci?" Abuturrab ya juya yana kallonta yace "Ehh, 'yar ku nake aure ba ku ba ai, so i see no reason xa ku tare a gidana for more than a week now..." Mikewa Aunty tayi ita ma ta nufesa xuciyarta na bararraka tana nuna sa da yatsa tace "Don ubanka ai baka burge ba da har kai ka kasa magana sai da ka gayyato mental kakarka... Kuma baka burgeni ba da baka gayyato axxalumar uwarka ta xo mun goga a nan da ita ba, ita ya kamata ta xo ta nuna iko ba tsohuwar can ba, daga nan sae mu cashe da ita" Abuturrab na kallonta da kyau yace "I do respect u for being my father's wife then.... Kar ki sake involving mahaifiyata a lamarin ki, take my mothers name off ur mouth Aunty Hafsah, do not push me...." Bude baki Aunty tayi tana kallonsa da mugun mamaki, Ita dai Jiddah tunda ta lallaba ta shigo gidan ta haura sama abunta ba tare da ma anyi noticing dinta ba, mari Aunty ta kai masa tana huci, cikin tsawa tace "Ni kake warning Aliyu?? Ni yau kake warning a kan uwarka?" Kallonta kawai yake trying so hard to control his rising temper, ta cakumosa tace "I am asking u, ni kake yi ma warning? To da kai da matsiyaciyar uwar taka kun ci kaxa kaxan ku" Falmata dake tsaye wajen tace "Atoh ae ba ke kika haifesa ba what did u expect..." Ko rufe baki bata yi ba Abuturrab ya sauke mata tagwayen mari masu lafiya, lkci daya ya nufi Aneesah dake tsaye har sannan bakin kofar kitchen, sae da idanuwansa suka bata tsoro amma ta dake tana kallonsa, strictly yace "Minti ashirin idan suka kara min a gidan nan to a bakin aurenki, minti ashirin din na cika dama ki tattara ki bi su, don ko kayanki baxa su kwana min a gida ba" Daga haka ya nufi stairs kamar xai tashi sama, Aunty ta bi sa da kallo baki a hangame, Falmata kuwa ji tayi gaba daya jinta ya dauke sai dumm kawai take ji, daga sama aka dinga jefo jakunkuna da handbag downstairs, Aneesah ta nufi Safara'u da sauri cikin tashin hankali tace "Don girman Allah Aunty ku rufa min asiri ku tafi kar ku kashe min aurena, i will sort everything out my self, don Allah ku rufa min asiri ku tafi" tana gama fadin haka ta tafi da sauri tana dauko jakunkunan da Hajja ke watsowa tana ajiye masu a tsakar parlon, tsaf sai da Hajja ta watso komai kasa sannan ta sauko tana huci tace "Ko wace karuwa ta dau jakarta ta bar min gidan jikana, idan kuwa ba haka ba wllh yanxun nan sai in sa shi ya saki Nanisar in ga ta tsiya, daga nan kunga ba ku ba, har ita baxata kwana gidan ba...." Aneesah da duk ta rikice ta nufi Hajja da sauri tace "Xa su tafi Hajja, duk yanxu xasu tafi idan Allah ya yarda" Safara'u da tunda take ba a ta6a mata cin mutunci irin na ranan ba a tunaninta ta nufi jakarta ta dauka ko gyale bata tsaya yafawa ba ta nufi kofa tana rike da shi a hannu, Falmata ma ta tafi ta dau jakanta ta bi bayan Safara'u, Hajja tace "Banda ma arne wa xai yi wannan abinda ku ka yi?? Ke an sake ki kin ki tafiya benue kin tattaro kin dawo gidan d'an kishiyar da kika yi ta cuta na shekara ashirin da shidda, tirrrr anji kunya wllh Hafsah" Hafsah na kallon Hajja tayi Murmushi rainin hankali tace "Ai ni da Usman mutu ka raba, ko ke da kika haifesa baki isa ki raba mu ba wllh, ke dai ce kike tunanin ai ya sakeni, amma babu abinda ya canxa game da matsayina a wajensa lkci kawai ake jira" Daga haka ta nufi kofa bayan ta dau gyalenta, ko ta kan jakarta bata bi ba.... Hajja ta bi ta da kallo baki bude tana tunanin to aurensu Usman ya mayar bata sani ba??? Ai bayan fitansu ko minti biyar bata kara a gidan ba ta sa Abuturrab ya maida ta gida, tana isa gidan kuma ta doka ma Abba kira duk inda yake ya dawo ya sameta, da kyar dai ya lallabata a kan sai ranan lahadi xai shigo kaduna, sai karfe shidda saura Abuturrab ya koma gida bayan ya ajiye Hajja, don gaba daya hankalinsa na kan Jiddah duk da ya sa ta kulle dakin nata da makulli. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppJiddah ta mike ta isa kofar dakinta ta bude a hankali jin ana knocking, juyawa tayi ta koma ciki bayan sun hada ido, Abuturrab ya shiga dakin sannan ya kulle kofar yace "Kin ci abincin?" Ta girgixa masa kai, bude warmers din da ya ajiye mata kafin ya maida Hajja gida yayi, yace "Why, baki son tuwon ne?" A hankali tace "Aa xan ci" Debar mata yayi a plate ta sauko kasan carpet ta xauna, ya ajiye mata abincin a gabanta, tace "Kai baxa ka ci ba?" Ya mike yace "Nahh.. Bana cin tuwo" Kallonsa kawai take, ya cire agogon wrist dinsa ya ajiye gaban mirror dinta ya nufi bathroom, bin sa tayi da kallo sannan ta fara cin tuwon a hankali, a nan dakin Abuturrab yayi sallan la'asar don bai samu jam'i ba, bayan ya idar ya dau agogonsa yana mayarwa ta kallesa tace "Sai me xaka ci?" Juyawa yayi ya kalleta ya wara mata manyan idonsa yace "Kin damu in ci abinci ne?" Turo baki tayi ta ci gaba da cin tuwonta, ya xauna yana facing dinta yace "Idan kina son in ci sai ki girka min, don ni bana cin tuwo" shiru tayi tana kallonsa, ya mike ya nufi kofa ya fita daga dakin, downstairs ya sauka yayi powering Tv ya xauna, maganganun Aunty ne kawai suke dawo masa da xagin da tayi ma Umminsa, sosai yaji xagin ya tsaya masa a rai, she insulted his world and went scot free, ya jinginar da kansa da kujera yana mata fatan Allah ya sa na karshen kenan tayi a gabansa don next time ta sake xagin mahaifiyarsa xata ga true color dinsa he won't mind duk abinda Abbansa xai masa, rayuwarsa a baya ya dinga tunawa da yanda komai nasa sai yace sai Aunty, she knows all his savings, infact everything wanda Ummi ma bata sani ba, haka kawai yaji ya fara jin haushin kansa, he regret everything.... Jiddah ta gama cin tuwon da miyar vegetable ta tafi bandaki ta wanke bakinta sannan ta fito ta dau warmers din ta bude kofa ta fito, dai dai nan Aneesah ma ta bude kofar dakinta ta fito, hada ido suka yi Jiddah ta dauke kai ta nufi stairs ta fara sauka a hankali, Aneesah ta bi ta da kallo ko kiftawa bata yi, tunani iri iri ne a ranta a lkcn, sai kuma kawai tayi murmushi, Jiddah na sauka parlon ta karasa dining ta ajiye warmer din hannunta sannan ta dawo, shi dai Abuturrab bin ta kawai yake da kallo, ta shigo cikin parlon ta durkusa kan carpet daga kusa da kujeran da yake xaune, sai kuma ta sunkuyar da kanta tace "Me xa a dafa maka?" Kallonta kawai yake, ta daga kai ta kallesa, yayi kasa da murya ya kamo hannunta yace "Xa ki iya girki duk gajiyan da kika yi?" Tace "Xan iya idan akwai kayan girkin" Xai yi magana Aneesah ta sauko da mayafinta da jaka a hannu, sake hannun Jiddah yayi ya ci gaba da kallonsa, ta karaso cikin parlon tana kirkiran murmushi tace "Sannun ku..." Ita dai Jiddah ko kallonta bata yi ba, Aneesah ta koma ta daya side din tana satan kallon Jiddah ganin yanda ta wani durkusa gabansa kamar me neman gafara, wai miji xaka durkusa ma haka, what for? Kamar yanda Jiddah taki kallonta haka Captain ma da ya kafe idonsa kan tv yaki kallonta, can ta dai ta kallesa tana daga tsaye cikin sanyin muryarta tace "Captain pls ka d'an ara min car key dinka xan amso sako yanxu in dawo, baxan wuce minti ashirin xuwa talatin ba" a takaice yace "Ki jira ni a daki" ta d'an yi jim tana dubansa, Jiddah ta dago kanta suka hada ido da ita, wani shegen kallon tsana ta watsa mata sannan ta wuce sama kamar xata tashi, Abuturrab ya kalli Jiddah a hankali yace "Ki dafa duk abinda xai maki sauki baxai baki wahala ba" Shiru tayi bata ce komai ba, can ta mike ta nufi kitchen din figure dinta ya bi da kallo ba ita ba, sosai atamfar jikinta yayi mata kyau ya amshi fatar ta, xaka fi tunanin she is 20 not 18, tashi yayi ya shafa kansa ya wuce sama, Jiddah ta fi minti biyar tsaye kitchen din tana bin sa da wani irin kallo ganin yanda kitchen din is very untidy with dirty utensils scattered everywhere, shi kansa gas din duk abinci ne ya xuxxube yayi wani baki, sai a snn ta lura da wasu sabbin kayan kitchen a cikin kwalayensu masu yawa da aka jibge a babban store din dake kitchen din, juyawa tayi ta fito daga kitchen din ganin baya parlon ta haura sama ta shige dakinta tayi kwanta. Aneesah ta dinga kallon Abuturrab amma ta ki ce masa komai, ya rungume hannunsa yace "Lastly wannan fitan da kike anyhow babu excuse a gidan nan is cancelled from today henceforward, idan kin shirya xaman aure da ni kiyi respecting duk opinion dina Aneesah...." Cikin rawar murya tace "Yanxu don ka kara aure captain shkkn sai ka maida ni banxa a gidan nan bani da kima da mutunci a idonka? Did i deserve this... Me nayi maka da irin wannan dokokin da ka shimfida min?" yace "Wait... da nayi aure kin rasa ci ko sha a gidana? Kawai ina gaya maki abubuwan da xai sa mu xauna lafiya dake a gidan nan ne, idan kuma kina son xaman lafiyan nan dole kiyi abiding to all what i said" Ta fashe da kuka sosai tace "Har ni xaka kalla kace babu ruwana da matarka inyi harkana tayi harkarta kamar dai ni macuciya ce? dama haka ake yi ashe? Ba xaunar da mu xaka yi ka gaya ma kowa matsayin kowa a gidan ba sannan ka nemi mu hade kanmu kada a ji mu a wani wajen ba? Ba haka ko wani namiji yake yi ba ashe? Anya xaman lafiya kake son mu yi kuwa Captain?" Abuturrab yace "It's not necessary, kowa kuma ta san matsayinta a gidan nan ba sai na fada ba...." Ta goge idonta tace "To a kan me kuma xaka ce kada wata yar uwata ta sake shigo maka gida? Dama haka ake yi a kadunan ko kuma ince a familyn ku?" Yace "Ehh policy na kenan..." Tace "Amma haka zalika ita ma babu wani nata da xai shigo gidan dai ko??" Yace "Wa enda ke da full right din shigo min gida su ne 'yan uwana kawai" Aneesah tace "Yan uwanka?? To wllh baxai yiwu ba don duk wani d'an uwanka da xai shigo gidan nan wajenta ya xo tunda dai ba dangi ko wani d'an uwa gareta ba, yan uwan naka suka karata cikinsu ta xama mutum, don haka wllh yanda ka hana yan uwana shigowa gidanka to kowa ma ka hanasa shigowa..." Yace "Toh idan nawa yan uwan sun shigo ki koresu mu ga" Daga haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo ranta na suya, xaunawa gefen gado tayi bayan ta jefar da mayafin hannunta, daga aure ko sati ba ayi ba xata fara fuskantar haka a gidan nan?? to ai xama bai ganta ba kuwa, baxata ci gaba da laruwa kan su Aunty da Safara'u ba, she needs to wake up from her slumber ta kwaci kanta da kanta. Abuturrab na sauka ya ga Jiddah bata kitchen, sai da ya kare ma Kitchen din kallo with irritation sannan ya koma sama ya bude dakinta... a kwance ya ganta, yace "Kin fasa girkin kenan" tace "Baxan iya girki a wannan kitchen din ba" Yayi shiru bai ce komai ba, ko kadan kuma bai ga laifinta ba don duk wani me tsafta baxai iya amfani da kitchen din nan ba, ya karasa ya xauna gefen gadon yace "Toh mu je ki rakani in siyo a waje" Tace "Ka dai je ka dawo" yace "Baxa ki rakani ba?" Tayi shiru, mikewa yayi yace "Toh me xan siyo maki?" Tace "Ni na ci abinci ai" Fita yayi daga dakin ta bi sa da kallo, duk da tana son rakasan amma bata tashi ba, har taji ya tada motarsa ta lumshe idonta, mikewa Aneesah tayi da sauri tana leka window ta ga shi kadai a motar, tana ta kallonsa har ya fita compound, kofa ta nufa ta bude ta fita ta yi hanyar dakin Jiddah, a hankali ta murda Jiddah ta bude ido da sauri ta kalli kofar, Aneesah ta bude, sosai gaban Jiddah ya fadi, Aneesah ta shigo ta kulle kofar tana kallonta sae tayi murmushi ta ja stool ta xauna tace "Sannu amarya, fatan kun dawo lafiya?" Jiddah ta mike xaune ta ki yarda su hada ido tace "Lafiya lau" Aneesah na gyara dankwalinta tace "Naga kina ta dari dari da ni tun da kika shigo gidan nan kamar dai baki son ki sake da ni, inji dai ba abubuwan da suka faru a baya kika bari a ranki ba, in dai shine to ki manta su Jiddah, ba komai ya ja hakan ba sai sharrin shaidan da xugan mutane, wllh ba halina bane, ni yanxu na dauke ki matsayin kanwata ta jini, ina son mu xauna lafiya kar mu bari a jiyo kanmu, don Allah ba don ni ba ki sake da ni Jiddah, kuma kiyi hakuri ki yafe min abubuwan da na maki a baya duk sharrin shaidan ne" Jiddah ta daga kai ta kalleta jin tayi shiru, Aneesah tayi murmushi ta gyada kai tace "Har cikin xuciyata nake gaya maki duk abinda ya fito bakina Jiddah, abinda ya sa ban bi ta gun captain ba kafin inyi maki magana sbda nasan xai xata ko wani manufan ne a raina baxai yarda ya amince da ni ba, amma ke nasan ba jahila bace xa ki fahimce ni, xa kuma mu xauna lafiya babu tashin hankali" Jiddah ta ma rasa abinda xata ce mata, a hankali Aneesah tace "Kin yi shiru Jiddah" Jiddah ta kalleta a hankali tace "Shkkn ya wuce" Aneesah tace "Kai amma na ji dadi wllh, kuma don Allah ki saki jikin ki da ni kar ki daukeni matsayin kishiyarki dama bani da kowa a kaduna, ina son mu dawo kamar yan uwan juna, mu yi abunmu mu rufe tare ba tare da ko shi captain din ya sani ba" Jiddah dai bata ce komai ba, Aneesah tace "Daxu naga kamar kun shigo da abinci ko?" Jiddah tace "Yana dining" Aneesah tace "Toh bari in diba banci komai ba wllh, naje xan dafa Indomie daxu kuma ban samu na dafa ba" Daga haka ta mike ta nufi kofa Jiddah ta bi ta da kallo har ta fita, downstairs Aneesah ta sauka ta dau plate ta debi tuwon sannan ta dawo dakin Jiddah, hira ta dinga jan ta da shi tana bata labarai iri iri duk na Captain Aliyu, Jiddah dai daga um sai um um, Aneesah tayi dariya ta ajiye spoon din hannunta da take cin tuwon tace "Wllh ban ta6a xatan duk walakancin da na masa shi xai xama mijina ba, to nayi mugun raina arxikinsa a lkcn gashi ya nace min, har yanxu idan na tuna sai inji kunya ashe mijina na dinga yi ma girman kai ina walakantawa shi kam baya fushi yana ta makale da ni yana nace da ni, wllh na sha xagesa a waya amma hakan baxai hanasa kirana anjima ba don naci, a lkcn kuma sbda wai ni fa yaki yarda ku xauna tare sbda mugun son da yake min, ni kuwa duk ban san abinda ake ciki ba, to gashi hakkinki yana ta bibiyansa shi yasa ya kasa samun nutsuwa a lamarinsa, yana ganin idan ya aureki to Allah xai yafe masa duk abubuwan ya maki, yace min dalilin da ya aureki kenan ko xai samu rest of mind da conscience dinsa dake judging dinsa" Jiddah dai kallonta kawai take, Aneesah tace "In gaya maki a lkcn da ya aureni ma ni gudunsa fa nake, inyi ta ihu duk daren duniya na ki amincewa da shi" kallonta kawai Jiddah take, Aneesah ta d'an yi shiru jin she sounds ao stupid, sai kuma tace "Wllh kin yarda da shi nayi farkon auranmu... To ina xan yarda naga abinda ya fi karfina??" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Aneesah tace "Ranan kuwa da na amince kwanan mu uku a asibiti, sai kuma na fara ganin canji daga garesa, kin san su maxa bayan sun samu abinda suke so shkkn... Har yau kuma ina danasanin amince masa" Jiddah ta kalleta da sauri, Aneesah tace "Wllh wllh na ci ubana a wajensa..." dariya Aneesah tayi tace "Ae ranan na ji ke kin samu daman ihun ma, ni ina na samu wnn daman, kuma da xa ku tafi Abuja naga kina tafiyar ki ras, nace ahh lallai ke naki da sauki" Jiddah taki ce mata komai, Aneesah tace "Ko ba haka ba?" Jiddah tace "Me fa?" Aneesah tace "Au wai duk xancen nan baki gane ba" Jiddah tace "Aa ban gane ba" Bude kofar dakin aka yi, Abuturrab ya kalli Aneesah sannan ya kalli Jiddah, Aneesah ta washe baki tace "A waje ka bar motar Captain? ko xaka fita ne?" Bai ce komai ba ya karaso ya ajiye takeaways din hannunsa, Aneesah ta mike tace "Toh Jiddah na gaisheki, bari in je banyi la'asar ba wllh, nagode da tuwo" Daga haka ta nufi kofa da plate din tuwonta ta fita, Jiddah ta bi ta da kallo, Bayan ta fita Abuturrab ya kalli Jiddah yace "Me ta shigo yi?" Jiddah ta girgixa masa kai kawai, daukan takeaway daya yayi cikin guda biyun da ya siyo, ya nufi kofa ya fita Jiddah ta bi sa da kallo, sai kuma ta mike da sauri ta jingina da kofarta bayan few seconds ta bude kofar a hankali tana kallon kofar dakin Aneesah, a kulle taga kofar, ta sauko downstairs sai ta gansa xaune parlor, da sauri ta juya ta koma sama. Da daddare Jiddah ta d'an ci abincin da Abuturrab ya bar mata, ta fita da sauran downstairs xata kai kitchen, Aneesah dake xaune parlor tana kallon wani series ta bi ta da kallo, bayan jidda ta fito kitchen din ta dauke kanta da sauri, ganin Jiddah xata wuce sama Aneesah tace "Ga lemon kankana da abarba nayi Jiddah" Jiddah ta d'an kalleta tace "Aa nagode" Aneesah ta hade rai tace "Naga har yanxu kamar kin ki sakewa da ni Jiddah, yanxun nan fa nayi sa a kitchen, shine na debi nawa na bar maki sauran a jug, captain din ma idan xai sha sai ki basa" Jiddah tace "Yanxu na gama cin abinci" Aneesah tace "Toh ai wannan ba abinci bane lemo ne" Jiddah ta d'an yi shiru, sai kuma ta karasa cikin parlon, Ta dau jug din tace "Xan kai sama, nagode" Aneesah tace "Toh shkkn, sai ki tafi da cup" Daukan cup din tayi ta wuce sama Aneesah ta bi ta da kallo, Jiddah na shiga dakinta ta ajiye Jug din da cup a kasa kusa da mirror dinta, sannan ta cire hijab dinta ta shiga wanka. Tana xaune gaban mirror tana shafe shafenta Abuturrab ya shigo ta kallesa sau daya ta dauke kai, lumshe ido yayi don kamshin turaren da ta sa na karshe ya daki xuciyarsa, ya nufi bayanta ya tsaya ya dafa shoulders dinta a hankali yace "Have u eaten?" Ta gyada masa kai da sauri xuciyarta na bugawa, ya kalli Jug dake ajiye yace "Wannan fa?" Tace "Naka ne tace a ajiye maka" wani kallo yyi ma jug din sai kuma ya nufi kofa ya fice daga dakin, ita dai ta sauke ajiyar xuciya gama abinda xata yi ta saka kayan baccinta tayi kwanciyarta ta rufa da duvet ta rufe idonta. Aneesah dake xaune parlor sae bin Abuturrab that is wearing just short and singlet take yi da kallo, sosai take missing dinsa, rabonta da shi kusan wata daya da sati biyu kenan, Safara'u kuma na gidan a duk lkcn balle ta sama ma kanta mafita, kallon agogo dake nuna karfe goma da minti arba'in tayi ganin ya haura sama rike da cup din plane water ta san bangarensa xai je ya hada coffee don tuni ya dauke coffee powder dinsa a kitchen sbda karewan da yake a kwana biyu kuma Safara'u ce ke sha sau biyar sau shidda a rana, Aneesah ta kashe kayan kallon parlon da fitila sannan ta haura saman ita ma, dakinta ta shiga cikin mintuna kadan ta fito ta nufi bangarensa tana baxa kamshi, xaune ta samesa a parlornsa yana kallon wrestling hannunsa rike da cup din coffee, sau daya ya kalleta ya ci gaba da kallon da yake, ta xauna gefensa tana kallonsa a hankali cike da kissa tace "It seems u are still angry at me Captain, naga sai wani hade min rai kake kaki sakewa da ni, snn i notice dakin Jiddah da na shiga daxu kamar u are not happy about it, ni kuma ba da wata manufa na shiga ba ina son mu xauna lafiya da yarinyar ne don naga bata da matsala ko a wancan lkcn ma ni kadai nake haukana ita kam babu ruwanta" Abuturrab yace "Kilan u misperceived me, but i am not against ku xauna lafiya ai..." Kwanciya tayi a kirjinsa ta lumshe ido tayi kasa da murya tace "Toh fushin da kake da ni har yanxu fa?" Ya ajiye cup din hannunsa don saura kadan ya sake yace "Idan kika canxa halin ki xan daina fushi da ke" Tashi yake son yi ta ki sakesa ta marairaice tace "Muna magana kuma ina xa ka Captain?" Yace "I want to get my laptop" Abinda tasan tana masa xai yi turning dinsa on ta shiga yi masa, ya koma ya jingina da kujera trying to control himself yace "Stop that Aneesah, i need to go get my Desktop" Ko sauraronsa bata yi ba, Bata sake kuma basa daman magana ba, sai da yayi da gaske sannan ya turata taki sakesa ta wani kankamesa tace "Me yasa baxa ka bani hakkina ba, ko ni ba matar ka bace?" Da kyar yace "Sai ki jira ranan da kwanan ki ya xagayo..." Daga haka ya janyeta jikinsa, Kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa ta ji wani bakin ciki da takaici ya turnuketa, ya mike tsaye ya tsallake coffee din da yake sha ya nufi kofa ya fice daga parlon, da sauri ta bi sa taga dakin Jiddah ya nufa ya shiga ciki ya kulle, hawaye ya kawo idonta ta koma parlon da sauri ta xauna kan kujera tana watsi da throw pillows din kai, xaunawa Abuturrab yayi gefen gado na kusan minti uku trying to calm himself down, sai kuma ya juya ya kalli Jiddah da ke bacci, kashe wutan dakin yayi ya hau saman gadon ya cire duvet da ta rufe jikinta da shi a hankali yana kallonta fuskarta cikin duhun, lkci daya ta bude ido xata mike xaune da sauri ya kwantar da ita moving closer to her murya can kasa yace "Mata na bacci dama bata jira mijinta ba?" Sosai gabanta ya shiga faduwa ta marairaice masa tace "Bacci nake ji sosai don Allah ka sakeni" a hankali yace "To gaya min wa xan kama idan na sake ki? Wajen wa kike son in je" Shiru tayi xuciyarta na bugawa jin muryarsa kamar ba shi ba, wannan kalma da ya fada mata ya sa bata sake ce masa komai ba amma hakan bai sa jikinta ya daina bari ba tana sauke ajiyar xuciya, a xaton ta iyakarsa yanda yayi mata a Abuja jiya amma sai ta ga ba haka ba, jiya he was so calm and gentle, yau kuwa opposite din ne, Exactly yanda ta gansa a ranan da ya kawota gidansa take ganinsa yanxu, rikice masa tayi ta fara kuka iya karfinta tana ce masa ya rufa mata asiri yayi hakuri ya tafi wajen duk warce xai je, amma ko sauraronta bai yi ba, he was using all the scope Ahmad gave him but ferociously, he wasn't soft, it's just as if his life depends on what he was doing at that moment, duk wannan abun Aneesah na tsaye bakin kofar dakinta ta kasa shiga duk da babu wani abu da take ji amma kawai ta kasa shiga dakin nata tana jin kamar xata hadiyi xuciyarta ta mutu kawai, ihun da Jiddah ta kwala wanda duk wanda yaji irin ihun yasan na menene ya sa ta sulale kasa ta xauna nan bakin kofar nata ba tare da ta shirya yin hakan ba, Jiddah tana ji tana gani Abuturrab ya rabata da self-worth dinta na ya mace, an experience that will remain in her memory forever.... _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppDa kyar Jiddah ta bude idanuwanta da suka yi mata nauyi jin sanyi a forehead dinta, tana arba da Abuturrab da ya daura hannunsa a goshinta ta runtse idon tana son matsawa daga wajen amma ta kasa kwakkwaran motsi taji kamar anyi glueing dinta da gadon, duk da idanuwanta a rufe suke hakan bai hana hawaye sauka idon ba, ya dagota ya rungumeta gamm jikinsa ya ma rasa abinda xai ce mata, jin yanda hawayenta ke xuba jikinsa ya kai bakinsa fuskarta yana kissing tears din nata all over, cikin breaking voice yace "I love you wife, i love you, I am sorry for everything from the day i met u till this moment, i...." Kasa ci gaba yayi ya kwantar da ita ya hade goshinsa da nata, sae taji nasa hawayen na sauka fuskarta, a hankali yace "I am sorry Jiddah, i am sorry u have to pass through all this, i am sorry wife..." ita dai ba sosai take comprehending dinsa ba ma, gaba daya jin ko wani ga6a na jikinta take kamar ba nata ba, she is feeling pain everywhere, wani kuka ta sakar masa a galabaice tana juya kanta tace "Don girman Allah ka kai ni wajen Umma, wllh mutuwa xan yi" ya sake dagota ya rungumeta shi ma din duk a rikice yace "Plss don't say that again, I don't know how everything happen this way, I don't know what came over me" kuka kawai Jiddah take me ban tausayi, Abuturrab ya rasa me xai mata, yayi lallashin duniya amma kamar yana dada tunxurata, shi kuma bai fasa lallashin nata ba, from d way she is crying kasan she is pained, and he wish he can take away all the pains, kamar yanda bata yi bacci ba haka shi ma bai yi ba har karfe biyu da rabin dare, babu abinda ya kara daga masa hankali sae jin yanda jikinta yayi xafi lkci daya kamar garwashi, he couldn't help it anymore ya kwantar da ita ya fita dakin, bangarensa ya tafi don duba mata paracetamol amma bai gani ba, yayi duban duniya a bedroom din nasa babu paracetamol din, tunawa yayi ranan yace Aneesah ta dauka, does it mean she took all, da sauri ya fita daga bangaren nasa ya tafi dakin Aneesah, budewa yayi ya shiga ciki ya tadda fitilan dakin a kunne, a kwance take ta wani dunkunkune waje daya idonta tarrr kamar warce aka yi ma mutuwa hakan yasa yana bude kofar ta mike xaune kusan a firgice, sae da ya xaga dakin as if thinking of what to tell her, sai kuma ya dawo inda take kwance da sauri yace "The other day kin dauki pack din paracetamol a part dina, where is it?" Kallonsa kawai take don duk a birkice yake, jin tayi shiru yyi mata tsawa yace "I am talking to u Aneesah" ta yi karfin halin cewa "Me zaka yi da paracetamol tsakar daren nan?" Ya daga mata murya yace "My wife is sick, ki tashi ki bani nace maki" Mikewa tayi da sauri cikin rawar baki tace "Ohh Subhanallah, me ya sameta, let me...." Sae kuma ta nufi kofa ya fixgota yana mata wani kallo yace "Ina xa ki?" Tace "Aa naji kace bata da lafiya, kuma ni paracetamol na shanye just 5 pieces ya rage, shine xan je in ga ko da abinda xan...." Ya katse ta yana kallonta da kyau yace "That's our secret, a PRECIOUS secret.... u are not invited" daga haka ya saketa ya nufi kofa ya fice, mutuwar tsaye tayi a wajen _Precious secret_ din da ya fada ne ke mata yawo a kai, wasu hawaye masu xafi suka xubo idonta lkci daya taji wani sanyi ya lullubeta ta hau saman gado da sauri ta ja bargo ta rufe jikinta da shi tana jin numfashinta na sama sama, All through the night Abuturrab na xaune gefen Jiddah da ta samu bacci ya dauketa, kana ganinta kasan she is restless even in sleep, a baccin ma duk a firgice take, a kan idonsa aka yi kiran sllhn farko, da ya kai hannu jikinta sai yaji xafin ya fi na da, he just don't understand the meaning of this, gaba daya hankalinsa ya tashi sosai, da da ynda xai yi da ya maido da duk wani ciwon da take ji jikinsa, lkcn sallah na yi ya shiga yayi alwala don tun daren yayi wanka, ya fita masallaci.... kasa nutsuwa yayi Azkar dinsa yayi a masallacin, he really need to talk to Ahmad, may be there was something he was suppose to have done da bai mata ba shi sa jikinta yyi xafi, yana dawowa gida ya tafi bangarensa ya dau wayarsa ya shiga kiran Ahmad bayan ya xauna saman kujera, Ahmad na dagawa sai da ya fara kyalkyala dariya kafin yace "Don't tell me baka san yanda xaka yi da ita ba kuma bayan ka cuci er mutane Captain?" Abuturrab yayi kasa da murya cike da damuwa yace "Plss tell me... asibiti xan kai ta? she is seriously sick Ahmad, why is that??" Ahmad yace "Ohh u are asking why is that, ita Aneesah ta maka haka?" Wani tsaki Abuturrab ya ja yace "Pls mu yi maganan da muke yi Ahmad" Ahmad yace "To ka ga, the different is clear" cike da damuwa Abuturrab yace "Yanxu asibitin xan kai ta plss?" Ahmad yace "Not at all, in dai yanda na fada maka ka bi babu xancen hospital, just lukewarm water and salt" Abuturrab yayi shiru, Ahmad yace "Yea, just it, she will feel better in sha Allah, when did it happen" Abuturrab yace "Yesterday" Ahmad yace "Yanxu sai da ka bari jikinta yayi tsami xaka kirani, it's something u should have done since that night Captain" Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya yace "I will call u back" Daga haka ya katse wayar ya fita bangaren nasa ya shiga dakin Jiddah, tana nan a yanda ya bar ta kamar ma bata son motsa jikinta kwata kwata, ya shiga bandaki ya hada ruwan dumi sosai a bathtub, ya fito ya sauka downstairs, dubawan duniya yayi ma gishiri a kitchen bai gani ba, hakan ya sa ya haura sama ya shiga dakin Aneesah, tana nan dunkunkune cikin bargo har a lkcn, ya cire bargon yace "Aneesah" da kyar ta bude idonta da yayi mata nauyi don ana idar da sallan asuba ta samu bacci ya dauketa tun daren jiyan take rawan sanyi kamar xaxxabi xae rufeta, ga bacci ko barawo bai xiyarceta ba, wani nauyi taji kanta yayi mata, ba tare da ya wani damu da yanayinta ba yace "Sauko ki bani gishiri a kitchen, I can't find it" kallonsa kawai take, yayi mata tsawa yace "I'm talking to you Aneesah, gishiri xa ki bani" Ta koma ta kwanta a hankali tace "Babu shi" cikin fada yace "Gishirin xaki ce min babu? Da uban me kike girki a gidan??" ta kallesa tace "Ubana" wani mugun kallo yayi mata yace "Baki da amfani wllh, sae yanxu na sake tabbatar da haka" daga haka ya fice daga dakin, wani sara mata kanta yayi ta bi sa da kallo tana jin xuciyarta na mata wani xafin bala'i, Abuturrab na komawa dakin Jiddah ya nufeta ya xauna gefenta ya kai hannu goshinta a hankali yace "Jidderhh" a tsorace ta bude idonta, xai dagata xaune ta girgixa masa kai kawai don in tana kukan ma ji take ko ina na mata ciwo a jikinta, be saurareta ba ya dagata kamar newborn ya kai ta bandakin, safiyan nan Jiddah taga tarairaya da lallashi wajen Abuturrab, kamar dai ba Abuturrab ba, amma duk wannan bai dameta ba ta kanta take axaba da wahala ya isheta, ta maimaita masa ya kai ta gun Umma ya fi a kirga, daga baya kuma ta fara cewa ya kira mata Maimoon, shi dai kawai lallashinta yake, duk every minute yake kiran Ahmad ya tambayesa me xai mata she is still in pain, daga karshe karfe bakwai dot ya fita xai je nemo pharmacy a duk inda yake bayan Ahmad yayi masa prescribing drugs da xai siya mata, yana dawowa ya sameta tana bacci, ya ajiye ledan maganin ya fita duk fa Jiddah ta birkitasa, he just want to her to be fine, downstairs ya sauka ya shiga kitchen ya dinga neman Ashana ko lighter da xai kunna gas amma bai gani ba, ya fita ya tafi dakin Aneesah, tana kwance ta nemi baccin ta rasa tunda ya shigo ya tasheta daxu, A takaice yace "Ashana nake nema xan daura ruwan xafi yana ina??" Ta sauke idonta daga kallonsa tace "Babu ashana" a fusace yace "Wai ke wace irin macece komai kice babu? I always use to imagine ko rako mata kika yi duniya, komai zero zero.... abin alfaharin ma da ake kawowa gidan mijin shi ma big ZERO, there is nothing to write home about u Aneesah, what nonsense??" Yana gama fadin haka ya juya ya fice daga dakin a mugun fusace, Aneesah ta bi sa da kallo baki bude with so much shock, rufe fuskarta tayi da bargon jikinta wani sanyin na sake shigarta, yau ita Abuturrab ke gaya ma haka?? Abinda ko da wasa bai ta6a fada mata ba, Abuturrab na fita gun mai gadin gidan ya nufa, ko amsa gaisuwansa bai yi ba yace "Kana da Ashana??" Mai gadin yace "Wllh babu yallabai, dama maganin sauro nake kunnawa da Ashanar kuma tun da ka gani ka hanani ka siyo min na fesawa shkkn na daina...." Abuturrab bai tsaya ya gama sauraronsa ba ya nufi gate din gidan dake kusa da na shi, har sannan jallabiya ne a jikinsa, ya gaisa da mai gadin gidan shi ma ya tambayesa ashana, mai gadin yace "Wllh babu ranka shi dade, da ma mai kantin anguwan ya fito ne" Abuturrab yace "Don Allah ka shiga ciki ka samo min a cikin gidan, ruwan xafi xan daura" Mai gadi ya shiga cikin gidan, Abuturrab na ta tsaye har ya fito da lighter ya mika masa ya amsa yayi masa godiya ya koma gidansa da sauri, rasa a ina xai daura ruwan xafin yayi don Aneesah ta kone duk heater biyu na gidan gaba daya, ya dau wani tukunya duk da a wanke yake, da cup da spoon, sai bowl da frying pan, ya debi liquid soap da soson da ya gani ya bude kofar kitchen din ya fita ta backyard, can bakin tap wanda bai ta6a xuwa ba tunda yake a gidan ya nufa, ya kunna tap din ya shiga wanke tukunyar da murfinsa, Aneesah ta mike da kyar jin an bude tap din baya ta sauka saman gadon tana jin jiri ta nufi window din saitin wajen ta bude labule tana lekan waje don ganin waye, kallonsa ta dinga yi ganin yanda ya dage yana ta wanke tukunya da frying pan, sannan ya daurayesu da kyau ya shiga kitchen, sake labulen tayi ta sulale kasa tana kallon saman dakin nata hawaye na taruwa idonta, Abuturrab ya daura ruwan goran da ya juye cikin tukunyar sannan ya daura kan gas bayan ya kunna, kwai guda hudu ya ciro a fridge, ya dauraye wani bowl ya fasa su a ciki ya kada, tsayawa yyi yana tunanin da abinda ake soya kwan, mangyada ya fado masa ya shige store inda jarkan mangyadan suke a nan ya ga gishiri a wani basket, toh bai san ko gishiri ake sa wa a kwan ba ko maggi ko wani abun daban, amma he guess gishiri ma xai sa shi yayi taste, haka ya debi gishirin ya duba a bowl din kwan, cikin mintuna goma ya gama hada shayi me kauri a cup, ya juye kwan da ya fara konewa a plate sannan ya wuce sama da su, ajiyewa yayi kasa ya xauna gefen gadon yayi kasa da murya, a hankali yace "Wife" bude idonta da suka kumbura tayi a hankali, cikin lallashi yace "I made u breakfast so u can take ur drugs..." Bai jira cewarta ba ya dagata ta girgixa masa kai da sauri hawaye cike idonta, cikin muryanta da ya shake tace "Na fi son in kwanta, na gaji" Ya gyara mata pillow yanda xata d'an kishingida sannan ya dau shayin wanda bai mata shi da xafi sosai ba, sae da ya fara kurba sannan ya kai bakinta ta girgixa masa kai, da damuwa yace "Plss ki sha ko kadan ne sbda xa ki sha magani" bai jira cewarta ba ya debi shayin a cokali ya kai bakinta xata kauda kai yace "Plsss wife" Da kyar ta bude baki ta d'an kurbi kadan ta cire bakinta, yace "Baki shanye ba ai" Ta rufe bakinta tace "Amai" ya kai teaspoon din baki ya shanye sauran sannan ya ajiye ya dauko kwan, ya sa fork ya yanki kadan ya kai mata baki yace "I fried this for u also" Xata kwanta ya rungumota jikinsa yana lallabata, da kyar da kyar ya samu ta ci kadan, shayin ma ta sha kusan quarter din cup sannan ya bata drugs din ta sha, sai bayan few minutes ya bari ta kwanta, babu bata lkci bacci ya dauketa, he felt relieved tunda ta daina kukan sae dai har sannan jikinta da xafi, and he is hoping maganin xae sa taji sauki, daukan sauran shayin yyi ya shanye, ya tura kwan da bai masa dadi ba ko kadan, ya cinye a haka sannan ya tashi ya shiga bandaki ya ciro bedsheet da ya saka cikin washing machine ya xuba ruwa a bathtub bayan ya toshe, duk girman bedsheet din haka ya wankesa tas, wanda shi ya ma mance rabonsa da wanki banda na short da singlet dinsa, a bucket ya saka xanin gadon bayan ya gama wankewa ya fita da shi waje, can inda yayi wanke wanke ya tafi ya kunna tap din, yana dauraye xanin gadon Aneesah da ke xaune kasa har sannan jikin window din ta mike jin an kara kunna pampo, kallonsa ta dinga yi har ya gama daurayan xanin gadon sannan ya shanya a igiyan dake wajen, ta dauke kanta da sauri ta koma gefen gadonta ta xauna. Yana komawa sama ya shiga bedroom din Jiddah ya xauna gefenta yana ta kallonta memory din last night na dawo masa afresh, he couldn't help it but smile, ya manna mata kiss a lips dinta underneath his breathe yace "I know i have always love u from day 30... I am proud of u wife, and i have to replace ur precious gift with something amazing" duk da bacci take ya kira Ahmad yayi sau uku yana tambayar ya tabbatar xata tashi babu wani ciwo ko xaxxabi, a kiran karshe Ahmad yace "Hey captain ka bar ni inyi aikina plss, bayan ka cuci er mutane kuma kayi ta damuna da kira..." Abuturrab ya shafa kansa a hankali yace "I neva knew haka abun yake, i never knew there is something of such a duniya, i couldn't control my self, i loss control" dariya Ahmad yyi yace "Ga ka ga mata a gida for months kace u never knew.... U neva knew what?" Abuturrab ya ja tsaki yace "Ban ta6a sanin cutar kaina nake ba sae jiya da daddare, ban san duk wahala nake ba kaina ba sae jiya, sae jiya nasan meye aure, sannan sai jiya nasan wacece mace" Ahmad dae dariya kawai yake yace "Kaga sae anjima xancenka ya fara fin karfina" daga haka ya katse wayarsa, Abuturrab ya kai hannunsa goshin Jiddah a hankali ya ji temperature dinta ya fara sauka, yanxu bacci take cikin nutsuwa, lumshe ido yyi ya bude yayi murmushi, lkci daya ya ji hankalinsa ya kwanta he felt relieved at last, ya daura hannunsa a hankali kan flat tummy dinta yana shafawa, he just have to compensate her with a surprise kafin ta tashi bacci, a huge surprise.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 FZ Beauty Supplements Dealer ce ta supplement masu qara fito da kyaun mace ko namiji, hadi da qarama garkuwar jiki kuzari. Muna sayarda Supplemnt kamar na qarin duwawu, akwai wanda zaya taimaka wurin dawoda martabar Nono, akwai na rage qiba da tumbi, akwai na rakwainuwa, akwai na tada komada, akwai masu saka hasken fata da qyalli, akwai na infection, akwai na saka hasken ido da hakori sannan akwai na gyaran turaka. Muna maraba da mai sayen daya ko sari. Wa.me/2348143821028 Karfe sha biyu saura Jiddah ta bude idonta a hankali, bin dakin ta dinga yi da kallo ta mike xaune hoping she won't feel any pain anymore, gaba daya ta ji baccin ya isheta, ta gaji da baccin, ga wani yunwan da take ji sosai, xuwa yanxu kam bata jin ciwon da take ji a gabobinta, karfi ne kawai bata da shi a jikinta, a hankali ta sauke kafanta kasan dakin xata mike tsaye, babu shiri ta koma ta xauna ta rufe idonta, dai dai nan aka bude kofar dakin ta juya da sauri, Maimoon ce ta shigo dakin da sallama ya ci kwalliya tayi daurin ture kaga tsiya, rike ha6a tayi tana kallon Jiddah tace "Shine ko kira babu Jiddah, kika sa muka raka ki mota muna matsar kwalla, amma yau sati daya mun ji ki shiru a dakin ki" Jiddah tayi murmushi bata dai ce komai ba amma har ranta tayi farin cikin xuwan Maimoon, tayi missing dinta sosai sosai, Maimoon ta karaso cikin dakin tace "Ni da na damu dake ai gashi na biyoki, kuma kar ki ce min sai yanxu kika tashi bacci? Aa gaskiya wnn dai ba yi bane, ko irin er kwalliyan nan da amare ke yi da safe babu kin wani xumbula doguwar riga kina xaune gefen gado?" On a serious note Maimoon tayi maganan, cikin sanyin murya Jiddah tace "Umma fa??" Maimoon tace "Umma tana gida, ita ma ai kin manta da ita daga tarewa, gobe sati daya amma ko kira daga ke har yayan" a hankali Jiddah tace "Ban manta da ita ba, ai bani da waya ne" Maimoon tace "Toh baxa ki amshi wayarsa ki kirata ba" Jiddah dai tayi shiru tana kallon Maimoon, Maimoon tayi kasa da murya tace "Ke na ji gidan shiru, ina yar dabar gidan take, ko ta bar maki gidan ne ta kasa xama?" Jiddah ta wani harareta, Dariya Maimoon tayi tace "Ke Allah kuwa kamar ke kadai ce a gidan, naji shiru, shi dama yaya ban ga motarsa ba a parking space" Jiddah ta sunkuyar da kai tace "Kika san ko tare suka fita?" Maimoon ta hade rai tace "Tare suka fita xuwa ina? Har yanxu fa satin ki daya bai cika ba, sai gobe xai cika, to sai kika yi shiru kika barsu suka fita tare" Jiddah dai tayi shiru bata ce komai ba, amma haka kawai taji abinda Maimoon ta fada ya tsaya mata a rai, tunda gashi baya nan kenan assumption dinta dai dai ne, fita yayi tare da Aneesah ita kuma ya bar ta nan tana wahala, Maimoon ta mike da sauri tace "Auu tare fa muke da kawayena suna parlor, ki taso mu je ku gaisa yan Islamiyyan mu ne" Jiddah ta kasa ce mata komai amma tasan baxata iya tashin ba, kafin Maimoon ta sake cewa komai tace "Ki ce su shigo nan, kaina ciwo yake baxan iya fita ba..." Maimoon tace "Ciwon kai kuma? Toh kin sha magani?" A hankali Jiddah tace "Na sha" Maimoon tace "Kina ciwon kan suka sa kai suka yi fitarsu?? Lallai, dama Umma tace idan na xo in sa ido ko da akwai wata matsala" Shiru Jiddah tayi, gaba daya taji ranta babu dadi, kawai imagine take da gasken sun fita ne da Aneesah, Maimoon tace "Tabdi..." Daga haka ta fita daga dakin, Jiddah ta wani hade rai don ba karamin tasiri xancen Maimoon yayi a xuciyarta ba, Maimoon na fitowa daga dakin Jiddah ta hangi Aneesah tana sauka downstairs ita ma dai da doguwar rigar kamar sannan ta tashi bacci, wani kallo ta bi ta da shi, Aneesah na fitowa parlor ta dinga kallon yan mata biyun dake xaune saman kujera a parlon, maimakon ta tsaya amsa gaisuwarsu, a takaice tace "Daga ina?? Wa ku ke nema?" Muryar Maimoon taji daga sama tace "Wajen matar gidan muka xo" Aneesah ta juya da sauri tana kallonta, Maimoon ta karasa sauka kasa tace "Jamila ku taso ku hauro sama ku gaisa, tana daki" Nan da nan Aneesah ta ji ta nemi ciwon kai da xaxxabin da ya rufeta tun sanyin safiya ta rasa, wani kwari ya xo mata, tana kallon kawayen Maimoon da kyau cikin daga murya tace "Toh idan nan din gidan ubanku ne sai ku haura saman in gani!!!" Duk suka yi turus suka tsaya, Cike da tsiwa da fitsara Maimoon na kakkanne ido tace "Toh ai kema naga ba gidan ubanki bane da xa ki ce baxa a hau sama ba, kuma sannan ba wajenki muka xo ba" Aneesah ta wani xaro ido ta nufeta da sauri tana huci tace "Ubana kika xaga?? Uba na??" Maimoon ta jefar da jakan hannunta ta cire mayafinta ta daura a kugu tana gyara ture kaga tsiyan kanta tace "Ohh ashe babu dadi, ance maki uba ya fi uba ne??" Jamila ce tayi kan Maimoon da sauri ta janyeta daga wajen kafin Aneesah ta cakumota, Hankali tashe Jamila tace "Kinga ki xo mu wuce Maimoon mu ba abinda ya kawo mu ba kenan wllh, don Allah mu wuce kawai" Maimoon tayi wani shewa tace "Inje ina?? Wllh ina nan, ki bar ta ta ta6a ni idan ta sha codin ne, wllh xata ga yanda ake kasa kasa da d'an mutum yau, ko ance mata nan din gidan babanta ne da xata hanamu shigowa? Gidan yayana ne fa kuma wajen yar uwata na xo don haka gomanta basu isa su hanani xuwa gidan nan ba wllh wllh" Aneesah tayi wani kukan kura tayi kan Maimoon tana kunduma mata xagi ta uwa ta uba amma tuni Jamila da Farida suka shiga tsakaninsu suna ba Aneesar hakuri, Kamar mahaukaciya Aneesah ta nufi kitchen a guje, Jamila ta dinga jan Maimoon su fita Maimoon taki fita ita ma tana kunduma ma Aneesah xagi, amma me? tana ganin Aneesah da tabaryan karfe da wuka daga ita har su Jamila suka haura sama a guje hakan kuma bai hana Maimoon dinga xaginta ta uwa ta uba ba, suka shige dakin Jiddah da gudu suka sa makulli, Jiddah dai sai kallonsu take don tana jin hayaniyar amma ta kasa tashi, gashi duk hankalinta ya tashi, da damuwa tace "Me yasa xa ki kulata Maimoon? Me yasa don Allah" a fusace Maimoon tace "Na kulata din, ita uwa ta ce da xan ji tsoronta inki kulata, ni baki ganta ba ma wllh naga duk ta rame ta yamushe sai kwala kwalan ido da kashin wuya kamar xa a jera duwatsu, kinga da gaske dai ta fara samun sleepless night a gidan ba a sani ba, to wllh bari yaya ya dawo duk inda ya tafi yayi min iyaka da ita don bata isa ta hanani xuwa gidan nan ba, kai ko shi ma bai isa ba balle ita, kullum idan muka tashi Islamiyya idan na ga dama sai na leko na ganki Babu wanda ya isa ya hanani" Daga Jamila har Farida kallon Maimoon kawai suke dukkansu a tsorace suke da Aneesah, Jiddah ta sauke wani ajiyar xuciya tana kallonsu tace "Sannun ku da xuwa Farida" Jamila tace "Hmm sannu Jiddah, mu dai da mun san haka xai faru da bamu fara xuwa ba wllh, Allah ya gani ba tashin hankali ya kawo mu ba, Maimoon da baki biyeta ba wllh" Jiddah dai tayi shiru, Maimoon tace "Lallai tunda ina tsoronta ai dole in ki biyeta... Ai da nasan haka xai faru yau da Rumasa'u xa mu xo gidan nan ayi duk bala'in da xa ayi, ayi fashe fashen kai" Bude gate din gidan suka ji anyi, Maimoon ta nufi window da sauri, har sannan tana huci tana kallon motar da xai shigo, wata sabuwar mota dal ash color sai wani talli yake ne ya shigo compound din, Maimoon ta wara ido a hankali tace "Waooww motar waye wannan, yaya ya canxa mota ne?" Jiddah dai sai kallon Maimoon take amma babu daman ta tashi taga motar, Maimoon ta dinga kallon wanda xai sauka daga motar ta ga Abuturrab, ta rufe bakinta tace "Lahh wllh yaya ne, ya canxa mota, waow latest ride wllh, wannan shi ake kira da ride" Jamila da Farida dai suna xaune kan kujeran da suka xauna a dakin, Maimoon tace "Ta so ki gani Jiddah wllh sabuwar mota ce..." Jiddah na ganin Maimoon xata dagata ta ga motar da sauri tace "Noo Maimoon am not feeling fine ina jin jiri" Kyaleta Maimoon tayi sai yaba kyan motar da yayi mugun tafiya da ita take, haka ta sa sai da su Farida suka taso suka ga motar ta window su ma suka ya6a sosai, Lkci daya Maimoon ta dawo sense dinta ta kalli Jiddah tana xare ido da sauri tace "Yaya nan xai shigo?" Jiddah bata kai ga ce mata komai ba suka ji an murda kofar dakin, Maimoon ta nufi kofar da sauri ta shiga bude makullin, tana budewa tace "Yaya sannu da xuwa" Daga sama har kasa yake kallonta kafin yace komai ya ga su Farida a xaune, gaishesa suka yi gaba daya kansu a kasa, ya amsa masu da murmushi fuskarsa yace "Yauwa sannunku da xuwa" Maimoon ta marairaice tace "Yaya in gaya maka wllh Aunty Aneesah hana mu xama tayi a parlor..." Da mamaki yace "Saboda me?" Tace "Wai ba gidan ubanmu bane, sai kaga abinda ta mana yaya, gashi da bak'i yan makarantan mu na taho duk ta bani kunya, ta xageni ta xagesu, ni dai ban kulata ba yaya, muna dai xaune parlon still sai ga ta da ta6arya da adda daga kitchen shine fa muka hauro sama da gudu muka shigo nan muka kulle kofa, Banda haka da Allah kadai yasan abinda xata aikata mana yau, ni dai ban kulata ba" Kallonta kawai yake boiling from inside, can ya kalli su farida yace "Ku yi hakuri don Allah" Duk suka ce ba komai wllh, Ya ajiye ledan hannunsa gaban mirror, ya kalli Maimoon yace "Kun ci abinci??" Maimoon ta rufe bakinta tace "Ina fa yaya?? Ko ruwa bamu sha ba tana neman rotsa mana kai da tabarya da adda balle abinci" Yace "Mu je ki daura maku abinci" Tayi wani murmushi tace "Toh yaya" Tana biye da shi suka sauko downstairs, su Farida ma duk suka fito daga dakin wanda su basu ki su yi wucewarsu gida a lkcn ba, Aneesah na xaune parlor har lkcn, Maimoon ta fara wani cartwork tana jujjuya ido tana biye da Abuturrab, shi kam ko kallon Aneesah bai yi ba ya nufi kitchen Maimoon na wani smiling ta yi ma kawayenta alamar su biyota kitchen din, da yake duk sun sha jinin jikinsu da Aneesah haka suka nufi kitchen din gaba daya, Aneesah ta bi su da kallo xuciyarta na suya taji kamar ta kwala ihu ko xata samu saukin abinda take ji a xuciya, is this really happening to her?? Yau ita ce ke witnessing wannan abubuwan, ko a mafarki bata ta6a xaton haka ba, bata ta6a xaton akwai daren da xai xo ta gansa yanda ta ga rana ba, a da idan taji wani na cewa bai yi bacci ba throughout dare ta xata karya ne, sai gashi yau hakan ya faru a kanta, don ko rintsawa bata yi ba, bata yarda tayi kukan dake cinta ba xuciyarta na mata xugu, ta wani dake tana huci daga xaunen da take, Sai da Abuturrab ya nuna ma su Maimoon foodstuffs din kitchen din sannan ya juya ya fita, yana kallon Aneesah da kyau ya nufeta yace "I think i told u the other day, i think i warned u cewar only my relatives are allowed into this house, and i am giving u this last warning today Aneesah, ko kallon banxa kar ki sake yi ma wani jinina idan ya xo gidan nan, that is idan har kina son ci gaba da xama da ni..." Mikewa tayi tana iya kokarin ganin bata fashe da kuka ba tana wani vibrate tace "Do ur worst Aliyu!! Wannan sabon threat din da ka tsira yi min na miye? Abu kadan kace idan ina son xama da kai, ka fito ka gaya min abinda ke ranka game da ni mana, ka fito ka fada nace, na gaji da walakancin ka, na gaji da walakancin da kake min, don ban gane ma'anar idan ina son ci gaba da xama da kai ba, a kan wata yar iska can kanwar bayana xaka tsaya kana gaggaya min wannan magana Aliyu, duk ka sa kanninka sun raina ni, to wllh wllh hakurina ya kare, bayan kauda kai da nake ta yi ina tausan kai na akan auren cin amanar da kayi sai an kara min da wani xafin" Abuturrab ya mata wani kallo yace "Idan har a tunaninki ina threatening dinki to ki dau matakin da kika ga ya dace, find a way out for ur self idan kin gaji da walakanci na kuma hakurin ki ya kare da ni, ki dau action din da ya dace and stop barking" yana fadin haka ya nufi stairs ya bar ta nan tsaye, ta sulale saman kujera ta rike kanta tana dannar xuciyarta kar ta fashe da kuka sbda su Maimoon dake kitchen, wai yau ita Captain ke mata wannan abubuwan, yau ita Captain ke gasa ma magana anyhow har da ce mata she is barking?? mutumin da a baya ko ci kanki baya ce mata komai tayi masa sai dai yayi overlooking baya tanka ta, what is happening to her!! Abuturrab na haurawa sama ya bude kofar dakin Jiddah suna hada ido ta sunkuyar da kanta, ya isa gabanta ya durkusa yana kallonta, ita dai ta ki yarda su hada ido, ya kamo hannunta yace "How are feeling now?" Bata ce masa komai ba, yace "Kina jin yunwa ko?" Still tayi shiru, yace "Ohk u need to sit bath first before eating" Daga haka ya mike ya cire agogon wrist dinsa ya ajiye kan bedside drawer ya nufi bathroom ta bi sa da kallo, bayan ya hada ruwan xafi a bathing tub ya fito, ya bude ledan drugs dinta ya dau iodized salt ya koma bandakin, yana fitowa ya ajiye ledan sauran yana kallonta yace "Should i?" Sai a sannan ta kallesa kamar xata yi kuka tace "Ni wllh bana so, i am okay" Bai tsaya ya saurareta ba yayi leading dinta with his help xuwa bandakin. Abinda tayi masa da safe shi din dai ta kara maimaitawa yanxu ma, ga uban shagwaba da ita ma bata san tana yi ba, shi kam hakan narkar masa da xuciya yake, ya dinga lallabata yana bata hakuri, da kansa ya ciro mata atamfarta da aka yi ma dinkin doguwar riga, ta shirya bayan yayi mata duk abinda ya kamata.... har ta gaji da kunyan nasa ta hakura and she felt much relieved now don da kanta ta maida turarrukan da ya kwaso gaban mirror, sannan ta dawo a hankali ta xauna gefen gadon, ya durkusa gabanta yace "Tell me, me xaki ci? Nasan baxa ki jira Maimoon ta gama girki ba ko?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "Talk to me pls wife" A hankali tace "Xan jira ta gama" Yace "Are u sure?" Ta gyada kai kawai, mikewa yayi ya isa gaban mirror ya dauko ledan da ya ajiye ya dawo ya xauna gefenta ya ciro kwalin dake cikin ledan ya mika mata yana kallonta, kallon kwalin wayar k'iran samsung ta dinga yi sai kuma ta kallesa, murmushi ya sakar mata yayi kasa da murya yace "For u" Sauke idonta tayi ta amsa cikin sanyin murya tace "Nagode Allah ya kara budi" Bata rufe baki ba ya kamo hannunta ya saka mata makulli a palm dinta sannan ya rufe palm din a hankali yace "For you wife" Bude hannunta tayi tana kallon makullin motar, sai kuma ta kallesa with surprise, ya gyada mata kai yace "Naki ne" fadawa jikinsa tayi ba tare da ta shirya ba ta rungumesa ta ma rasa abinda xata ce masa.... Ya lumshe ido a hankali yana jin wani sabon sonta na fixgarsa, ya kai bakinsa kunnenta underneath his breathe yace "I love you Jidderh, i have always love you, ban san tausayi na rikidewa ya koma so farat daya ba sai a kanki, i sacrificed a lot because of u wife, and u changed my mentality toward many things in life, the worst day of my life was the day i was forced to divorce u, i felt empty Jidderh... I was hurt, i was devastated, amma duk yanda Allah ya tsara abu dole hakan xai faru, and the most happiest day of my life was yesternight..." A hankali ya ci gaba yace "I am happy ur pride was mine, and i am appreciating it with a car key, in return i am giving u all my heart, i mean all...." Hawayenta da yaji na sauka jikinsa ya sa ya dago kanta, a hankali ya dinga goge idon nata, gaba daya ta kasa ce masa komai, ya mike ya dagata ya dau mayafinta ya mika mata yana rike da hannunta ya nufi kofa, a hankali take tafiya tana bin sa, har suka sauko downstairs, har sannan Aneesah na xaune parlor yanda Abuturrab ya bar ta, tun da Jiddah ta hangota suna saukowa stairs bata sake kallonta ba har suka shigo parlon, shi kansa Abuturrab bai kalleta ba ya nufi kofa still holding onto Jiddah's hand, Aneesah ta bi su da kallon gefen ido, dai dai nan Maimoon ta fito daga kitchen tare da su Jamila bayan sun daura girkin, ganin Abuturrab da Jiddah sun fita waje ta lallaba ta bi bayansu ba tare da ta bi ta kan Aneesah ba ta tsaya window tana lekansu, Abuturrab na rike da Jiddah har xuwa gun sabuwar motar ya kalleta ya wara ido a hankali yace "Ya maki ko aje a canxa wife?" Rufe bakinta tayi don ta ma kasa ce masa komai, ta bi compound din da kallo ganin babu mai gadin gidan ta nufesa ta rungumesa tana shessheka, Sai da Maimoon ta murxa idonta don tabbatar da abinda take gani sannan ta maxa ta fito daga parlon, wani kara tayi ta nufesu almost running, Jiddah na son sakesa jin muryan Maimoon shi kam ya ki sakinta ya rungumeta gamm, Maimoon na xaro ido tace "Yaya motar ta ne?" Yana murmushi yace "Yeahhh" Ai da gudu ta tafi ta gayyatosu Jamila cike da murna kamar ita aka siya ma mota tana cewa "Ku fito, ku fito, wllh wannan tsaleliyar motar ta Jiddah ce wllh tata ce, ita Yaya ya siya ma ashe..." Gaba dayansu suka fito daga parlon, Maimoon ta dinga tsalle a bakin kofa tana kallon Aneesah dake kokarin fahimtar abinda Maimoon ke cewa, Maimoon ya dinga cewa "Wllh na Jiddah ne motar..." Lkci daya Aneesah ta mike, Maimoon na ganin haka ta bar bakin kofar ta fita tsakar gida don dama so take taga ta tashi, Aneesah ta nufi window da sauri tana lekan waje taga ubansun motar, ga Abuturrab rungume da Jiddah har sannan.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you MG'S SKINCARE In kid'a ya chanza rawarma semutaru asauyata, Wani Kaya se amalende Haka Wani Hadi na musamman se MG'S, Ina ma'abota amfanida kayan MG'S SKINCARE? To bana fa tafi bara munqarawa kayanmu inganci muncire muntsefe munkawo maku qayatattun kayan gyaranjiki da Baki taba amfanida irinshiba a wannan qarnin, Wani irin salo na gishirin kyan daukar magana zakiyi duk kikayi amfanida hadinmu b cika bakiba,ko yayan Hutu basa nuna maki tsadar fataba,duk a 11k fa kachal👌🏻 Beauty kit:11k Student package:7k Soap:3k Bridal kit 18k Kicire kokonto ki warwaro Lalita kidebi Kaya n kerewa SAA Chat:08062991549 or 07046881166 or 07067210195 Call:08064532391 Available in Kano and Kaduna We also have beautiful yet luxury and unique frames for your apartments chat or call 07046881166 Serious buyers only please, Inamasu bukukuwa😍 Kugarzaya @inteesar cakes nd more kuyi order small chops domin bakinku irinsu Cupcake,fishroll,samosa,spring rolls dama duk kayan kwalam da makulashe kunemata 07067210195 Cika alkawari shine takenmu🤝 Thank you [7/31, 12:24 PM] Ummuanwar🥰: Mutuwar tsaye Aneesah tayi jikin window tana kallonsu gaba daya, ta kasa kwakkwaran motsi, lkci daya taji xaxxabin da take ji tun safe ya sake dawo mata, Muryar Maimoon a compound din gidan kuwa ba a magana, sai ka rantse ita aka siya ma mota duk da abun nata har da gayya, Hotuna ta dinga ma Abuturrab da Jiddah tana masu video da wayarta, Jiddah dai taki bude idonta gaba daya kunya ya rufeta, tayi kokarin xame jikinta daga na Abuturrab amma ya ki saketa, duk kunyan kawayen Maimoon dake tsaye ya cikata, Aneesah ta dauke idonta ta juya ma window din baya kirjinta na wani heaving kamar xai fito, mota?? Tambayar da tayi ma kanta kenan a fili, da hannu biyu ta dafe kirjinta tana jin wani abu da bata ta6a ji ba, da gudu ta nufi kitchen kamar wata ta6a66iya.... shigowar Mai gadi compound din ya sa Abuturrab ya sake Jiddah ta juya masa baya da sauri, Maimoon ta tafi ta rungumeta cike da farin ciki take cewa "Congratulations Jiddah, i am really happy for u sis, Allah ya sanya alkhairi" Jiddah dai ta kasa cewa komai suna rungume da juna, Mai gadi ya nufo Abuturrab da sauri duk da bala'in da ya sha a bakin gate, da ladabi yace "Ranka shi dade anyi baki ne, xa a shigo da mota.. nace bari in fara sanar da kai" Abuturrab yace "Ohk ka bude gate din" komawa yayi da sauri xai bude sai ga Hajja ta shigo compound din rataye da katon jakanta wanda babu komai ciki, Cike da fitina take kallon mai gadin tace "Wllh Allah ya isa ban yafe maka ba..." Abuturrab ya nufeta yace "Me ya faru Hajja?" Kamar xata yi kuka tace "Wllh su a Masar in xa su dau mai gadi sai an fara kai sa asibitin kwakwalwa an binciki kwakwalwarsa ciki da bai, basa daukan masu gadi kansu tsaye, banda haka har wannan tsukakken mutumin xai ce bai ta6a ganina ba a gidan nan? Idan ma bai ta6a ganina ba xai ce bai ga kamanni ba? To ni dai Allah ya isa wllh, ya min axabbabben walakanci bakin gate din nan wanda da a Masar ne titi xa a mika ma yara shi suyi ta jifan d'an banxa, ai ba a ma tsofaffi haka a Masar, sun san mutuncin tsoho, to idan ma ni bai ga kamannina da kai ba xai ce bai ga kamannin Hauwa tare da kai ba, tare da ita fa muke, nace yau wllh ko taki ko ta so sai mun taho gidanka tare tunda bata ta6a xuwa ba, amma mutumi kawai ya walakanta mu a bakin gate yace mana daga ina? Allah ya saka min wllh, ita kuma Hauwa ta wani ja6e a mota tayi shiru maimakon tace kai don uwarka gidan d'a na ne ni na haifesa wannan tsohuwar kuma ta haifi ubansa, to wllh bata yi haka ba sai ta ja bakinta tayi gum, mata kawai matsoraciya malam" Dai dai nan driver ya shigo compound din da motar yayi parking Ummi ta bude motar ta sauka, rungumeta Maimoon ta tafi tayi tana murmushi tace "Sannu da xuwa Ummi" Abuturrab kam sai kallon Ummin nasa yake don ko hanyar gidansa kam bata ta6a xuwa ba sai yau, ya kuma yi farin ciki har ransa da xuwan nata, Jiddah ma ta nufi Ummi ta gaisheta da ladabi, Ummi ta sakar mata murmushi tace "Ya ku ke Jiddah, ya gida?" jiddah tace "Lafiya lau Ummi" sauran kawayen Maimoon ma duk suka gaishe da Ummi, Hajja dai taki hakura sai tsine ma mai gadi take tana nuna sa da d'an yatsa wai shi ma sai an masa abinda ya mata a bakin gate, Abuturrab sai danne dariyarsa yake don kawai tsayawa mai gadin yayi yana kallonta kamar ya ga sabon kamu, Abuturrab yyi kasa da murya yace "Yi hakuri Hajjaj xa a canxa sa in sha Allah, wanda kuma xa a canxo xa a duba kwakwalwarsa" Yasan hakan kadai ne xai sa ta hakura, Hajja ta wani sauke ajiyar xuciya tace "To ko da na ji, amma wllh ba a ta6a ci min mutunci irin na yau ba, har kuka sai da nayi a xuciyata, to wannan fitina da axababben walakancin har ina" dariya Abuturrab yayi ya nufi Umminsa yayi mata side hug a hankali yace "Welcome Ummi" ta hade rai tayi masa kallon gefen ido tace "Meye haka?" Dariya Maimoon ta dinga yi, Jiddah dai ta nufi Hajja ta gaisheta cikin sanyin muryarta, Maimoon na washe hakora tace "Hajja ga motar Jiddah, yaya ya siya mata..." Hajja ta juya da sauri ta kalli motar, ta kai minti daya tana bin motar da kallo, sai kuma ta saki wani kabbara tace "Shi Abuntural din ya siya ma Jiddah wannan xukekiyar mota?" Cike da farin ciki Maimoon tace "Wllh kuwa Hajja, yanxun nan aka kawo motar" Ummi dai sai kallon Abuturrab take da mamaki but deep down she is so happy for Jiddah, Hajja ta rike kanta ta kuma sakin wani kabbara tace "Wayyo wayyo, to ko dai na kyautan budurci ne wannan xukekiyar mota ba mu sani ba? Banda haka me yasa bai siya ma Nanisa kazama ba duk xamansu tare, to ko a bazawara ya aureta bamu da labari...." Ummi dai tayi hanyar entrance din gidan bakinta alekum, Maimoon ta bi bayanta da sauri tana kunshe dariyarta, Hajja na kallon Jiddah da ta kasa dago kanta tace "Toh wllh wlh ki kama mijinki ki rike gam yana sonki so ba na wasa ba, da kyar ake samun miji irin Aliyu a wannan xamanin na yan banxa da en iska, ki rikesa ya xama uwarki da ubanki, shine gatanki a nan duniya dai, kishiyarki kuma...." Shiru Hajja tayi jin tarwatsewan abu a cikin gidan, duk suka kalli entrance din gidan, Hajja na gwale ido tace "Ruwa xa ayi ne ba hadari, naji kamar tsawa" Wani tsawan glass din suka kuma ji, Abuturrab ya nufi cikin gidan da sauri... Upstairs Abuturrab ya dinga jin tarwatsewan glasses, Ummi da Maimoon dai na tsaye parlon suna kallon sama su ma, haurawa yayi Maimoon ta bi sa da sauri, Hajja na xare ido ta labe daga balcony tana leko parlon, Jiddah ma dae na tsaye gefen Hajja gabanta sae faduwa yake, kawayen Maimoon dai dama gate suka nufa gaba daya, still Abuturrab yayi bakin room din Jiddah with mouth agape yana kallon Aneesah da tayi kwatsa kwatsa da mirror ta tarwatse duk kwalaben gaban mirror din a kasan tiles, sannan press din dakin ma tayi kaca kaca da madubin jiki, ko ina a kasan tiles din dakin glass ne a kwance da drop din jini, furniture din gadon ma duk ta mummuka masu katon ta6aryan hannunta, daga hannun nata har kafanta jini ne ke diga kasa, gashin kanta duk a baje kamar sabon kamu sae wani huci take, da gudu Maimoon ta sauka kasa tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un..." Ummi da hankalinta yayi mugun tashi tace "Me ke faruwa haka?? What's happening?" Maimoon bata tsaya ba Ummi amsa ba ta nufi kitchen da gudu ta dubo wani tabaryan, ko ta kan Ummi bata bi ba balle Hajja ta haura sama tayi hanyar dakin Aneesah, sae dae kash taji dakin a kulle an sa makulli... Abuturrab yayi ma Aneesah tsawa for d second time kamar Zaki yace "Nace me kika aikata haka Aneesah?? Are you mad??" Ta juya tana kallonsa da idanuwanta da suka koma kamar garwashi tana huci, sae kuma ta fashe da wani dariya tace "Dakin amaryarka na tarwatsa kaga nima sae ka tarwatsa ni... babu fetur ne da wllh wuta nayi niyyar cinna ma dakin without minding ko da ita a ciki ko babu, Aliyu shigo ka kasheni shine hukunci mafi ma'ana da ya kamata ka yi mani ka huce, nayi hakan ne don ka kasheni kawai, ba dai dakin Jiddarka na mayar haka ba, come in and take revenge, nace shigo ka dau fansa..." Tana fadin haka ta nufesa a guje jini na xuba jikinta ta cakumosa tayi wani ihu kamar xata tsaga gidan tace "Ka dau fansa nace Aliyu, dakin matar so fa na mayar haka, wai ma uban wa ya haifeka da xaka ke walakanta ni don ka auri warce aka yi ma like like aka kawo maka, har ni xan xama abar walakancin ka?? me matsiyaciyar ta fi ni da shi banda rashin asali da kauyanci????" Bata gama rufe baki ba ya dauketa da wani wawan mari ya shaketa sannan ya bugata da bango ya kuma kai mata wani marin, tayi taga taga xata fadi har sannan jini na xuba sosai daga jikinta, duk jirin da take gani haka ta dinga kunduma masa xagi da shi da Jiddan tana ci gaba da fashe fashe a dakin, juyawa yayi ya nufi bangarensa direct kamar xai tashi sama, Maimoon ta hauro sama tare da Hajja da jikinta ke bari, Hajja na leka dakin Jiddah suka yi ido hudu da Aneesah dake huci, ta fasa wani ihu a gigice ta sauka kasa ta nufi kofar fita parlor tana cewa "Huhuhu.... Idan nayi magana sae a dinga min kallon er ta'adda, idan nayi magana sae a maidani salubabbiya hotiho, wayyo Allah!!! Wato tun daga ranan da nayi arba da Aneesah a gidan Usman tana amarya nasan ba lafiyayya bace a kwakwalwa, ni nasan sabuwar kamu ce, wllh tun daga ranan nasan ta6a66iya Aliyu ya auro na dai ja bakina ne nayi shiru, to duk ba wannan ba don bai dameni ba.... amma me??? kai kana ganin kazantarta kasan da ta6in hankali a tare da ita, don me lafiya baxae yi wannan kazanta da take yi ba, to yau dai hauka muraran ya ta66ata a gidan Aliyu, wayyoo jama'a, babu dawanau ne a kaduna stey? Duk girman kaduna babu dawanau ne?" Fita tayi parlon tana kwala ihu tana cewa "Masu gadi ku kawo dauki, jama'an anguwa ku kawo dauki, masu gidaje a anguwan nan ku taimake mu ku kawo dauki, jikana ya auri mahaukaciya bamu sani ba...." Mai gadi ya ja gefe da sauri yana kallon Hajja baki bude, wata mota taga ke tahowa ta sa hannu bibbiyu tana tsayar da motar cikin daga murya tana cewa "Wayyo ku kawo mana dauki, ni daga Masar nake ban san wani gidan mahaukata a kaduna ba wllh" motar ta tsaya, aka sauke glass din baya da gaba, wata mata da baxata wuce shekaru hamsin da biyar ba ta bude motar ta sauko da sauri tace "Lafiya kaka, me ke faruwa?" Tana magana ne tana kallon gidan don a xaton ta gobara ne, Hajja ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Wllh matar jikana ce ta haukace mu kuma bamu san dawanan Kaduna ba" Matar ta xaro ido tace "Subhanallah, a nan gidan take?" Hajja na kuka tace "Wllh kuwa, daga Masar nake ban san dawanan garin ba" Wanda ke driving din motar ya sauko shi ma jin abinda Hajja ke cewa yana kallonta da mamaki, dattijuwar matar tace "Toh me gidan fa?" Hajja tace "Wani me gida?? Ai yana ciki ya rasa yanda xai yi da ita duk ta rotsa kaf kayan gidan tayi kwatsa kwatsa da shi har kayan kallo" Guy din da ya sauka daga motar ya shiga cikin gidan Hajja ta bi bayansa da gudu tana cewa "Ku taimakemu mu daureta kafin a mika ta gidan mahaukatan" Matar ma ta bi bayansu xuwa cikin gidan, Basu tadda kowa parlon ba, Hajja ta nuna masa hanyar stairs tace "Suna can sama, ka lallaba ka haura" Mahaifiyarsa dai na tsaye ya juya ya kalleta tace "Be very Careful Aliyu" Hajja tace "Ehh wllh gidan Aliyu ne ashe kun san sa, ai jikana ne, ni na haifi ubansa, ko ba wani matukin jirgin sama ba" Wanda aka kira da Aliyu dai ya haura sama bai tsaya ba Hajja amsa ba, Hajja ta bi sa da sauri jikinta na rawa, Ummi ce tsaye corridor ta amshi takarda da biron hannun Abuturrab cikin fushi take cewa "Baka da hankali ne ina magana kana magana Aliyu? Ban isa da kai bane kake son ka nuna min" Abuturrab ya juya kawai ya nufi bangarensa xuciyarsa na tafarfasa, Hajja na kallon Ummi kamar yanda Ali da mahaifiyarsa da suka hauro sama suka tsaya suna kallonta, a hankali Hajja tace "Ya dauretan ne?" Bata jira me Ummi xata ce ba ta leka dakin taga Aneesah tsaye sai huci take har sannan tana rike da tabarya, Jiddah da Maimoon suna can karshen corridor din sai kallon Ali dake tsaye da mum dinsa Jiddah take sai dai shi bai ganta ba, meanwhile ita kuma mahaifiyar Alin sai kallon Jiddah take, Ummi ta tsaya kofar dakin tana kallon Aneesah tace "Ajiye abun nan na hannunki ki fito" Jefar da tabaryan Aneesah tayi ta fito dakin, bata kalli kowa a cikinsu ba ta nufi dakinta kamar xata tashi sama, cikin daga murya Hajja ta dinga cewa "Allah ya tsine maki albarka shegiya, in sha Allahu karshenki ya xo a gidan nan tunda kika ta6a kayan Jiddah, biliyoyi aka kashe kafin ayi mata wannan kayan, don haka ko waye ubanki a Habuja yau sai an kai ni wajensa idan ma bara xai fara ya fara don kaf dukiyarsa basu kai su siya kayan dakin Jiddah ba..." Ko kallonta Aneesah bata yi ba ta ciro makullin dakinta da ta tusa a kirjinta ta bude kofar ta shige sannan ta kulle dakin da key, Mahaifiyar Ali da mamaki ya cikata tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, menene amfanin haka?? Me mata suke son mayar da rayuwarsu a wannan xamanin?" Hajja dake ta xufa tace "yan iska mana... to wllh karshenta ya xo a gidan nan, in har xata iya ma kayan dakin da basu ji ba basu gani ba wannan tijaran to wllh tsaf xata kashe mutum da ta6aryar hannunta, ga fa yar mitsitsiyar kishiyar tata can, warce a haihuwan kaji tayi jika da ita kai har tattaba kunne, da er cikinta fa take kishi don bala'i har da lalata mata daki haka, toh Allah ya tsine maki Nanisa" Ali ya kalli Jiddah da Hajja ta nuna, kallonta ya dinga yi da mamaki ko kiftawa babu, Mum dinsa ma kallon Jiddah take har sannan, Jiddah ta sunkuyar da kanta, Hajja ta kalli Ummi tace "Huhuhu.... da na san abinda xai faru gidan nan kenan yau wllh da Ramlah xan taho asirina a rufe ba ke ba, a kira min ita yanxun ma ta xo taga abinda aka yi ma kayan yar ta, maxa kira min ita Maimoon ba mu ga ta shiru ba ai" a hankali mahaifiyar Ali tace "Toh Allah ya kiyaye, Allah ya kyauta, but this is so bad wannan wani irin bakin kishi ne haka ni Amina?" Hajja ta karbi wayar da Maimoon ke mika mata bayan ta kira Umma, Umma na daga kiran Hajja ta fashe da kuka tace "Ramlah ki taho gidan Aliyu yanxun nan ba lafiya babu dalilinta, ki saka hijabinki ko ba kaya ki taho kawai Ramlah" tana gama fadin haka ta mika ma Maimoon wayarta, Hajja ta kalli su Ali tace "Ku kuma da ku ka saurareni har ku ka shigo ku ka gane ma idonku wannan abun al'ajabin Allah ya maku albarka, kun dai ga me rayuwa ke ciki yanxu, kishi ne ake yi irin na tsinannun bayi, gashi nan dai sbda kishi ta hallaka kayan dakin kishiyarta har lahira, to karshen aurenta ne kawai ya xo ba mu sani ba" Ummi ta sauka downstairs ta xauna tana al-ajabin wannan abun da ya faru, tare Hajja ta sauko da Ali da mum dinsa, sai a sannan suka gaisa da Ummi, Hajja na nuna Ummi tace "Ita ce uwar mai gidan fa, amma kun ga babu wani hukunci da ta dauka, gata dai da takarda a hannu kamar malamar makaranta bata ta6uka komai ba, ai samun uwa tsayayyiya ma wani abu ne a rayuwan nan wllh, tirrrr" Hajiya Amina na kallon Ummi tace "Can we talk outside pls" Mikewa Ummi tayi ta bi bayanta suka fita compound, Ali na kallon Hajja yace "Duk matansa ne kenan kaka?" Hajja tace "Ehh wllh, ita warcan yar farar yarinyar da ka gani a rakube kamar mage sai gwale ido take to kayan dakinta aka yi ma wannan cin mutuncin da tijara, kuma gobe satinta ke cika daya da tarewa a gidan, ita kuma me k'irar yan da6a warce tayi aika aikan ta kai wata shidda ko shekara daya ina ga a gidan yanxu, toh kai in kai ne Aliyu don Allah wani hukunci xaka dauka bawan Allah?" Ya sauke ajiyar xuciya yace "Sai kawai in sallami ita wannan me 6arnan don da alama baxa ta bari a xauna lafiya ba" Hajja tace "Allah ya maka albarka, don kuwa wataran kashe Jiddar xata yi har lahira ko??" Ali dai yayi shiru, Hajja tace "Xa ma ka san me gidan idan kana shige shigen jirgi sbda matukin jirgin Najeriya ne, kuma ance shi kadai ne bakin fata" Murmushi yyi yana shafa kansa yace "Allah sarki" Bayan wani lkci Ummi ta shigo parlon ta kalli Maimoon dake saukowa tace "Kira min Aliyu" Mikewa Hajja tayi tace "A kira maki shi kiyi masa me?? Idan kina da wani amfani wllh shegiya nake Hauwa, ke da xaki sa sai ya rabu da matsiyaciyar yarinyar yau amma kinyi shiru kin ja gefe kamar dai kin samu fim din hausa kina kallo" Ummi bata ko kalli Hajja ba tace "Maimoon daga nan ku sauko har da Jiddah driver ya kai ku can gida yanxu" Ali ya sauke ajiyar xuciya don fa gaba daya case din nan ya daure masa kai, yace "Allah ya rufa asiri, Allah ya tsare gaba Kaka" Hajja tace "Wllh sai Aliyu ya saketa baxai xauna da yar da6a ba a gaskiya da raina, don daga wnn abun da ta aikata xaka san tana hulda da rikakkun yan daba" Ba a dau lkci ba Abuturrab ya sauko downstairs, har sannan fuskarsa a daure yake xuciyarsa na tafarfasa, Hajja tace "Ba daure fuska xaka yi ba kamar wawa, mataki xaka dauka yanxun nan, ni abinda ya tsaida ni kenan don da na tafi tuntuni, da fa a Masar ne har ni xa a kwashe idan yan sanda suka xo gidan nn wllh, sbda kamata yayi tun farkon lamarin a kai masu rahotu, to wannan sai Ramlah kuma tace tana hanya" Abuturrab ya nufi Ali yana kallonsa ya mika masa hannu, Ali yace "You just have to be calm and take things easy, do not make conclusion while angry" A hankali Abuturrab yace "In sha Allah" Ali ya mike yace "Toh kaka Allah ya tsare gaba" Hajja tace "Toh ina xaka kuma? Uban wa xa mu nuna a matsayin shaidun mu idan ka tafi?" Yayi murmushi yace "Ai gidanmu na kusa da wannan Kaka" Hajja tace "Atoh shkkn, duk kai da mahaifiyarka xa ku yi shaida ko gidan uban wa xa aje da kess din nan" Ali yayi ma Ummi sallama ya fita parlon, mikewa Ummi tayi ta hade kan su Maimoon suka bar gidan tare da driver, bayan tafiyar su da mintuna kadan sai ga Umma ta shigo babu ko sallama fuskar nan nata bbu yabo bbu fallasa ta jefar da jakanta saman kujera tace "Me ke faruwa Hajja?" Hajja ta mike ta rushe da wani kuka tace "Hau sama ki gane ma idonki Ramlah, je ki sama Ramlah..." Umma ta haura sama da sauri, tana arba da dakin Jiddah ta sauko tayi wani irin dariya tace "Wllh wllh ban ga shegen da xai hanani daukan fansan abun nan ba, ban ga wanda ya isa hanani daukan matakin da ya kamata ba, kuturin uba..." Tana kai wa nan ta figi jakanta ta nufi kofa kamar xata yi tsuntsu tana huci, Hajja ta dau katon jakarta ta bi bayanta sum sum tace "Ni da nasan kan komai" Ummi ta sauke boyayyen ajiyar xuciya ta kalli Abuturrab da kansa ke kasa tace "Aliyu" Dagowa yayi ya kalleta da idanuwansa da suka koma kamar garwashi, shi dai ya san ba don mahaifiyarsa dake gidan nan yau ba babu abinda xai hana shi yi ma Aneesah dukan tsiya wanda har sai ta suma, bai yi farin cikin kasancewar Ummi a gidan ba wannan abun ya faru, Ummi tayi kasa da murya tace "Kayi hakuri Aliyu, kar ka yanke hukunci cikin fushi, kuma ina umartanka duk hukuncin da xaka dauka banda saki...." ya marairaice mata yace "Ummi me yasa xaki ce haka? To meye amfanin xama da ita Ummi? Wllh baxan iya ci gaba da xama da ita ba, ta fita raina gaba daya, ko na xauna da ita ni nasan baxan kwatanta adalci tsakaninsu ba" Ummi tace "Xaka yi Aliyu, now tell me meye amfanin sakin nata? Shkkn sbda saki abun banxa ne sai ku maida shi ado kai da mahaifinka? Haba Aliyu, ni ban hanaka daukan duk matakin da xaka dauka ba amma kar ka saketa, Alhmdlh abun ya tsaya iya kayan daki kuma ba komai ya ja tayi haka ba sai kishinka, da bata sonka kuma baxata yi kishinka ba, kowacce mace da kalan nata kishin a xuciya, abinda tayi kuma yana nuni da how frustrated she is, ba wai nace abu me kyau tayi ba Aliyu, dole dama xa a hukuntata, but plss do everything except divorcing her, ko kadan bana son kalman nan ta saki, ban hanaka nuna mata bacin ranka ba amma don Allah banda saki kayi hakuri ka ji, kaga ta dalilin wannan abinda ya faru kila Abban naka ya hakura ka raba masu gida, sannan ina son tambayarka motar da ka siya su biyu ka siya ma ko yaya?" Ya kalli Ummi yace "Kawai warce ta cancanci motar na siya ma Ummi" Ummi tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Toh kai ka tsokano bala'in kenan, wa yace maka ana haka? Idan Kyautatawa kake son yi ma daya a cikinsu sai dai kayi shi a boye ba a sarari ba ai" Shiru yayi ba don maganan Umminsa na masa dadi ba, gashi baxai ta6a iya cewa xai ce mata Aa ba, yanxu yana ji yana gani xata hanasa sakin Aneesah, jinginar da kansa yayi jikin kujera yana jin xuciyarsa na tafarfasa, Ummi ta mike ta haura sama kofar dakin Aneesah ta tsaya ta kwankwasa tace "Aneesah?" Sai da ta kwankwasa sau uku sannan Aneesah ta bude dakin, Ummi ta shiga bedroom din nata ta kulle kofar tana kallonta, Aneesah ta koma ta ci gaba da xamanta a kan carpet idanuwanta sunyi jajir ga yanyankewan da tayi a hannu bai fasa xuban jini ba, Ummi ta ja kujera ta xauna tace "Me yasa kika aikata abinda kika aikata Aneesah" Kamar jira take ta fashe da wani matsanancin kuka tace "Ummi tunda yayi auren nan yake walakanta ni yake ci min mutunci, ya fita harkata bai damu yayi magana da ni ba, bai damu da halin da nake ciki ba, all he is after is his new wife..." kuka sosai take, Ummi tace "Kuma a tunaninki fasa kayan dakin Jiddah da kika yi xae canxa komai ne?" Aneesah ta hade kai tana kuka sosai, Ummi tace "Baki kyauta ba Aneesah, ko mahaukaci baxae aikata wannan abun da kika aikata ba, yanxu meye amfanin hakan?" Aneesah dai kuka kawai take, Ummi tace "Yanxu baki tunanin abinda xae je ya dawo wannan barnan da kika yi? Ko shi Aliyun kina ganin kyaleki xai yi da ba don ina gidan nan ba yau? Balle warce Jiddah ke hannunta?" Shiru Aneesah tayi tana share idonta, Ummi tace "Tashi mu je parlor" Tashi tayi ta dau hijab dinta ta saka tana hawaye ta bi bayan Ummi, suna saukowa downstairs, suka shiga parlon, kafin Ummi tace komai ta durkusa gaban Abuturrab tana kuka sosai tace "Don Allah kayi hakuri Captain, wllh sharrin shaidan ne, I don't know what came over me, kayi hakuri ka yafe min..." Ji yayi kamar ya haureta yana jin wani mugun tsanarta a xuciyarsa, ko ganinta bai son yi a sight dinsa wllh, ganin kallon da Ummi ke masa ya dake yace "I have nothing to say in here, tunda ba kayana kika yi ma haka ba, u wait for the consequence from the owners" Aneesah ta kalli Ummi, Ummi tace "Tashi" mikewa tayi Ummi ta dau handbag dinta suka nufi kofa Aneesah na biye da ita, Abuturrab ya bi Aneesah da wani mugun kallo har suka fita, he just can't keep on staying with her as his wife, ya tsaneta har ransa. Ko minti sha biyar basu yi da fita ba sae ga Umma da yan sanda Hajja na biye da su sae cewa take "Da kafinta ya kamata a xo don shegiyar ta garkame kofa tun daxu, shi ae jijjige kofar baxata masa wahala ba tunda aikinsa ne" Umma ko kallon Abuturrab bata yi ba ta nufi sama yan sanda mata biyu na biye da ita, bayan wasu mintuna suka sauko Umma na masa wani kallo yace "Ina take?" Abuturrab yace "Ummi ta fita da ita" da mamaki Umma tace "Ummi??" Hajja ta saki wani salati ta rike kanta tace "Amma daga tambadadde sae Hauwa, ta fita da ita ta kai ta ina? Kun dai ga jaraba ko?? Wato yanda Hafsah ta dinga gallaza mata taki barin a dau mataki haka take so a dinga yi ma Jiddah sbda bakin hali da mugunta? To wllh baxata sabu ba, to wa ma ya sani ko ita ta saka Aneesar ta aikata abinda ta aikata tunda har xata iya fitar da ita daga gidan? Kai jama'a, wa Hauwa take so ta burge a nan? Ita a dole ta Allah wai ko? to Allah ya wadaran naka ya lalace dai.." Umma ta fice da yan sandan xuciyarta na tafarfasa, Hajja ta bi bayanta tana cewa "Na gaji da Hauwa wllh, na gaji da halinta, to wai uban wa xata burge ne ban gane ba, da kyar idan bbu hadin bakinta a wannan tsiyar da Aneesah ta tafka, wato gwara ta hade kai da Aneesah a cuci Jiddah, ai kuwa xan nuna mata ni er banxa ce wllh" Mikewa Abuturrab yayi ya wuce sama rai babu dadi, ko kadan bai son ya kwana da auren Aneesah a kansa yau, Umma ta sallami yan sandan ta nufi gidan yayarta tare da Hajja, har sannan xuciyarta na tafarfasa, ai wllh Aneesah bata ci bilis ba, sae dai idan canxa sunanta aka yi daga Ramlah..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 FZ Beauty Supplements Dealer ce ta supplement masu qara fito da kyaun mace ko namiji, hadi da qarama garkuwar jiki kuzari. Muna sayarda Supplemnt kamar na qarin duwawu, akwai wanda zaya taimaka wurin dawoda martabar Nono, akwai na rage qiba da tumbi, akwai na rakwainuwa, akwai na tada komada, akwai masu saka hasken fata da qyalli, akwai na infection, akwai na saka hasken ido da hakori sannan akwai na gyaran turaka. Muna maraba da mai sayen daya ko sari. Wa.me/2348143821028 [8/1, 3:32 AM] Ummuanwar🥰: Ummi dake xaune parlor ta daga kai tana kallon Umma da Hajja da suka shigo parlon babu ko sallama kamar an jefo su, Umma tace "Yaya na je can gidan na samu labari kin tafi da yarinyar nan Aneesah" Ummi tace "Ehh ya aka yi?" Umma tace "Ban gane ya aka yi ba Yaya, kin kuwa je sama kin ga abinda ta aikata ma kayan Jiddah?" Ummi tace "Na je, Allah kuma ya tsayar a nan Ramlah" Umma tace "Ba xancen kinje bane yaya, dukiya ce ta walakanta haka fa?? Ba sato kudin wanda ya siya mata kayan yayi ba" Ummi tace "Toh ya kike son ince Ramlah tunda dai abinda ya faru ya riga da ya faru sai ayi addu'an Allah ya tsare na gaba, ko da abinda kike son ince da ya wuce wannan? shi mai gidan ne xai dau hukuncin da ya dace amma ba mu ba, iyaka idan mun ga baxai yi adalci ba sai muyi involving kanmu" Hajja da ta kankance ido tana ta kallon Ummi tace "Tabdii, ashe haka kike ban sani ba Hauwa? Ashe haka kike? Tun ranan alhamis nake ta baxa ido Usman ya dawo in yi masa kaca kaca akan maganaganun da Hafsah ta min ranan a gidan Aliyu, sannan in nuna iko na da isata ya rabu da ita na har abada don ta ci min mutunci ta xageni ta min rashin da'a, shine kiri kiri yanxu kike nuna ma Jiddah bakin ciki kin je kin dauko kishiyarta mahaukaciya da tayi mata axababben ta'adi kin xo kin boyeta, kawai muka kwashi kafa muka je da yan sanda kika kunyata mu a gabansu?" Ummi tace "Hajja shi fa duniyar nan da muke ciki d'an hakuri ne, wata rana sai labari, sai a ga kamar ba ayi ba wllh, meye riba don ka xuba ido an ci ma sa'ar er ka mace mutunci, 'ya yan nan fa muna da su ta ko ina, kishin nan kuma halitta ce a xuciya sai dai na wani ya fi na wani, ko ince wani yayi na jahilci, sannan abinda Aliyu yayi bai kyauta ba wllh in dai xancen gaskiya xa ayi, idan xai kyautata ma amaryarsa don wani dalili na daban sai yayi sa cikin sirri ba a sarari ba, to what was he expecting dama idan ba tashin hankali ba a gidan nasa yau, ke kuma Ramlah halan har yanxu yan sanda basu gaji da ganin fuskarki bane a yankin nan? Komai kice yan sanda abu da xa ayi solving cikin gida sai ki kwasa ki kai ma yan sanda? Who does that for God sake?" Hajja ta rike kai tace "Huhuhu Allah ya wadaran naka ya lalace, na kara tsoron Hauwa, na tsorata da lamarinta!! waiiiiii Allah" Umma dake ta kallon Ummi babu ko kiftawa tace "Fine and good, daga yanxu duk wani abu da ya shafi gidan Aliyu dama na cire hannuna in sha Allah" Ummi tace "Aa gwara ki cire wllh da wannan sintirin gidan yan sandan dai, don wannan ba yi bane... kullum ana ganin yan sanda na kai komo a gidansa, babu saiti ne abun?" Umma tace "Ai sai ki tsaya ki saurareni yaya, ban gama ba" Ko kallonta Ummi bata yi ba, Umma tace "Amma kinga a kan lamarin Jiddah? Wllh babi wanda ya isa ya sa in cire hannuna, sai inda karfina ya kare ba sani ba sabo, kuma wallahil azeem sai an biya aika aikan nan da yar iskar tayi mata a daki, babu ruwana da wanda xai biya, kawai abinda na sani a mayar ma yarinya da dakinta yanda yake, kuma wllh baxata koma gidan ba sai an canxa mata kayan dakinta dai dai da yanda nayi mata" Hajja tace "Lallai... Toh da fa, ai babu tantama Hauwa ta aiki Nanisa tayi aika aikan da tayi, ko rantsuwa nayi baxan yi kaffara ba, sannan Usman na dawo xan basa shawaran ya dawo da matarsa Hafsah tun dai kishiyar abar dadi ce, kowa sai yayi ta fama da na shi" Ummi tayi murmushi tace "Kowa fa da halinsa yake xaune Hajja, ni wllh bana mata bakin cikin dawowa dakinta, karya ce ke karewa ba dai gaskiya ba..." Kwafa Hajja tayi ta nufi dakinta, Umma kuma ta fice daga gidan gaba daya.... Abuturrab na xaune parlor tun bayan fitar su Umma, gaba daya good mood dinsa yau ya baci, hukuncin da xai ma Aneesah kawai yake tunani, ga shi Ummi ta hanasa hukunci me kankat wato saki, abubuwan da ta dinga masa tun farkon aurensu ne ke dawo masa da yanda ya sameta ba virgin ba, and he hate himself for everything, he hate himself for being silent for that long babu wani hukunci da ya dace da ita banda ya rabu da ita na har abada don ba canxa halinta xata yi ba, ba daina abubuwan da take yi xata yi ba, babu abinda yake basa mamaki irin yanda ya iya xama da ita for this long duk da mugun kazantarta, a yanda ya ba ma tsafta muhimmanci a rayuwarsa bai ci ace ya iya ci gaba da xama da Aneesah ba, kai bai ma ta6a xaton xai iya rayuwa a inda kazanta yake ba, duk wa ennan tunanin suka hadu suka sa yaji inaa baxai iya rayuwa da ita a matsayin mata ba, banda he was impatient tun xamansu na farko da Jiddah ya gano me tsafta ce sosai, bai ta6a dawowa ya tarar da gidan ko jikinta ba dai dai ba, komai ya gwada mata a rananta na farko a gidan yayi sinking a kanta, bude kofar parlon aka yi ya daga kai da sauri Umma ta shigo da Maimoon da wasu yan mata biyu, ko kallonsa bata yi ba ta wuce sama su Maimoon na biye da ita, Maimoon sai boye hannunta take cikin Hijab dinta, Abuturrab ya bi su da kallo har suka haura sama, next thing da ya fara ji shine fashe fashe da tarwatse tarwatse a sama, ya jinginar da kansa da kujera sai kuma yayi murmushi, shi dai ko motsawa bai yi ba har suka sauko kasa bayan minti talatin, Umma ta nufi kofa kamar boss su Maimoon na biye da ita a baya, ko da wasa Maimoon bata yarda ta kalli inda Abuturrab yake ba, ya bi su da ido har suka fita sannan ya mike ya haura sama, dakin Aneesah da ya gani a wangale ya nufa, ya tsaya bakin kofa yana kallon yanda suka yi kwatsa kwatsa da dakin don har ya fi na Jiddah muni, har akwatunanta sai da suka faffasa, ga show glass dinta me shegen tsada da aka kawo mata kwanan nan shima duk sun hallaka shi, ya fi minti biyar tsaye kafin ya juya a hankali ya bar bakin kofar, yana tunanin dama haka auren mata biyun yake? Shi ya xata a film kawai irin haka ke faruwa, so even in reality, reality din ma a gidansa, ya sauke wani ajiyar xuciya shi dai baxai ce ya ji haushin su Umma ba ko kadan that serves Aneesah right, downstairs ya koma ya ci gaba da xamansa a nan. Throughout ranan a dakin Ummi Aneesah ta yini, haka nan kawai taji hankalinta ya kwanta sosai, ko ba komai ta samu saukin abinda xuciyarta ke mata tun shekaranjiya, ganin idon Ummi ya sa duk aka kira sallah kafin a ajiye mic a masallaci xata tashi taje tayi alwala a bandaki, da yake kafin su dawo gidan sai da Ummi ta kai ta chemist aka duba mata yankewan da tayi aka yi mata alluran tetanus sannan aka bata drugs shi sa ta samu saukin xafin wajajen da ta yanke, rabon da ta ci abinci har ta manta sai yanxu a dakin Ummi da aka kawo mata tuwo me xafi da miyar kubewa, ramar da tayi was so obvious shi yasa Ummi ta sake tausaya mata don a hakikanin gaskiya kishiya ko ma wace iri ce babu dadi kai ko da kishiyar rana daya ce, balle wnn irin bambanci da Abuturrab ya nuna kiri kiri ai sai mutum ya hadiyi xuciya ya mutu, Aneesah ta gama cin tuwon ta ajiye plate da bowl din gefe ta tafi bandaki ta wanke bakinta ta fito ta xauna saman darduma, ita fa bata ji tayi regretting abinda ta aikata ma dakin Jiddah ba, da son samu ne har da motar ya kamata ta hada a lkcn, ta share hawayen da ya kawo idonta duk da xuciyarta ya rage xafin da yake mata amma har sannan bai dawo dai dai ba, duk son da take ma Abuturrab xai walakantata ya ci mata fuska haka dama... tana son kiran Aunty da yan uwanta amma bbu dama tunda bata taho da wayarta ba, bude kofar dakin aka yi ta daga kai, suna hada ido ya wani daure fuska ya juya ya fice daga dakin don bai san tana ciki ba da baxai shigo baz ta bi sa da kallo. Main parlor ya koma ya xauna sai ga Ummi ta fito daga bangaren Abba wanda ko minti talatin bai yi da dawowa gidan ba, ya gaisheta ta amsa tana kallonsa, mikewa yayi yace "Abba ya dawo ne?" Tace "Ehh" parlon ya nufa ya shiga ya gaida Abban nasa, yana xaune cikin parlon Hajja ta shigo, Abba ya gaisheta da ladabi yace "Dama yanxu xan shigo ai dakin naki Hajja" Hajja tace "Aa ba ruwana ni ba sai ka shigo ba, ni da abu ya tsaya min a rai ba gashi na taho da kaina ba" xaunawa tayi parlon tace "Toh abubuwan da suka faru dai yau Usman da a Masar ne kai da kake tushen komai xa a daure, abubuwan da suka faru yau kam sai godiyan Allah waiiii, Aa ban ta6a ganin haka ba ko a pim" Abba dai kallonta yake ta yi, Hajja tace "Toh ba dai komai bari Ramlah ta iso na sa yara sun kira min ita daxu so nake ayi komai gaban idonta, tun da na dawo Masar abubuwa ke ta faruwa a garin nan, wanda lkcn da nake bauchi babu haka wllh" Abba ya sauke ajiyar xuciya yana kallon Abuturrab yace "Do u have any idea of what happened?" Hajja tace "Aa ba sai ka juya masa yare ba, ni nan xan maka bayanin komai tunda a kan ido na aka yi, amma sai Ramlah ta iso, to amma kafin ta iso ina son kayi kiran Hafsah ta xo, nasan ai tana garin, kayi kiranta ta xo gidan nan" Kallonta kawai Abba yake, Hajja ta kalli Abuturrab tace "Ta shi mu je, idan kowa ya hallara sai a dawo ayi magana sinka sinka" Ya kalli Abbansa, Abba yayi masa alaman da su tafi, mikewa yayi ya bi bayanta suka fita, shi fa duk gaba daya tunaninsa na kan Jiddah amma shakkan xuwa gidan Umma yake, bai ta6a tunanin xai yini yau ba tare da ita a gefensa ba, is she even feeling much better now? Ta iya ta ci abinci kuwa, duk wa ennan tunanin suka taru suka damesa a dakin Hajja, wanda kawai Hajja surutunta take bai san me take cewa ba, Da karfi Hajja tace "Ko ba haka ba Aliyu?" Ya daga kai ya kalleta duk da bai san me take cewa ba a hankali yace "Haka ne" Tace "Atoh, kowa xai san ni er banxa ce wllh, shiru shiru na nacutata tun ba yau ba na sani" Yana kallonta yayi kasa da murya yace "Hajja don Allah idan an xauna kice masu su bar ni in tafi da matata, sai ta xauna bangarena kafin a canxa mata kayan daki, ita kuma Aneesah dama xance taje gida ta huta ne na kwana biyu don na gaji da halayyanta wllh" Hajja tace "Nima nan da ba gida daya muke ba na gaji da ita balle kai, ita kuma Jiddah uban wa ya isa ya hanaka tafiya da ita mutum da matarsa, ai dama tare nace Ramlah su taho, kafarta kafarka, babu shegen da xai shiga hakkin ka ina gidan nan" Sosai Abuturrab ya ji hankalinsa ya kwanta, sallama aka yi bakin kofar dakin, Hajja ta daga kai da sauri tayi mici mici da ido kamar me son gano muryar, Sai kuma ta amsa tace "Bismillah" Aka bude kofar Aunty ta shigo dakin kanta a kasa hannunta rike da karamin cooler, Hajja sai satan kallonta take, Aunty na murmushi ta xauna saman carpet bayan ta ajiye coolern hannunta tace "Sannu Hajja" Hajja tace "Yauwa sannu" Cike da ladabi kanta a kasa tace "Ina yini Hajja?" Hajja ta hade hannunta yanda manya ke gaisuwa tace "Lafiya lau Hafsah, lafiya lau wllh" Aunty tace "Fatan mun same ku lafiya, ya jiki jiki" Hajja tace "Aa wllh Alhmdlh, ashe kina dai kadunan" Aunty tayi d'an murmushi tace "To ya xa ayi Hajja, muna nan wllh, sai yanda hali yayi" Hajja tace "Allah sarki, to sannu da xuwa" Aunty tace "Yauwa Hajja, rayuwar ce sai hakuri wllh" Abuturrab da ya dauke kansa da farko don bai yi niyyar gaisheta ba sai kuma ya juya ya d'an kalleta babu yabo babu fallasa da nufin gaisheta, amma me?? buda ido yyi sosai ganin abu take kokarin cusawa karkashin gadon Hajja tana jan Hajja da xance, ya kalli Hajja dake ta wani murmushi tana cewa "Hakuri kam ai ya xama wajibi a wannan xamanin" Aunty ta gama tura abinda xata tura ta dauke hannunta da sauri, sai kuma ta mike tace "Toh Hajja bari in karasa parlon Yallabai shi yayi kirana dama" Hajja tace "Aihoo ai ni nace ya kiraki, ni na sa shi wllh" Aunty tace "Allah sarki Hajja, bari in je in dawo" Xata fita suka kusa cin karo da Umma, Aunty ta koma gefe, Umma ta shigo Aunty na wani murmushi tace "Ina yini Hajiya Ramlah" Umma bata tsaya ba tana tafiyarta tace "Lafiya lau" Kujera ta nema ta xauna, Aunty ta amsa gaisuwar Jiddah da wani irin fara'a tace "Sannunku da xuwa" Jiddah ta sunkuyar da kanta ta karasa parlon ta xauna saman carpet daga kusa da Hajja, Abuturrab sai kallonta yake babu ko kiftawa, Aunty dai ta fita parlon ta nufi bangaren Abba tana murmushi. Hajja ta yi wani murmushi tace "Shegiya matsiyaciya wai ni xata yi ma siyasa kamar warce bata yi xaman Masar ba, to xata ci kaza kazanta yau wllh" Tana fadin haka ta bude warmer din da Aunty ta ajiye taga farfesun kayan ciki sai turiri da xuba kamshi yake, Hajja ta kalli Jiddah da ta sa hijab har kasa tace "Maxa Dauki d'an iskan naman nan ki boye a hijabinki ki tafi can kwararo ki juye ki dauraye mata kulanta ki kawo, maxa maxa" Jiddah ta mike ta amshi warmer din ta nufi kofa a hankali Abuturrab ya bi ta da kallo, yana son tashi ya bi bayanta but he have to bring out abinda Aunty ta tura karkashin gado kuma yana son yin hakan ne ba tare da kowa ya lura ba, a hankali ya gaida Umma ta amsa tana danna wayarta, Hajja tace "Bari Jiddar ta dawo duk mu baxama parlon Usman" Umma dai bata ce komai ba, ba a wani dau lkci ba Jiddah ta shigo ta ajiye warmer din sannan ta xauna Hajja tace "Allah ya maki albarka, tashi parlon Usman xa mu tafi" mikewa Jiddah ta kara yi, Hajja ta mike Umma ma ta tashi suka nufi kofa gaba daya Abuturrab ya bi su da kallo, bayan fitansu ya tashi ya tafi karkashin gadon dai dai ta inda Aunty ta xauna ya tura hannunsa a hankali yana laluban kasan, bai ga komai ba alamar ta wuntsular da shi can ciki, hakan yasa shi dage katifar dakin, can ya hango wani katon abu kamar laya an garkame da wani irin kwado ya dinga kallon abun snn ya ciro handkerchief dinsa ya durkusa ya dauka yana kallo da wani irin mamaki, nannadesa yayi da handkerchief dinsa ya saka a aljihu snn ya mayar da gadon yanda yake ya fita dakin xuwa parlon Abbansa. Abba ne xaune parlon sai Aunty, Ummi da Aneesah dake xaune kasa daga gefen Ummi, Jiddah kuma ta xauna kasa kusa da Umma, Hajja ta shimfida darduma tayi xamanta a kai ta mimmike kafa tana kallon Aunty da Aneesah kasa kasa, xaunawa Abuturrab yayi shi ma a kasa, Abba ya bude taron da addu'a sannan yana kallon Hajja yace "Kin yi kirana kwanaki kadan da suka wuce ban samu tahowa ba sai yau, ina fatan lafiya Hajja" Hajja ta gyara xama tace "Toh ni dai kafin ince komai a nan so nake in ji ko kauron Mama nayi maka ya sa kaji gwara ka mayar she ni gantallaliya kawai Usman" Abba dai yayi shiru yana kallonta, Hajja ta kalli Aunty da kyau tace "Maimaita abubuwan da kika gaya min a parlon Aliyu ranan" Sosai gaban Aunty ya fadi ta dinga kallon Hajja. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppBayan few seconds Abba ya kalli Umma yace "Furnitures din na nawa aka siya mata?" Umma ta gyara xama tace "2.3m" Abba yace "Shkkn, xa a san yanda xa ayi, Allah ya rufa asiri" a takaice Umma tace "Ameen" kallon Jiddah tayi tace "Tashi ki dauko min jakata a parlon Ummi mu tafi, dare na yi Jiddah..." A hankali Jiddah ta mike ta nufi kofa Abuturrab ya bi ta da kallo, sai kuma ya kalli Umma, bayan fitar Jiddah da few seconds ya kalli Abba yayi kasa da murya a hankali yace "Allah ya kara girma Abba, mun gode" Abba yace "Ameen" mikewa yayi ya nufi kofa da sauri, Aneesah ta bi sa da ido har ya fita, sai kuma ta daga kai ta kalli Ummi cikin sanyin murya tace "Nagode Ummi, Allah ya kara girma" Ummi tayi murmushi tace "Ameen, sai ayi ta hakuri kuma" mikewa tayi ta fita parlon ita ma, Umma dai ta ta6e baki ta kalli Abba ta ga Ummi yake kallo.... Jiddah na shiga parlon Ummi ta dau jakar Umma da wayarta dake ajiye saman kujera xata fito aka bude kofar parlon, ta daga kai da sauri, suna hada ido ta sauke nata idon har ya iso inda take tsaye, ya jawota kusa da shi yyi wrapping hannunsa daya a bayanta ya dago kanta yana kallonta yayi kasa da murya yace "How are u feeling now?" Ta dauke kanta tace "Fine" Da damuwa yace "Are u sure? Me kika ci a gidan Umma daxu? Where u able to eat?" Tace "Na ci" yace "Kina kai mata jakar ki fito mu wuce gida yanxu" Ta xaro ido tana kallonsa, ya hade rai yace "To bin ta xa ki yi?" Kafin tace komai aka bude kofar parlon, da sauri ta turasa ta koma baya, Aneesah ta shigo parlon babu ko sallama, kallo daya tayi masu ta wuce dakin Ummi fuskarta a daure ta kulle kofar, Abuturrab ya bi ta da wani harara, Jiddah dai bata ko kalleta ba ta bi gefensa xata wuce ya rikota da damuwa yace "Are u serious bin ta xa ki yi Jiddah? Kin ga fa gobe xan koma aiki" Ta kallesa a hankali tace "Toh ni baxan iya ce mata a'a ba" amsar jakar da wayar yayi a hannunta yace "Ki tafi dakin Hajja ki jira ni" Bai jira me xata ce ba ya nufi kofa ta kasa cewa komai ta bi sa da kallo har ya fita, direct parlon Abba ya koma ya shiga da sallama bai bari sun hada ido da Umma ba ya ajiye mata jakarta da wayarta a gefe kansa a kasa yayi masu sae da safe, daga haka ya fita daga dakin, Ummi ta bi sa da kallo sae kuma ta mike ta bi bayansa, tana fitowa Main parlor tace "Aliyu" Abuturrab da har ya nufi dakin Hajja ya juyo yana kallonta sannan ya dawo, tace "Tafiya xa ku yi gidan naka yanxu?" Ya sunkuyar da kai yace "Eh Ummi" tace "You should be taking them both then" Ya daga kai ya kalli Ummi amma ya kasa ce mata komai, Ummi tace "Ka tsaya kallona ko da matsala ne?" a hankali ya girgixa mata kai, tace "Toh sae da safe, sae ayi ta hakuri kuma, Allah ya baku xaman lafiya" ko kadan ransa bai so haka ba, bai yi niyyar komawa da Aneesah gidansa yau ba, amma babu yanda ya iya, Ummi ta tafi bangarenta to meet Aneesah, shi kuma ya tafi dakin Hajja, Hajja na xaune tana matsar kwalla a hankali tana kallon Jiddah tace "Ke tunda aka haifeki kin ta6a gani ko jin haka? Me na mata da ta nemi garkame min bakin da Allah ya tsaga min? Yanxu ba don Aliyu ya gani ba shkkn tawa ta kare kenan a duniyar nan tunda an garkame baki? Bebiye fa xan koma" Jiddah dai sai kallonta take ta rasa ma me xata ce mata, Hajja ta kara rushewa da matsanancin kuka ta rike kai tace "Allah ya isa tsakanina da Hafsah, Allah ya isa wllh, Allah kadai yasan yanda xai yi da ita" bude kofar aka yi Abuturrab ya shigo, Hajja ta kuma sakar masa kuka tace "Toh wai garkame bakin na meye Hafsah tayi niyyar yi min Aliyu? Ina da wani mugun hali ne wanda ban sani bane ku ka ki fada min ku kuma, Wllh kwadon fa ya isa a garkame bakin mutane biyar da shi, amma wai ni kadae raina ta so garkame ma baki, wayyo duniya ina xa ki damuu...." Abuturrab yayi murmushi ya xauna yace "Toh ai babu xancen garkame baki yanxu tunda asiri ya tonu, kuma wa ya gaya maki bakinki xa a rufe, kika san ko soyayya tayi niyyar kullawa tsakaninku" Hajja tace "Huhuhu da uban wa xata yi soyayya? Sai dai tayi da uwarta dake kabari wllh" Abuturrab ya shafa kansa yace "Mu xa mu tafi sai da safe" Hajja ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh cikin kwalaben xata je ta kwana?" Yayi murmushi yace "Ga dai bangarena" Hajja tace "Shkkn ta tattara kayanta kawai ta mayar can, shi kuma Usman idan yan uwansa xai bi ya nemi taimako to duk ya bi, su hada masa taro da sisi don wllh shi xai siya mata wani kayan dakin ba wani ba, Maimoon tace min Miliyan biyar ne kayan dama" Abuturrab na kallon Jiddah yace "Mu tafi...." Jiddah ta kalli Hajja, Hajja tace "Tashi ki bi mijinki, amma anya Aliyu baxa a kira Hafsah aji dalilin garkame min baki da ta so yi ba kuwa, ko kuma in shirya gobe ka kai ni gun shegiyar yayarta kyauta dake can barnawa sai naji dalilin garkame min bakin da xa ayi" Shi dai Abuturrab bai tanka ta ba sai kallon Jiddah da taki tashi yake, ya karasa kusa da ita xai dago ta, xaro ido tayi ta mike da sauri, ya kama hannunta suka nufi kofa.... Xaune ya tadda Aneesah a main parlor da dogon Hijab dinta, tana ganinsu ta dauke kai, Jiddah ta xame hannunta daga rikon da yayi mata tana biye da shi a baya har suka fita parlon, mikewa Aneesah tayi ta bi bayansu kamar yanda Ummi ta umarceta, fuskar nan nata kamar bata ta6a dariya ba, suna fita kofar gida Abuturrab ya bude motarsa yana kallon Jiddah murya can kasa yace "Ki Shiga gaba" Ita dai bata ce komai ba ya xaga xai shiga driver seat, ta kai hannu xata bude gaban motar Aneesah ta rigata budewa ta shiga ta kulle fuskarta babu yabo babu fallasa, Abuturrab ya dinga kallonta, taki yarda ta kallesa, Jiddah dai ta koma baya ta bude motar a hankali ta shiga ta xauna, tada motar yayi suka bar layin, a wani eatry ya tsaya siya masu abinci, sannan suka wuce gida.... Abuturrab ya ajiye abincin hannunsa a parlor yana kallon Jiddah da ta nemi kujera ta xauna fuskarta babu walwala, tuni Aneesah ta haura upstairs, tayi tsaye a corridor ganin kofar dakinta a wangale, ta karasa da sauri tayi turus bakin kofa gabanta na faduwa ganin yanda dakinta ya dawo kaca kaca an tarwatse komai na ciki, bin dakin ta dinga yi da kallo ta kasa kwakkwaran motsi, can ta juya ta sauko downstairs bata ko kallesu ba, kamar xata tashi sama ta nufi waje, Abuturrab dake xaune kusa da Jiddah ya bi ta da kallo, takalminta ta dauko xata wuce sama yace "Idan kin gama abinda xa kiyi ki sakko, i have one or two things to say" Ta juya ta masa kallon gefen ido sannan tayi wucewarta sama, takalmin ta saka ta shiga cikin dakin tana takawa a hankali kar ta taka kwalba, ji tayi kamar ta rushe da kuka ganin yanda furnitures dinta suka koma, tayi saurin goge hawayen da ya kawo idonta ta dau wayarta ta fito daga dakin, ta dawo parlor ta nemi kujera ta xauna tana kallon hanyar dining, Abuturrab ya ta6e baki ya gyara xamansa yace "Dama ce maki xanyi you can use the visitor room upstairs har ayi clearing dakunan naku, Jiddah kuma xata tsaya bangarena till then...." Aneesah ta kallesa da sauri, calmly tace "A saboda me?" Yace "Saboda ita ce Uwar gida, kuma haka na shirya" Shiru Aneesah tayi ta kasa cewa komai, Sai kuma ta kallesa tace "She can use the room upstairs ni kuma xan tsaya a dakin dake nan kasa" Yace "Ohk then" Mikewa tayi ta bar masu parlon ta wuce sama. Duk wani abu da Abuturrab ya san Jiddah xata bukata ya shiga dakinta kamar dai yanda Aneesah tayi da takalmi, ya dauko mata sannan ya kai mata visitor room din, sannan ya sauko yana kallonta yace "Mu je ki ci abinci a sama" Tashi tayi ya dau ledan abincin ya bi bayanta, ta shiga dakin da ya nuna mata ta xauna gefen gadon dakin, ya ajiye mata leda daya na abincin sannan ya fita, yana jin Aneesah na ta share sharen kwalabe a dakinta yayi knocking tana bude kofar ya mika mata ledan hannunsa ba tare da ya kalleta ba, ta figi ledan sannan ta kulle dakinta, bangarensa ya tafi ya ajiye nasa abincin sannan ya koma dakin da Jiddah take, ruwan wanka ya hada mata a bathroom ya fito yana kallonta yace "Na sa maki ruwa kije kiyi wanka, or do u need any help" A takaice kamar jira take tace "No" ya rungume hannu yana kallonta, sai kuma yayi murmushi yace "Ko nayi wani laifi ne?" Karasawa yyi kusa da ita ya xauna gefenta ya jawota jikinsa a hankali yace "Tell me what happen wife, ko sbda ban bari kin bi Umma ba? To me xaki bi Umma kiyi bayan ga mijin ki?" Ya cire mata hijab din jikinta murya can kasa yace "Mu je to kiyi wanka" Da sauri tace "Xan iya da kai na" Yayi murmushi yayi kissing forehead dinta yace "Toh je kiyi..." Tashi tayi ta nufi bandaki ya bi ta da kallo har ta shiga ta kulle kofar sannan ya mike ya fita dakin, nasa bangaren ya koma... Sai wajen karfe sha daya saura Abuturrab ya fito daga bangaren nasa sanye da Pajamas dinsa, ga mamakinsa Aneesah na dakin nata har sannan ta ki sauka downstairs, ya kuma gane tana dakin nata ne ta dalilin waka da ta kunna, ya bude kofar dakin Jiddah ya ganta kwance gefen gado tana sanye da rigan baccinta dogo har kasa, ya kalli Abincin da ya ajiye mata tun daxu, da mamaki yace "Baki ci ba wife? Why? Ko baki son shinkafan ne? Tell me what u want to eat" Dagota yayi ya xauna kusa da ita yana kallonta da lumsassun idonsa, ya rungumeta a hankali yace "Jiddah" Tace "Uhm" yace "Ki sake jikinki da ni pls, ko da akwai wani abu dake xuciyarki game da ni ne har yanxu? Tell me plss" cikin sanyin murya tace "Ba komai" Yace "Har yanxu kina tuna da ko?" Ta lumshe idonta tace "Ehh" yace "Gaya min me kike tunawa..." A hankali tace "Ina tuna...." Sai kuma tayi shiru, ya kalleta, kin bude idonta tayi, underneath his breathe yace "Tell me plss" murmushi ya ga tayi sannan tace "Kawai na tuna lkcn da nace maka babu Awara" ya buda idonsa sosai yace "Really?" Tace "Uhm, da kuma lkcn da ka xo kace.... In yi hakuri" Murmushi kawai yake yana kallon kyakkyawan fuskarta, ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Ni kuma ina tuna lkcn da na dinga ganin ki a sararin samaniya a duk sanda nake piloting jirgi, duk na waiga a sky ke nake gani" ta bude ido a hankali tana kallonsa, Dagota yayi ya dau abincin nata da bata ci ba ya fita dakin da ita yana rike da hannunta suka tafi bangarensa, a nan parlonsa ya xaunar da ita ya bude abincin ya dau cokali ya deba ya kai bakinta, ta kai hannu xata amshi cokalin tace "Xan ci da kai na" Yace "Aa ni xan baki" babu yanda ta iya haka ya dinga 6ata abincin da kansa, sai dai bata ci da yawa ba, ya kyaleta ta tafi bathroom ta wanke bakinta, kafin ta fito har yaje dakinta ya dauko mata drugs dinta, ya bata ta sha sannan ta kwanta, ya gama abinda xai yi a laptop dinsa ya mike ya kulle kofar dakin ya dawo ya kwanta kusa da ita, ganin kamar tayi bacci don idonta a lumshe suke ya kwanta side dinta not wanting to disturb her yana shakan kamshinta me dadi da saka nutsuwa, Lumshe ido yayi shi ma, yana tunanin da ya tafka asara babba in har ya rasa Jiddah, kasa daurewa yayi, yayi wrapping dinta jikinsa, lkci daya ya ga ta juyo ta rufe fuskarta a kirjinsa a hankali tace "I really appreciate the car, Allah ya kara budi da daukaka, Allah ya kare ka ya tsare ka duk inda xaka shiga, Allah ya bani ikon kyautata maka kamar yanda ka yi min tun daga watanni sha daya da suka wuce har xuwa yanxu, i know I can't pay u, i.... " Kasa ci gaba tayi Hawaye na sauka idonta, cikin rawan murya tace "U stoop too low for my sake, duk da bambanci me taxara dake tsakaninmu a komai na rayuwa, u neva left me, u were der throughout... Ur sacrifice will for ever remain in my memory, how can i ever pay for this?" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you It’s S.SQAURE COLLECTION ANNIVERSARY YAYY🎊🎉 Jama’a gawata gagarumar sanarwa ku gyara zama kuji. S.SQUARE COLLECTION na celebrating 9years anniversary dinsu na fara business, hakan yasa suke bada wata gagaruman discount akan all abubuwan dasuke saidawa, bafa shikenan ba ku gyara zama kuji. A shagon S.SQAURE COLLECTION zaki samu abubuwa da dama kaman haka; Hadaddun dinkakkun Gowns wato dogayen riguna. Lafiyayen Hijab na Eyptia ne, Sudanese ne, Naijeriya ne dasauran su duk sunada shi. To ina masu baki achan achan irin mu gafa namu nan. S.SQAURE COLLECTION na saida su Iloka, Gullisuwa, Tsamigaye, Aya, Tuwon madara Dasauran kayan kwalama masu dadi dandano da sanya mutum mantawa da duk wata damuwa tasa! Hehehe badai kun fara gajiya ba danfa ba anan kadai S.SQUARE COLLECTION suka tsaya ba. Ina matan kamshi dasu Anty turare S.SQAURE COLLECTION also dey for una ooo suna saida Turarukan wuta, Humra, Kulaccam, Turaren tsuguno da Turaren Kaya Kayan mata kayan saka zakin wajen suma akwaishi Tsumi, Daka, Gumba,Dasauran maganin mata. All this abubuwa tanada shi ku garzaya kuci wanan garabasar tasu ta anniversary ta hanyar danna wanan link din dan musu magana direct. wa.me/+2347030037697 Abuturrab was Speechless.... ya rungumeta sosai, wani sabon sonta na fixgarsa ya rufe ido cikin sanyayyan muryarsa yace "I have a lot to say to you but not today, i will reserve it for another sweet night, they are so many lovely night to come...." Ita dai bata bude idonta ba tana sauke numfashi a hankali. Washegari da asuba Abuturrab na dawowa masallaci har ya nufi bangarensa sae kuma ya dawo yana kallon kofar dakin Aneesah ya karasa ya bude kofar dakin yana kallon ciki, kwance ya ganta kan manyan duvets dinta guda biyu da ta shimfida a kasan tiles daga gefen gadonta, ya karasa cikin dakin ya kai hannu ya buga duvet din, ta bude ido yace "Sallah" Daga haka ya mike ya fita dakin ya koma bangarensa, xaune ya tadda Jiddah kan darduma tana azkar dinta a xuciya, ya xauna gefen gado ta daga kai a hankali ta kallesa, bayan wani lkci tace "Ina kwana" kallonta kawai yake, ta mike ta dauke darduman da tayi sallah ya tashi shi ma ya nufeta ya jawota jikinsa yace "Good morning Jiddatul Khair" daga kai tayi ta kallesa ya sakar mata murmushi yace "How was ur night?" A hankali tace "Alhmdlh" yace "Let sleep a little more" Kafin ta ce komai ya ja ta saman gadon suka kwanta, sae da yayi cuddling dinta iya son ransa sannan ya kyaleta, har bacci ya fara daukarta ta bude ido da sauri tana kallonsa taga ya koma baccin, kallon dogon hancinsa ta dinga yi da eyebrows dinsa, ta sauke idonta a hankali ta xame jikinta daga nasa ta sauka daga saman gadon ta fita parlonsa agogo ta kalla taga bakwai saura na safe, ta daure gashinta da yayi scatter waje daya sannan ta fita parlon ta sauka downstairs, sae da ta fara share ko ina a parlon tayi mopping, kayan kallon ma duk ta gogesu, parlon ya dawo wani fess da shi, da alamar an dade bai samu irin wannan gyaran ba, ta haura sama ta bude kofar dakinta a hankali tana kallon ciki, takalminta ta tafi ta dauko a downstairs sannan ta dawo dakin ta saka takalmin ta shiga cikin dakin da shi, burner dinta dake ajiye gefen madubi ta dauka sannan ta samu ta harhada turarrukan wuta a wani kwalba da bai karasa fashewa ba ta sauko downstairs ta jona burner din a socket, ta debi turaren ta xuba a ciki ta mike, kitchen ta wuce, sae da tayi minti daya tsaye tana kare ma kitchen din kallo snn ta girgixa kai, ta fara tidying din ko ina har cikin store ta fitar da duk kwalayen da babu komai ciki ta kofar backyard, bayan kitchen din ya dawo a bit tidy ta fara wanke wanken duk plates da cups, sai kusan karfe takwas da rabi ta gama da kitchen din, ta goge ko ina ta wanke abinda xata iya wankewa a jikin gas ta goge na gogewa, tayi dusting ko ina, kan kace me kitchen din ya dawo so sparkling kamar ba shi ba... gas ta kunna ta daura ruwan Lipton, ta duba taga babu kayan kamshi, kawai ta debi irish ta fara ferewa, dicing it almost equally, tana son making Crispy french fries na dankalin ne ba irin wanda aka saba soyawa ba, bayan ta wanke dankalin da ta yayyanka ta bar sa cikin ruwa ya d'an jiku na wasu mintuna sannan ta wuce sama, corridor din rooms da bata share ba ta share tayi mopping, sai kuma ta shiga part din Abuturrab, parlon kadai ta gyara tsaf nan ma ta goge da kayan kallon, ta koma downstairs ta dauko burnern turaren wuta ta jona a parlon nasa sannan ta sauka ta koma kitchen, paper towel ta shimfida saman tray, ta xuba dankalin da ta tsane daga ruwa ta dau wani paper towel din, patting the potatoes very dry, bayan nan ta daura veg oil a saman gas heating it for about just 300° Fahrenheit, wato man bai yi wani xafi ba, bayan nan ta xuba wasu quantity na dice Irish din a cikin man gyadan, ta soya dankalin for just 3mins sannan ta kwashe ta xuba su a kan wani paper towel din, mutum na iya ajiyesa a freezer a hakan har xuwa sanda xai yi amfani da shi even if not that day, amma tunda ita a lkcn xa a ci, barinsa kawai tayi ya huce, ta tafi tana yanke yanken abinda xata soya kwai da shi, bayan ta gama ta juye ruwan Lipton dake tafasa cikin flask, ta duba dankalin da ya d'an huce ta barbada masa a little quantity of salt sannan ta sake daura man gyadan a wuta ta bar shi yayi xafin 400° Fahrenheit sannan ta xuba irish din, ta soya shi dai dai yanda take so, cikin minti sha biyar ta gama soya har da eggs din sannan ta fita da warmer din dankali da kwan ta kai saman dining, ta dawo ta kara gyara kitchen din kamar bata yi girki a ciki ba ta koma sama, dakinta ta shiga da takalmi a kafarta ta tafi bandaki tayi wanka ta fito, bayan ta dau abubuwan da xata dauka ta koma can dakin baki ta shirya, bayan ta gama shafe shafenta ta dau doguwar riga na atamfa ta saka ta daura dankwali, sosai kayan yayi mata kyau ta dawo sak amaryarta, lallen da ya haska hannunta sai sheki yake gwanin sha'awa, babu abinda ta shafa a fuskarta banda kwalli sai man lebbe, amma kyan da tayi ba a cewa komai, ta kalli agogo dake nuna goma da minti biyar ta mike ta fita dakin, dae dae nan Aneesah ta fito daga nata dakin sanye da kayan bacci, Suna hada ido Jiddah ta dauke kanta kamar yanda Aneesan ma tayi da sauri, ko tsayawa bata yi ba ta sauka downstairs abun ta, kamar ance Jiddah ta juya taga Abuturrab shi ma ya shirya cikin kananun kaya lkci daya kamshin turarensa ya xagaye corridor din, ya d'an kalli Aneesah da har ta kai downstairs don bata gansa ba ma, ya karasa gun Jiddah ya rungumota jikinsa yayi mata light french kiss, underneath his breathe yace "U look beautiful" A hankali tace "Thank you" ya xame dankwalinta yayi kissing bak'in gashinta me tsantsi sai kuma ya sauke lips dinsa xuwa wuyanta, jin taku a stairs ya saketa da sauri ya koma baya, Aneesah ta hauro saman tayi masu kallo daya ta yi hanyar dakinta, ya bi ta da kallon gefen ido, kafin ta shiga dakin yace "Good morning" Ta watsa masa wani kallo tace "Same" Daga haka ta shige dakinta, tuni Jiddah ta sauka downstairs, murmushi yayi ya shafa kansa sannan shi ma ya sauka. Ko kadan Abuturrab bai yi mamakin abubuwan da Jiddah tayi ba, da yanda tayi transforming kitchen da parlon gida, he was so happy ya xauna gefenta yace "Allah ya maki albarka Wife, a haka gidan nan yake a ko da yaushe kafin ki bar sa" Ita dai ko kallonsa bata yi ba, ya bude warmer din ya dau irish daya ya kai baki, ya juya ido bayan few seconds yace "U made this or u bought it??" Still ta ki cewa komai, sauka kasa yayi ya xauna saman carpet ya tankwash kafa ya bude kwan ya dau spoon ya deba ya kai baki, lumshe ido yayi yace "umm.... So Yummy" mikewa tayi ta durkusa kusa da abincin ta dau plate ta dibar masa, sannan ta fara hada masa shayi, shi dai kallonta kawai yake babu ko kiftawa, komai tayi burgesa yake, ba kuma yau ya fara jin hakan ba, for long ya ke ji hakan... bayan ta hada shayin ta dauka ta ajiye masa a gabansa a hankali tana kallonsa, kissing lips dinta yayi ya lumshe ido yace "Thank you MPG💖" ita dai kallonsa kawai take da manyan idanuwanta, under neath his breathe yace "My Precious Gift 💖" Ta sauke idonta amma har ranta taji dadin words din nasa, yace "kiyi serving kanki sannan ki dibar ma Aneesah ma, i will be back soon" Daga haka ya mike ya wuce sama, ta bi sa da kallo. Yana shiga dakin Aneesah ya tar da ita xaune can karshen dakin ko tunanin me take oho, ta d'an kallesa yace "Taso mu yi breakfast" Shiru tayi yace "I am talking to you" a takaice tace "Aa ku dai ku ci, ai kune masu gidan yanxu" Ya karaso cikin dakin yace "U admitted kina son xama da ni as ur husband Aneesah, and for peace to continue reigning in our midst duk abinda na fada just adhere and obey that's all, nace ki taso mu yi breakfast, i wasn't expecting you to decline that" Bayan few seconds ta mike ta dau mayafinta ta yafa sannan ta nufosa ya bi ta da kallo har ta fita, fitowa yayi ya kulle kofar dakin sannan ya bi bayanta downstairs din, Can gefe jikin kujera ta samu ta xauna, ya dau dankali da kwan da Jiddah ta debar mata ya ajiye gabanta, sannan ya hada mata shayi ya ajiye mata, Jiddah dai ko kallonsu bata yi ba, a hankali take shan shayin hannunta, Ya dau fork din dake plate din potatoes da Jiddah ta debar masa yana kallonsu both yace "Kun gaisa yau?" Babu wanda yace komai cikinsu, ya kalli Jiddah sannan ya kalli Aneesar duk babu wanda ya kallesa, yace "I am talking" Jiddah ta ajiye shayin hannunta ta mike, ya daga kai ya kalleta yace "Ina xa ki?" Without looking at him tace "I want to ease ny self" daga haka tayi wucewarta sama, Aneesah ta dau fork ta fara cin abincin gabanta, shi dai Abuturrab bai ce komai ba, bayan mintuna kadan ya kalli Aneesah yace "You met her downstairs, sannan she made this meal and tidied the whole house, why not even tell her weldone" Aneesah ta kallesa tace "Ni ban taso a gidanmu naga Babba na gaida yaro ba, ai darajar girmanta da nayi ya ci ace ta gaisheni kafin ni kuma in ce mata sannu da aiki, but tana jira ni in gaisheta, na san kuma na bata at least 7 good years, autarmu ma ta girmeta" Abuturrab yace "Amma sai ki yi mata sannu da aiki ki ga ko xata gaisheki ko baxata gaisheki ba, balle u met her ba ita ta xo ta sameki ba" Aneesah tayi wani murmushi tace "I am not surprise u are always supporting her, to ta dawo ta xauna sai in gaisheta i know i won't loose" Abuturrab bai ce mata komai ba, bayan some minutes yace "U asked for something few weeks ago, do u still need it?" Ta ajiye fork din hannunta tace "Bana bukatarsa, kawai yanxu cikon kudi xaka bani a kawo min wasu furnitures din, kudin da xa a turo min baxa su isa ba...." Ya girgixa kai yace "Bani da kudin furnitures because i didn't budget for it this month... anjima xan saka maki abinda kika tambaya 2 weeks ago" Bata dai ce masa komai ba, yace "And ki shirya before 12 xa mu shiga gidan neighbors dinmu a gaisa, so we can know each other more" Tace "Aa ni baxan je ba, ku je dai da matarka..." Calmly yace "Ni kuma nace ki shirya mu je" Bata ce masa komai ba, hakan ya sa ya mike ya koma saman kujera ya dau wayarsa dake vibrate, kallonsa take har ya gama wayar sannan ta sunkuyar da kanta tace "Captain i think i have to go to do hospital don jikina baya min dadi, ina yawan jin jiri da kasala sannan i don't have appetite na cin abinci...." yace "Ohk, Allah ya sauwake" tace "Ameen, i need to see a doctor" kwashe duk kwanukan tayi da plate ta wuce kitchen da su ya bi ta da kallo. Mikewa yayi ya wuce sama, bangarensa ya tafi hoping to see Jiddah there, ganin bata nan ya dawo dakin baki, kwance ya ganta saman gado idonta rufe, ya xauna gefenta yayi kasa da murya yace "Jiddah" Kin bude idon tayi ya dagota ta 6ata fuska tace "Ni bacci nake ji" Yace "Me yasa kika ki cin abincin?" Ta bude ido tace "Saboda na koshi" Yace "Amma baki ci komai ba" shiru tayi masa, yace "Or are u angry at anything?" Tace "Not at all" Ya kamo hannunta yayi lowering voice dinsa yace "U know what?" A hankali ta daga ido ta kallesa, yace "For the sake of ta girmeki ku dinga gaisawa da safe pls idan kin ganta..." Ta xame hannunta daga nasa tace "It's not necessary" da mamaki yake kallonta, can dai yace "Why?" Tace "That's just my stand on it" yayi kasa da murya yace "No Jiddah ina son ku xauna lafiya kamar yaya da kanwa pls, nasan in sha Allah Aneesah ta canxa halinta xa ku xauna lafiya without any problem" Murmushi kawai Jiddah tayi tace "Ae da kai ya kamata ta xauna lafiya ba ni ba, ni ina ruwana da ita tunda ba xamana take ba" Mamakin furucin dake fitowa bakinta upon her age ya dinga yi, and he saw nothing other than sheer jealousy a idanuwanta, ta mike tayi shigewarta bandaki ta bar sa a xaune, shafa kansa yayi thinking of where to start from, can ya mike ya sauka downstairs yana ta xaune parlon har kusan 12 jin footstep a sama ya daga kai, Aneesah ce ta sauko cikin English dressing da veil dinta ta karaso parlon ta xauna ba tare da ta kallesa ba tace "Na shirya" kallon agogo yayi sai kuma yace "Ohkk" ya mike ya tafi sama, dakin Jiddah ya shiga, ya sameta xaune da wani littafi a hannunta, yace "Xa mu shiga gidan neighbors dinmu mu gaisa yanxu, are u ready?" Taki cewa komai, ya karasa ya xauna gefenta ya amshi takardan yayi kasa da murya yace "Shkkn babu wanda xai gaida wani cikinku tunda baki so, i am sorry plss ban san ranki xai baci ba" Rungumeta yayi jikinsa yace "I am so sorry for making u sad wife" Kuka ta sakar masa, lkci daya ya rikice mata yace "Na fa ce kiyi hakuri ni ban san ranki xai baci ba wllh, don Allah kiyi hakuri" Cikin rawan murya tace "Bayan ita ce ta sauko ta gan ni ko sannu da aiki bata ce min ba tun asuba na tashi nake gyara gidan da bata gyarawa, sannan...." Bai bari ta ci gaba ba ya fara kissing dinta. Har aka kira azahar Aneesah na xaune parlon bata ga saukowarsu ba, tana ta xura idon ta ga ya fito xai je masallaci nan ma har aka idar da sallah bai fito ba, ganin karfe daya da minti arba'in ta mike ta wuce sama ta shiga dakinta. Karfe biyu da minti biyar Abuturrab ya fito daga dakin Jiddah sai a sannan ya tuna Aneesah da ya bari a parlor, ya d'an buda ido ya sauka kasa da sauri bai ganta ba, dawowa yayi ya bude dakinta ya ganta kwance tana danna wayarta, ya kasa hada ido da ita, ya dai shiga dakin, kallo daya tayi masa taga wani kayan ya canxa ta dai ci gaba da danna wayarta, still not wanting to look at her yace "Sorry i kept u waiting, i was busy with my laptop, taso mu je" Bai jira me xata ce ba ya fita daga dakin, Jiddah ta fito daga dakinta ta ki yarda ta kallesa kana ganinta kasan ta sha kuka, ta nufi stairs tana sauka a hankali, shi dai da ido ya bi ta, sai ga Aneesah ma ta fito daga dakinta ya sauka downstairs tare da ita, Kallo daya Aneesah tayi ma Jiddah dake xaune kan kujera a parlor ta dauke idonta, abaya ne jikinta da veil dinsa, Abuturrab ya kalli Jiddah yace "Ta so mu je" Daga haka ya nufi kofa, Jiddah ta mike ta bi bayansu. Abuturrab ya xauna a wajen shan isa bayan sun shiga compound din gidan, Aneesah ta danna bell din parlon aka bude kofar wata warce da alamar mai aikin gidan ce ta gaishesu, Jiddah dai ko kusa da kofar bata je ba sbda Aneesah dake tsaye, mai aikin tayi masu Bismillah, Aneesah ta fara shiga parlon sannan Jiddah ta shiga, wata matashiya da baxata wuce shekara talatin da biyar ba dake xaune parlon ta shiga welcoming dinsu tana kallon Jiddah, mai aikin gidan ta tafi ta kawo masu ruwa da lemo, Matashiyar matar dai tana jiran su fadi daga inda suke, Aneesah na wasa da xobunan hannunta tace "Nan makota ne, gidan da yake kusa da naku" Matar tace "Ayya sannunku da xuwa, ai kam ba a ta6a gaisawa ba, bari in kira Hajiyar tana sama" Wata yarinya ce da baxata wuce 19 ba ta fito daga kitchen, Matar tace "Yauwa Khaleesat ce ma Mama tayi baki" Khaleesat tace "Toh" Sai da ta fara gaida su sannan ta wuce sama, Jiddah ta bi yarinyar da kallo, haka ma Aneesah... Matar na kallonsu tace "Yaya da kanwa ce amma" Aneesah ta kirkiri murmushi, Ita dai Jiddah ta sunkuyar da kanta, Aneesah tace "Haka ne" Khaleesat ta sauko mahaifiyarsu na biye da ita a baya, da fara'a ta shiga welcoming dinsu, duk suka gaisheta ta amsa tace "Maa sha Allah naji dadin shigowarku wllh, ina me gidan naku?" Aneesah tace "Yana waje" Tace "Au haba, ce masa ya shigo mana" Aneesah ta mike ta nufi kofa ta fita... Hajiya Fatima tace "Khaleesat xo ga me shige da ke" Matar dake xaune parlon tace "Auu, ashe kema kin lura Mama, wllh tun daxu nake ta kallonta dubi har dimple din" Khaleesat tayi dariya tana kallon Jiddah tace "Ya sunanki?" Jiddah tayi murmushi a hankali tace "Jiddah" Hajiya Fatima tace "Maa sha Allah, amma in ji dai babu wata matsala yanxu jiddah?" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Hajiya fatima tace "Duk sanda kika samu lkci ki shigo xan yi magana da ke kin ji?" A hankali Jiddah tace "Toh" Matar dake xaune warce ita ce first daughter din Hajiya Fatima tace "Ashe kin sansu Mama, ni ban ma ta6a lura da su a anguwar ba" Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "Nima shekaranjiya na shiga gidansu, warce ta fita yanxu ai kishiyarta ce" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp[8/4, 7:02 PM] Ummuanwar🥰: Duk wannan xancen da Hajiya Fatima da er ta suke, Jiddah dai kanta na kasa sai dai tayi murmushi, Hajiya fatima na kallonta tace "Ko dai baki da lafiya ne Jiddah?" Jiddah ta daga kai da sauri ta girgixa mata kai tace "Lafiyana kalau" Hajiya fatima tace "A nan garin iyayenki suke?" Jiddah ta gyada mata kai tace "Ehh" Hajiya Fatima tace "Allah sarki, yaushe mijin naki ke komawa aiki, naji kakarsa tace pilot ne shi ko?" Jiddah ta sunkuyar da kanta tace "Wani lkcn yana komawa ranan litinin da safe, ko kuma yau da yamma" Hajiya Fatima tace "To idan ya koma sai ki tambayesa ki kara leko mana kin ji" a hankali Jiddah tace "Toh" haka kawai Hajiya Fatima taji Jiddah ta kwanta mata, gashi kana ganin alamarta kasan bata da hayaniya da ma yanda take magana cikin sanyi, a ranta kuwa ta riga ta saka cewar uwargidan ce mai matsalar don a tunaninta Jiddah ce amarya, ita kanta daughter din Hajiya Fatima kallon Jiddah kawai take, Jiddah kuwa ta kagu su koma gida ta kwanta don ta ji bata jin dadin jikinta, taji kamar gabobinta ciwo xa su mata, Hajiya Fatima tace "A kawo maki abinci Jiddah?" Jiddah ta girgixa kai da sauri tace "Aa mama na ci abinci" Aneesah ce ta shigo parlon Abuturrab na biye da ita a baya, Hajiya Fatima ta dinga kallonta sai ta ga ita din ma ba mummuna bace, kawai dai kana gani kasan ta girmi Jiddah sosai, kuma da gani kasan wayewarsu da Jiddah ba daya ba, Abuturrab ya xauna saman kujera ya gaida Hajiya Fatima da first daughter dinta Rahmah, Hajiya Fatima na murmushi tace "Ya gidan fatan komai lafiya" Yace "Alhmdlh" Tace "Toh maa sha Allah, sai ayi ta hakuri Ali, Allah ya ba ku xaman lafiya, ya kauda fitina" Yace "Ameen" Tace "Takwaran naka baya nan yana wajen aiki..." Abuturrab ya kalleta yace "Ohk toh, ina gaishesa idan ya dawo" Tace "Xa a gaya masa in sha Allah" Mikewa yayi yace "Mun gode Mama, just to say hi ne dama" Tace "Haba dai har xa ku tafi, ko ruwa baku sha ba fa" Ya d'an yi murmushi yace "Alhmdlh...." tace "Toh xauna ban gama magana ba" komawa yayi ya xauna, Nasihan few minutes Hajiya Fatima tayi ma Aneesah da Jiddah, sai dai kuma ta fi stressing nasihar tata a kan Aneesah, Aneesah dai ba ma direction dinta take kallo ba amma tana sauraron duk abinda take cewa, daga karshe Hajiya Fatima ta kalli Abuturrab tace "Kai kuma reminder daya xan maka Ali... kayi kokarin xamo me adalci tsakanin matanka in har kana son wanyewa da duniya lafiya" Abuturrab ya sunkuyar da kansa yace "In sha Allah" Tace "That's all i have to say, Allah ya hade kanku, ya kauda duk wata fitina a tsakaninku, idan ma kaga da wata matsalar i am always around kafin dae ayi involving close ones" Da haka suka yi sallama da Hajiya fatima yana kara yi mata godiya, Aneesah ta mike ta bi bayan Abuturrab, sannan Jiddah ma ta tashi tayi masu sai anjima ta nufi kofa, Hajiya Fatima ta bi ta da kallo... Abuturrab na tsaye compound Aneesah ta fito, ya dauke idonsa daga kanta ya mayar kan kofar yana jiran fitowar Jiddah sae ga ta ta fito, kallonta ya dinga yi ganin kamar she is finding it a bit difficult to walk, Aneesah dai ta nufi gate abunta ta fita, yayi lowering voice dinsa bayan Jiddah ta iso inda yake yace "Are you okay?" Bata ce masa komai ba, ya kama hannunta suka fita daga gidan. Jiddah ta xame hannunta daga nasa bayan sun shiga parlon su ganin Aneesah a xaune, ta wuce sama tana tafiya a hankali, Aneesah ta bi ta da kallon gefen ido, kwanciya Jiddah tayi ta rufa da bargo jin kamar xata yi xaxxabi, Abuturrab ya dau makullin motarsa dake parlon yana kallon Aneesah da ta kunna tv yace "Xan fita siyo abinci yanxu, hospital da kika ce kuma I think it will be better a bar shi anjima da daddare tunda gobe xan koma aiki" Ta kallesa tace "Baxan iya jira har dare ba saboda ni kadai nasan me nake ji a jikina" Ya dinga kallonta yana juya key din hannunsa, sai kuma yace "Nan da awa nawa ne daren xai yi idan Allah ya yarda?" Tace "Kaga Captain.... ni bance lallai sai ka kai ni asibiti ba, idan ka dawo daga siyo abincinku ka bani makullin mota kawai in kai kaina asibiti ba wani big deal bane, ko kaji na tilasta maka ka kai ni hospital?" ya mata wani kallo ya juya ya fice daga parlon, ta hararesa sannan ta ci gaba da kallonta, tana ji motarsa ya fita gidan, ta kalli hanyar stairs, ta fi minti biyu tana kallon saman deep in thought taji an kara bude gate din gidan, ta juya da sauri sai kuma ta mike ta isa window tana leka waje, kallon babbab motar da ya shigo na sababbin furnitures ta dinga yi babu ko kiftawa, ta koma da sauri ta xauna a parlor, knocking aka yi bakin kofa ta ki tashi balle ta bude, sun kusa minti biyar a tsaye suna kwankwasa kofar, ita dai ko motsawa bata yi ba daga inda take, ta kalli wayarta dake ringing bayan wani minti biyar din, ganin me kiranta tayi silencing wayar ta ajiye a gefe, ya sake kira ta ki dagawa daga karshe ta mike ta haura sama, kallon kofar dakin da Jiddah take tayi kafin ta shige nata dakin ta kulle, har sai da Abuturrab ya dawo daga wajen da yaje siyan abinci sannan ya bude ma masu kawo furnitures din gidan suka shiga, yana xaune parlor suka dinga fitar da fasassun kayan dakin Jiddah suna sakawa a motar bayan sun sauke sababbin, ya mike jin mota ta shigo compound din ya fita waje, motar Ahmad ya gani, and he couldn't help it but smile, yana tsaye har Ahmad ya sauko, Ramlah ma ta fito daga cikin motar, Ahmad yayi er dariya bayan sun hada ido ya nufosa yace "This is serious.... kaga wani fresh da kayi kuwa Captain?? Meye haka Jiddah ke baka?" Abuturrab ya shafa beard dinsa a hankali yace "Abinda ya kamata ta bani" Dariya kawai Ahmad yayi, giving him a hug yace "I guess yanxu kasan kayi aure right?" Abuturrab ya dage girarsa murya kasa kasa yace "I am telling u" dariya kawai Ahmad yake yana gathering tsokanar da xai yi ma Abuturrab a xuciyarsa amma ba yanxu ba, Ramlah ta karaso wajen ta gaishe da yayan nata da ladabi ya amsa mata, ta shiga parlon, Ahmad yace "Ina matan naka?" Murmushi Abuturrab yayi ya juya ya shiga ciki Ahmad na biye da shi, stairs Abuturrab ya haura ya fara bude dakin Jiddah ya ganta kwance tana bacci, ya karasa ya duka kusa da ita yana shafa hancinta ta bude ido a hankali, turo baki tayi ganinsa xata juya masa baya ya dagota yace "Baccin ya isa haka, yamma yayi..." Kamar xata masa kuka tace "My legs are aching" ya cire duvet din yana massaging kafar ta hade rai ta rike hannunsa gabanta na faduwa tace "Bana so" ya kalleta da lumsassun idonsa yayi kasa da murya yace "Baki son me?" Bata san lkcn da ta fashe da kuka ba cause it started just exactly like this daxu, ya saketa da sauri, a rikice yace "Toh yi hakuri plss..." Ta hade kanta da gwiwa tana shessheka, bai ta6a ta ba ya marairaice yace "Na fa ce kiyi hakuri wife, don Allah kiyi hakuri" ta dago kanta taba goge idonta a hankali, ya langwabar da kai yace "To taso ki gaisa da su Ahmad, they are around" ta bude ido sosai tace "Da gaske?" a hankali yace "Yea wife..." Mikewa yayi ya dagota tsaye, kamar xata sakar masa kuka tace "Ni wllh bana jin dadi" Ya xaunar da ita gefen gado da damuwa yace "Toh ko mu tafi asibiti yanxu?" Ita dai tayi shiru ya rungumeta tayi lamo jikinsa yana patting bayanta, ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Toh baxan kuma ba, till u are healed...." Ta lumshe idonta tana jin yanda xuciyarsa ke bugawa a kirjinta, murya can kasa yace "I love u with every breath of mine Wife" Ta kara shigewa jikinsa amma taki cewa komai kuma bata bude idonta ba, shi haka kadai ma ya ishesa ko bata mayar masa i love u din ba, narkar masa da xuciya da tunani gaba daya Jiddah take, she is the best thing that have ever happened to him, he felt complete with her, kamar me rada yace "Mu tafi asibitin a dubaki?" Ta make masa kafada, yace "Toh kin ce baxa ki iya tashi ba, ko in kira Ramlan ta shigo ku gaisa a nan kawai su tafi?" Da sauri ta bude ido tace "Aa xan je" Ya dago kanta ya shiga yi mata single lip kiss... Vibration din wayarsa ne ya dawo da shi ya mike xaune da sauri sannan ya dau wayar ya duba yaga Ahmad ne, buda ido yayi sosai sai kuma ya kalleta ganin yanda ta kulle idonta ya ja hancinta ya mike ya fita daga dakin, Yana sauka downstairs Ahmad yace "Captain da sai kace mana mu tafi kawai da dai shanya mu da kayi a parlor haka" Abuturrab ya kasa kallonsu yana shafa kansa yace "Ohk... I was suppose, ohhh sorry..." Sai kuma ya juya da sauri ya koma sama, dakin Aneesah ya shiga yana kallonta yace "Ki sauko ku gaisa da su Ramlah" ya juya ya fita ya koma downstairs yana kallonsu yace "Jiddah bacci take, she is having headache since morning, so Aneesah will be coming down now" Yana fadin haka ya nemi waje ya xauna, Ahmad dae kallonsa kawai yake yana murmushi ganin duk a birkice yake, masu gyara sababbin kayan dakin Jiddah dai na ta faman gyara a sama, Aneesah taji wani abu ya tokareta a makogwaro bayan ta fito, kallo daya tayi ma dakin Jiddah ta sauka kasa da sauri, babu yabo babu fallasa ta gaida Ahmad sannan ta amsa gaisuwan da Ramlah tayi mata, Shi dai Abuturrab fa gaba daya hankalinsa yayi sama, soul dinsa kawai ne a parlon amma spirit dinsa na can sama, can dai ya kalli Aneesah yace "Baki basu ko ruwa ba" ya mike ya dau abincin da ya siyo ya ajiye masu ya dau daya xai kai ma Jiddah sama, A stairs ya ganta tana saukowa a hankali, hakan ya sa ya ajiye ledan, har ta shigo parlon taki yarda ta hada ido da su Ahmad ta xauna kan kujera ta gaishesu cikin sanyin muryarta tana murmushi, Ahmad dake kallonta yace "Duk kewan Umma ne yasa kika rame haka Jiddoh" Ita dai murmushi kawai take ta d'an kalli Ramlah tace "Yaushe ku ka xo?" Ramlah dake ta kallonta ganin yanda ta kara haske tayi kyau amma kuma ta rame kamar yanda Ahmad ya fada, ta sakar mata murmushi tace "Yau da safe muka xo Aunty Jiddah, ya gida?" A hankali Jiddah tace "Alhmdlh, ya jiki?" Ramlah tace "Mun gode Allah" Tun da Aneesah ta shiga kitchen kmr xata dauko ruwa ta ki fitowa, Ahmad ya lura how uncomfortable Jiddah is a parlon kamar dai bata jin dadi, shi kuma ogan da ya xo wajensa sai kallonta yake kamar xae cinyeta, it's just as if he is obsessed with her... Ahmad yayi wani murmushi yana mamaki iri iri, sai kuma yace "Dama nace bari mu xo mu duba amarya Jiddah, yanxu kuma xa mu je can gida wajen Ummi, sae kuma wani lkcn in sha Allah" Abuturrab ya kallesa da sauri yace "So early, naga baku ci abincin ba fa...." Ahmad yace "Aa sae yanxu nayi reason, ba a wannan lkcn ya kamata mu kawo ziyara ba, in sha Allah xa mu dawo lkcn da ya kamata, but before then yaushe xaka barta ta koma makaranta Captain? cause satinsu biyu kenan da resumption" Abuturrab ya shafa kansa yace "Makaranta kuma?? Wani makaranta?" Ba Ahmad ba har Jiddah kallonsa take da mamaki, Ahmad yace "Ohh baka san ma wani makaranta ba ko, to Umma xata maka bayani da kyau" daga haka ya mike yace "Mu xa mu koma" Abuturrab yace "Shkkn sai mun yi waya" tare suka nufi kofa suka fita yana son gaya ma Ahmad abubuwa da yawa, bayan sun fita Ahmad bai basa daman magana ba yayi patting shoulder dinsa yace "Kar dai kayi ma er mutane ciki da wuri, kaga she is still very young...." Abuturrab ya d'an 6ata fuska yace "Ciki kuma? Aneesah bata dau ciki ba sai ita?" Dariya Ahmad yayi sosai ya ma kasa ce masa komai, wato Aneesah da suke yi for long bata dau ciki ba sai wata Jiddah tunda an gaya masa it's by that, kwafa Ahmad yayi yace "Xaka sha mamaki ka ci gaba da relying a kan haka... Sae kaga cikawar aikin ka" Jiddah na kallon Ramlah da ta mike da kyar, cike da damuwa tace "Baki ci komai ba kuma xa ki tafi, ko in kawo lemo sai ki tafi da shi?" Ramlah tace "Wllh mun ci abinci gidan Umma kar ki damu, Maimoon tace yaya ya siya maki waya da mota, and i saw the car da muka shigo yanxu, a very hearty congratulations dear, Allah ya sanya alkhairi" Da murmushi ta kare maganar, Jiddah dai ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Nagode" Ramlah ta bi parlon da kallo to make sure Aneesah bata nan ta mika mata ledan hannunta murya can kasa tace "Duk na rubuta maki yanda xa ki yi amfani da ko wanne, idan ma baki gane ba ki amshi lambata wajen yaya ki kirani" Jiddah ta amsa tana kallonta cikin sanyin murya tace "Toh nagode, yanxu haka xaku tafi ko ruwa fa baku sha ba" Ramlah tace "Sai kace wata bakuwa, kar ki damu wllh... Sannan maganar makarantarki ki lallaba yaya don naga kamar in don ta shi ne baxai bari ki ci gaba ba, do all u can ya barki ki xana waec dinki kin ji?" Jiddah tace "Toh nagode" Ramlah bata bi ta kan Aneesah da ta walakanta su ba ta nufi kofa, ta juya ta kalli Jiddah dake biye da ita, ganin kamar tafiyar na mata wahala ta dafa ta tace "Ki koma Jiddah, we will talk on phone in sha Allah..." Daga haka ta fita parlon Jiddah ta daga mata hannu ta bi ta da kallo, dai dai nan Aneesah ta fito kitchen tayi wucewarta sama kamar xata yi tsuntsu Jiddah ta bi ta da kallon gefen ido.... Bayan magrib Abuturrab na dawowa mosque ya shiga dakin Aneesah, earpiece ne jone kunnenta tana daga xaune kan duvet da ta kwana jiya, dakin nata dai babu kyan gani kamar anyi yaki a ciki, suna hada ido da shi tayi pausing wakar da take ji amma bata cire earpiece din ba, bai ga alamar tayi sallah ba ma shi ma kuma bai damu yace tayi ba, ya rungume hannunsa yace "Naga u didn't make any food ko baki amshi girkin bane har yanxu?" Tace "Make food for who?" Yace "For the entire house" tace "Ohk let me make this clear captain, ko wacce ta dinga girka abinda xata ci iya cikinta ko ranar girkinta ne ko ba ranan girkinta ba, idan ita ce da girki sae tayi har mijinta, yau da na amshi girki kuma ban yi maka ba ma sbda bani da lafiya!!" Ya dinga kallonta thinking if at all Aneesah xata iya canxawa daga yanda ya santa, duk da fa ba cikin fada take masa maganar ba, yace "Ke kika ajiyeni gidan nan ko ni na ajiyeki da xaki tsara min yanda xa ayi Aneesah?" Ta cire earpiece din kunnenta tace "Baxan kulaka muyi tashin hankali ba Captain, amma dai naga gidaje da yawa haka suke yi, ni idan na amince na ci abinda kishiya ta girka kana tunanin ita kishiyar xata yarda ta ci nawa? So u just have to reason it captain, shi yasa kawai na kawo wannan shawaran amma ba hukunci na yanke maka ba" Yace "Ki shirya in the next five minutes mu tafi asibitin" Daga haka ya juya ya fice daga dakin, ta jawo wayarta da ta ajiye ta danna ma Chef salma kira, murya can kasa tace "Ke ya ake ciki ne wai shiru shiru har yanxu?" Chef Salmah tace "i am almost done my dear, ya xa ayi tahowan da shi kenan?" Aneesah tace "Probably yanxu xa mu fita hospital da shi...." Salmah tace "Tooo har da amaryar xa ku dugunzuma xuwa hospital din?" A takaice Aneesah tace "Akan wani dalili? Shi ma baxai fara wannan haukan ba tunda ai ba girkinta bane" Dariya Salmah tayi tace "Goben dai xai koma aikin ko?" Aneesah tace "Eh" Salmah tace "Yana tafiya xan shigo in Allah ya yarda, akwai magananganu da yawa ke dai" Aneesah na kyabe baki tace "Wai ki ji shigowa yayi yanxu wai ina abinci, ni kuwa nace kowa yayi nasa" Salmah tace "Kika gaya masa haka??" Aneesah tace "Eh mana" Salmah tace "Amma wani lkcn idan kin yi wani abun kamar warce bata ta6a shiga aji ba wllh Aneesah, ta ya xaki gaya masa haka bayan ga chatting da mu ka yi dake daxu?" Aneesah ta xaro ido tace "OMG na mance wllh..." Tsaki Chef Salmah tayi tace "Sai ki nemi yanda xaki gyara tunda kika bata, haba a gama magana dake kawai ki shigo da wani salon da xai 6ata, ni dai gaya min inda xa a bar maki abubuwan idan kun fita" Aneesah ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Kawai idan an kawo a xagaya a kai min ta kofar baya kawai a ajiye i will stock dem all in the freezer idan mun dawo daga hospital din cikin dare" Chef salmah tace "Ohk to, sai dai na shigo goben" Aneesah tace "Toh ki shigo da wuri don Allah gobe xa a kawo min furnitures, i have to borrow ontop of wanda kika ara min fa wllh..." Chef salmah tace "Sai dai na shigo din, kar ki wani damu" Daga haka suka yi sallama, Aneesah ta mike a hankali bayan ta ajiye wayar, wani kayan ta sauya ta cika turare ta dau karamin veil dinta da handbag ta fito ta kulle rubabben dakin nata da makulli tana ma kofar dakin Jiddah wani kallo, tun bayan da aka gama jera mata furnitures din ta koma dakin, sauka downstairs tayi taga Abuturrab xaune alamar ita yake jira, bayan ta shigo parlon ya mike ya wuce sama ta bi sa da kallo, dakin Jiddah ya bude ya ganta xaune saman darduma, ya xauna gefen gado yana kallonta yace "Me xaki ci Baby?" Wani iri ta ji sunan, ta dai daga manyan idonta ta kallesa, yyi mata murmushi yace "Yes tell me duk abinda kike so" a hankali tace "Anything" Ya d'an shafa kansa yace "Ohkk xan je in siyo yanxu in dawo" a hankali tace "Allah ya tsare" Ya sakar mata murmushi yace "Ameen" Sannan ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, ta kwantar da kanta jikin gadonta a hankali, Aneesah na ganin saukowarsa parlor ta koma sama, ya bi ta da wani kallo yace "Kin san kina bata min lkci kuwa?" Tace "One minute" tana haurawa sama dakin Jiddah ta bude ta shiga dakin tana tsaye daga bakin kofa tana kalle kalle, Jiddah tayi mata kallon mamaki, Aneesah na murmushi tace "Pls ki d'an ara min body spray dinki i couldn't get access to mine sbda yanayin dakin..." Jiddah ta nuna mata gaban mirror dinta, ta tafi ta dau kala uku ta feshe jikinta da shi sannan ta juya ta kalleta tace "Thank you dear" Daga haka ta fita Jiddah ta bi ta da kallo, Bayan few seconds ta mike ta nufi jikin window tana kallon waje, sai ga Abuturrab ya nufi parking space din Aneesah na biye da shi a baya, yana shiga driver seat ta bude gaba ta shiga, kallonsu take ko kiftawa babu har ya ja motar suka fita compound din, sauke idonta tayi ta nufi kofa ta sa makulli ta bar makullin a jiki ta tafi ta kwanta gefen gado ta rufe har kanta da duvet. Sai da Abuturrab suka 6ata kusan 2 and a half hour a hospital din sbda series of test da aka yi ma Aneesah, ya so su wuce gobe ko ita ta koma ta amshi result din ta ki yarda wai ita gwara a tsaya ya fito a bata magunguna ko xata iya bacci yau, gaba daya hankalinsa na kan Jiddah sai kallon agogo yake, har karfe tara ya gota... wani kallo ya jefa ma Aneesah da ko ajikinta sai chatting take a reception din, yace "Yanxu meye amfanin haka Aneesah kina ganin karfe nawa yanxu kuwa?" Ta kallesa calmly tace "Kana da appointment da wani ne ko wata? Idan ma matarka ta can gida kake tunani naga dai ba girkinta bane ai, so ko kwana muka yi a asibitin nan girki na ne, lkci na ne... Sbda a ba a jikin ka ciwon yake ba shi yasa xaka axalxala haka kace mu tafi??" Dauke kansa yayi, ta hararesa ta ci gaba da chatting dinta, har ranta taji dadin wannan dadewar da suka yi a asibitin, sai kusan karfe tara da minti arba'in suka ga likita da test results din, magunguna kawai aka rubuta mata, bayan likitan ya sanar masu malaria din ma babu yawa a jikinta, kila tana stressing kanta ne kawai, shi dai Abuturrab fuskarsa a daure yake, ya mike ya amshi takardan da likitan ke basa na magungunan, Aneesah ta mike ta bi bayansa ranta fess, sai da Abuturrab ya siya mata duk drugs din a pharmacy din hospital din sannan suka fita, wani eatry ya tsaya yayi masu take away sannan ya dau hanyar gida, ba su suka shiga gidan ba sai kusan karfe goma da minti goma, Yana sauka motar bai tsaya ta fito ba ya kulle side dinsa yayi wucewarsa ciki yana rike da ledan abincin, ta bi sa da wani kallo ta kulle motar tana murmushi ta bi bayansa, dakin Jiddah ya nufa direct, ya murda ya ji a kulle knocking yayi nan ma no respond, juyawa yayi ya tafi part dinsa, Aneesah ta tsaya bakin kofar Jiddah tana kwankwasa tace "Jiddah, are u asleep, mun dawo ki bude ki amshi abincinki" Tana tsaye tana ta kiran Jiddah tana cewa sun dawo ga abincinta har ya dawo rike da spare key yana ganinta ya hade rai, ya sa makullin jikin kofar amma yaki buduwa sbda makulli na jiki ta ciki, Aneesah tace "Then probably she isn't hungry tunda ta kulle kofa don wanda ke jin yunwa xai jira har sanda aka kawo masa abinci" Tana fadin haka ta wuce dakinta, Abuturrab ya koma bangarensa, kasa cin abincin yayi shi ma, shayin ma da yake sha da daddare bai sha ba, yana kwance saman gadonsa karfe sha biyu saura bayan ya kashe wutan dakin Aneesah ta shigo sanye da kayan baccinta, rufe idonsa yayi as if sleeping, tsaff sai da jera duk abubuwan da Chef salmah ta bada a kawo mata a deep freezer dinta, tun daga soups kala uku, da stew me yawa, sannan ga danyen samosa da su spring rolls duk ta ajiye su a ciki, har da lafiyayyen jollof rice, da fried rice... kulle kofar dakin tayi bayan ta shiga ta tafi ta kwanta daga gefensa, duk da kamshinta da ya cikasa da abinda ya soma ji lkci daya, haka yayi ignoring yyi feigning bacci. Da ya farka cikin dare sai yaji hankalinsa ya tashi sbda wnn turaren Aneesahn amma ko kusa da ita xuciyarsa bai yarje masa yaje ba, amma wani lkcn cikin bacci sai ya ga kamar Jiddah ce a side din nasa sai yyi saurin kawar da thought din, dab da asuba yaji ta matso kusa da shi a hankali sbda dakin yyi sanyi tunda Ac a kunne yake, ya lumshe idonsa ya kai hannu ya ta6ata, Aneesah bata ta6a xaton bayan duk abinda Abuturrab yayi a wnn lkcn baxai kusanceta ba, infact mara lafiya ne kadai xai iya hakuri a wnn lkcn, haka kawai yaji xuciyarsa ya kasa yin hakan abun ya fita kansa lkci daya, ganin ya juya mata baya ta rikesa murya can kasa tace "Meye haka Captain?" Juyowa yayi, yayi kissing forehead dinta yace "I am only after the romance, nothing more" Daga haka ya mike ya shige bandaki ta bi sa da kallon mamaki. Yana dawowa masallaci da asuba ya murda kofar dakin Jiddah dake a kulle still, ya kwankwasa kofar ya tsaya for almost 3 mins bata bude ba, yayi kasa da murya yace "Meye haka pls Jiddah? Why are u doing this?" Bayan few seconds ya kara kwankwasawa bata bude ba, juyawa yayi ya koma part dinsa, shiryawa kawai yayi don gaba daya yaji ransa ya baci, Aneesah ma na bacci ko sallah bata yi ba ya dau jakar laptop dinsa da komai, snn ya buga gefen gadon yace "Na tafi...." Ta mike xaune tana murxa ido duk da haushinsa da take ji tace "Da wuri haka?" Yace "Yea i will be driving to kano, plss and pls Aneesah i want nothing but peace, i am begging u, kinga kece babba i am expecting nothing sai kwanciyar hankali har in dawo" Tayi wani murmushi tace "In sha Allah Captain baxa ka samu akasin haka ba, Allah ya tsare" Juyawa yayi ya fita ta mike da sauri bayan ta ji fitarsa gaba daya daga parlonsa, lekawa tayi taga ko xai tsaya kofar dakin Jiddah amma sai ta ga otherwise don sauka kawai yayi downstairs bai ko kalli kofar dakin ba, tayi wani murmushi ta juya ta koma ta ci gaba da baccinta, Jiddah na xaune kan darduma ta ji ya kunna motarsa, mikewa tayi a hankali ta isa jikin window tana kallon compound din, booth taga ya rufe bayan ya saka jakarsa ya nufi driver seat ya shiga yana gama warming motar mai gadi ya bude masa gate ya fita, Jiddah ta sauke idonta sannan ta juya ta koma gefen gadonta ta kwanta a hankali. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you FZ BEAUTY SUPPLEMENTS Dealer in all kind of dietary supplements such for skin whitening, skin glowing, weight gain, slimming, flat tummy, infection killers, dark spots removers, fertility booster, Hips boosters, Breast firming and Enlarging, Teeth whitening, eye, joint, stretch marks, and for marital pleasure. All supplement are available for wholesale and retail. For more information contact FZ via wa.me/2348143821028 FZ Beauty Supplements Dealer ce ta supplement masu qara fito da kyaun mace ko namiji, hadi da qarama garkuwar jiki kuzari. Muna sayarda Supplemnt kamar na qarin duwawu, akwai wanda zaya taimaka wurin dawoda martabar Nono, akwai na rage qiba da tumbi, akwai na rakwainuwa, akwai na tada komada, akwai masu saka hasken fata da qyalli, akwai na infection, akwai na saka hasken ido da hakori sannan akwai na gyaran turaka. Muna maraba da mai sayen daya ko sari. Wa.me/2348143821028 [8/5, 9:02 PM] Ummuanwar🥰: Karfe goma saura Jiddah ta bude kofar dakinta a hankali ta dalilin yunwan da taji ya dameta, tun da taga fitan Abuturrab daxu da sassafe ta tsorata da gidan kuma, material ne a jikinta na doguwa riga sai hulan da ta rufe gashinta da shi, ta fito daga dakin ta kulle kofar without making any sound tana satan kallon kofar dakin Aneesah dake can karshe duk tunaninta tana ciki, ta fara sauka downstairs shi ma bata yarda tayi making any sound ba, sosai gabanta ya fadi ganin Aneesah xaune parlon tana sanye da rigar bacci har sannan, ta daura kafa daya kan daya tana cin cake tana danna wayarta, xuciyar Jiddah ya dinga bugawa ta karasa cikin parlon tana tafiya a hankali, duk da yanda ta dinga avoiding su hada ido sai da suka hada idon da ita, daburcewa tayi, bata san lkcn da tace "Ina kwana" Aneesah tayi mata wani kallon daga sama har kasa, ta ja wani tsaki ta ci gaba da cin cake din hannunta tana danna waya, Jiddah ta sauke idonta ta nufi kitchen duk jikinta yayi sanyi, kulle kitchen din tayi ta turo baki ta jingina da kofar, sai taji haushin kanta gaisheta da tayi, to amma ai bata ma san sanda ta gaisheta ba, bin kitchen din ta dinga yi da kallo, duk da babu wani plate da aka bata amma kitchen din na bukatar gyara, rabon da ayi masa komai tun jiya da safe da ta yi, ta ta6e baki ta shiga store ta dau indomie guda daya a kwalli sannan ta fito, sai da ta fara daura kwai a kan wuta, tana tsaye har ya dahu, sannan ta fara girka indomie din, bata jima a kitchen din ba ta gama, ta juye indomie din a plate sannan ta rufe da wani plate ta dau fork ta bude kofar kitchen din ta fito, sosai gabanta ya fadi ganin wasu manyan mata har hudu a parlon tare da Aneesah duk sun cika parlon da muryarsu kamar ganga, da yake ta rufe kofar kitchen din shi yasa bata jiyo su ba tun daxu, tana fitowa parlor duk suka yi shiru, duk da ba kallonsu take ba amma jikinta ya bata duk ita suke kallo, har wani hardewa take tana tafiya da sauri, Chef salmah ce da Rabi'ah sai Suhaila da Fauziyya, duk kawayen Aneesah ne kuma sa'aninta da suka yi karatu tare a Abuja kana ganinsu ka ga gogaggun yan matan Abuja, Aneesah kadai ce ta dace tayi aure cikinsu, sauran duk gantalinsu kawai suke, kuma yawanci duk babu warce iyayenta ke nan kaduna kawai xamansu suke a garin, Chef Salmah da Rabi'ah ma su biyu kadai ke xaune gidan iyayen Rabi'ah dake Unguwan sarki, dukkansu suka bi Jiddah da kallo, Rabi'ah ta kalli Aneesah da wani expression tace "Wait... wai wannan er yarinyar ce kishiyar taki?" Aneesah ta kyabe baki tace "Wai ba" Wani dariya suka yi gaba daya har da kyakyatawa, Chef salmah tace "Kuturin uba!!! Yo ai wannam karamar alhaki ce Aneesah, ni wllh duk tunanina sa'ar mu ce aka kawo maki xa ku gwabza, yanxu da wannan er cikin naki aka hada ki kishi? To kiyi kishi da ita kice kinyi kishi da wa Aneesah?? Wllh ni duk sai naji raina ya baci, me aka yi aka yi wnn yarinyar, dubeta fa duk a tsorace kamar zomo...." Jiddah dake jin su ta nufi stairs ko juyowa bata yi ba tana jin kamar xata fadi sbda hardewar da take, Suhaila ta rike ha6a tace "Ikon Allah, yo minti nawa xa a 6ata wajen gamawa da wnn er yarinyar? Ni har kin ban kunya wllh Aneesah, ni fa na xata wata uwar mata ce ashe wai wnn kwailar aka kawo maki gida kika bi kika daga hankali kika bi kika ishemu a group" wani tsaki ta ja, Fauziyya ma ta ja tsakin tace "Wllh kwana uku yayi kadan idan ban sa xaman gidana ya gagareta ba shegiya nake, look how meek she is, wannan ai kamar kin samu er wanke wanke ne da share share, ya wuce ma ki aiketa ta amso maki kati ko cingam a kofar gida??" Duk suka kyalkyale da dariya, Rabi'ah tace "Toh ke yanxu Aneesah fasa kayan daki shine iya abinda xaki iya yi ki burge kenan? Is that all u can do? Haba wannan ai karamar alhaki ce" Aneesah tayi wani dariya tana jinjina kai tace "You guys are only being faster than ur shadows" Jiddah dai tuni ta shiga dakinta ta saka key, gaba daya ta tsorata da su, on a serious note Chef salmah tace "Kinsan Allah Aneesah lamarinki ya kunyata ni wllh, na xata xan xo in ga er 35 ne, wai ashe a kan wnn da kilan bata wuce 18 ba kika daga hankalinki haka" Aneesah tayi kasa da murya tace "I think i told u all yanda abubuwa suka dinga faruwa tun ma kafin ta tare, da rashin mutuncin da na dinga yi, yanxu abu kadan captain yake jira inyi shi yasa ku ka gan ni a yanda ku ka gan ni, shi yasa ku ka ga nayi shiru, wllh ba don mahaifiyarsa fa ranan da nayi ma kayanta aika aikan nan saki na yayi niyyar yi don har ya dauko takardan ta hanasa, banda haka ni dai kunsan ba kanwar lasa bace, kawai ku bar ni in ci gaba da bin su da ido for the mean time, ko kun ta6a ganin mutumin da bai kama dahir ba yana iskanci? Ai yanxu sai dai kawai in bi komai a hankali, domin kuwa a wuyar captain nake yanxu, nasan kuma babu wanda yake jin haushi sama da ni a duniyar nan, sarai na sani" Rabi'ah tace "Toh Allah ya kyauta, idan an kawo kayan mun gama gyare gyaren da xa mu yi sai mu tafi inda xa mu je kawai since akwai lkci, ni fa shi sa har yau ku ka ga naki amsa ma Alhaji Salisu, so kawai nake sai na gama duk abinda ya kamata tun daga waje, ta yanda ina shiga gidan komai ya dawo hannuna baxan iya wahala ba gaskiya, don haka sai na shirya tsaf anyi duk abinda ya kamata sannan xan basa izini ya turo" Fauziyya tace "Kina da gaskiyar ki wllh, wa xai xauna? Yan iskan uwayen gidan nan da jira kawai suke Allah ya kawoka su nuna maka takama da isa, to wllh ba ayi matar nan ba, shi sa muke shiri sosai kafin mu shiga...." Aneesah dai sai wani murmushi take tana girgixa kafa, jin ringing din wayarta ta mike ta isa gun wayar dake caji da sauri ta dauka ganin me kiran ta daga ta kai kunne, a d'an fusace tace "Ni ban ga wani alert ba har yanxu wllh, haba abu tun jiya dae kamar xa a turo min miliyan goma, gashi sbda rashin cikon kudin ba a turo min kayan ba har yanxu" Ta kyabe baki tace "Toh ina jira ni dai..." daga haka ta katse wayar, Fauziyya tace "Yanxu da mun xo karfe takwas da rabi haka xa mu yi ta xama kaya basu iso ba" Aneesah tace "Toh ba sai an samu cikon kudin ba sannan xa su iso Fauziyya, kun san fa na canxa furnitures din daga wanda na tura maku a group, wannan ya fi shi tsada, daga baya company din suka turo min wannan naga ya fi kwanta min kawai na xa6e sa" Sai karfe sha biyu motar kayan Aneesah suka iso gidan, kamar dai yanda aka yi na Jiddah ita ma haka sai da suka sauke sababbin kayan snn suka dinga fitar da fasassun waje suna lodawa a babban motar, kafin karfe uku masu kawo kayan duk suka shirya mata furnitures din sannan suka wuce... Suna xaxxaune da kawayenta a dakin bayan an gyara ya dawo fess, sai ya6a furnitures din suke, ita kuwa sai murmushi take tana bin dakin da kallo don ya fi nata na da kyau, miliyan 1.5 tayi kayan dakin, Babu warce ke da alamar tashi tayi sallan axahar cikinsu, Aneesah ta fita tayi masu rechauffe din jollof din dake freezer ta kawo masu dakin da drinks da ruwan gora, ko wacce ta sauko kasa xa a ci abinci. Sai wajen karfe biyar da rabi suka shirya ta rakasu bakin motar Rabi'ah dake kofar gida, Chef salmah tayi wani dariyan yan da6a tace "Sha kuruminki aminiya, mota kamar Aliyu ya siya maki wanda ya take wancan na garage, ke dai Allah ya bamu nasara kawai.... Mu ne fa!!" Rabi'ah tace "Banda ma tana ta mana xurfin ciki ai da ba a kai ga haka ba wllh, ni duk a xatona don taga tayi aure ne ta wani fita harkanmu take shan kamshi shi sa nima na sakata a kwadon shara, kawai na sha iskanci ne tsabagensa take mana, ashe tana nan tana ta kunsar takaicin d'a namiji, ni da na maida maza kamar rigar sawa ta, in cire sanda na ga dama in mayar, ga dai su da yawa a gari kamar ledan pure water, wani lkcn sai in ji bana ma son auren, gwara kawai inyi ta duniyanci na wllh" Dariya su Salmah suka yi suna hailing dinta da karfi, Suhaila tace "Toh kar dai ki manta karfe takwas xa ki fito Aneesah, don wllh wajen da nisa sosai" Aneesah tace "In sha Allahu takwas din kuwa..." Da haka tayi sallama da su ta dawo cikin gida cike da farin cikin xuwansu, kawayenta ne na kut da kut tare suke watsewarsu a Abuja, lkcn da aurenta da Abuturrab ya tashi babu irin shawaran da Rabi'ah bata 6ata ba kan kar tayi aure yanxu tana yarinyarta da ita ta fara fuskantar matsalolin rayuwa amma Aneesah taki ji, wnn ne ma yasa Rabi'ah bata yi attending bikinta ba sae su Fauziyya da Suhaila kawai. Jiddah na kwance daki kana ganinta kasa she is very sad, tun indomie da ta ci shi ma ba sosai ba da safe bata sake cin komai ba har yanxu sbda tana tsoron fita parlor, yunwa take ji sosai amma ta rasa yanda xata yi, ta mike xaune a hankali tana share hawayen da ya kawo idonta ta mike ta isa jikin window ta tsaya wani hawayen na sauka idonta, sosai take jin kewar Abuturrab, and she wished he is around da baxata ji yunwa ba.... Aneesah na shiga dakinta ta shiga wanka da sauri, bayan wasu mintuna ta fito, cikin gaggawa ta mulke jikinta da turarruka iri iri snn ta fito da wani ubansun English wears ta saka ta dau babban handbag dinta ta saka brush da maclean, sai panties biyu, ta debi turarruka kala uku ta xuba su a jakar, Hijab dinta ta dauko har kasa ta saka sannan ta dau flat shoe dinta shi ma ta sa ta dau dubu hudu ta xuba a jaka ta dau jakar ta nufi kofa ta fita, kulle kofarta tayi da makulli a hankali snn ta fara sauka downstairs without making any sound, Jiddah na tsaye jikin window dinta har sannan taga Aneesah da hijab har kasa da handbag ta nufi gate da sauri, Jiddah ta dinga kallonta har ta fita gidan. Da sauri Jiddah ta nufi kofa ta bude ta sauka da nufin tayi duk abinda xata yi a kitchen kafin dai ta dawo, tana ta tsaye kitchen tana tunanin me xata dafa da baxai dau lkci ba, kawai tayi deciding ta dafa jollof din pasta, ba kifi ba nama don a tunaninta xai bata mata lkci, cikin minti ashirin ta gama don pasta din rabi tayi amfani da ta juye a warmer ta dau ruwan gora a fridge ta fita kitchen din ta koma sama da sauri tana sauke ajiyar xuciya.... Har aka kira magrib bata ga Aneesah ta dawo ba, aka yi isha still tana ta xuba kunnen ta ji an bude gate an shigo amma shiru, wanka Jiddah tayi ta sauya kayan jikinta xuwa na bacci sannan ta kwanta gefe, she is just missing everything about Abuturrab so much, sau da yawa sai taji kamar lips dinsa a nata har sai ta kai hannunta bakinta, ta lumshe ido ta takure waje daya tana ta kwance har karfe goman dare, ta mike xaune cike da mamaki don har yanxu bata ji Aneesah ta shigo ba, a haka har bacci ya dauketa wajajen 11. Da asuba tana farkawa ta fito ta sauka downstairs don haka kawai taji hankalinta ya tashi ganin har bacci ya dauketa jiya Aneesah bata dawo ba, ta kofar parlon kadai xata san ko ta dawo ko bata dawo ba don in har ta dawo to xata kulle kofar parlor, ga shock dinta a bude taga kofar da ta murda, alamar ba a shigo ba balle a kulle, ta dinga kallon kofar a tsorace sai kuma ta juya a hankali ta koma sama. Gari na wayewa karfe bakwai Jiddah ta sauko parlor don bata jin dadi taga gidan so dirty, tunda ita dai ba me kiwiya bace, ga shi Aneesah da bakinta na jiya sun yi kaca kaca da parlon kamar yan yara, duk cake ne kan tiles da goran drink da ruwa, tana cikin sharan parlon aka bude kofa, daga kai tayi da sauri, Aneesah na ganinta ta hade rai taki yarda ta sake kallon inda take har ta haura sama, Jiddah ta bi ta da kallo tana ci gaba da sharanta a hankali, bayan ta gama tayi mopping xata kai bokitin waje sai ga Aneesah ta sauko daga sama da saurin ta again, atamfa ne a jikinta da mayafi sai handbag dinta sai xuba kamshi take, nan ma ko kallon Jiddah bata yi ba ta fice daga parlon tana picking call dinta tace "Kai Rabi'ah gani na fito yanxu, wllh na makara ne" Jiddah dai ta bi ta da ido don a bude ta bar kofar.... Bayan la'asar Jiddah ta fito kitchen kenan bayan ta wanke plate din da ta ci abinci, har sannan Aneesah bata dawo gidan ba, xata tafi sama ta ji an bude kofa ta juyo da sauri, Hajja ce ta shigo parlon ba ko sallama, Jiddah da ta ji dadin ganinta ta dawo parlon da sauri tana murmushi tace "Sannu da xuwa Hajja" Hajja tace "Bari Jiddah ba wannan ne gabana ba, Ina mijin naki?" Jiddah ta girgixa kai tace "Ya tafi aiki ai" Hajja ta rike kai tace "Kashh, wai nan na shirya ne ya kai ni gidan kyauta ance min shi kadai ya san gidan a Barnawa tunda a lkcn da ya maida Hafsah uwarsa da ubansa kusan duk kwana biyu sai sun je gidan da shi da ita, yanda yake xuwa gidan ma ko gidan Ramlah bai xuwa... Amma wllh ban ji dadin wannan shegen aikin da ya tafi ba, wai fa daga na d'an kishingida in huta yanxu kawai sae nayi mafarki an kwama ma bakina katon kwado bana um bana um um, kuma ni kadai ke ganin kwadon babu me gani wllh, su Usman da Hauwa sun tsaya kai na suna ta hajja lafiya, Hajja lafiya, amma ina ba baki an garkame sae kallonsu kawai nake kamar bebiye, to shi yasa ban ga ta xama ba a xo a kaini gidan Kyauta ayi min iyaka da Hafsah, wllh da kyar idan baxan kai wannan xancen kotu gobe ba, don ya gigita ni shiga bandakina biyar kafin in xo gidan nan, yanxu haka xancen da nake maki sae na kara xagawa a gidan nan, ai ko dabba ba a kulle ma baki ba balle mutum" Jiddah dake ta kallonta tace "Hajja ai ana kulle na doki" Hajja ta saki baki tace "Toh ni doki ce? Ina ruwana da doki xaki ce min ana kulle na doki, ana maganar mutane me ya kawo na dabba kuma Jiddah? Kawai mata matsiyaciya ki nemi garkame min baki ban maki komai ba, wllh baki ga ba ko abincin kirki ban iya ci a kan wannan xancen yau kwana hudu kenan, kwatsam sai ga mummunan mafarkin nan daxu, kin ga kuwa ai ba lafiya, to tun kan a cuceni a mayar dani Bebiye gwara a xo a biya min tikiti in koma Masar bakina alekum" Jiddah dai sauraronta kawai take, Hajja tace "Shi kuma yaushe xai dawo daga gararin samaniyar tasa?" Jiddah tace "Kilan juma'ah ko asabar, Hajja ki xauna in kawo maki ruwa" Hajja tace "Wani ruwa bayan abinci ma wannan na kasa ci, meye kuma ruwa, naga alama kun dau wannan kess din karamin kess, wllh da a Masar ne sai an bata kwadon gaske ace ta kulle bakin nawa a gani, Allah sai an mata zindir an xane shegiya sannan a mika ma yara su yi ta jifa, me na mata xata min haka??" Tana kai wa nan ta nemi waje ta xauna tana fiffita xufar da tayi da mayafinta, Jiddah ta nufi kitchen dauko mata ruwa da lemo ta ajiye gabanta, Hajja ta dau goran ruwa daya sai da ta kwankwadesa tass, sannan ta ajiye tace "Rabona da shan ruwa tun kan inji wannan mummunan batun" Bude kofar parlon aka yi duk suka daga kai, sosai gaban Jiddah ya fadi ganin Abuturrab ya shigo parlon, suna hada ido ya dauke idonsa fuskar nan tasa a daure, ta sunkuyar da kai, Hajja ta kalli Jiddah tace "Kika ce min ya tafi aiki?" Kafin Jiddah tace komai yace "Ehh daga can nake" Hajja ta mike tace "Abinda Allah ya ga xuciyata ko daga sararin samaniyar ne ai sai a hankado min kai kawai, wllh ina cikin garari Aliyu, gidan Kyauta yayar Hafsah xaka kai ni a Barnawa don girman Allah" Abuturrab yace "Daga Abuja fa nake yanxu ko hutawa ban yi ba Hajja" Hajja tace "Oh oh Allah, Aliyu mafarki nayi an kulle min baki da kwado fa? Wa xai xauna da wannan mugun mafarkin idan ba gantalalle ba" Yace "Toh ki bari in huta na gaji, bayan nayi aiki kuma na sake shiga mota na taho kaduna" Hajja ta koma ta xauna tace "Toh tafi ka huta ko na minti sha biyar ne, ai ni ba bakuwar xafi bace, banda Ramlah ma bata san gidan ba ai ita nayi niyyar ta rakani don naga ita dai dai take da ko wani d'an banxa a duniya" Abuturrab bai ce mata komai ba ya nufi sama, Jiddah ta bi sa da kallo, Hajja tayi kasa da murya tace "Ina gantallaliyar abokiyar xamar ta ki?" Jiddah tace "Kila tana daki ban sani ba" Hajja tace "Atoh, ina ruwanki da ita da xaki san inda take dama" Mikewa Jiddah tayi tace "Ina xuwa Hajja" Hajja tace "Toh ni dai kar a shanya ni, ba ruwana da iskanci da rana tsaka" stairs Jiddah ta nufa, tana haurawa sama ta tsaya corridor tana tunanin ta je ko kar taje side din nasa, haka kawai ta ji tana shakkarsa sosai, bayan few seconds kawai ta nufi bangaren nasa tana tafiya a hankali, bude kofar parlon tayi kamar munafuka ta shiga ciki ta gansa xaune, ta karasa ciki ta d'an durkusa kasa daga gefensa ta ki yarda su hada ido tace "Sannu da dawowa" Ba tare da ya kalleta ba yace "Thank you" Kallonsa tayi a hankali, jin bai sake cewa komai ba ta mike ta nufi kofa ta fita ta koma wajen Hajja. Bayan minti ashirin Abuturrab ya sauko parlor kafin nan sai da ya bude kofar dakin Aneesah ya ji sa a kulle, kallon Jiddah yayi yace "Lend me ur car key" Ta mike tana kallonsa don babu yabo babu fallasa yayi maganar, ta wuce sama ta dauko masa makullin a dakinta ta risina ta basa, ya amsa yace "Tashi mu je Hajja" Hajja ta mike tace "Allah yayi maka albarka, mu je in ji ba'asin kulle min bakina" Kofa ya nufa tana biye da shi ko sallama bata tuna tayi ma Jiddah ba har suka fita, Jiddah ta bi su ta tsaya bakin kofa tana kallon Abuturrab, ya ki yarda ya kalleta, nan da nan hawaye ya kawo idonta, kamar ance ya juya ya ga hawaye a idonta, ya jefa mata wani kallo, turo masa baki tayi ta juya ta koma parlon da sauri. Abuturrab na ajiye Hajja kofar gidan Kyauta ya ciro dubu biyar ya mika mata yace "Hajja gashi idan xaki koma sai ki samu adaidaita sahu, ni yanxu xan koma aiki ne, nayi mantuwa ne yasa na dawo" cike da masifa Hajja tace "Yau naga jalala, dama ba da kai xa mu shiga ba ni kadai raina xan shiga?" Yace "Toh ni macece da xan bi ki mu shiga Hajja, excuse na dauka wajen aiki, jirgi na can a airport din Abuja xan daga xuwa kano" Hajja tace "Toh na fi jirgi ne? Ko ina ruwana da shegen jirgin naku? Sbda ba bakin uwarka aka yi niyyar garkamewa ba shi sa baxa ka bi ni mu shiga ba ko??" Dariya ta basa amma ya cije yace "Toh sai in bar aikina in shiga ayi ta xancen garkame baki da ni?" Hajja tace "Toh Allah ya isa, ai sbda kai da uwarka aka yi niyyar kulle min bakin nawa Allah ya toni asiri, kuma wllh daga yau ko kasheku naga xa ayi kai da uwarka shiru xanyi abina in koma gefe tunda gashi ta dalilinku aka nemi hallaka min bakin da nake salati nake ba Allah gaskiya" Daga haka ta fixge dubu biyar din ta shige gidan tana rafka wani uban sallama, dariya yayi ya juya kan motarsa ya dau hanyar gida. Yana komawa gida bayan ya haura sama dakin Aneesah ya bude ya ji a kulle har sannan, ya d'an tsaya sai kuma ya nufi dakin Jiddah ya bude, kwance ya ganta tayi kukanta ta koshi, ta mike xaune tana kallonsa ya wani hade rai, cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" yace "Ban yi ba" Tura masa baki tayi ta juya masa baya, ya shafa kansa yana kallonta, sai kuma yace "Ina Aneesah?" Ta kallesa a hankali tace "Nima ban sani ba" ya karasa dakin ya rungume hannunsa yana kallonta, lkci daya ya dauke idonsa daga kanta, yyi kasa da murya yace "Make me a cup of tea" daga haka ya juya ya fita, ta mike a hankali ta fita ita ma ta sauka downstairs. Bangarensa ya tafi ya dauko spare key ya bude dakin Aneesah thinking ko kulle kanta tayi a ciki, amma babu kowa dakin haka ma bathroom din... A ranan Abuturrab xai koma Abuja don ko awa biyu bai yi niyyar yi ba a gidan, but ya kasa tafiya yana ta xaune parlor downstairs yana jiran ya ga sanda Aneesah xata shigo gidan, Jiddah ta fito daga kitchen tana kallonsa tace "Na gama in xubo maka yanxu?" Ya daga kai ya kalleta yace "Tun yaushe Aneesah ta fita gidan nan?" Ta d'an buda hannunta tace "Nima ban sani ba ina daki" Yayi shiru, ta koma kitchen ta xubo masa girkin da tayi ta fito ta ajiye masa kusa da shi, kallon kirjinta kawai yake da ta durkusa ajiye abincin, ya lumshe idonsa ya jinginar da kansa jikin kujera, don ba karamin nesa yake kai xuciyarsa ba a kanta tun daxu, barin da ya shiga dakinta ya ga tana kuka he wish he can hug her tightly and tell her he isn't angry and he is back all because of her, ta mike tana kallonsa ta wuce sama ta shiga dakinta ta xauna tana tunanin yanda xata yi Aneesah ta san ya dawo gidan, mikewa tayi ta tafi bangarensa tana kallon wayarsa da ya bari kan kujera, dauka tayi ta kulle kofar parlon, ta shiga call logs dinsa amma bata san yanda yayi saving number Aneesah ba, Blossom ta gani can kasa nan da nan ta tuna ta ta6a ganin sunan a phone dinsa da dadewa tayi dialing number, yana fara ringing aka daga..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppJiddah tayi shiru, daga daya bangaren ta ji muryar Aneesah kasa kasa tace "Hello My captain..." ta fadi hakan yayi sau uku, jin shiru Aneesah ta katse wayar ta sake kira, Jiddah ta dinga kallon screen din kamar baxata daga ba, har ya kusa katsewa sai kuma ta daga a takaice tace "Dama kawai ce maki xanyi ya dawo tun daxu..." Aneesah ta xabura lokaci daya tace "Captain din?" Jiddah bata ce mata komai ba ta katse wayar, Ta ajiye masa kan kujera sannan ta fito ta wuce dakinta.. Abuturrab na dawowa masallaci bayan magrib ya dinga kallon motar da yayi parking kofar gidansa, sai ga Rabi'ah ta sauko daga maxaunin driver ta bude back seat ta riko Aneesah ta fito da ita, Banda nishi babu abinda Aneesah take tana tafiya da kyar Rabi'ah na rirrike da ita tana mata sannu, ya dinga kallonsu sai kuma ya shige gate kawai, yana xaune parlor suka shigo bayan minti goma irin da kyar Aneesah ke tafiya din nan, Aneesah ta kwanta saman kujera tana sauke numfashi da kyar tace "Ka dawo ne Captain? Hope all is well?" Shiru yayi yana kallon tv, Rabi'ah tace "Haba dai Captain, kai da ya kamata ka fara tambayar lafiya ka dawo gida baka sameta ba kuma daga ina take? Sai kuma kayi shiru? To daga asibiti muke" Ko kallonta Abuturrab bai yi ba, Aneesah ta mike xaune ta jingina da kujera tana nishi tace "Ban yi bacci ba kwata kwata jiya da daddare captain wani xaxxabi me xafi ya rufeni na rasa yanda xanyi, ga shi drugs da aka min prescribing a hospital kamar shi ya sake triggering xaxxabin da ciwon kai, na daure da sassafe na fita na kwankwasa ma matarka kofa tana ji ta ki budewa, har ce mata nayi bani da lafiya ne, wllh sai ce min tayi ita baxata iya fitowa ba bacci take, ban ta6a xaton haka ba wllh, na dai koma dakina ina son sake shan drugs din nawa amma ban ci komai ba, sai na daure na sauko downstairs wajen karfe sha biyu tana xaune tana kallo tana cin abincin da ta girka, jin kamshin girkin ya sa naji amai ya taho min, wllh captain a nan parlon na gama amai na, na gyara wajen Jiddah ko sannu balle Allah ya sauwake, shine na koma daki nayi ta kiran layin Aunty Safara'u taki dauka kuma nasan fushi take da ni har yanxu, da na rasa yanda xanyi kai kuma ina tunanin kana bakin aiki sai na kira Rabi'ah ta xo ta kai ni asibiti, shine sai yanxu fa" Rabi'ah ta ajiye mata ledan magungunan hannunta tace "Sai da safe Aneesah, Allah ya sauwake ya kara lafiya, ciwo kuma na kan kowa ai...." Daga haka ta nufi kofa ta fita, Abuturrab ya dinga kallon Aneesah dake sauke numfashi da kyar, yace "Wani asibitin ku ka je?" Tace "Nima ban sani ba, sai dai a tambayeta, i almost lost conscious a hanya" Bai kuma ce mata komai ba ya mike ya wuce sama, ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya, ta tashi ta tafi dakinta da sauri ta kwanta ta lulluba da bargo, bayan isha Abuturrab ya shigo dakin nata, duk da idonta biyu taki nuna hakan, ya karasa ya xauna gefen gadon yana kallonta yace "Ya jikin?" Ta bude ido da kyar tace "Da sauki" yace "Me xa ki ci?" Tayi kasa da murya tace "Shayi kawai xan sha kar in yi amai" mikewa yayi ya sauka kasa ya shiga kitchen, yana making cup of tea Jiddah ta shigo kitchen din, ya kalleta sau daya ya ci gaba da abinda yake, ta wanke plate din hannunta ta ajiye xata fita ta ji yace "Me yasa da Aneesah ta ce maki bata da lafiya kika yi shunning din ta?" Kallonsa Jiddah take with confusion, ya juya ya kalleta yana jiran amsanta, jin tayi shiru yace "Just like that?" Tace "Ehh, haka nayi niyya" tana fadin haka ta juya ta fita ya bi ta da kallo, lkcn da Aneesah ta fada masa he find it hard to believe ya dai ji ta kawai, amma yanxu ya tabbatar hakan ne, ya dau shayin ya fita ya kai ma Aneesah daki, Jiddah ta xauna gefen gadonta tambayar da Abuturrab ya mata na rotating a kanta, wai me yasa tayi shunning Aneesah, a ina ta ganta balle tayi shunning dinta?? Karfe hudu da rabi na asuba Abuturrab ya gama shiryawansa a dakin Aneesah, ita ce ma ta tashesa don yace mata he will be leaving very early kafin sallan asuba sbda karfe takwas xa su yi piloting jirgi xuwa PH, ta hada masa ruwan wanka ta dauko masa kayan da xai saka daga bangarensa har hakan ya basa mamaki don duk xamansu bata ta6a yi masa haka ba, da damuwa tace "To breakfast fa? Haka xaka tafi baka karya ba?" Yace "I will... At the airport, how are you feeling now?" Tace "Aa na ji sauki sosai" Yace "Alright, Allah ya sauwake" Tace "Ameen My Captain, yaushe xaka dawo?" Yace "Friday in sha Allah" tace "Toh wai me ya dawo da kai jiya, ko dai ka ji a jikinka bani da lfya ne?" Yayi murmushi kawai ya dau jakar laptop dinsa yace "Probably.... Take care, sae na dawo" tace "Toh xa ma ka samu motar da xai je Abuja this early kuwa?" Yace "Aa i will drive" daga haka ya nufi kofa tace "But ina son magana na minti daya captain" ya juyo ya kalleta, tayi kasa da murya cike da damuwa tace "I don't know why Jiddah bata son mu xauna as one Captain, ko don sbda abubuwan da na dinga yi a baya ne ya sa ta ki sakin jiki da ni ban sani ba, dama shi mutum baya canxawa Allah baya canxa sa? Wllh nayi nadaman abubuwan da na aikata a baya, naga ba shi da amfani ba shi da fa'ida, i was just behaving like an illiterate a lokacin, baya bayan nan na gane babu abinda ya kai xaman lafiya dadi, balle ita da nake mata kallon warce bata da hayaniya xa mu xauna lafiyan, amma wai bani da lafiya Jiddah tayi kamar bata sani ba a gidan nan alhalin a gabanta nayi amai ta kauda kai, rashin lafiya ae ya fi gaban komai... da bata min haka ba wllh" Yace "Sai na dawo" fita yayi dakin, ya nufi dakin Jiddah ya murda kofar ya bude ya shiga, bude kofar ya farkar da ita, ya kunna wutan dakin yana kallonta yace "Lend me the car key" Sauke ido tayi daga kallonsa ta sauka kan gadon ta tafi gaban madubi ta dau makullin ta ba sa, har ya nufi kofa ya dawo yana kallonta yace "Ke yanxu abinda kika yi jiya kin kyauta Jiddah? Komin abinda mutum yayi maki kika ga bashi da lafiya ai xaki yi masa abinda ya kamata a matsayin ki na musulma, Did u know what it means to have a forgiving heart kuwa?" kallonsa kawai Jiddah take ta ma rasa abinda xata ce don bata san a kan me yake maganan ba ma, a xuciyarta kuwa tunani ta shiga yi waye ba lafiya? Ganin taki ce masa komai ya nufi kofa ya fice daga dakin. Da safe karfe tara Jiddah ta sauko ta ga Aneesah xaune parlor tana kallo da plate din samosa da spring rolls a hannunta tana ci, aikin kenan ta ci tayi kallo... Tana ganin Jiddah ta dinga mata wani kallon raini daga sama har kasa, Jiddah dai bata kalleta ba har ta wuceta, ta ja wani dogon tsaki tace "Shi dan talaka dama idan ya samu waje ya fi kowa gogewa da girman kai, banxa kawai er matsiyata" Jiddah ta tsaya ta juya tana kallonta, Mikewa Aneesah tayi ta nufeta a fusace tace "Ko xa ki rama ne da kika tsaya kallona haka?" Jiddah ta girgixa kanta tace "Not my home training" Ta juya xata wuce Aneesah ta fixgota da karfi tace "Home training din waye kenan?" Duk da yanda gaban Jiddah ya dinga bugawa haka ta hade rai tace "Cika ni..." Aneesah ta dunguri kanta tace "Anki a cika ki don ubanki, kiyi abinda xa kiyi" Jiddah tace "Babu abinda xanyi tunda ni ba mahaukaciya ba..." Bata rufe baki ba Aneesah ta sauke mata mari sannan ta hankadeta da karfi tace "Uwarki ce mahaukaciyar, ehh uwarki da ba a san ko cikin shege tayi ta haifeki ba tunda har yau ba a ga dalilin asalinki ba..." Jiddah ta dafe kuncinta tana kallonta, Bata san lkcn da ta figi flower vase dake saman center table ba ta buga mata shi a kai, duk da Aneesah ta kauce sai da abun ya sameta, wani ihu ta fasa ta dafe kanta lkci daya idonta ya fara juya mata sai dai kan nata bai fashe ba, ta nufi kitchen da gudu kamar mahaukaciya, Jiddah na ganin haka tayi hanyar kofar fita, kan kace me sai ga ta a bakin gate, gaba daya ta tsorata, mai gadi na tambayarta lafiya ko kallonsa bata yi ba ta fice ta shige gidan Hajiya Fatima, da gudu Mai gadin ya nufi entrance din gidan don ganin abinda ya faru.... Babu kowa parlon gidan, Jiddah ta xauna saman kujera a hankali tana bin parlon da kallo, lkci daya ta rufe fuskarta da kujera ta fashe da kuka a hankali, ji tayi ta gaji da komai na rayuwan, ta rasa me ke mata dadi, ta ma rasa wani tunanin xata yi, kuka tayi sosai a parlon daga karshe ta goge hawayenta a hankali ta jinginar da kanta da kujera tana tunanin rayuwarta, she wish she have another place to go apart from Umma's house, she wish tana da yan uwanta na jini da ta sani, she wish her father is alive today, kilan da gorin da xa a dinga yi mata bai kai haka ba, wasu hawayen masu xafi suka sauko idonta tunawa da maganganun da Abuturrab yayi mata daxu bata san hawa ba bata san sauka ba, Rahama ce ta shigo parlon daga kitchen, da mamaki ta tsaya take kallon Jiddah, tace "Aa Jiddah? Yaushe kika shigo?" Jiddah ta daga kai a hankali tana kallonta ta kasa ce mata komai, tace "Bari in sanar ma Hajiya" juyawa tayi ta koma sama ba a dau lkci ba sai ga ta ta dawo da mum dinta, Hajiya fatima na kallon Jiddah ganin hula ne kawai a kanta ga shi doguwar riga ta saka, ta nufota tace "Lafiya Jiddah? Daga ina haka?" Jiddah bata san sanda ta fashe da kuka ba cikin sanyin murya tace "Nemana take da fada mama" Hajiya Fatima tace "Ikon Allah, amma wannan yarinya dai ina ga ta hada iri da maguzawa, bata da mafada ne ko hankali ne kawai yayi gardama? ina shi mai gidan naku?" Cikin rawar murya Jiddah tace "Ya koma aiki" Hajiya Fatima tace "Wannan wace irin fitinanniya ce kuwa? Taso mu je sama, shi ma yasan mara tarbiyar da ya ajiye gida ya xa ayi ya dinga barin ku ku biyu kadai a gida? Haba wannan ai ba dubara bane, yaushe aka gama wancan case din ina jin ko sati ba ayi ba, shi tunaninsa bai basa cewar bai kamata ya bar ku a gida tare ba tunda yasan matar tasa yar tasha ce? Wani bala'i ne wannan ke cin ta kamar jahila?" Dago Jiddah Hajiya Fatima tayi ta wuce sama da ita xuwa parlonta, Rahama ta bi bayansu ita ma ta ji ranta ya baci sosai, tace "Yarinyar nan na bukatar wa enda xa su koya mata hankali wllh, tana bukatar a koya mata lesson, ita ko kunya bata ji ba da er cikinta take tashin hankali kullum? Ko dai bata da saiti ne?" Hajiya fatima ta xauna bayan ta xaunar da Jiddah saman kujera, Rahama ma ta xauna, duk ranta ya gama baci, cikin fada tace "Allah Mama wannan ba karamin issue bane wllh, ya kamata ayi masu iyaka me karfi ko kuma a raba masu gida kada wataran ta illata ta tun da ba sa'arta bace karfinsu ba daya ba, yanxu me ya hadaku?" Jiddah ta share hawayen dake xubo mata tace "Kawai na sauko kasa shine ta fara xagina har da iyayena tana dungurina, kuma take tambayata ko xan rama ne nace mata ai ni ba mahaukaciya bace shine fa ta mareni" Kuka sosai Jiddah take tana kallonsu, Rahama tace "Kan bala'i, ta mareki? Sai kika yi me?" A hankali tace "Ni kuma na dau vase na kwala mata a kai na fito" Rahama tace "Good!!! Dai dai kenan da fuskarta kika saita kika maka mata vase din a kai tunda ita yar matsiyata ce bata san mutunci ba, banda jahili wa ke irin wannan kishin en kauyen da take? Ai kai ya waye yanxu matured kishi ake na kwalliya da kamshi da iya tarairayan miji, sai kuma kayi takama da kwallinka, wa ke irin wannan kishin na hauka a yanzu dai? Aa wllh babu sai a kauye" Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "A wani anguwan iyayenki suke Jiddah?" Jiddah ta d'an yi shiru, lkci daya wasu sabbin hawayen suka kawo idonta ta ma rasa abinda xata ce, Hajiya Fatima tace "Ko ba a kaduna suke ba?" Hawaye na sauka idonta cikin sanyin murya tace "Iyayena duk sun rasu" Hajiya Fatima tace "Hasbunallah!!" Allah ubangiji ya gafarta masu yayi masu Rahama" A hankali Jiddah tace "Ameen" Hajiya Fatima tace "Toh ina relatives dinki kuma suke?" Jiddah ta goge idonta cike da karfin hali tace "Wajen stepmom dita na taso" Rahama sai kallon Jiddah cike da tausayinta cause ta yanda tayi maganar xaka san she is hurt, a hankali Hajiya Fatima tace "Toh dangin mahaifiyarki da Mahaifinki fa?" Jiddah ta kalleta, bata san sanda wani kuka ya taho mata ba ta fashe da kuka sosai tace "Ban san su, i only know my step mum, ita kawai na sani, wajenta na taso" Duk suka yi shiru suna kallonta cike da tausayi, Hajiya Fatima tace "Ina ita stepmom din taki take?" Cikin rauni Jiddah tace "Hayin rigasa" Hajiya fatima tace "A can din Aliyun ya auro ki?" Jiddah ta kasa ce mata komai hawaye wani na bin wani a idonta, Hajiya Fatima tace "Ki daina kukan nan kiyi min magana Jiddah" Tayi kokarin daina kukan da take, cikin sanyin murya tace "Ina yi mata awara a bakin titi ya gan ni, a hayin rigasa...." Daga Hajiya Fatima har 'er ta where a bit shock, don dai a class din Abuturrab da kyansa, da kudinsa, da kuma profession dinsa, infact Abuturrab bai yi kama da wanda xai yi stooping kansa that low ba at all, Rahama a ranta ta dinga tunani to kyanta ne ya tafi da shi, ko haskenta? Ko da yake babu yanda Allah baya ikonsa, l Hajiya Fatima tace "Ikon Allah, a can ya auro ki kenan?" Jiddah ta girgixa kai tace "Ya dai taimakeni, kuma ba wai don ya aureni ya taimake ni ba, ya taimakeni ne saboda halin da ya ga nake ciki wajen stepmom dita" Hajiya Fatima tace "Kamar yaya kenan?" Cikin sanyin murya Jiddah ta fara basu labarin tun daga farkon haduwarta da Abuturrab har xuwa yanxu da ya sake aurenta for the second time ya hadasu da Aneesah, Rahama dai sai hmm take cause she is speechless, Hajiya Fatima kuwa tagumi tayi tana ta kallon Jiddah don labarinta ya sanyaya mata jiki, wani tausayinta ta dinga ji har kasan ranta, Rahama ta kara sauke ajiyar xuciya for the third time sannan tace "Yanxu na gano dalilin da ya sa ta sako ki gaba, na farko tana ganin baki da kowa baki da wani me tsaya maki banda dangin Aliyun, ta yanda idan ta tafka tsiyarta a kanki sai ace family issue ne kamar yanda aka yi last week ta lalata maki furnitures, na biyu kuma tana ganin ke ba class din kishinta bane, ta raina wacece ke, ta raina personality dinki, tana ganin ta fi ki komai ta fi ki gata, but she is mistaken, she is deceiving her self don ko nayi rantsuwa baxan yi kaffara ba kin fita value a wajen mijinku from the way i saw things..." Hajiya Fatima da tayi nisa a tunanin da take ta kalli Jiddah bayan ta sauke ajiyar xuciya tace "Ina gidanku yake a hayi Jiddah?" A hankali Jiddah ta gaya mata, Hajiya Fatima tace "Tashi ki sauka downstairs akwai breakfast a dining ki deba ki karya tukun" Jiddah ta mike a hankali ta juya ta fita daga parlon duk suka bi ta da kallo, Rahama tace "Mama don Allah kar ma ki nuna tana gidan nan, ki bar ta tayi xamanta a nan ta samu nutsuwa, kalli fa duk a firgice take kana ganinta kasan bata da rest of mind a gidan miji? For what reason? She is too young to be experiencing this bull shit, Wllh kawai don kin hanani shiga abinda babu ruwana ne banda haka sai na nuna ma kishiyarta karamin hauka take, Allah sai na rama mata marin" Hajiya Fatima tace "Aa bbu ruwanki, ki bar komai a hannu na kawai..." Rahama tace "Allah ya sa mai gadinsu bai ga shigowarta nan ba, a barta ta huta na kwana biyu wllh, shi ma banda dama ya so a cuceta ne ai yasan mahaukaciya ya ajiye a gida, ta yaya xai tafi ya barsu su biyu kadai, wato ya ba kura nama kenan, ko kanninsa baxai kawo gidan ba su xauna saboda Jiddan, haba tayi kankanta da yawa da fara fuskarta matsalan gidan aure, kamarta yanxu ai ya kamata ace karatu take ba wai facing marital crisis ba, gaskiya banji dadin wannan labarin ba, na tsani in ga ana walakanta 'ya mace, macen ma karama, idan bata samu kwanciyar hankali a gidan aure ba albarkacin shekarunta ai baxa a dinga musguna mata haka ba, no plss this is too bad..." Hajiya Fatima tace "Ke wannan ne ya fi damunki, ni damuwata ta yaya xa ace mutum bashi da dangin uwa bashi da dangin uba kamar daga sama ya fado? Ai idan tana son samun 'yan cin kanta dole sai ta san su waye danginta, idan ba haka ba no matter kwanciyar hankalin da xata samu dole sai an mata gorin dangi, kishiyarta baxata ta6a daina mata wannan gorin ba, kai har shi wataran wllh sai ya mata gori, ki kyale maxan nan kawai" Rahama tace "Gaskiya ne kuma, to yanxu ya xa ayi kenan mama?" Tace "Ni nasan yanda xanyi in sha Allah" Aneesah na xaune parlor da kawayenta su hudu tun bayan da ta kirasu ta sanar masu abinda ya faru suka yo xuga xuwa gidan, labarin yanda captain ya ji da ita daren jiya ta dinga basu, da irin yanda suka rabu yau da asuba, Fauziyya da Rabi'ah suka yi wani shewa suka ce "Gaba da gabanta, ba kin tsaya sanya ba da, kin xauna kina ta hauka da fashe fashe da dambe a asibiti, to ai yanxu kin fara ganin aiki da cikawa" ita dai sai wani blushing take, Wayarta ne ya fara ring tayi masu alama duk suyi shiru daga surutun da suke, lkci daya suka yi tsit, ta daga ta kai kunne a hankali ta rausaya murya tace "My Captain" Yace "How are you feeling?" Tayi fari da ido tace "Alhmdlh, da sauki, sai dai ciwon kan ne kawai bai tafi gaba daya ba" Yace "Toh Allah ya kara lafiya" Tana wani murmushi tace "Ameen, na ga sakon da ka turo daxu, nagode My captain" yace "You are wlcm" tace "Kana lagos ne?" Yace "Yeah... Kai ma Jiddah waya" Ta d'an yatsine fuska tace "Ai kam daxu na ga ta shirya ta ci kwalliya ta fita, bata ce min komai ba nima ban ce mata ba gaskiya, don abinda ta min jiya yayi min ciwo" Yace "Ta fita?? To where?" Tace "Aa ban sani ba karya haramun, na dai ji tana waya wai ga ta nan fitowa yanxun nan, har nake tunanin ashe tana da waya don ni ban ta6a ganinta da waya ba sai yau" Shiru yayi bayan few seconds yace "Sai anjima" Tace "Alright my captain" Daga haka ya katse wayar, ta fashe da dariya tana kallon kawayenta da suka hau hailing dinta, tayi kasa da murya tace "Kun ga anjima sai in ce masa an kawota an ajiye a mota naje raka Rabi'ah da ta xo dubani na gani da idona" Abuturrab na gama waya da Aneesah ya shiga kiran Maimoon, Maimoon na dagawa bayan ta gaishesa yace "Kina ina?" Tana magana kasa kasa tace "Islamiyya" Katse wayar yayi, ya ma rasa tunanin da xai yi, sai kuma ya hau kiran Umma, bayan sun gaisa tace "Ya su Jiddah?" He was short of word at first, sai kuma yace "Alhmdlh Umma" Tace "Ahmad ya gaya maka sun koma makaranta ko bai gaya maka ba" Yace "Ya gaya min" Tace "Toh yayi kyau" sallama yayi mata yace "Dama na kira ne in gaisheku" Tace "To madallah, Allah yayi albarka" ya amsa da Ameen ya katse wayar, Ummi ya kira nan ma sai da ta tambayesa Jiddah da Aneesah hakan ya nuna masa Jiddah bata gidan, yayi mata sallama ya katse wayar.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp[8/7, 9:36 PM] Ummuanwar🥰: Aneesah na ta shiryawa a dakinta bayan magariba, ta dau duk wani abinda ta san xata bukata a er jakarta bata da yanda xata yi ne kawai amma yau kam bata yi niyyar fitar ba ma, wayarta ne ya fara ring, ta xaro ido ganin Abuturrab ne ke kiranta, ta dauka ta xauna gefen gado tayi kasa da murya tace "Hello my Captain" Yace "How are u doing?" Ta langwabar da murya tace "Alhmdlh wllh" yace "Ya jikin?" Tace "Aa naji sauki Alhamdulillah yanxu" Yace "Ohk, ta dawo gidan?" Tace "Ehh fa, Rabi'ah just left few minutes ago na fita in rakata motarta naga ita kuma an dawo da ita ta sauka daga wata mota" Yace "Motar??" Tace "That was what i saw, dama da baka tambaya ba ba ruwana ai tunda ban san wa ya sauketa ba, xai yiwu ko d'an uwansu ne" Yayi shirun kusan second ashirin, har sai da tace "Hello" Yace "Alright, sai mun yi magana" Tace "Ohk my captain" Katse wayar tayi, ta ajiye tayi shiru, anya ya kamata ta fita yau kuwa, kar ta fita ya dawo unexpected fah, but his schedules tomorrow are so tight don karfe bakwai da rabi take jin xa su yi piloting xuwa lagos, tana ta tunane tunane wayarta ya fara ring kuma, ta duba da sauri taga shi ne, ta daga ta kai kunne tace "Hello my Captain" Yace "Can u pls go give her d phone?" Sosai hankalinta ya d'an kwanta, which means baxai dawo din ba kenan, mikewa tayi sai kuma ta tuna fa bata ji shigowar Jiddah ba har yanxu, har kawayenta suka gama jiranta suka bar gidan bata dawo ba, kilan ma gidan Umma ta tafi, da sauri tace "Kana ganin babu matsala captain, kar in kai mata kuma fa ta xageni, kaga ni bana son fitina wllh" Yace "Ki kai mata" mikewa tayi tace "Toh" daga haka ta fita daga dakin ta nufi dakin Jiddah ta bude kofar a hankali ta leka ciki taga babu ita babu alamarta, kulle kofar tayi ta fara knocking ta yanda xai ji... tana cewa "Assalamualaikum, Jiddah xa ayi maki magana a waya, Jiddah, Jiddah..." Ta kira sunanta yayi sau biyar, sai kuma ta juya tace "Ka dai ga... Tana ji wllh taki cewa komai Captain, kofar ma ta sa key" Yace "Ohk, sai da safe" Tace "Toh Allah ya kai mu captain, goben xaka dawo ne?" Yace "No, sai friday da safe in sha Allah, i will be piloting all throughout" Tace "Toh shkkn Captain Allah ya kai mu Friday din, Allah ya tsare min kai, sai mun yi magana gobe" Yace "Ameen... In sha Allah" Daga haka ya katse wayar, tayi wani murmushi tana jujjuya wayar hannunta ta koma dakinta ta karasa shirinta a hanxarce, wardrobe dinta inda take ajiye bedsheets ta bude ta daga squeezed bedsheeta din nata ta dau wani sealed abu a leda ta cusa cikin handbag din nata, tana ganin xanuwan gadon suka xubo kasa ko bin ta kansu bata yi ba ta dau Hijab dogo ta saka ta boye handbag din ta cikin hijab din ta bude dakin ta fito ta kulle da makulli ta sauka downstairs, ta daga wayarta da ya fara ring tace "Gani nan tahowa na fito yanxu" daga haka ta katse wayar ta fito compound, sosai taji dadin ganin mai gadi yana sallah a compound din yayi backing dinta, ta lallaba tana tafiya a hankali ta nufi gate, ta bude ta fice daga gidan. Jiddah na xaune parlon Hajiya Fatima sanye da Hijab din Khaleesat, Hajiya Fatima ta gama waya da mai gidanta da baya kasar bayan ta nemi izininsa na cewa xata fita, ajiye wayar tayi ta kalli er ta Rahama tace "Toh yanxu ita haka xa a fita da ita babu izinin shi mijin nata?" Aunty Rahama tace "Atohh ai komai kamawa yake Mama, ba kuma fitar shiririta xa ayi ba, da ma dai ana son yasan tana nan ne sai ki amshi numbersa a wajenta ki kirasa, amma ni wllh bana son ma yasan tana gidan nan" Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh ko dai a amshi number tasa a wajenta sai a kirasa kar ma aje ayi ta nemanta mun ajiyeta a nan" Aunty Rahama tace "Mama don Allah mu je mu dawo, ayi ta nemanta din, yasan baya son ya nemeta me yasa xai barta da wnn rikakkiyar matar su biyu kadai a gida, ai shima yayi kuskure wllh, bai yi tunanin abinda xai je ya dawo ba" Mikewa tayi ya fita, mahaifiyarta ta bi bayanta, Jiddah dai kanta na kasa, Hajiya Fatima tace "Kina da number Aliyun ai ko?" Jiddah ta girgixa kai tace "Aa bani da shi" Tace "Toh tashi mu je" Mikewa tayi ta nufi kofa suka bi bayanta, Aliyu dake xaune parlor yana jiran fitowarsu tun daxu ya mike ya fita yana rike da makullin motarsa, Jiddah da Hajiya Fatima suka xauna back seat, Aunty Rahama kuma ta xauna a gaba, cikin minti ashirin suka isa hayin rigasa, Jiddah ta nuna masu hanyar gidan nasu, bayan Aliyu yayi parking ya juya yana kallon Mum dinsa, Hajiya Fatima na kallon Jiddah tace "Xa mu shiga ciki ke ki xauna a mota kin ji" a hankali Jiddah tace "Toh" Duk suka sauka motar har Aliyu suka bar ta ita kadai, Aunty Rahama ce tayi sallama kofar xauren gidan, wani d'an tsoho ya fito yana kallonsu yace "Wa ku ke nema?" Hajiya Fatima ta gaishesa tace "Sannu baba, matar gidan fa?" Ya d'an buda ido yace "Wai matata?" Sake lekowa waje yayi yana xaro ido ganin katuwar motar dake parke a firgice yace "Bayin Allah lafiya kuwa?" Hajiya Fatima tayi murmushi tace "lafiya lau baba, kar ka wani samu damuwa" Tsohon da ya ji hankalinsa ya kwanta yace "Toh bari ayi kiranta..." Juyawa yayi ya koma ciki sai gasu sun dawo tare da matar tasa, ita ma a tsorace take kallonsu tace "Lafiya??" cikin kwantar da murya Hajiya Fatima tace "Ba ke ce Malama Hafsatu ba" Da sauri matar tace "Aa bani bace ba wllh...." Tsohon yace "Hajiya siyan gidan muka yi, ko wata uku bamu yi da dawowa nan ba..." Matar tace "Kuma tunda muka dawo nan yan bashi ke xuwa neman matar nan da kika ambata, kusan kullum sai an xo mana nan... idan ku ma bashin ya kawo ku to kuwa ance bata ma garin ta gudu, ta cinye ma jama'a kudi ta tsere" Hajiya Fatima tace "Hasbunallah, yanxu bata garin nan kuma?" Matar ta tafe hannu tace "Wllh kuwa, wannan gidan ma da ta siyar ance ko dubu hamsin bata tsira da shi ba sbda duk bashin lapo ta biya, kuma har yanxu da nake maki wannan magana mutane sun fi ashirin da take bi bashi a hayin nan, ta tsallake kawai ta bar garin, an dai ce hakkin er marigayin mijinta ke bibiyarta, mu ma haka muka ji, wllh babu wanda yasan inda take" Hajiya Fatima tace "Toh Allah ya kiyaye Allah ya kyauta" Suka amsa da "Ameen" Hajiya Fatima da su Aunty Rahama suka juya suka koma gun motarsu, Jiddah dake cikin motar sai kallon wasu mutane da suka fito daga gidansu a maimakon babarta da Bibalo take, nan da nan taji gabanta ya fadi, Hajiya Fatima ta bude bayan motar tana kallonta, sai kuma tayi kasa da murya tace "Babu wani naku a unguwar nan bayan stepmum din taki Jiddah?" A sanyaye Jiddah tace "Basa gidan kuma ko Mama?" Hajiya Fatima tayi shiru tana kallonta, sai kuma a hankali tace "Ta siyar da gidan, ta bar garin" Jiddah bata san lkcn da ta fashe da kuka ba, Hajiya Fatima ta hade rai tace "Meye haka kuma? Meye na kuka? Kukan naki ne xai dawo da ita" Jiddah ta girgixa mata kai tana share idonta wasu hawayen na xubo mata tana tausayin rayuwarta kuma, Hajiya Fatima da duk jikinta yayi sanyi tace "Wa kike tunanin a unguwar nan gaba daya xai iya sanin inda ta tafi ko inda ta koma?" Jiddah na share idonta da kyar tace "Kila Iyah, ga gidanta can" Hajiya Fatima ta sa ta sauko daga motar suka nufi gidan Iyah gaba dayansu, banda Aliyu dake jingine jikin motarsa, sosai shi ma yake tausayin Jiddah... her story is heartbreaking, no relatives, no siblings, no parent, nothing nothing, what a life, Jiddah ta rungume Iyah bayan sun shiga gidan, Iyah ta kasa boye farin cikinta ta rasa inda xata sa Jiddah tsabar murnan ganinta sai ta fara hawaye, Hajiya Fatima dai kallonsu kawai take tana tsaye daga gefe da Aunty Rahama, Iyah ta farga da su ta dauko tabarma da sauri bakinta har kunne ta shimfida masu tace "Sannunku da xuwa, kun xo bamu da wutan nepa, fitina kuma batur yayi sanyi, ku xauna don Allah" Hajiya Fatima ta xauna, Aunty Rahama ma ta xauna sannan suka kara gaisawa, Iyah na kallon Jiddah dake xaune ita ma tayi nisa tunanin da take tace "Jiddah Hansai dai ta siyar da gida ta bar garin..." Jiddah ta sauke idonta kasa wasu hawayen na taruwa idonta, A Hankali Hajiya Fatima tace "Haka muka samu labari kaka, domin can muka fara xuwa kafin nan, yanxu kaka baki da masaniyar inda ta koma" Iyah tace "Ai babu wanda yasan inda wannan mata dai ta koma, duniya tayi mata xafi, kowa ya juya mata baya, er ta kuma Bibalo ta dauko mata abun kunya, ko kafin su bar anguwan nan bibalo Haihuwa yau ko gobe, abun dai babu dadin fadi, Hansai na cikin gararin rayuwa yanxu..." Hajiya Fatima tace "Ya salam, Allah ubangiji ya bamu dacewa..." Iyah tace "Ameen, alhakin Jiddah kadai ya isa hanata xaman lafiya a duniya duk inda xata je kuwa, haba ai Allah ba axxalumin bawansa bane, ta xalunci yar nan da kike gani, ta xalunci uwarta... Duniya kam ta juya ma Hansai baya, ita kanta kawarta me xuxxugata tana can ciwon kafa ya sa ta gaba ana tunanin yanke kafar ma xa ayi, bata iya xuwa ko ina, Zulai ba" Jiddah dai sai kallon Iyah take hawaye na sauka idonta, Hajiya Fatima tace "Toh ita zulan yanxu bata san inda Hansatun take ba?" Iyah tace "To sai dai ko gobe in shirya inje in jiyo maku, amma babu tabbas ta sani, in sha Allah ni dai xan je" Hajiya Fatima tace "Mun ko gode kaka Allah ya kara girma" Dubu uku Hajiya Fatima ta ajiye ma Iyah daga haka suka yi mata sallama da xummar gobe xa su dawo su ji yanda suka yi da Zulai a kan whereabout din Hansai, har suka koma gida Jiddah jikinta a sanyaye yake sai goge hawaye take a idonta, Hajiya fatima ta sa yayar Khaleesat ta kawo mata dinner don bata ci ba kafin su fita. Karfe tara da yan mintuna that same day Abuturrab yayi horn bakin gate din gidansa, Mai gadi ya taso da sauri ya bude masa gate din ya shiga yayi parking sannan ya sauka, gaba daya a gajiye yake, kwanan nan stressing kansa yake sosai na kai wa da komowa da yake xuwa kaduna, ya shiga ciki yana jin shoulders dinsa na ciwo saboda driving da yayi, sama ya tafi ya bude kofar dakin Jiddah ya shiga ciki, ya dinga bin dakin da kallo kafin ya juya ya fita, dakin Aneesah ya nufa ya murda kofar ya ji sa a kulle, mamaki ne ya cikasa, ya tafi bangarensa ya xauna, bayan minti sha biyar ya mike ya sake komawa dakin Jiddah don a tunaninsa daxu tana bathroom ne, ganin har sannan bata cikin dakin ya karasa ya tura kofar bayin yaga wayam babu kowa ciki, juyawa yayi ya sauka kasa da mamaki, ya shiga kitchen yaga babu kowa ciki nan ma, ya fito yana bin parlon da kallo cike da surprise, Ya kalli agogo dake nuna goma saura ya nufi kofa ya fita, gun mai gadi ya tafi mai gadin ya taso da sauri ya sake gaishesa, bai damu ya amsa ba yace "Babu kowa gidan... Da yaushe suka fita?" Mai gadin yace "Toh ita dai Hajiya daxun nan bayan magriba ina sallah naga fitarta, ita Hajiya karama kuma gaskiya tun da safe naga fitowarta kamar da matsala don hankalinta ma baya jikinta ta fito, ina tambayarta lafiya ma bata saurareni ba ta fita gate, sai na tafi da sauri in ga meke faruwa, to ni dai ban ga kowa a parlon ba ma" Abuturrab ya rasa ma exactly tunanin da xai yi ya dinga kallon mai gadin xuciyarsa na bugawa, juyawa yayi da sauri ya koma ciki ya dau wayarsa ya shiga kiran Maimoon tana dagawa yace "Jiddah tana gidanku ne?" Maimoon tace "Jiddah kuma? Aa yaya bata nan, lafiya?" Strictly yace "I am not joking" Tace "Wllh Allah bata nan yaya" he was shock at that, yace "Look, bance kice da Umma komai ba" Daga haka ya katse wayarsa ya kira Nafisah ita ma tambayar da yayi mata kenan tace bata xo ba, lkci daya ya ji hankalinsa yayi mugun tashi, ya juya da sauri ya fita ya koma gun mai gadi yace "Ita warce ta fita da safen ina kaga ta nufa?" Mai gadin yace "Yallabai ai ina ganin yanda ta fito kamar da matsala cikin gidan sai na yi cikin gidan da sauri, wllh ban san inda tayi ba, kuma ko da na fito babu alamarta" Abuturrab ya ji wani xufa na keto masa duk da yanda garin yayi sanyi don da akwai hadari, he was shock, a xuciyarsa ya dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ya nufi gate ya fice daga gidan direct ya tafi gidan Hajiya Fatima.... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp [8/8, 9:43 AM] Ummuanwar🥰: Abuturrab na shiga compound din gidan ya tafi entrance din parlon yayi knocking, he is just trying his very best to be calm, mai aikin gidan ta bude kofar, ta gaishesa bai amsa ba yace "Mama na ciki?" Tace "Eh Bismillah" shiga parlon yayi ya xauna saman kujera, sosai ya ji kansa ya masa nauyi dama ga gajiyar da yake tare da shi, Mai aikin ta tafi dakin Hajiya Fatima, bayan kusan minti biyar Hajiya Fatima ta fito parlon ganinsa tace "Aa, ashe kai ne, welcome son" Ya daga kai ya kalleta ya kasa cewa komai, ta xauna saman kujera cikin sanyin murya yace "Ina yini Mama?" Tace "Lafiya lau, ya su Jiddah da abokiyar xamanta" Bai san lkcn da ya kara gyara xama ba xuciyarsa na bugawa yace "Mama Jiddah bata shigo nan ba?" Hajiya Fatima tace "Jiddah kuma? Tace maka xata shigo nan ne?" Rike kansa yayi ya kasa bata amsa, ita dai sai kallonsa take, can tace "Aliyu" ya dago da kyar ya kalleta tace "Ina Jiddar tace maka xata je?" Cike da confusion yace "Mama daga wajen aiki nake yanxu haka... I have to drive all the way from Abuja after piloting d whole day..." Rasa ma takamaiman abinda xai ce mata yayi, sai kuma ya dafe kansa yace "Ban san inda ta je ba, ban san me ya faru ba, i called home duk ance bata je can ba, bata da wajen xuwa kuma da ya wuce can..." Mikewa yayi ganin he is just sounding foolish, ba abinda ya ke fada da yake making sense, bata lkci kawai yake karawa gashi dare yayi, to shi a ina xai ga Jiddah? Ina Jiddah ta je? He felt like he is going to collapse, lamarin yayi ma xuciyarsa nauyi, ya rasa exactly tunanin inda Jiddah xata je da xai yi, is this really happening, gaba daya ya ma mance batun Aneesah ma bai ganta a gida ba, gathering much courage yace "Sai da safe Mama, dama na xata nan ta shigo" Juyawa yayi yana jin kafafuwansa sun masa nauyi ya nufi kofa, tace "Aliyu" ya juyo ya kalleta, tace "Me yasa xaka bar Jiddah da matarka kadai a gida bayan kasan halin wannan ita matar taka?" Dawowa yayi da sauri xuciyarsa na bugawa, tace "Why Aliyu?" Ya marairaice mata yace "Mama ta shigo nan ne? Wllh ban san abinda ya faru ba, daga Abuja nake few minutes ago ban tadda kowa a gidan ba" Hajiya Fatima tace "Tashin hankali Abokiyar xamanta ta nemeta da shi shine ya shigo nan, don ko takalmi balle mayafi babu a jikinta ta shigo gidan nan" Abuturrab ya buda ido sosai yana kallonta so speechless, Ta girgixa kai tace "Sakacin yayi yawa Aliyu, ganganci ne barinsu su biyu kadai a gidan nan, a da ni banyi niyyar nuna maka Jiddah tana nan ba sbda naga kamar u are not ready to take any action, it's not as if i am trying to intrude into ur privacy amma naga bai kamata in xuba ido ba a matsayina na babba, ba wai ina maku shisshigi bane amma lamarin abun dubawa ne kada wataran ayi kisan kai" Ya duka gabanta without knowing he did so yace "Don Allah yanxu tana cikin gidan nan Mama?" Hajiya Fatima tace "Tana nan" Mikewa tayi ya bi ta da kallo har ta wuce ciki, ya sauke wani irin ajiyar xuciya ya rufe idonsa sai dai har yanxu xuciyarsa bai dawo dai dai ba, bayan kusan minti hudu Hajiya Fatima ta shigo parlon tare da Jiddah dake biye da ita a baya, Jiddah na hada ido da Abuturrab dake kallonta ko kiftawa babu ta sunkuyar da kai fuskarta babu walwala, Sounding so grateful yace "Nagode Mama Allah ya kara girma..." Tace "Aa ba ka gode ba, so kake matarka ta kasheta ne ko kuwa kana da wata manufarka daban na barinsu a gida daya?" Ya marairaice mata yace "Not at all Mama..." Tace "Toh tashi ka dau matarka ku tafi, xa mu yi magana gobe" Godiya ya dinga yi mata kamar warce tayi masa albishir da aljanna, infact shi tunda yake bai ta6a yi ma mutum irin godiyan nan da yake mata ba, sai taji ya bata tausayi kana ganinsa kasan matan nan nasa suna basa tension, Hajiya Fatima tace "Ku tafi Jiddah sai da safe, xan shigo in sha Allah da safen" Mikewa Abuturrab yayi yana kallon Jiddah da taki yarda ta hada ido da shi, babu yanda ta iya haka ta bi bayansa tana jin kamar ta fashe da kuka har ranta taji bata son xaman gidan, duk da yayyafin da aka fara, haka suka fito compound din ya kama hannunta kamar xa a kwace masa ita suka fita gidan sannan suka shiga nasu, suna shiga parlor ya kulle kofar ya rungumota jikinsa gam, ya runtse ido da damuwa yace "Me yasa kike bani wahala haka Jiddah, me yasa kike sa min ciwon xuciya? Kince ban maki komai ba duk xaman mu na farko balle ko ince ramawa kike yanxu, why are u giving me heart attack jiddah, tell me pls wife, kin ki barin in nutsu in yi aikina, so kike a bani query Jiddah? Do u want me to lose my job?" Tayi shiru tana jin yanda xuciyarsa ke bugawa, ga kamshinsa da ya cikata, lumshe ido tayi ita ma xuciyarta na bugawa, ya dago kanta a hankali yace "Me ya faru kika fita gida just like that? tell me plss" Hawaye ya kawo idonta a hankali tace "Nemana take da fada a ko da yaushe" yace "Me ta maki? Tell me" Cikin sanyin murya tace "Daxu da safe na sakko xan shiga kitchen shine ta xageni ta xagi iyayena, kuma har da marina" Ta fashe masa da kuka, lkci daya mood dinsa ya koma na bacin rai karara, yace "Ta mareki?" Cikin kuka tace "Ehh shine ni kuma ta kwala mata wancan vase din na fita parlon" Ya rungumeta bai ce komai ba yana tunani iri iri a ransa, hannunta ya kama suka wuce sama, ya tafi bangarensa ya dau wayarsa ya shiga bedroom dinsa ya dau spare key sannan ya fita, Jiddah dai na tsaye parlonsa ta bi sa da kallo har ya fita, ta xauna a hankali gefen kujera, bude kofar dakin Aneesah yayi yana kokarin dialing numberta, har ya katse mata daga ba, ya sake kira yana bin dakin nata da kallo, dagawa aka yi daga daya bangaren, murya kasa kasa tace "Hello my Captain" Yace "How are you?" Tace "Lafiya lau My captain, are u missing me this much?" Yace "Ya jikin yanxu?" Tace "Yanxu na sha magunguna na na kwanta har na fara bacci kiranka ya tasheni" Yace "Ohk kina daki ne?" Tace "Ehh wllh, ina daki a kwance" yace "Ohk can u go give Jiddah the phone plss?" Tace "Why not my captain, Allah ya sa ta karba din, bari in kai mata" Shiru yayi bayan wani lkci yaji tana cewa "Assalamualaikum, Jiddah, Jiddah..." Sai kuma tace "Ohh kofar ma a bude take ashe, bari in Shiga" Shi dai yayi shiru yana sauraronta xuciyarsa na throbbing, ya ji tace "Captain bata ciki fa, na duba bathroom ma ban ganta ba, let me check downstairs" Ya dake yace "Ohk" again bayan wani lkci tace "Bata nan wllh captain, and I can't even see her shoes da ta bari bakin kofa daxu da ta shigo, probably taje siyo abu ne a waje" yace "Ohk, gobe da safe xan dawo in sha Allah" Tace "Toh Allah ya kai mu my captain" Katse wayar yayi ya xauna gefen gado yana jin wani mugun bugawa da xuciyarsa ke yi, is this for real? Wait ina ma ta tafi tukun? Bai san sanda ya bude baki ba mamaki kaff ya gama cikasa, sai yake ganin abun kamar film, Aneesah?? Ya kara bin dakin nata da kallo ya kalli xanuwan gadon da suke xube a kasa, mikewa yayi ganin sachet kusan hudu dake xube daga gefen xanin gadon ya karasa ya durkusa ya dauka yana dubawa, sai dai xuciyarsa ya daina aiki na kusan second biyar, ya dinga kallon sachet din babu ko kiftawa da wani expression da ya fi kama da na shock, juyasu ya dinga yi yana kallonsu kamar idanuwansa xa su fito, lkci daya ya runtse ido ya nufi kofa ya fice daga dakin ya tafi bangarensa, bai ga Jiddah a nan ba ya shige bedroom ya kwanta jin kamar sanyi yake ji, ya fi minti ashirin a haka duk jikinsa yayi wani irin sanyi, he is really shocked, ruwa ya sauka sosai, can yayi karfin halin tashi ya tafi bandaki ya hada ruwan dumi yayi wanka ya fito, yana ta xaune gefen gadonsa yayi wannan tunanin yayi wancan tunanin, can ya mike da kyar wearing just his short nd singlet ya fita dakin, dakin Jiddah ya tafi ya kunna wutan dakin ya ganta kwance ta rufa da duvet, idonta biyu kuma ba bacci take ba, ita duk tunaninta wajen Aneesah ya tafi ya bar ta xaune parlonsa kawai, ya kashe wutan a hankali ya tafi kusa da ita ya cire duvet din gently ya kwanta drawing her closer to him ya juyo da ita, underneath his breathe yace My Precious Gift... Ta ki bude idonta tana sauke numfashi a hankali.... Da asuba Abuturrab na dawowa masallaci ya xauna downstairs ya jinginar da kansa a hankali jikin kujera ya rufe ido, gaba daya ya rasa me ke masa dadi, upon how sweet the night was to him bai yi wani baccin kirki ba, he was disturb all through, and he is still finding it hard to believe Aneesah bata kwana cikin gidan nan ba, yana ta xaune parlor har bakwai saura sannan ya mike da kyar ya haura sama yana jin kansa na sara masa, bude kofar dakin Jiddah yayi ya sameta ta koma bacci bayan ta idar da sallah, ya nufeta ya lulluba mata duvet a hankali yana kallon innocent face dinta, ya daura lips dinsa a nata ya lumshe ido, sai kuma ya mike ya fita, gently ya kullo kofar don ya san she really need the sleep, ya tafi parlonsa ya xauna ya rike kansa yana jin damuwa a ransa, sai kuma ya jawo wayarsa ya shiga dialing number Aneesah, har ya katse bata daga ba, ya kuma kiranta sai ta daga cikin muryan bacci tace "Hello my Captain" Yace "How was ur night?" Tace "Alhmdlh, are u still coming back today?" Yace "Yeah at 10" tace "Alright dear Allah ya kai mu, hope u slept fine?" Yace "Yeah, can u pls take ur phone to Jiddah?" Ta wani shagwabe tace "Captain naga kamar fa ba don ni kake yawan kiran nan ba, kawai kai dai kira kake saboda matarka, banda haka ni a rana daya ma a ina nake ganin call dinka, i assume this call isn't for me" Yace "Aa ba haka bane...." Ta katse sa tace "Alright, i will go give her d phone now, I was only joking my captain" Yace "Ohk" yana ta sauraronta har bayan minti biyu ta fara knocking tana kiran sunan Jiddah, sai kuma tace "Captain bata ciki fa? It seems bata dawo jiya ba" Yace "Bata dawo jiya ba?" Tace "Wllh, her door is open and the room is still d way it was yesterday da kace in kai mata waya, bari in sauka kasa" Ya kasa ce mata komai wani axababben mamaki ya cikasa, bayan few seconds tace "Bata dawo ba kam Captain" A hankali yace "Alright, sai anjima" Tace "Ohk my Captain, i love you" a hankali yace "Same" sannan yyi maza ya katse wayar ya rike kansa da yayi masa wani nauyin bala'i yana jin xuciyarsa na wani tafarfasa, lkci daya ya mike ya tafi gaban mirror dinsa ya bude yana kallon abubuwan da ya kwaso a dakinta jiya bbu ko kiftawa, xaunawa yayi gefen gado ya kara dafe kansa maganganun Ahmad na dawo masa tiryan tiryan. Karfe takwas Jiddah ta farka ta bi dakin da kallo, da sauri ta mike xaune har xata shiga bandaki ta tuna tayi wanka tayi komai da asuba, ta tashi ta dau hularta ta saka sannan ta fita dakin ta sauka downstairs tana tafiya a hankali ta wuce kitchen, tunanin abinda xata yi for breakfast ta shiga yi, can dai ta fara wanke few plates din dake kitchen din da Aneesah ta bari, sannan ta gyara kitchen din tsaf ta daura ruwan shayi, ta fara fereye doya... Karfe tara da few minutes ta fito da breakfast din parlor ta durkusa ta ajiye saman carpet, dai dai nan aka bude kofar parlon ta daga kai da sauri. Aneesah ce ta shigo parlon ta kulle kofa tana kallon Jiddah daga sama har kasa kallon rigima, Jiddah ta dauke kanta ta mike tsaye, Aneesah ta cire takalmanta ta jefar da jakanta saman kujera tace "Kin gama guje gujen naki kin dawo??" Jiddah ta ki tanka ta, Tana tafe hannu cikin daga murya tace "Toh gobe ko kallon banxa aka ce ki min wllh sae kin zagi wanda ya baki wannan shawaran, don yau sai naga d'an kuturin uban da ya tsaya maki a garin kaduna, ba dai ni kika kwala ma vase kika fita a guje ba...." Jiddah ta bar wajen da sauri ganin ta nufota fiercely, ganin da gaske take sae xaga parlon suke ta kwala wani kara da karfi gabanta na faduwa, Aneesah tayi wani kukan kura ta cafkota ta sa ta a hammata ta shake wuyarta, Jiddah dae sae ihu take da karfi tana kokarin kwace kanta, ko gama buttoning shirt dinsa bai yi ba yake saukowa stairs da saurin sa, still Aneesah tayi tana kallonsa baki bude, kamar ranan ta fara ganinsa, Jiddah ta fashe da wani kuka ta xube nan kasa, ya shigo parlon walking faster, Aneesah bakinta na rawa tace "Ca.. Captain yaushe ka shigo..." Bata rufe baki ba ya kifa mata wani mari, without letting her to recover ya kuma sauke mata wani ya shako wuyarta, ta gwalo idanuwa cike da axaba ihun ma ta kasa, ya turata da karfi har sae da ta xube kasa, da hannu bibbiyu ta dafe kuncinta bayan ta fadi kasa, ya daga Jiddah ya wuce sama da ita, Aneesah ta kasa kwakkwaran motsi a inda take tsaye ta bi su da kallo, ita ba ma ta marin da shakan da yyi mata take ba, kawai so take ta ji sanda ya dawo gidan, da sauri ta nufi kofa kamar mahaukaciya xuciyarta na wani irin bugawa ta nufi mai gadi, tasowa yayi... tana kokarin calming kanta tace "Salisu yaushe mai gidan ya shigo? Yaushe ya dawo???" Yace "Tun jiya bayan magariba Hajiya" Bata san sanda ta furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un da karfi ba, taji cikinta ya hautsine, da sauri ta juya xata koma ciki sae a sannan ta lura da motar Jiddah a parking space don da ta shigo bata lura ba, shi dai ya bi ta da kallo ya girgixa kai kawai ya koma ya xauna, gaba daya hankalin Aneesah yyi mugu mugun tashi, bata ta6a shiga tashin hankali irin na wannan moment din ba, ta ma rasa wani kalan tunanin xata yi, jikinta na rawa ta dau handbag dinta ta haura sama da gudu ta bude zip ta ciro makulli xata saka taga makulli jikin kofar already, all her body was shaking, ta murda kofar ta ji a bude, ta jefar da jakanta kan gado ta shige bandaki a guje, sae da tayi minti goma sannan ta fito har sannan jikinta rawa yake, ta kalli xannuwan gadon dake xube a kasa, ko ta kansu bata bi ba ta ciro wayarta ta shiga kiran Rabi'ah, tana dagawa ta sakar mata kuka tace "Rabi'ah wllh na dawo na tadda captain a gida, kuma a gidan ya kwana Rabi'ah, Rabi'ah am i not done today???" Rabi'ah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ya dawo??" Aneesha ta kara fashewa da matsanancin kuka tace "Na shiga uku na Rabi'ah, na shiga uku na lalace, yanxu me xance masa, ta ina xan fara? What will i tell him, ki gaya min don Allah Rabi, ina xance masa na kwana??" Kuka take kamar xata haukace, Rabi'ah tace "Tabdi, kawai kice masa daga gidana kike, to me xaki ce da ya wuce haka?" Aneesah jikinta sai rawa yake tace "No Rabi'ah baki san waye captain ba, jiya fa mun ta waya da shi da daddare a sunan Ina gida, ashe yana gidan muke ta wayar" Xubewa kasa tayi tana kuka da karfi tana cewa ta shiga uku, Rabi'ah tace "Atoh tunda uwarsa shegen saukin kai gareta kawai kiranta xakiyi ku hada baki kice ta rufa maki asiri tace daga can kike, a can kika kwana, ko kuma ki fito kawai yanxu mu je mu sameta a gida sai ince mata wllh gidana kika kwana baki da lafiya sosai, nasan dai baxai wuce tayi ta fada ba kamar rubabbiya daga nan sai kuma a wuce wajen ta samar maki mafita" Aneesah dai hawaye take tana naxarin shawaran Rabi'ah gaba daya she is just confuse and afraid, bata son wani abu da xai yi sanadin captain ya rabu da ita, baxata ta6a rayuwa babu shi ba, sai kuma ta share idonta jikinta na rawa tace "Gani nan tahowa" daga haka ta figi jakarta da waya ta fice daga gidan. Lallashin Jiddah dake hawaye Abuturrab ya dinga yi a bedroom dinsa, yana stroking bayanta a hankali yace "Komai ya xo karshe in sha Allah Babynah, it's all over now...." Ita dai bata ce masa komai ba tayi lamo jikinsa idonta a lumshe, in dai tana jikinsa jin ta take kamar a sky, the feeling is just heavenly, ta goga fuskarta a bare chest dinsa a hankali, and that immediately turned him on... Ummi ta dinga kallon Aneesah da mamaki ta ma rasa me xata ce mata, Aneesah ta durkusa da gwiwowinta biyu cikin matsanancin kuka tace "Don girman Allah Ummi ki taimakeni ki rufa min asiri, wllh kawai don bani da lafiya ne ta xo ta daukeni xuwa gidansu, shima kuma yasan bani da lafiya don har asibiti ya kai ni, Na rantse babu abinda nake iya yi da kai na Ummi, shi kuma muna ta waya da shi ban san ashe yana gidan ba, kuma bai nuna min ya dawo ba, don Allah Ummi ki ce masa s gidan nan na kwana" Kuka take kamar ranta xai fita ta kife kanta da kujera tana kukan da karfi, Ummi tace "Wannan wani irin shashanci ne ki bar gidan mijinki ki tafi gidan kawa ki xauna wai baki da lafiya Aneesah, Jiddah bata gidan ne da baxa ta taimaka maki ba idan baki da lafiya?" Aneesah ta dago cikin kuka tace "Ummi har amai na sha yi a gabanta ko sannu bata ce min ba, ko ruwa xan sha dole haka xan lallaba in sauka kasa da kaina, har gida Rabi'ah ta xo ta daukeni ba wai da kaina na tafi can din ba Ummi" Ummi dai ta rasa abinda ma xata ce, can ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh Allah ya kyauta, xan kirasa amma gaskiya baxan ce a nan kika kwana ba, menene amfanin karya a rayuwa? Maimakon ya gyara maka lamarinka ma sae dai ya cakudesa, don haka xance gidan kawarki kika kwana kuma xan basa hakuri..." cikin rawan murya Aneesah tace "Nagode Ummi" Rabi'ah bata dade a gidan ba ta wuce.... throughout ranan Aneesah a kwance ta yini kamar mara lafiyar ta lulluba da uban bargo a dakin Ummi, she wish xa a gama issue din nan a wuce wajen ta samu rest of mind, da taji an Shigo parlorn Ummi sae ta kasa kunne ta ji ko captain ne. Abuturrab na kallon Hajiya Fatima bayan ta gama jawabin da take, a hankali yace "Allah ya kara girma Mama, mun gode kwarai da wannan effort din naki, in sha Allah xa mu je can din gaba daya xuwa goben da kika ce in sha Allah" Tace "Madallah da fahimtata da kayi Aliyu, su kuma iyalanka ina ga idan da hali da ka raba masu gida, amma ka fara shawartar iyayenka yanda ku ka yi da su, in my thought hakan kadai ne xai sa kai ma hankalinka ya kwanta kayi concentrating a aikin ka...." Yayi Murmushin karfin hali yace "Haka ne Mama, nagode sosai Allah ya saka da alkhairi" Ta mayar masa da murmushin tace "Ameen my son" Mikewa yayi jin an tada sallan azahar ya mata sallama yace "Xan shiga masallaci" Tace "To shkkn Aliyu, a gaida Jiddar" Yace "Xata ji in sha Allah Mama, bacci take ne shi yasa bamu shigo tare ba" Tace "Toh maa sha Allah" Fita yayi daga gidan ya shiga masallacin dake layin, bayan an idar ya koma gidansa, makullin main entrance din gidan ya ciro a aljihunsa ya bude kofar ya shiga, sama ya haura ya shiga bangarensa xuwa bedroom, bacci Jiddah ke yi har sannan, ya xauna gefen gadon yana shafa fuskarta a hankali ta bude idanuwanta, ya hade goshinsa da nata yayi kasa da murya yace "Sallah... My lazy wife" ta lumshe idonta bata ce komai ba, yayi kissing lips dinta yace "Wa ya koya maki shagwaba haka?" Ita dai bata bude idonta ba, ya juya yana kallon wayarsa dake ring ya mike ya tafi gun wayar ita kuma ta tashi xaune ta sauka daga saman gadon ta shiga bandaki, Abuturrab ya daga wayar ya kai kunne ganin Ummi ke kiransa ya xauna gefen gado yayi mata sallama sannan ya gaisheta, ta amsa tace "Kana gari ne?" Ya d'an yi jim, sai kuma yace "Eh na shigo jiya da daddare" Tace "To ina nemanka yanxu" yace "Toh Ummi, hope all is well?" Tace "Alhmdlh" yace "In sha Allah xan shigo nan da some minutes" Tace "Maa sha Allah" daga haka ta katse wayar, yana xaune dakin har Jiddah ta idar da sallah sannan ya kalleta yace "Ki shirya xa mu je can gida" Tace "Toh" tashi tayi ta nufi kofa xata tafi dakinta, ya bi ta da kallo har ta fita, ya lumshe ido ya kwanta saman gadon yana jin wani sonta na musamman na ratsa can kasan xuciyarsa, she is just the perfect wife a man can pray for, both on bed and vice versa.... Karfe biyu da minti sha biyar Abuturrab ya bar gidan tare da Jiddah xuwa gidansu, lkci lkci yake murxa hannunta a cikin motar har suka isa gidan,, parking yyi a waje suka shiga compound din, tana biye da shi suka shiga parlon Umminsa bayan Jiddah ta gaisa da Ummi ta mike ta fita xuwa dakin Hajja, Ummi tace "Me ya hadaku da Aneesah Aliyu?" Da mamaki yace "Aneesah kuma? Tace wani abu ya hada mu ne?" Ummi tace "Ehh ce min tayi ta maka laifi koh" Yace "Ohh ohk, kawai tasan abinda tayi bata kyauta bane shi yasa ta damu kanta, ae ni ban ce mata komai ba, ta kira ki ne?" Infact tun da ya shiga dakinta yaga bata nan bai sake bin ta kanta ba, Kuma da ya ganta shi kansa yasan hukuncin da xai dauka a kanta ba karami bane, Ummi tace "Tana gidan nan" shiru yyi ya ki cewa komai, Ummi tace "Tace taje gidan kawarta har ta kwana without ur knowledge kuma tayi maka karya tana gida without knowing kana gidan kai ma, is that so?" A hankali yace "Ummi ban dau issue din personal ba ni, it's okay..." Ummi tace "Kayi hakuri Aliyu, i know it's painful ko don karyan da ta maka, shine ma worst part din, bata kyauta ba wllh, amma just over look it, tunda har ta gane kuskurenta and she is remorseful..." Yayi murmushin karfin hali kawai yace "Babu komai Ummi" Ummi tace "Good, but she is still sick tun safe take kwance abincin ma bata iya ci wai, asibitin xaka mayar da ita?" Yace "Toh Ummi" mikewa tayi ta fita, ya jinginar da kansa ransa na wani irin baci, she even have the guts to come to his mother, rike bakinsa yyi cike da mamaki da takaici, can ya ciro wayarsa yyi dialing number Ahmad yana fara ringing Abuturrab yace "Plss tell me u are in kaduna" Daga daya bangaren Ahmad yace "What happened?" Abuturrab yace "Tell me so pls" Ahmad yace "Yeahh i am in..... Abuja" Abuturrab ya hade rai, Ahmad yyi dariya sosai jin Abuturrab yyi shiru don ko ba a gaya masa ba yasan hade rai yyi, Ahmad yace "Toh me ke faruwa kake hoping am in Kaduna?" Abuturrab yyi kasa da murya cike da damuwa yace "It's something very very urgent Ahmad, i have nobody to talk to da ya wuce kai wllh" Ahmad yace "Ba a maganan ta waya ne?" Abuturrab yace "Ya fi karfin ta waya Ahmad" Ahmad yace "So what are you insinuating? In taho kd yau?" Abuturrab yyi kasa da murya yace "Plss" Ahmad yace "Ka ci kai, to matata labor take a tsattsaye, and she just start today, don haka kaga baxan bar ta in taho kd ba" Abuturrab yace "Allah ya raba lafiya, but baxa ka taho tare da ita ba" Ahmad yace "Saboda issue din Captain sae matata ta haihu a titi?" Abuturrab yace "I was thinking sati uku ake dauka ana labor din ae" Dariya Ahmad yayi yace "Aa sae dai wata uku" Shiru Abuturrab yyi, and Ahmad gets that he is so disturbed nd tensed, Ahmad yace "Xa mu yi magana, sae anjima" a hankali Abuturrab yace "Alright" daga haka ya katse wayar ya dafe kansa. Sae kuma ya mike ya fice daga parlon, Ummi da ke can main parlor tace "Xa ku tafi asibitin ne yanxu?" Yace "Ahmad xae xo dubata yanxu, ae munje asibitin few days ago" Ummi tace "Eh haka ta ce min, Ahmad din na gari ne?" Yyi kasa da murya yace "Ehh" Ummi tace "Ohkk" Dakin Hajja ya nufa yana tafiya slowly ya bude kofar, Hajja na kallon Jiddah tace "Toh kin ga ai baxan biyesa mu raba hali a titi da girmana koh?" Jiddah dake ta kallonta tace "Kuma kin shiga gidan?" Hajja tace "Ka ji ki ke kuma da wata magana kamar ta yan wiwi, idan na shiga ai tarwatsa gidan xan yi in tara masu jama'an anguwa in tona masu asiri, ae abun baxae yi kyau ba wllh, sannan gaskiya a Masar ba a goyon bayan tonon asiri, ke baki ga unguwar ba ma na talakawa birjik duk kutaren gida ne a jere bi da bi..." Abuturrab ya gaisheta tayi banxa da shi tana ci gaba da maganarta, Jiddah tace "Yana gaisheki Hajja" shiru Hajja tayi sai kuma tace "Wa yake gaisheni?" Jiddah tace "Shi" Hajja tace "Shi wa?" Kallon Abuturrab Jiddah tayi kamar yanda yake kallonta shi ma, A hankali Hajja tace "Yanxu ke saboda har kin san dadin miji in gama baki labarin walakanci da cin kashin da bawan Allahn nan yayi min a Barnawa kawai mutumi ya shigo ya gaisheni na ba banxa ajiyarsa sai kice min yana gaisheni? To ya gaisheni a saboda me? Me na hada da shi? Mutumin da ya yasar da ni a Barnawa? Ban fa hada komai da shi ba wllh banda Usman da na haifa shi kuma ya haifesa, xumuncin da Allah yace ayi fa kawai nake dubawa ba don haka ba wllh ban hada komai da shi ba, wato ke me miji ko, iyakarsa fa ya dirka maki ciki ya bar ki da wahala yana gantali da tsuntsaye a sararin samaniya, har ki gama wahalanki ki haihu yana kabu kabunsa sama babu abinda ya sha masa kai, don haka idan xa ki kama kanki ki kama kar ya kai ki ya baro ki" murmushi kawai Abuturrab yake yana kallonta, Jiddah kuma ta sunkuyar da kanta ta ki dagowa, mikewa Hajja tayi tace "Ko a fitar min a daki ko kuma ni in fita kawai" Ya ki fita a dakin, hakan ya sa ta fice a fusace, Ya durkusa kusa da Jiddah ya dago kanta yana kallonta a hankali yace "Kina son cikin?" Kauda kanta tayi da sauri, yayi murmushi yana jawota jikinsa. Abuturrab na fitowa masallaci bayan la'asar wayarsa ya fara ring, yana dubawa yaga Ahmad ne, da sauri ya daga Ahmad yace "To kuma don walakanci sai in xo gida baka nan?" Abuturrab ya buda ido sosai yace "Are u for real?" Ahmad yace "Ban sani ba" Da sauri Abuturrab yace "Pls ka jira ni in few minutes time xan iso yanxu, kar ka bar kofar gidan plss" Katse wayar yayi ya shiga motarsa don dama Makullin motar na aljihunsa ya nufi gidansa, yana isa ya tadda Ahmad xaune cikin motar a kofar gidan, yayi parking ya sauko yana murmushi, Ahmad ma ya sauko yace "Wannan ai kanka ka siya ma sabuwar mota ba Jiddah ba, har Abuja fa naga kaje da motar, dama yaudara ce kawai kayi mana??" Abuturrab couldn't help it but laugh hard, Ahmad dai sai kallonsa yake, Abuturrab yayi patting dinsa yace "Idan ma tace bata son motar nan kuma wllh sai in canxa mata, ai aro nake yi ba komai ba, infact ko gidan nan Jiddah tace tana son in mallaka mata wllh i will do so without second thought, i will give her wholeheartedly, ba gida ko mota ba, ni kai na i belong to her, and her wish is always my command" Sake baki Ahmad yayi yana kallonsa, can ya fashe da dariya yace "Ita murhun? Ita me Awaran?" Lkci daya smile din fuskar Abuturrab yayi fading, Ahmad ya dinga dariya don ba da niyyar ya 6ata masa mood ya fadi haka ba, ya kama hannunsa suka shiga ciki yana cewa "Pulling my brothers leg" har suka shiga ciki kuma gaba daya Abuturrab ba shi da walwala duk yayi wani sanyi, Ahmad yace "I left Abuja all because of u now, don haka cheers and tell me what's up?" Abuturrab ya sauke idonsa sai kuma ya mike ya wuce sama, ba a dau lkci ba ya sauko rike da sachet din jiya da ya gani dakin Aneesah ya mika masa su yace "I need more explanation on this pls" Ahmad ya dinga juya abun a hannunsa da mamaki ya kalli Abuturrab yace "This is a prophylactic for ladies, a ina ka samo wannan?" A hankali Abuturrab yace "Dakin Aneesah" Ahmad ya bude ido sosai yana kallon Abuturrab, Abuturrab yace "Yea, i saw them yesterday" Ahmad yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to me take yi da su" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera, Ahmad yace "Did she know u saw it?" Abuturrab yace "I don't think so" Ahmad yayi shiru yana naxari, Abuturrab yace "kasan me ya faru?" Ahmad yace "No" A nutse Abuturrab ya shiga narrating masa yanda suka dinga yi da Aneesah har xuwa safiyan yau, da kuma lkcn da ta shigo gidan, Ahmad ya buda baki yana ta kallon Abuturrab da mamaki ko kiftawa baya yi, Abuturrab da yaji xuciyarsa na masa kuna, yayi kasa da murya yace "I'm really shock Ahmad, i couldn't sleep well yesternight, I'm still finding it hard to believe this, but i need more evidence before anything Ahmad, yanxu maganan da nake maka tana gidan Ummi taje ta shirya mata karya da gaskiya wai gidan kawarta ta tafi ta kwana... Ban ta6a sanin da gaske akwai karyan da ke girgixa mutum ba sai jiya, wllh i am shock, but all the same i am happy don duk karyan nan da ta dinga min a kan Jiddah ko sau daya ban fito na nuna ma Jiddah bacin rai na ba, I was super calm all that while, sai gashi tun ba aje ko ina ba...." Ahmad ya girgixa kai shi ma dai lamarin da alama ya girgixa sa yace "So what next Captain?" Abuturrab yace "Ba tace bata da lafiya ba? Dama nace ma Ummi xaka je ka dubata tunda mun riga munje asibiti, yanxu abinda nake so shine kawai mu siya alluran bacci mu je can gidan kayi mata, bayan tayi bacci xan yi unlocking wayarta da finger print dinta sai in binciki wayarta, and i am hoping we will find concrete evidence a wayar nata, yanxu if i should show this stuff to our parent the first thing that will come to der mind shine bata son haihuwa ne kawai, infact kowa ma haka xai yi tunani, kaga kuma ai ni bani da abinda xance..." Ahmad ya sauke wani ajiyar xuciya yace "Exactly, at first nima na xata haihuwan ne bata so, not until this ur story..." Abuturrab ya mike yace "Mu je" Tashi Ahmad that is just speechless yayi ya bi bayan Abuturrab suka fita, sai da suka fara biyawa Pharmacy ya siya alluran bacci sannan suka tafi can gidan. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppAhmad ya gaisa da Ummi sannan ya shiga hada alluran, Ummi ta mike bar masu parlon nata, Abuturrab dai na xaune har Ahmad ya gama ya mike, leading dinsa yayi xuwa bedroom din Ummi, ta blanket Aneesah ta lekosu a hankali don ganin wa ya shigo, sai da gabanta ya fadi da suka hada ido da Abuturrab sannan Ahmad, wani tsanarta yake ji har ransa, ya dai dake yace "Kince ma Ummi baki da lafiya bayan ni kince min kin ji sauki, so Ahmad is here xai dauraki kan wani treatment din...." Ta mike xaune tana sauke numfashi kamar gaske, cikin rawan murya tace "Wllh bana son inyi ta daga maka hankali ne kana wajen aiki My Captain, shi yasa nake ta ce maka ni naji sauki" hawaye ta fara yi tana kallonsa, Ko sauraron muryarta Abuturrab bai ma son yi, yana kallon Ahmad yace "Yi mata mu fita, i have somewhere to go m" Ta kalli Ahmad haka nan ta ji gabanta ya fadi, ta girgixa kai a hankali tace "Ni ban son wani allura gwara a bani drugs kawai in sha.... Ban son alluran" Ahmad yace "Alluran xai fi maki drugs din kuma ai" tana kara girgixa kai tace "Aa gaskiya gwara min kwaya baxan iya amsan wani allura ba bayan wa enda na amsa a baya" Kallonta kawai Abuturrab yake yi cike da mugun tsanarta, can ya juya ya fice daga dakin, da Ummi ya tafi ya hadata, Ummi ta shigo dakin tare da shi, tana kallon Aneesah tace "Ya haka ana nema maki sauki kuma kina cewa Aa Aneesah, tunda suna ga alluran ya fi sai ki bari ayi maki ai... Meye a cikin allura" Aneesah ta kasa cewa komai ta rasa me yasa gabanta ke faduwa, Ummi tace "Kiyi hakuri ayi maki kawai" Daga haka ta juya ta fita, Abuturrab ya fita shi ma, haka nan hankalinta bai kwanta ba Ahmad yayi mata alluran, sai wani hahhade masa rai take tana hararansa, dama kuma yana sane ko gaishesa bata yi ba, shima din bai ko kalleta ba bayan ya gama alluran ya juya ya fita xai yi disposing din syringe din, a parlor ya tadda Abuturrab xaune, Ahmad ya dage masa gira sannan ya fita, Abuturrab ya shafa kansa a hankali waiting to proceed for the worst, should he really do this? Yana gudun abinda xai daga masa hankali shi kam, ba a dau lkci ba Ahmad ya dawo parlon ya xauna shi ma, a hankali Abuturrab yace "So where did u leave ur wife?" Ahmad yace "Nayi dropping dinta gidan Umma" Yace "Ohk..." Ahmad na murmushi yace "Captain the once upon a time Hygienist.... Not anymore" Abuturrab ya kallesa da sauri yace "Har yanxu ma kuwa" sai kuma a hankali yace "Is just that one have to adapt to every situation he finds himself in life, i still appreciate Cleanliness, and it's still my priority...." Dariya Ahmad yayi yace "Gaskiya ne..." Lkci lkci Ahmad ke kallon agogon wrist dinsa har ya mike daga karshe ya nufi bedroom din Ummi ya tura kofar a hankali yana kallon Aneesah...., karasawa yayi ciki yaga she is already fast asleep, ya leko yana kallon Captain yayi masa alamar ya taho, captain ya mike ya shiga dakin gabansa na faduwa, jawo jakarta dake makale gefenta yayi ya bude zip din ya ciro wayar, ajiye wayar yayi ya hau bincika jakar, panties ya gani, da toothpaste and brush, with turarruka, sai kuma Rubber irin wanda ya gani a dakinta har biyu" Juyawa yayi ya kalli Ahmad dake tsaye yana kallon ikon Allah shi kam, Abuturrab ya dinga kallonta da wani expression, sai kuma ya mayar da kayan gaba daya cikin jakan ya kulle, ya dawo wayarta ya kamo hannunta a hankali ya manna finger print dinta a jiki, nan da nan wayar ya budu, sai da ya fara shiga settings yayi adding nasa finger print din yayi saving sannan yana kallon Ahmad yace "Mu je" Fita suka yi dakin xuwa cikin motar Ahmad, tun Abuturrab bai shiga wayar ba yaji xufa na keto masa all over, he don't even get why, ga gabansa da ya dinga faduwa babu kakkautawa, WhatsApp dinta ya fara shiga, Ahmad dai na xaune a maxaunin driver, shi kuma Abuturrab na xaune a kujera me xaman banxa. Alhaji Mukhtar ya fara cin karo as wanda suka yi chatting last, ya shiga chat din ya dinga scrolling yana karanta content din with mouth agape, magana ne a kan inda xa su hadu ya shigo kaduna state from Adamawa, take ce masa mai gidanta is around sai dai next week idan ya koma aiki, tunani Abuturrab ya dinga yi, su hadu su yi me? Wani business din take wanda bai sani bane, iyakar chat din kenan sai kuma dubu ashirin da tace ya tura mata, kuma ya tura mata din don ga receipt, wani chat din Barrister Ismail ya shiga, first abinda ya fara cin karo da shi shine compliment da yake mata a kan darensu na jiya how awesome it was, lkci daya jikin Abuturrab yayi sanyi qlau, ya duba date din chat din ya ga just 3 days ago ne, jinginar da kansa yayi da kujeran mota yana jin xuciyarsa na bugawa da karfi, Ahmad dai sai kallonsa yake kuma bai bukaci ya nuna masa komai a wayar ba cause it's more like his privacy, Abuturrab ya daure ya ci gaba da scrolling chat din, wanda duk erotic talks ne, wani video ya gani na minti daya da some seconds wanda tayi ma iya private part dinta ta tura masa, Abuturrab couldn't hold it any more ya fita chat din ya sauka Whatsapp din gaba daya, without looking at Ahmad a hankali yace "Na gama duba abinda xan duba Ahmad" Ahmad could sense how hurt he is from d way he sound, Ahmad ya kasa ce masa komai, Abuturrab ya kara jinginar da kansa jikin kujera ya runtse idonsa jin kansa yayi masa wani nauyi, Ahmad ya sauka motar yace "Mu Shiga ciki" Da kyar Abuturrab ya bude idonsa ya sauka daga motar, ganin abun yake kamar a mafarki, is this for real?? Ahmad ya xagayo yayi patting shoulder dinsa a hankali yace "It's well bro..." Abuturrab bai iya yace masa komai ba suka shiga gidan yana tafiya slowly. Parlor ya xauna yana kallon Ahmad alamar ya ma rasa abinda xai ce masa, Nafisah da ta shigo parlon xata tafi dakin Hajja ya bi da kallo yace "Ba ni takarda da biro" Ahmad yayi kasa da murya yace "I won't tell u no Aliyu.... Idan baka mance ba farkon aurenku na ta6a gaya maka in har mace ta saba biye biyen maxa a waje in har tayi aure idan ba wani ikon Allah ba it's hard ta iya bari, she is already used to different men, so daya baxai ta6a iya gamsar da ita ba, she can neva be contented with her husband, sai in Allah ya so ta da Rahama wllh, ban ce fa babu wa enda basu dainawa, but gaskiya sune wa enda Allah ya so da Rahamarsa kamar yanda na fada maka, don haka before coming to ur final decision, talk to Ummi first, convince her, and you can even go ahead and show her all this evidence, ba wani xancen jin kunya a issue din nan" Abuturrab ya kasa ce masa komai, duk jikinsa yayi sanyi ba kadan ba, this is the worst thing dat have happened to him na bacin rai da shock, matarsa ta sunna take harka da wasu mazan a waje, shi da yake namiji me yawo gari gari ya iya rike kansa... Ohh This is so sad, ya rike kansa with so many thoughts running his mind, can ya mike ya tafi dakin Hajja don Ummi na ciki, tun da ya shigo Ummi ke kallonsa ganin yanayinsa, Jiddah ma kallonsa take, Hajja kam dama shiru tayi ta hade rai taki kallonsa irin haushinsa take ji har sannan, Abuturrab ya shiga Whatsapp din ya mika ma Ummi, cike da karfin hali yace "Ki d'an duba Ummi" Daga haka ya juya ya fice daga dakin, Hajja ta dago da sauri tace "Ki duba me?" ummi dai sai kallon What'sapp din take bata ma san chat din wa xata shiga ba, kuma taga wayar kaman na Aneesah, Hajja ta mike a rikice tace "Ya xa ki min shiru Hauwa, matsala ya samu wajen aikin ne?" Ummi ta kalleta tace "Aa Hajja, magana ce ya bani in duba" Daga haka ta mike ta fita dakin ta koma parlonta, kamar hadin baki da Abuturrab iya chats din da ya shiga ita ma ta shiga a lkcn, and she couldn't scroll further, har ta fi sa shiga shock din ta kasa rufe baki, dai dai kan video din ita ma ta sauka what'sapp din gaba daya ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Abuturrab ya shigo parlon nata rike da paper da pen, Kasa kallonsa tayi, duk jikinta yayi sanyi qlau, ya xauna saman kujera yana kallonta yace "And i just have to do this Ummi, ni ba mazinaci bane, don haka baxa a so in ci gaba da rayuwa da mazinaciya ba...." Kai kawai Ummi ta iya gyada masa, ta ji tausayin d'an nata ya ratsata, Aneesah ta ci amanar aure, Cikin few minutes Abuturrab ya rubuta abinda xai rubuta a takardan ya mike yayi folding dinsa neatly ya shiga dakin ya ajiye mata a dai dai inda tana juyawa xata ga takardan sannan ya juya ya fita daga dakin, mika masa wayar Ummi da ta ma rasa abinda xata ce tayi, ya amsa yace "Xan tafi da wayar idan Abba ya dawo anjima xan dawo in basa shi ma..." Ummi tace "Aa, xan sanar masa da baki ba sai ka nuna masa wata waya ba" sae kuma kawai ya ajiye ma Ummi wayar yayi mata sallama ya fita ta bi sa da kallo. Abuturrab bai kara minti goma a gidan ba ya dau Jiddah Ahmad yayi dropping dinsu a gida, Ahmad na kallonsa bayan sun sauka yace "We will talk on phone Captain" Abuturrab ya gyada masa kai kawai, ko magana bai son yi, Ahmad yayi reverse ya bar anguwan, Tun da suka shiga parlor Jiddah ke kallon Abuturrab ganin bata ta6a ganinsa a wannan yanayin da yake ciki ba, gashi ya ki ce mata komai, har xata wuce sama ta kasa, ta dawo ta xauna dab da shi tana kallonsa a hankali tace "Are you okay?" Ya dinga kallonta bai ce komai ba ya sauke idonsa, da damuwa tace "You are not saying anything" Ya jawota jikinsa cikin sanyin murya yace "I am fully okay Jiddah, ki je ki huta probably anjima xa mu fita da su Mama" Kallonsa ta dinga yi, can ta mike ta wuce sama ya bi ta da kallo, kwanciya yayi kan 3 seater din yana jin kamar xaxxabi xai rufesa ya runtse idonsa. Kiran Magrib ya sa Abuturrab mikewa duk da ba bacci yayi ba, ya shiga bandakin dake downstairs ya fito ya tafi masallaci. Ana idarwa bayan ya dawo gida yayi minti goma xaune parlor still thinking, sai kuma ya tashi ya tafi dakin Jiddah, yana shiga dakin ya ji kamar an yaye masa damuwar da ta cika masa xuciya, xaune ya ganta can karshen gado ita ma ta yi sallan, tana ganinsa kuma ta dauke kai, ya karasa ya xauna kusa da ita yana murmushi ya kamo hannunta yace "U are sulking" xata kauda kai ya rike kanta giving her a deep kiss, don kansa ya gaji ya kyaleta, yana kallon fuskarta with much love yace "Tell me fushin me kike?" Tayi shiru bata ce komai ba, ya jawota jikinsa yace "I love you Jiddah, and I won't halt saying I am sorry over and over again, i am sorry wife...." Ta turo baki tana kallonsa tace "You are sorry for what?" Yayi kasa da murya yana murxa hannunta yace "For everything i have done to you hitherto...." Tayi murmushi a hankali ta kwanta kirjinsa cikin sanyin murya tace "You did nothing to me than molding me to who i am today, you influence me..." Ya rungumeta sosai yana shakan kamshinta me rikitarsa. Bayan isha Aneesah ta farka daga baccin da take, ta ji kanta yayi mata nauyi sosai, ta dinga bin dakin da kallo, sai kuma ta mike xaune da sauri idonta ya sauka kan farin takardan dake gefenta, dauka tayi tana jujjuya takardan that is folded neatly, haka nan kawai taji gabanta yayi mugun faduwa, sai kuma tayi tunanin ko maganin da Ahmad yayi mata prescribe ne, ta warware takardan da sauri tana kallon content din, "Ni Aliyu Usman na sake ki saki daya, na sake ki saki biyu Aneesah, duk xamanmu idan na ta6a wronging dinki in anyway, forgive me, nima ki je na yafe maki" Wani ihu ta kwala kamar xata tsaga gidan, ta sauka saman gadon dama Hijab dinta na jikinta har sannan, ta fito kamar mahaukaciya parlon Ummi taga babu kowa, main parlor ta fito taga Hajja xaune da Ummi sai Umma a parlon, ta rushe da wani matsanancin kuka ta nufi Ummi ta durkusa tana rike kafarta da karfi take cewa "Me nayi masa ya sakeni, saki ya rubuta min a takarda fa, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un na shiga ukuna, don girman Allah Ummi ku rufa min asiri, wllh ina son mijina, me nayi masa ya sakeni kina kallo" Tashi Hajja tayi tana d'an tattaka rawa tace "Rana dubu ta barawo, rana daya ta me kaya...." Haka ta dinga nanatawa tana d'an takawa abinta, Umma dai takaici ma yasa ta kasa kallon Aneesah, she just finish checking all what is on the phone few minutes ago, ita ta ma fi Ummi da Abuturrab shiga wayar deeply, abun yayi muni ainun, Kuka kawai Aneesah take yi tana cewa ta shiga uku a gaya mata me tayi Aliyu ya saketa, Ummi ta girgixa kai cike da takaici tace "Baki kyauta ma kanki ba Aneesah, baki kyauta ba, kin cuci kanki, kin xalunci kanki, kin cuci rayuwar ki, kuma kin ci amanar aurenki, gaya min menene amfanin fornication Aneesah? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aneesah ta dakatar da kukan da take xuciyarta na wani irin bugawa tana xare ido, Umma ta jefa mata wayarta tace "Allah ya shiryeki, ya kuma shirye masu ire iren halinki ya sa su gane, Allah ya rabamu da son xuciya irin naki Aneesah, sai kije kuma kiyi ta istigifari Allah ya gafarta maki...." Sai da Aneesah ta dauke wuta na kusan second goma ta dinga kallon wayarta da Umma ta jefo mata, Hajja ta tafe hannu tace "Allah ya isar ma jikana, Allah ya isar masa wllh...." Sai kuma ta fashe da kuka ta nemi waje ta xauna tayi tagumi tace "Dama duk tsawon lkcn nan da mazinaciya fasika yake xaune a gidansa bai sani ba, bawan Allah yana can yana neman na abinci a sararin samaniya bai rageki da komai ba na bukatar yau da kullum amma kike cin amanarsa haka, ashe dama uwarki bata gasa maki matancinki yanda ya kamata ba Aneesah, mu dai Allah ya isa wllh, na kuma gode Allah da bai sa mun hada xuri'a da mazinaciya ba, wllh da a Masar ne dama katon rami xa a haka a jefa yar iska ciki a bar iya katon kanki a waje, ayi ta jifa har sai kin mutu" Tsam Aneesah ta mike ko ina na jikinta na rawa ta dau wayarta ta fice daga parlon, kamar xata tashi sama ta dinga tafiya har xuwa inda xata samu adaidaita sahu, ta tsayar ta sakar masa kuka tace "Don girman Allah ka taimaka ka ajiye ni nan nan ba nisa bawan Allah, wllh ina cikin tashin hankali babu ko sisi a jikina, ka rufa min asiri bawan Allah" Mai adaidaitan ya tausaya mata yace ta shiga, ya ajiyeta har kofar gidan Abuturrab, ta sauka bakinta na rawa tace "Nagode" a guje ta shiga gidan ta nufi entrance, mai gadi dai ya bi ta da kallo, murda kofar parlon tayi ta shiga kamar an cillota, Abuturrab na xaune parlor kasan carpet Jiddah kuma na xaune opposite dinsa tana yanka masa watermelon ya kafeta da ido ko kiftawa baya yi.... Duk suka daga kai suna kallon Aneesah. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppMikewa Abuturrab yayi ganin ta nufo su yana mata wani kallo furiously ya nuna mata kofa yace "Fitar min daga gida Aneesah, don't make the mistake of coming closer, leave my house immediately Aneesah..." Cikin tsawa ya kare maganar, ta taho kamar mahaukaciya without minding his words ta cakumosa cikin daga murya tace "Ka gaya min abinda na maka ka sakeni Aliyu?" Bai jira ta rufe baki ba ya shaketa sannan ya wurgar da ita kasa da karfi, Jiddah ta mike da sauri ta nufesa ganin yayi kan Aneesah ta rikosa tace "What is this u are doing?" Ko sauraronta bai yi ba ya dago Aneesah da ta kasa motsi bayan ta fadi kasan tiles, wasu tagwayen mari ya kai mata yace "U still have the guts to question me, u still have d guts to walk into my house? who advice u to come after me? Who gave u this deadly advice" Ya sake lafta mata mari, ya jefar da ita kasa yana ball da ita towards d door kamar ya samu kwallo, fixgosa Jiddah tayi cikin tashin hankali tace "Wai don Allah meye haka kake yi? What is this u are doing" Sai kuma ta fashe da kuka still holding onto him tana jijjigasa ganin bai fasa ball da Aneesah ba, ta dinga cewa "Stop this plss Aliyu, me tayi maka haka, do u have the heart of beating a woman this way??? Are u this wicked? Did a lady deserve this from u?" Bai san sanda ya tura Jiddah saman kujera ba, ya tafi xai dau wayan wuta gun kayan kallon da ke parlon gaba daya ransa ya gama baci biyosa da Aneesah tayi, Da Aneesah ta samu ta mike ta xagaye kujeran a guje ta cafko Jiddah ta shaketa da karfi tana cewa "Ke kika rabani da mijina, ke ki sa ya sakeni, ke kika hada komai da ya faru, yau xan ga ko da gawarki xai kare rayuwarsa, wllh sai dai wata ba ke ba" Abuturrab ya nufeta with full speed yana kokarin freeing Jiddah daga rikonta, komawa tayi kamar mahaukaciyar gaske tana gwale ido tana ci gaba da shake Jiddah, duk da dukan da yake kai mata taki sakinta, gaba daya hankalinta da idonta na kan wukar da ke kasa kan tray, kamar dai wancan lkcn da ta rike Jiddah a asibiti yau ma hakan ne tayi, duk karfin Abuturrab he couldn't free jiddah, duka ba na wasa yake mata ba amma taki cika jiddah, idan kuma yace xai yi amfani da force he will definitely hurt Jiddah, wani kukan kura Aneesah tayi ta hankade Jiddah ta fada kanta tana kokarin jawo wukan da take ta kallo da hannunta tana cewa "Wllh sai na kasheta idan ya so nima a kasheni, gwara in kasheta nima a kasheni duk mu bar duniyar babu me xama da kai...." Abuturrab yayi hanxarin sa kafa yayi wani ball da wukan kafin hannunta ya kai kansa, ya duka kasa ferociously ya kama hannun da ta so daukan wukan da shi yayi masa wani mugun murda har sai da yaji hannun yayi wani kara sannan ya sake, lkci daya jikinta ya mutu tayi wani karan axaba ta kasa ci gaba da rike Jiddah, with full strength ya dagota sama daga kan jiddah, ya dinga kifa mata mari yana kai mata kulli, jefar da ita kasa yyi yana haurinta yana tattaketa, ihu kawai take yi ta kasa tashi sbda hannunta da taji kamar baya jikinta gashi ta kasa daga hannun, ya kara dagota da hannu biyu ya bugata da pillar din dinning area, jini ke xuba ta bakinta da hanci, mari kuwa har sai da yaga palm dinsa sun kwanta a fuskarta sannan ya dinga jan ta kamar rago ya nufi kofa da ita, bai tsaya ko ina ba sai bakin gate ya wani cillata waje yana kallon mai gadi da ya ja gefe a tsorace, cikin tsawa yace "Kada ka sake barin ta shigo gidan nan, ka ji me nace maka??" Mai gadin ya gyada kai da sauri yace "Na ji Yallabai..." Aneesah ta mike da kyar ta xube kan gwiwowinta tana son hade hannunta amma ta kasa daga daya hannun nata, gaba daya tayi weak, cikin kuka sosai tana maida numfashi tace "Don girman Allah kar ka min haka Aliyu, wllh ina sonka baxan iya rayuwa babu kai ba, don darajan annabin Rahama kar ka gujeni, wllh xan iya kashe kaina idan na rasaka, I can't continue leaving without you Aliyu, wayyoo na shiga uku na lalace, kar ka rabu da ni Aliyu" Tuni Abuturrab yayi banging gate din ya sa lock ya nufi entrance din gidan da sauri, Xubewa yayi gaban Jiddah dake kwance yanda ya bar ta, ya dagota yana jijjigata yana kiran sunanta a rikice.... karfe sha daya da few minutes Abuturrab ya rako Ahmad bakin motarsa, gaba daya he isn't himself, Ahmad ya juya yana kallonsa yayi patting shoulder dinsa yace "She will be fine in sha Allah, u need not to worry Bro..." Abuturrab ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya kawai bai ce masa komai ba, Ahmad yace "Xan shigo gobe da safe idan Allah ya kai mu" Cikin sanyin murya Abuturrab yace "Ohk... Thank you Ahmad" Yana tsaye har Ahmad yayi reverse ya bar anguwan, sannan ya juya ya koma cikin gate din gidan ya kulle, yana shiga parlor ya kulle gidan ya haura sama, dakinsa ya nufa ya xauna gefen gado yana kallon Jiddah dake bacci, ya kai hannu goshinta a hankali yana kallonta with pity, bayan kusan minti goma ya jinginar da kansa jikin gadon ya lumshe idonsa. Cikin dare ya bude ido da sauri jin tana motsi don har bacci ya daukesa, ya gyara xamansa yace Jiddah, ta bude ido da kyar ya kamo hannunta yace "How are you feeling now?" Kanta kawai ta nuna masa, ganin mikewa xaune take son yi ya dagota da damuwa yace "Xai daina in sha Allah, should i make u tea or anything?" Ta girgixa masa kai da kyar tace "I want to ease my sef" Ya mike ya dagota ya kai ta har bathroom din suka fito tare, kuka ta sakar masa sbda ko ina na jikinta ciwo yake mata sosai, ya dauketa ya kwantar gefen gado ya durkusa gabanta yana kallonta cike da tausayinta yace "Kiyi hakuri plss wife, i caused u all this..." Throughout daren haka ya dinga lallabata bai yi bacci ba yana mata tausa a hankali, a haka har ta koma bacci wajen karfe hudu.... Ana idar da sallan asuba ya kawo mata shayi ya lallabata ta sha sannan ya bata magungunan da Ahmad ya taho da shi jiya bayan alluran da yayi mata, tana shan maganin babu dadewa bacci me nauyi ya dauketa, sai a sannan Abuturrab ya samu ya kwanta gefenta shi ma yayi baccin da bai yi ba daren jiya. Da rana ya dawo daga gidan Umma bayan ta kirasa yaje ya amsar ma Jiddah abinci don Ahmad ya bata labarin abinda ya faru, har da ta shirya xata taho yace mata ai da sauki ba sai ta je ba kawai tsorata Jiddan tayi but she is getting better, yana isa kofar gidansa ya tuna fa bai sake shiga gidan Hajiya Fatima yace da ita komai a kan xuwansu hayi ba, and that's very bad, sauka yyi motar bayan yayi parking a waje ya shiga gidan nata, bayan sun gaisa ya sanar mata jiddah ce bata ji dadi ba amma idan taji dama ko xuwa la'asar ne sai su fito su je can din, Hajiya Fatima tace "Allah sarki, Allah ya bata lafiya, kun je asibiti kuwa?" Yace "Cousin dina ya xo ya dubata kuma ya bata magunguna" Tace "Toh Alhmdlh, duk sanda taji saukin sai muje babu damuwa, kila xuwa magrib ma in shigo in dubata, Allah ya bata lafiya" Yace "Ameen na gode Mama, Allah ya kai mu" da haka yayi mata sallama ya fita gidan, motarsa ya shiga mai gadi ya bude masa gate ya shiga ciki yayi parking sannan ya sauka ya dau warmers din abincin ya wuce ciki, mamaki ne ya cikasa jin kamshi me dadi na turaren wuta dake tashi a each and every angle of the parlor, ya dinga bin parlon da kallo don an goge ko ina, murmushi yayi ya karasa tsakar parlon ya ajiye warmer din abincin ya haura sama, dakinta ya fara shiga nan ma dai sai kamshi yake tayi tidying ko ina, ya kullo kofar a hankali ya tafi nasa bangaren, lumshe ido yayi ya bude don kamshi ne ya hadu da sanyin ac, daga bedroom din har parlor nasa, yaushe rabo? Murmushi yayi ya juya ya koma downstairs ya shiga kitchen, ta gama wanke wanke tana goge wajen gas ta juya tana kallonsa, English dressing tayi ta daure dogon gashinta da ribbon, ko hulan ma bata sa ba, wanda ko tayi irin dressing din a gidan Umma sai ta sa hijab duk da isu isu ne a gidan, yau kuma kam bata sa hijab din ba, sunkuyar da kanta tayi tace "Sannu da xuwa" Ya shiga kitchen din giving her a hug from d back ya lumshe ido fuskarsa a kan gashinta yayi kasa da murya yace "Duk ke da baki da lafiya kika gyara gidan nan haka Babyna??" Ta rufe idonta a hankali tace "Na ji sauki" Rasa abinda xai ce mata yayi, yana jin sonta a ko da yaushe na komawa sabo a xuciyarsa, anya Jiddah xata bari yayi concentrating a aikinsa kuwa? Anya xai iya tsayawa without her close to him for good 5 days kuwa, da kansa ya ba ma kansa amsa da No a xuciyarsa, juyowa yaga tayi a hankali ta shige jikinsa tana boye fuskarta a kirjinsa, daga nan kuma labari ya canxa ma Abuturrab... Bayan la'asar yana dawowa daga mosque ya tafi bedroom dinsa, xaunawa yayi gefen Jiddah dake bacci yana jan dogon hancinta a hankali yana kallonta yace "Sallah plss" Ta bude idonta, ya dagota xaune yace "Kiyi sallah mu ci abinci" ta daure gashinta sannan ta sauka kan gadon ta tafi bandaki, ya mike ya sauka kasa. Da kansa ya dinga bata abincin tana jikinsa, idan ya bata sai shi ma ya ci, ya lura bata son cin abinci da yawa don sai lallabata yake tana ci da kyar, hakan da take kuma narkar masa da xuciya yake, he just can't get enough of her love... Daga karshe ya rufe abincin don wannan abinda take ma ya sa yaji ya koshi kawai, ya manna mata kiss a forehead dinta underneath his breathe yace "Ina sonki matata" tashi tayi xaune daga jikinsa tayi kasa da murya a hankali tace "Ka gaya min sanda xan koma schl pls" Shiru yayi ya ki ce mata komai lkci daya kuma mood dinsa ya canxa, ya dau remote yana changing channel, kallonsa kawai Jiddah take jin ya ki cewa komai, yayi mata side hug yayi kasa da murya yace "What do u need apart from me again in this life Jiddah? Me xa ki yi da wani schl?" Ta gyara xama tana kallonsa da mamaki tace "You mean i won't go to schl again? Ko waec din ma fa ban yi ba" Ya rungumeta ya kai bakinsa kunnenta pleadingly yace "Pls ki cire wani schl a ranki, babu abinda xaki rasa a rayuwar nan ko bayan rai na my wife..." sai kuma yyi shiru, kankameta yayi yace "Gaskiya ina da kishi sosai, bana son a dinga kalle min mata anyhow, don haka baxa ki kara komawa wani schl ba..." Jiddah ta rasa ma me xata ce masa don she is a bit shock, ya girgixa kai yace "Ba ki ga ko farkon xamanki gidana ba naki sa ki schl duk da maganan su Umma, why because ina kishin matata... Ina da kishi sosai, fiye da yanda kike tunani Jiddah, ko me kike son koya ni xan koya maki a gida babu abinda xaki yi da wani kwali bayan mijinki na da rufin asirinsa, idan ma kince salary kike son in dinga baki wllh ni xan raba albashina biyu in dinga baki rabi duk wata, i think that's what we will do plss, idan kina son farin ciki na kada ki sake min maganan boko plss...." Hawaye ya gani a idonta, ya dinga kallonta, sai kuma ya jinginar da kansa da kujera yace "Shkkn ki shirya ki koma schl din" daga haka ya mike ya wuce sama ta bi sa da kallo hawaye na sauka idonta. Har aka kira magrib bai sauko ba ita ma bata je saman ba, mamaki kawai take wai baxata sake xuwa schl ba, da ta tuna wannan furucin nasa sai taji hawaye ya taho mata, saukowa yayi ya fita parlon without looking at her ta bi sa da kallo, da kyar ta iya tashi ta tafi dakinta ta je tayi alwala. Da kayan shayi Abuturrab ya dawo gidan duk da ba wai na gidan ya kare bane, ya kai su kitchen ya ajiye ya dawo parlor ya xauna, bai kai minti goma xaune ba aka danna bell, ya juya ya kalli kofar sannan ya mike ya karasa can, yana bude kofar ya ga Hajiya Fatima ce, murmushi yayi ya bata hanya yace "Sannu da xuwa mama" ta shigo parlon tace "Yauwa sannu Aliyu, ya mai jikin" yace "Alhmdlh, bari in kirata" Sama ya wuce, Hajiya Fatima ta xauna parlon tana yaba wannan turaren wuta me shegen dadin kamshi da aka sa a parlon a ranta, don ya kama ko ina and the scent is so heavenly, Abuturrab ya fara saukowa kasa sannan Jiddah, da murmushi ta xauna ta gaida Hajiya Fatima, Hajiya Fatima tace "Lafiya lau Jiddah, ya kika kara ji?" Ta sunkuyar da kanta tace "Na ji sauki Mama....." Hajiya Fatima tace "Toh Allah ya kara afuwa, dama daxu da ya shigo yace min baki ji dadi ba shine nace bari in leko in duba ki, kuma naga kam jiki Alhmdlh" Jiddah tace "Nagode mama Allah ya kara girma" Hajiya Fatima tace "Ameen, amma wannan turaren wutan naki a ina kika siya kuwa" Jiddah tayi murmushi tana jan fingers dinta tace "Umman mu ce tayi order wajen S.SQuare Collection" Hajiya Fatima tace "Ikon Allah a wani kasuwan?" Jiddah tace "Aa a Gombe matar take, amma tana turawa ko ina" Hajiya fatima tace "Toh bani number ta, na jima ina neman turare me kyau haka ban samu ba sai dai a cinye maka kudi kawai" Jiddah na murmushi tace "Xan tambayar maki Umma idan na amshi number sai in kawo maki gida, ni wayata ta fashe" Hajiya Fatima tace "Toh shkkn, ina saurare" Sallama tayi masu Abuturrab yace "In sha Allah gobe xa mu je can hayin Mama" Tace "Allah ya kai mu lfya" Har balcony suka rakata ta wuce, Abuturrab ya haura sama Jiddah ta bi sa da kallo. Washegari da yamma suka wajajen karfe biyar dau hanyar hayin rigasa a motar Abuturrab, Hajiya Fatima na xaune bayan motar, Jiddah kuma na xaune gaban motar, tunda suka kamo hanya take bacci heavily, lkci lkci Abuturrab dake hira da Hajiya Fatima yake kallonta a gefensa, bayan yayi parking kofar gidan Iyah Hajiya Fatima ta bude motar ta sauka, ya jawo Jiddah don motarsa tinted ce ta bude ido a firgice, da damuwa yace "Wani bacci ne wannan kike yi haka throughout Baby?" Ta langwabe masa a hankali tace "Kilan aikin da nayi ne ya sa na gaji sosai" Yace "Toh baxa ki sake wani aiki ba, beside the house is too big for you to clean all alone, xa mu samu house help ko da biyu ne, i don't want my wife to be stressing her self" Girgixa masa kai tayi da sauri tace "Aa ni bana son wasu house help, xan iya yi da kai na...." Xaro ido tayi tana bin anguwan da kallo tace "Lahh har mun kawo ashe" sai kuma ta kalli bayan motar tana xaro ido don gaba daya ta mance tare da Hajiya Fatima suke, sai taga bata motar, bude side dinta tayi ta xame hannunta daga nasa a hankali, ta sauka... shi ma ya sauka ya kulle motar suka shiga cikin gidan don tuni Hajiya Fatima ta shiga. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppJiddah ta tafi kusa da Iya tana murmushi ta gaisheta, Iyah ta amsa tana washe baki tace "Sannunku da xuwa Jiddah..." Abuturrab ya xauna saman tabarman dake shimfide yace "Ina yini Baaba" Da fara'a tace "Lafiya lau Alhmdlh... Sannunku da xuwa" Hajiya Fatima tace "Ina saurarenki Mama" Iyah tace "Shine nace ko xa ku je wajen Jibirilun a gwada sa'a tunda Zulan tace babu tantama yasan inda take, mu dai nan yayi ta rantsewa bai san ina Hansai ta nufa ba... Zulai kam na can tana fama da kanta duk babu kafafuwan wai yanke su xa ayi, ita kanta Hansan ta gudu da dubu ashirin dinta tace min.. " Hajiya Fatima tace "Toh Allah ya kiyaye, mun gode kwarai mama Allah ya saka da alkhairi, yanxu wa xai kai mu can gidan wan nata?" Iyah ta kalli Jiddah tace "Ba kin san gidan Jibirilu ba?" Jiddah tace "Na sani" Hajiya Fatima tace "Au to shkkn, ashe ma ta san gidan" Abuturrab na kallon Iyah yace "Kiyi hakuri Baaba har yanxu ban kai ki can inda muke ba kamar yanda nayi alkawari, in sha Allah xan sa lkci in xo in dauke ki, ina sane, yanayin aikina ne ya sa bana samun lkci" Iyah tace "Allah ubangiji ya dafa maka, babu komai wllh, ai ka gama mana komai tunda ka rike Jiddah da amana, Allah ya saka maka da alkhairi ya dafa maka a lamuranka" Yace "Ameen nagode" Dubu goma ya ajiye mata, ta dinga godiya kamar xata ari baki, ta rakosu har bakin mota tana daga masu hannu har suka bar layin, tana murmushi tace "Allah sarki Isuhu, kyawun halinka kadai ma ya ishi a rike maka er ka da amana har abada kuwa" Parking Abuturrab yayi kofar d'an kuturun gidan Kawu Jibiril, Hajiya Fatima da Jiddah na tsaye daga gefe Abuturrab yayi sallama bakin kofar Zauren, Wata yarinya ce da baxata wuce Jiddah ba ta leko tana tambayar waye, kallon Jiddah ta dinga yi irin kallon sani, Hajiya Fatima tace "Babanki fa?" Tace "Baya nan, Hajiya Fatima tace "Yaushe xai dawo?" Tace "Ya tafi kauye duba gonarsa" Hajiya Fatima tace "Mamarki fa?" Tace "Tana ciki" Hajiya Fatima tace "Kice ana sallama da ita" Juyawa tayi ta koma ciki, sai ga ta sun dawo da uwarta, Lantana na gyara daurin kirjinta a d'an tsorace tace "Lafiya wa ku ke nema?" Hajiya Fatima na murmushi tace "Maganar ba ta tsayuwa bace, kar ki wani damu alkhairi ne ya kawo mu" Lantana ta hangame baki tana kallon Jiddah tace "Wacece wannan kamar Jiddar Hansai?" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Hajiya Fatima tace "Ita ce" wani salati lantana ta rafka tace "Ku shigo ku shigo, tsakar gidan ne dai babu shara, Bismillan ku" Da sauri ta koma ciki ta fito da wani bak'in tabarma ta shimfida masu, tana yi tana kallon Jiddah har sannan ta kasa rufe bakinta, Jiddah ce ta fara xama tace "Ina yini Maman Jummai" Lantana ta kasa amsawa sbda mamaki tace "Yanxu Jiddah kece kika dawo haka kamar wata er sarki?? Allah mai iko" Hajiya Fatima ta xauna kusa da Jiddah tana bin tsakar gidan da kallo, Abuturrab kuma ya ki xama saman tabarman, Hajiya Fatima na kallon Lantana tace "Mun wuni lafiya?" Da sauri Lantana ta xube kasa ta fara jero masu gaisuwa, Hajiya Fatima tace "Alhmdlh, fatan mun sameku lafiya" Lantana tace "Lafiya lau wllh, Wai yanxu Jiddah ce haka Jama'a" sai kuma ta rike kai tace "A gaskiya wanda bai ji tsoron Allah ba yayi asara a rayuwar nan" Jiddah dai kanta na kasa, Hajiya Fatima tace "Yau dai shine nace bari mu shirya ta xo ta gaida Baabarta, sai kuma da muka je anguwan muka samu labarin ai ta tashi gidan" Lantana ta rike ha6a tace "Cabdi, wannan ai tsohon xance ne, tun yaushe en lapun suka xo suka siyar da gidan suka cire kudinsu suka bata sauran canjinta, ai ko dai Hansai bata Hayi yanxu, bashin da ke kanta na jama'a ya fi dubu dari biyu.... Nemanta ake ido rufe" Hajiya Fatima tace "Ikon Allah, to yanxu ina ta koma?" Lantana ta dinga bin su da kallo daddaya da daddaya, Hajiya Fatima tace "Kar ki ji komai wllh, mu alkhairi ne ya kawo mu ba sharri ba, mun xo sada xumunci ne kawai, idan da wani taimakon da xa mu yi kuma sai mu yi..." Lantana tayi kasa da murya tace "Sai dai in kai ku a boye mu dawo a boye don ban ma son mai gidana ya sani, abun sirri ne, sannan Hansai dai bara take a Kana rad, er ta kuma fama take da cutan xamani, shegun da ta haifa ma Allah yayi masu rasuwa, kun san yan biyu ne, to ance dai cutar ce ta kashesu satinsu 3 a duniya, ni ko yaran ban gani ba don ba a hayi ta haihu ba, Iliya ne dai yayi mata cikin ya goga mata kanjamau" Hajiya Fatima ta bude jakarta da sauri ta fiddo en dari biyar biyar tace "Mun kuwa gode wllh, ki kai mu ko da taimakon da xa mu iya mata..." Ajiye mata kudin tayi a gabanta, Lantana ta mike da sauri tana kallon kudin tace "Bari in saka riga, Allah ya so mai gidan nawa baya nan, ina nuna maku inda ta koma xan juyo ni kuma" Da sauri ta shiga ciki sai ga ta ta fito sanye da riga ta yafa mayafi tace "Ku taso mu yi maxa kafin magariba yayi" shi dai Abuturrab sai kallon Jiddah da ta jingina da bango idonta a lumshe yake, Hajiya Fatima ta mike without noticing baccin da jiddah take, Xagawa yayi ya d'an ta6a shoulder dinta ta bude ido da sauri sai kuma ta mike tsaye ganin su Hajiya Fatima sun nufi xaure da Lantana, yayi kasa da murya yace "Baby are you okay?" Ta langwabe tace "Bacci nake ji" Kama hannunta yayi ta xame a hankali suka fita daga gidan... Can cikin Kabala lantana ta kai su, Abuturrab ba abinda ya damesa sai irin portholes da ya dinga shiga da motarsa a anguwan, parking yyi dai dai inda lantana ta nuna masa yana kallon gidan, wanda gidansu na hayi ya fi sa mutunci da daraja sau 100, Hajiya Fatima ta sauka motar Lantana ma ta sauka tace "Toh kun ga inda take yanxu, Allah ma ya sa ta dawo daga baran, amma ku shiga Bibalo na nan na sani tunda bbu inda take iya fita ciwo yaci karfinta" Abuturrab ya jawo Jiddah dake xaune gefensa yace "Baby are u sure Tse tse fly bai cije ki ba kuwa" Buda ido tayi da sauri sai kuma ta turo baki tace "Me ka ce?" Yace "Aa cewa nayi mun kawo..." Bin anguwan ta dinga yi da kallo kafin ta bude motar ta sauka, shi ma ya sauka, Lantana tace "Toh kunga ai gwara in yi wucewana ko?" Abuturrab ya ciro dubu uku ya mika mata yace "Mun gode" Har kasa ta risina ta amsa tana masa godiya.... Hajiya Fatima ta shiga d'an karamin tsakar gidan wanda ke dauke da kananun dakuna hudu, ga wani makeken kwata a tsakiya sai doyi yake, kallon wata mata dake daka a d'an mitsitsin tsakar gidan tayi tace "Ina yinin mu?" Matar tace "Wa ake nema?" Hajiya Fatima tace "Hansatu" Matar tace "Aiho bata dawo 6ara ba kuwa, amma kilan tana hanya yanxu" Jiddah dai na tsaye gefe duk jikinta yayi sanyi, yanxu wannan gidan su Baabarta suka dawo?? Hajiya Fatima tace "Ina dakin ta?" Matar ta nuna mata wani daki da babu ko labule tace "Ga ya can, er ta na ciki ma ai" Hajiya Fatima ta nufi kofa Jiddah na biye da ita, tun da Abuturrab ya shigo yayi arba da wannan gutter din ya fice daga compound din da sauri, Hajiya Fatima ta ciro wayarta tana haska dakin sbda duhu ta ga Bibalo da ta dawo uwa skeleton a can kan wani yamutsen karamin katifa irin ta yan boarding a kwance, babu komai cikin dan karamin dakin da duk cement din kasa ya dagargaje sai wasu bakaken Ghana must go biyu, da kwandon kwanuka da risho, Jiddah ta kasa karasawa cikin dakin xuciyarta na bugawa tana kallon Bibalo with shock, Hajiya Fatima dake kallonta ita ma ganin idonta biyu tace "Sannu" Kai kawai Bibalo ta gyada, Jiddah ta kasa cewa komai hawaye ya hau sintiri idonta ta xube nan kasa ta hade kanta da gwiwa abubuwa masu yawa na dawo mata a kai, Hajiya Fatima tace "Mamarki fa?" Murya can kasa wanda idan ba ka saurara ba ma baxa ka ji ba Bibalo tace "Bata dawo bara ba" Hajiya Fatima ta dinga furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a xuciyarta, Sallama Hansai tayi a tsakar gida Hajiya Fatima ta juya da sauri tana kallonta, ita kuwa tsaye tayi tana mamakin wanda ya kawo masu wnn fitila me uban haske da ya haska daki haka ga kuma takalma ta gani bakin kofa, Hajiya Fatima tace "Sannu da xuwa" kasa karasowa tayi kana ganinta kasan a tsorace take, Hajiya Fatima tace "Ki karaso mana... baki ne daga cikin gari, babu abinda ya kawo mu sai alkhairi" Hansai ta shigo dakin da kyar tana dogara sandarta tace "Wa ku ke nema" Tuni Jiddah ta dago kanta tana jin muryan Hansai na mata echo a kunne, and she remembered nothing but those days, those days she was her slave, those days that she was under her prison, memories marasu dadin tunawa ne suka yi ta dawo mata... hawaye masu xafi suka dinga xuba idonta, Hajiya Fatima ta haska ma Hansai Jiddah, Hansai ta saki roban baranta da sandan hannunta cikin rawan murya tace "Jiddah??" Mikewa Jiddah tayi da kyar tana kallonta hawaye na saukowa idonta, Bibalo ta fara kokarin xaunawa ita ma bayan hasken fitila ya gwada mata fuskar Jiddah amma ta kasa kawai sai ta hakura tana ta kallon Jiddah babu kiftawa, juyawa Hansai tayi, tayi backing Jiddah bata sake cewa komai ba, Jiddah ta dinga share hawayen da ya ki tsaya mata cikin sanyin murya tace "Ina yini Baabarmu" Kamar jiran jin hakan Hansai take ta fashe da kuka tace "Ni babu wanda ya ta6a xaunar da ni ya nusar da ni a kan kamun da Allah ke ma duk wanda ya ci amanar maraya ko ya xalunci maraya, babu wanda ya ta6a nusar da ni, da na samu me nusar dani da ba haka ba.... Yau ga yanda rayuwata da na 'ya ta tilo da nake bala'in so a duniya ya dawo, kaico..." Kuka take tana girgixa kai tace "Lallai Allah baya yafe hakkin wani..." Hajiya Fatima dai tayi shiru, Jiddah ta durkusa kasa tana kuka sosai tace "Ni baki ta6a min komai ba baabarmu, idan ma kin min ni na yafe maki tun tuni saboda ke mahaifiyata ce" Hansai ta juyo ta xauna kasan dakin hawaye na xuba idonta tace "Kin ga yanda rayuwa ta juya mana baya ko Jiddah, ba komai bane illa hakkin ki, idan ma ni ban cancanci yafiyar ki ba, ki yafe ma er uwarki Bibalo ubanku daya..." Jiddah ta hade kanta da gwiwa ta ma kasa ce mata komai sbda kuka, Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "Hansatu ai da Jiddah bata yafe maku ba da baxa ku ganta a nan ba, rike kun da bata yi a xuciya ba yasa ta taho har inda ku ke yau...." Hansae na share hawayenta tace "Ai kuwa na gode, na gode, Allah ya ji kan mahaifanta..." Bari in shimfida maku abu ku xauna, da sauri ta tashi ta dauko wani bugun cement ta shimfida masu, Hajiya Fatima ta xauna, Hansae ta koma can gefe ta rakube, Hajiya Fatima ta kalli Jiddah tace "Je ki ki kira Aliyu" Tashi tayi da kyar ta fita xuwa kofar gida. Fitowa Abuturrab yyi daga mota yana kallon Jiddah ganin hawaye idonta, ta sunkuyar da kanta ta nufesa ta rufe fuskarta jikinsa wasu hawayen na xuba idonta, bin wajen yayi da kallo ganin da mutane ya bude back seat ya sa ta shiga shima ya shiga ya kulle motar ya rungumeta a rikice yace "Why are u crying?" Kuka kawai take ta kasa ce masa komai tana kallonsa, duk tunaninsa Hansai ce tayi mata wani abu don ya ga shigarta gidan, ganin xai fita motar ta rikosa ta boye fuskarta jikinsa tana shessheka tace "I don't know what would have become of me da ace baka shigo rayuwata da wuri ba, I don't know what my fate will have been..." Kasa ci gaba tayi ta rungumesa sosai tana kuka, da damuwa yace "I am begging you Jiddah, forget the pass and face the future, forget ur pass... iyayenki mutanen kirki ne shi yasa Allah bai bar ki kin tagayyara ba..." Gyada masa kai kawai take hawaye na sauka idonta, ya dago kanta yayi kissing lips dinta yayi kasa da murya yace "Say Alhamdulillah for everything wife" Cikin sanyin murya tace "Alhamdulillah" yace "Ba xa ki sake shiga gidan ba kuma, u wait for us har mu fito" Tace "Noo plss, ban yi magana da kanwata ba" bai saurareta ba ya sauka motar ya kulle ya wuce cikin gidan don baxai iya jure ganinta tana kuka ba, Ba tare da ya kalli Hansai ba ya gaisheta yana tsaye a dakin, ita ma din dai ta kasa kallonsa sai sunne kai take, Hajiya Fatima na kallon Hansai tace "Ina jin ki Hansatu" A hankali Hansai tace "Toh wllh iya abinda na sani kenan Hajiya, amma da xa a gano inda kakar Jiddan tayi aiki nasan su mutan gidan baxa su rasa sanin wani abu a kan kakar ba don a can ma aka ba Marigayi isuhu auren Marigayiya Aisha wato mahaifiyar Jiddah, yanxu haka ma ina da hotan kakar tata da mahaifiyarta, ita Aishan ta bani hoton da kanta ana sauran watanni ta rasu wai in ajiye ma Jiddah, amma ban ta6a nuna ma Jiddah hoton mahaifiyarta ba" Tana magana ne tana goge sabon hawayen dake xuba idonta, Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh ko xaki bamu hoton..." Mikewa Hansai tayi ta bude Ghana must go dinta ta tono har can kasa ta ciro wasu hotuna, Hajiya Fatima na ta haska mata da wayarta har daga karshe tace "Toh ga hoton nan" Amsa Hajiya Fatima tayi tana ta kallon hoton Mahaifiyar Jiddah wanda da ace kyan mahaifiyar ta tayi da ba haka ba, babu ta inda take kama da mahaifiyarta da kakarta wanda hakan ke nuna cewa da Abbanta tayi kama, can ta girgixa kai tace "Allah sarki, amma ke baki da masaniyar inda tace maki kakar Jiddan tayi aikin? Wato ita Marigayiya" Hansai tace "Wllh ban sani ba, wanda xai san gidan dama Isuhu ne, Kuma rai yayi halinsa" Hajiya Fatima tace "Toh shkkn mun gode, xa mu tafi da hoton a ga abinda hali xai yi" A hankali Hansai tace "Toh shkkn Hajiya" Hajiya Fatima tace "Ita wannan yarinyar taki kin kaita asibiti kuwa?" Hansai tace "Ina muka ga kudin asibiti Hajiya?" Sai kuma ta fashe da kuka sosai, Hajiya Fatima tace "Babu damuwa in sha Allah, gobe ko ni kadai xan dawo nan sai in baku abinda xan baku a kai ta asibiti, Allah ya tashi kafadunta" Hansai na matsar hawaye tace "Ameen Hajiya" Abuturrab ya juya ya fice daga dakin don shi ko kadan bai ji tausayin Hansai ba idan ya tuna irin gallazawan da ta dinga yi ma Jiddah sai yaji ransa na baci, Hajiya Fatima ta mike tayi masu sallama ta bi bayansa. Bude back seat yayi ya ga Jiddah na bacci, kallonta ya dinga yi with surprise, Hajiya fatima da ta karaso wajen tace "Kyaleta kar ka tasheta" Bai ce komai ba ya shiga driver seat tace "Baxa ka tsaya kayi magrib ba son?" Yace "Aa bari mu tafi Mama, xanyi a gida" Dai dai kofar gidan Hajiya Fatima Abuturrab yayi parking, ya juya yana kallonta yace "Mun gode sosai Mama Allah ya saka da alkhairi, we appreciate ur effort" Tace "U are welcome son, ga hoton ka ajiye wajenka, sai kuma mu ga abinda Allah xai yi" Ya amsa yace "In sha Allah" daga haka ta sauka ta shiga cikin gidanta shi kuma ya juya xuwa kofar gidansa, mai gadi ya bude masa gate ya shiga ciki yayi parking ya sauka ya bude back seat yana kallon Jiddah yace "Jiddah" Dagota yayi ta bude ido da sauri, sauko da ita yayi daga motar ya kulle suka wuce ciki, Da kyar Jiddah ta iya jira aka yi Isha sannan ta kwanta ko wanka bata yi ba. Horn Abuturrab yyi kofar gidan Umma misalin karfe sha biyun rana, ana bude gate din gidan ya shiga yyi parking, har sannan bai nuna ma Jiddah hoton mahaifiyarta da kakarta ba, cause bai son duk wani abu da xai sa ta kuka, barin yanda ya ga duk bata da wani kuzari, don ko d'an aikin da take yi ma yau bata yi ba, shi ma kuma bai tasheta tayi ba breakfast din ma shi ya tafasa ruwan shayi dama da akwai bread, sai karfe sha daya ya tasheta ya sa ta shirya suka taho gidan Umma don yana son kai ma Umma hoton, tana biye da shi suka shiga parlon da sallama Umma dake xaune da Ahmad ta amsa sallaman tana kallonsu, har ranta taji dadin fresh din da taga Jiddah tayi, Jiddah dai ta sunkuyar da kanta ta karasa parlon ta xauna amma gaba daya she was uncomfortable da aroma din abinci dake shigowa parlon don a bude kitchen din yake, tun tana daurewa har ta kasa ta mike da sauri tayi hanyar dakinsu Maimoon, Umma ta bi ta da kallo tace "Lafiya?" Tashi Abuturrab yayi amma sai ya ji kunyan Umma bai bi ta ba, shi kam Ahmad bin ta yayi da kallo, Umma ta mike ta bi bayanta da sauri, Ahmad ya kalli Abuturrab yace "Toh ka kyauta" Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank youAbuturrab na kallon Ahmad confounded yace "For What?" Ahmad ya ki ce masa komai, hakan yasa ya nufi dakinsu Maimoon amma ya kasa shiga ciki ya tsaya nan bakin kofar dakin, dariya kawai yake ba Ahmad ganin yanda duk ya wani damu, lkci lkci Ahmad ke juyawa ya kallesa yana tsaye har sannan a bakin kofar gashi ya kasa shiga, bayan 10-15 minutes Umma ta fito daga dakin, da sauri Abuturrab ya koma baya yana shafa kansa, Umma tayi masa kallo daya ta karasa cikin parlon ta xauna fuskarta babu yabo babu fallasa, ya d'an saci kallonta sannan ya shiga dakin bayan ya bude kofar a hankali ya rufe, kwance ya same Jiddah kan gado tayi backing dinsa, ya xagaya inda take ya durkusa da damuwa yace "Did u throw up baby?" A hankali ta bude ido tana kallonsa, ya dagota xaune ya xauna gefenta yace "Amai kika yi?" Ta gyada masa kai, da mamaki yace "But u ate nothing today, u took just Lipton... are okay?" Ta kwantar da kanta jikin shoulder dinsa cikin sanyin murya tace "Bana son kamshin miyan da ake yi ne, but i am okay" Da mamaki yace "Why? What about the Aroma?" Ta buda hannu tace "Nima ban sani ba, pls mu wuce gida" kamar xata masa kuka tayi maganan, Yace "Right away baby, bari in yi magana da Umma sai mu wuce" Ta gyada masa kai kawai, ya kwantar da ita gently yana kissing dogon hancinta sannan lips dinta yace "I love you" Lumshe ido tayi, tayi murmushi kawai, xai tashi ta rikosa murya can kasa tace "I want shawarma pls" Ya koma jikinta ya shafa belly dinta ya kwantar da murya yace "Right away baby" Daga haka ya mike ya fita dakin. Umma na kallonsa bayan ya shigo parlon tace "Kun je asibiti ne?" Yace "Aa Umma she is fine da muka fito gida, may be there is something she perceived that she doesn't like, but she isn't sick" Umma dai ta ta6e baki tace "Na ga alama ai" shi dai Ahmad kansa na kasa yana murmushi, Abuturrab ya mike ya ciro hoto a aljihunsa ya mika ma Umma, Umma ta amsa tana kallon hoton, sai kuma ta kallesa tace "Who are they?" Yace "Jiddah's Mum and Grandmum" Umma na kallonsa da mamaki tace "Ina ka samo?" Yace "Jiya mun je can wajen stepmom dinta shine ta bamu" Umma tace "Ikon Allah, toh ta gaya maku wani abu a kansu ne?" Yace "She knows nothing, ta dai bamu hoton kawai..." Umma tace "Allah sarki, but this will be too hard, Ta ina kake ga xa a fara yanxu?" A hankali yace "I don't know too Umma, nima naga da kamar wuya lamarin" Umma dai tayi shiru, can tace "Toh Allah ya kawo mana komai cikin sauki kawai, i will keep d picture with me" Yace "To Umma" Tace "Allah ya sa a dace" Yace "Ameen" Ahmad dai sai kallonsa yake, Abuturrab ya shafa kansa yana kallon Umma yace "Xa mu koma yanxu Umma" Umma tace "Toh na hanaku komawa ne.... Nayi ta xuba maka ido in ga gudun ruwanka a kan karatun ta naga kamar baka san a saka maka ido ba, gaya min me kake nufi da rashin barinta ta koma makaranta?" Yayi shiru sai kuma ya sunkuyar da kai yace "Xata fara Umma" Umma tace "Aa ka ajiyeta kayi ta kallo dai, shashasha kawai, kai da baka yi karatun ba xaka kai matsayin da kake yau, ance maka kowa ke karatu don aiki? To wllh kayi gaggawar mayar min da yarinya makaranta" a hankali yace "Toh Umma" Sannan ya mike, shi dai yasan iyakar to din nan bakinsa... Dakin su Maimoon ya nufa ya bude dakin, Bacci ya sameta tana yi ya karasa ya xauna kusa da ita yana shafa fuskarta ta bude ido da sauri kama hannunsa tayi kamar xata yi kuka tace "Are we not going home now?" Yace "We are baby" Ya dagota ya dau veil dinta ya mika mata ta amsa suka fito parlor, Jiddah ta gaida Ahmad ya amsa da murmushi fuskarsa yace "Ya jiki?" Abuturrab ya kallesa yace "She isn't sick" Ahmad ya gyada kai yace "Ohh yes" Abuturrab yayi ma Umma sallama, Jiddah ta karasa kusa da Umma ta durkusa tace "Umma xa mu tafi" Umma tace "Toh Allah ya tsare, ki dinga daurewa kina cin abinci ko yaya ne, kuma ki dinga kama jiki ba wannan lagwai lagwai da kike ba..." Cikin sanyi tace "Toh Umma" Umma tace "Allah ya kara lafiya" Shi dai Abuturrab kallon Umma yake, why are they even thinking she is sick, Jiddah ta kalli Umma tace "Su Maimoon fa?" Umma tace "Sun je saloon" Jiddah tace "Umma wai number me turaren da kika siya min ake tambayata" Umma tace "Wa ke tambayar ki?" Murmushi tayi tace "Wata Mama ce, she is our neighbor, ta shigo shekaranjiya shine tace kamshin yayi mata dadi in bata number me turaren" Umma tayi dariya tace "Lallai kam, ni ina xan rike number me turare, kije daki akwai wani container na turaren in jin akwai number me turaren a jiki" Tashi tayi ta tafi daki sai ga ta ta fito da daya daga container din turaren dake dakin Umma wanda a jiki aka rubuta _S_Square-Incense_ , tana kallon Abuturrab dake tsaye tace "Xaka min saving number a wayarka sai in ba mama pls" Ya ciro wayarsa yana kallonta kiris ya rage yace "Ur wish is my command Baby" kawai ya kalli Umma sai yayi maza yayi shiru, a hankali yace "Alright" Jiddah ta maida idonta kan container ta kira masa number 07030037697.... Bayan yayi saving yace "Done" Mayar ma Umma container din tayi sannan ta fito, suka kara ma Umma sallama, Jiddah na kallon Ahmad tace "Yaya Aunty Ramlah fah?" Yace "Tana gida, kin ki xuwa mana ai" Tana murmushi tace "Xan xo" yace "Ai kam xaki xo kwanan nan ai ko babu niyya" Ahmad ya rakasu har bakin mota, bayan Jiddah ta shiga front seat yana kallon Abuturrab yyi lowering voice dinsa yace "Reduce bothering her or u loose the Baby" Abuturrab ya kallesa da mamaki yace "Which Baby?" Ahmad ya daga kafada yana murmushi yace "Sai mun yi waya" Daga haka ya shige gidan, Abuturrab ya tabe baki ya xaga ya shiga motar suka bar anguwan. Sai da ya biya ya siya mata shawarma da tace tana so ya hada har da ice cream sannan suka dau hanyar gida... A hankali yake tafiya a motar ganin kamar Aneesah a kofar gidansa, ai ko yana isa dai dai gate din nasa ya ga ita ce, horn yayi mai gadi ya leko ganin motarsa ya bude gate din, Aneesah ta taso ta nufo motar da sauri, yayi zooming off into the compound, mai gadi na hanata ta hankade sa ta shige cikin gidan, Abuturrab yayi parking a parking space ya bude motar ya sauka, kasa karasawa kusa da shi Aneesah tayi hawaye na sauka idonta ta durkusa tace "Don girman Allah ka tsaya ka saurareni ko na minti biyu ne Aliyu" Abuturrab ya nufi mai gadi yana kwala masa kira a fusace, mai gadin ya taho da gudu bayan ya rufe gate din yana amsa kiran, Abuturrab na huci yace "Me nace maka a kan matar nan Salisu?" Mai gadin yace "Wllh wllh bude maka gate da nayi ne ya bata daman shigowa ciki amma kusan kullum sai ta xo kofar gidan nan har ma ta yini, ko da wasa ban ta6a bude mata gate din ba yallabai" Abuturrab ya juya yana kallon Aneesah dake durkushe tana hawaye da white bandage a hannunta, strictly yace "Look Madam.. i will assume ban ta6a sanin ki ba a rayuwata, and i think i have to report you to the police to stay away from my house because i don't know who u are, i don't know what u are up to, this my take on you... don haka tun muna mu biyu tashi ki fitar min daga gida kada in nuna maki the other bad side of me.... About ur luggages or whatever xan fito da su nan tsakar gida kusa da parking space a rufe su da sheath and anytime aka ganki da babban mota sai a bude maku gate ku kwashi kayan ku" kuka kawai take tana girgixa masa kai tace "Aliyu ka bani minti biyu don darajan iyayenka ka saurareni" Fiercely yace "Get.. out... Of my house" Ta ki tashi tana rusa kuka tana kallon Jiddah tace "Don Allah ki sa baki ya saurareni Jiddah...." a guje ta mike ganin ya nufota, tayi gate da gudu ta fita mai gadi ya kulle gate din, juyawa Abuturrab yayi yaga Jiddah tsaye, ta juya a hankali ta nufi entrance din gidan, ya bude motar ya dau abubuwan da ya siyo sannan ya bi bayanta. Bayan isha Jiddah na kwance jikin Abuturrab dake kallon wrestling a parlor, bata dade da tashi daga baccin da take tun yamma ba, ya dago kanta da damuwa yace "Baby duk yau fa baki ci komai ba, nace ki gaya min me kike son ci kada dare yayi in fita in samo maki plss" Tace "Bayan shawarman da na ci?" Yace "Noo u ate just a bite..." tace "Hakan da na ci ya isheni" Yace "I'm beginning to think if u are really okay..." Tace "Toh kasan me xan ci?" Ya xaunar da ita da kyau yace "Tell me wife, ko kano ne xan je yanxu in samo maki abinda kike so in dawo" Murmushi tayi, tayi lamo jikinsa tace "Indomie nake so with plenty Scotch bonnet pepper, with onion" Yace "Ohk xa mu iya samu a restaurant ai, bari inje in nemo maki in dawo yanxu" Ta dago kanta tayi masa wani kallo tace "Ni dai kai nake so ka dafa min, idan aka siyo a waje baxan iya ci ba" Ya d'an buda ido da mamaki yace "Really" Ta marairaice masa, ya lumshe ido ya bude yace "But idan bai yi dadi ba fa kinsan ni ba girki na iya ba baby, ba gwara in je in samo maki me dadi a duk inda yake ba yanxu" Kwanciya tayi kan kujera ta turo baki tace "Baxan ci ba" Yayi shiru yana kallonta, sai kuma a hankali yace "Ohk... But I don't know all the ingredients u listed..." tace "I will show u" tashi yayi ya nufi kitchen ta mike ta bi bayansa, tana tsaye ta jingina da cabinet ya dauko indomie din a store, ta nuna masa albasa da uban tarugun da take son yayi mata amfani da, yayi ta kallonsu yace "Are they not too much, anyway ya xan yi masu yanxu?" Tace "Wankesu xaka yi" Da wani expression yace "With gloves or what?" Tace "Ka ta6a ganin an wanke pepper da gloves?" Innocently yace "But it's harmful for the bare hands, ba yaji garesa ba? Ba shine tattasai da ake cewa ba" Tace "To da hannun xaka wanke ka cire duk hancin, ka yanka albasan" Ya fi minti daya yana bin tarugun da kallo sai kuma ya dauka yaje sink yana wankewa a hankali, tace "And baka sa ruwan indomie din ba a wuta ai" Yace "Ohk" dawowa yayi ya kunna gas ya daura ruwa a tukunya ya rufe, ya ga ta fita ta ya bi ta da kallo yana mamakin wannan aikin da ta sa shi da bai ta6a yi ba a rayuwarsa, bai ma ta6a tunanin akwai ranan da xai shiga kitchen da sunan ya sarfa abinci ba sai first night dinsu da ya shiga ya soya kwai sannan yau da tace dole shi xai yi mata indomie, ya langwabe kai yace "And i have to make it very delicious for her" Dawowa kitchen din ya ga tayi da kujeran dinning ya dinga kallonta da mamaki, ta ajiye ta xauna tsakiyar kitchen din tana kallonsa, bayan ya wanke pepper din ya juya ya kalleta yace "Toh ya xan yi da shi?" Hannu ta buda alamar bata sani ba, ya ciro wayarsa a aljihu ya shiga google... Sosai Abuturrab ya wahala kafin ya hada wannan indomie na yan gayu da Jiddah ta sa shi, idonsa sai yaji yake masa sbda albasa, ita dai ko uffan bata ce ba sai bin sa take da kallo, duk yayi kaca kaca da waje kamar kwali biyu na indomie ya dafa, ta dinga kallon indomien da ya juye a plate sai uban ruwan da ya cika kamar farfesu ga Indomien har yayi extra done, da liquid soap ya dinga wanke hannunsa a sink sannan ya juya yana kallonta a hankali yace "Na gama baby" ta tashi tace "Toh ka kawo" daga haka ta fita ta tafi parlor ta xauna, ya sauke ajiyar xuciya ya fitar da kujeran da ta shigo da ya mayar dinning sannan ya dawo ya dau indomie bayan ya saka fork a ciki ya fita ya kai mata ya ajiye gabanta, ya koma fridge ya dauko ruwa da lemon five alive ya dawo ya ajiye yana kallonta, daukan fork din tayi ta fara cin indomie din a hankali, ko taste din kirki babu sbda uban ruwan da ya cika, haka tayi ta cin abunta, ya ji dadi sosai ya xauna saman kujera yana kallonta, sai da ta ci rabin indomie din taji xuciyarta ya fara tashi ta jinginar da kanta da kujera yace "Baby what?" Ta kallesa sai kuma ta tashi ta tafi kujeran da yake ta xauna ta kwanta kusa da shi tace "Amai nake ji" Ya rungumeta yana buga bayanta gently yace "Amai kuma baby bai maki dadi bane" Tace "Yayi" haka ya dinga yi mata har taji aman ya daina damunta, ta lumshe ido jikinsa tace "Yayi min dadi sosai" murmushin jin ddi yayi yana shafa gashinta yace "I am happy my baby like it" Da safe Abuturrab ya tashi da farin ciki wanda baya misaltuwa don faduwa ce ta xo mashi dai dai da xama, Jiddah na bacci ya shirya ya tafi gida wajen Umminsa... bayan ya gaisheta ta amsa tana kallonsa ganin how good his mood was, tace "Ina Jiddar?" Yace "Tana gida Ummi" Ummi tace "Toh maa sha Allah, baka koma aiki bane?" Yace "Dama na xo ne in gaya maki aikin da na nema few years back na samu offer dinsu sun turo min ta mail... daxu na gani da asuba" Da mamaki Ummi tace "Wani aiki?" Yace "Piloting also, a private pilot, ko kin mance sanda nayi applying?" Ummi tayi shiru sai kuma tace "License or certificate din fa Aliyu, isn't it cost?" Yace "Nahh, i got that since Ummi, may be u forgot" Tace "So u mean u are tired of being an Airline transport pilot?" A hankali yace "I need more time for my self and family Ummi, i have served them in the sky for long, so xanyi resigning yanxu..." Ummi tace "Toh Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi a gareka" Yace "Ameen Ummi" Wayarta ne ya fara ring ta dauka ganin Umma ke kiranta ta daga ta kai kunne, bayan sun gaisa Umma tace "Toh munyi grandson" Ummi tace "A'a toh Alhmdlh, Alhmdlh, yaushe ta sauka?" Umma tace "Few minutes ago" Ummi tace "Toh Allah ubangiji ya raya mana, Allah yayi masu albarka" Bayan sunyi sallama Ummi ta kalli Abuturrab tace "Ramlah ta haihu" Yace "Maa sha Allah, Allah ya raya, i left my phone at home kilan Ahmad din ma ya kirani" Ummi ta mike tace "Bari in sanar ma Hajja" Daga haka ta fita daga parlon. A ranan kamar yanda Abuturrab ya fada da rana ya kira masu fitar da kayan Aneesah ya sa aka ajiye mata su kusa da parking space sannan aka lullube da Sheath din, Jiddah dai na xaune parlor don ya sa ta shirya xa su fita amma bai ce mata ga inda xa su ba, tana ta kallon yanda ake fitar da kayan Aneesah, har lkcn she is speechless she don't even know what to say to Aliyu, she don't know why she felt bad about everything that have happen, duk da bai gaya mata abinda ya sa shi sakin Aneesah ba amma har ranta bata ji dadi ba, bayan yan fitar da kayan sun gama ya sallamesu sun wuce ya dau makullin motarsa ya sauko downstairs yana kallon Jiddah ya nufeta, yana jan hancinta yace "Mu je ki ga baby" Tace "Wani baby?" Ya kashe mata ido yace "Ramlah ta haihu" tashi tayi da sauri tana wara ido tace "Don Allah da gaske?" Yace "Yea" kasa boye farin cikinta tayi tace "Shine baka gaya min tun daxu ba... Ni dai don Allah mu je ka kai ni" ya kama hannunta suka fita daga gidan, da yake an sallamesu asibiti gidan Umma suka wuce, Jiddah ta wuce dakin Umma direct bayan Maimoon ta sanar mata Ramlah na ciki, Hajja na rike da jaririn tana shiryasa bayan ta gama masa wanka ta kankance ido tana cewa "Mata ki dinga abu isa isa da gadara kamar ni bare ce wajen Ramlar, toh dai ni na haifi uban Ramlah don haka ban ga ta inda kika fi ni kusanci da ita ba, kuma in don ta kece ma baxa ki gan ni gidan nan ba, to ina ruwana da wani Ahmad, ni sabida jikata na xo, daga nace a hada ma yaro gulucodi a fida sai ki kama min fitina, aa ni baxan biyeki ba aniyarki ta bi ki...." Ko kallonta Umma bata yi ba tana ta gyara sabon siff din baby, Ramlah kuma na kwance tana bacci kan gadon Umma, Hajja na ganin Jiddah tace "Xan dai ga uban da xai ce min haka xanyi ko ba haka xanyi ba idan matar Aliyu ta haihu... Ko ita Hauwan sai in tsine mata albarka idan tace xata min shisshigi a lkcn balle ke" kwafa tayi tace "Allah dai ya bamu lafiya ai kamar gobe ne, xan nuna ma kowa ni er banxa ce a lkcn" Jiddah ta durkusa ta gaida Hajja tana kallon kyakkyawan yaron hannunta, Hajja tace "Ga can jakata ki budu ki jera min kayana a kambodin Ramlah, atamfa a gefe, leshi a gefe, mayafan kuma ki saka su a tsakiya, basu fi kala ashirin ba kayan" Jiddah ta juya tana kallon katon jakan da Hajja ke nuna mata. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp Jiddah dake xaune gefen gado rike da Babyn Ramlah a hannunta ta kauda kanta da sauri ganin abinda ke hannun Huraira me aikin Umma, Huraira ta karaso ta ajiye plate din tuwo da miyar agushi a kusa da Hajja, Hajja ta kalli Umma dake hada ma Ramlah shayi tace "Toh kin ga rashin d'a'an maimakon a bani girmana a xubo min abincin a cooler na tuwo da miya amma an kawo min tuwo a plate kamar almajira miya kuma na galantoyi a plate, to dai ya fi babu wai d'an agwai da bak'in da" Umma dai bata ce komai ba ta gama kada shayin ta mika ma Ramlah, Hajja ta kalli Jiddah da ke kallon wani side din daban aroma din miyan na damunta tace "Ki ajiye masu yaronsu kiyi ta kanki ki xo mu ci abinci, yaron da ake ta nuna mana fin karfi kamar d'an gwal..." Jiddah ta kasa juyowa ga amai dake taho mata, Kafin Hajja ta sake cewa komai ta kwantar da jaririn da sauri ta ajiye gyalenta xata fita Umma dake lura da ita ta nuna mata bandakinta tace "Shiga nan" Dawowa tayi ta shiga bandakin Umma da sauri ta hau kwarara amai, Hajja da ta bi ta da kallo ta saki baki har sai da Jiddah ta fito bayan minti biyar, kwanciya tayi saman carpet din dakin tana maida numfashi, Hajja tace "Sai dai da kika bari ya kai ki ya baro kenan er nan?" Jiddah ta daga kai a hankali tana kallon Hajja, Umma na kallon Jiddah tace "Ta shi ki dawo nan" Jiddah ta kalli gadon da Umma ke nuna mata sannan ta tashi da kyar ta hau ta kwanta Ramlah na mata sannu, Hajja ta kyabe baki tace "Toh ai shkkn kuma" 4months later... Cikin bacci Jiddah ta ji ana jan hancinta a hankali, ta bude ido da kyar tana kallonsa, cikin shagwaba tace "Me yasa baka son ka dinga bari na ina bacci ne?" Ya marairaice mata yace "Baccin ya isa haka, tun safe fa, kin barni ni kadai kamar maraya...." Bai jira cewarta ba ya dagota xaune ta sakar masa kuka cike da shagwaba tana turasa tace "Ni wllh baka bari na inyi bacci" rikicewa yayi ya rungumeta sosai yace "I only want to show u something sai ki dawo ki ci gaba da baccin, i am so eager to show u" Tana kallonsa ta turo baki tace "Oya toh meye shi?" Dagota yayi suka mike tsaye, riga ce iya cinya a jikinta, idan kai ba me lura bane ba ma baxa ka san da wannan cikin na jikinta ba, sosai ta kara kyau tayi fresh, kuma ta d'an murmure kirjinta suka cicciko, da kansa ya daure mata gashinta sannan ya matso mata da takalman da take sa wa a daki ta saka yana rike da hannunta suka fita dakin, dakin Aneesah na da ya bude a hankali yana kallon Jiddah da murmushi fuskarsa, wara ido tayi ganin yanda aka gyara dakin for a new born, kamar dai irin gobe xata haihu din nan, gadon jaririn ciki kadai ma abun kallo ne... Dakin yayi masifaffen kyau, yana rike da hannunta suka shiga ciki ya bude press din kaya taga wasu uban kayan baby iri iri masu tsadan gaske, ya ja ta xuwa bathroom nan ma dai complete set iri biyu na kayan wankan jariri ne a ciki, ta juya ta kallesa tana wara ido, rungumesa tayi ta lumshe ido cikin sanyayyan muryarta tace "Thank you my world" Ya kankameta yace "Anything for u and my little pilot wife" Kissing lips dinsa tayi, sai kuma ta hade rai tace "little Pilot dinka kadai ka sani, don ni bani da kowa ko?" Dariya yayi yace "Ai sai mun gama da shi xa mu fara naki babynah" Turo baki tayi tace "Ka dai nuna yan ubanci tunda pilot din ka fara yi ma...." Yana murmushi yana shafa cikinta yace "Mama ta shigo daxu kina bacci" Tace "Me yasa baka tasheni ba?" Yace "Idan na tashe ki ai na tashi Lil pilot ne" Murmushi tayi tace "Toh in je gidan nata yanxu tunda baccin ya fita idona?" Yace "Ba ki ci abinci ba ai" Tace "Aa ban fara jin yunwa ba" Yace "Are u sure babynah?" Tace "Sure dear" Yayi pecking lips dinta yace "let me get you ur hijab, sai ki tafi amma kar ki dade plss, just 5mins ki gaisheta ki fito" Daga haka ya koma dakinta don dauko mata Hijab, ta dinga bin dakin da kallo tana kara jin son captain a ranta, tun bayan da aikinsa ya dawo twice to 3 times a week take samun kulawa na musamman daga garesa a ko da yaushe yana makale da ita, always there for her, komai shi yake mata, hakan yasa shakuwansu ya karu sosai... Ba a dau lkci ba ya dawo da hijab dinta da wata doguwar rigan, duk shi ya saka mata sannan ya rakata har bakin gate kafin ta fita ta kallesa cike da shagwaba tace "Plss ka dafa min white rice kafin in dawo ina son in ci da mai da ya ji" Yace "Right away baby" Daga haka ta fita shi kuma ya koma gidan ya shiga kitchen kamar Ummi ta sa shi aiki. Kasancewar ranan asabar ne su Khaleesat duk sun tafi makaranta, babu kowa downstairs sai mai aiki, bayan sun gaisa Jiddah ta xauna a parlon, mai aikin kuma ta tafi sama sanar ma Mama xuwanta, Jiddah na ta xaune ita daya parlon har taji shigowar mota compound din gidan, bayan few minutes aka bude kofar parlon ta daga kai, wani Dattijon da baxai wuce shekaru 73 ne ya shigo parlon da sallama hannunsa rike da karamin jaka, kallonsa Jiddah ta dinga yi babu ko kiftawa kamar idanuwanta xa su fito, can ta mike tsaye da sauri, ya karaso parlon shi ma dai yana kallonta, bata san sanda ta fasa wani kara a tsorace ba, dai dai fitowar Hajiya Fatima, tsaye Dattijon yayi daga inda yake yana kallon Jiddah da mamaki, Hajiya Fatima ta karaso da sauri tana kallon Jiddah tace "Lafiya Jiddah what happened?" Tana isowa dai dai wajen Jiddah taga ta sulale kasa, rikota tayi a raxane tana kiran sunanta tana kallon mai gidan nata, shi dai yana tsaye inda yake bai karaso ba yana ta kallonsu, Hajiya Fatima ta kallesa cikin tashin hankali tace "What just happened Yallabai, me ya faru da ita?" Yace "Shigowata kenan fa, and at first i tot Khadija ce, who is she? She just shouted after seeing me sai kuma tayi collapsing" Hajiya Fatima ta dinga kwala ma first daughter dinta kira, mai aiki dake tsaye gefe ita ma a tsorace ta tafi sama da gudu ta kira Aunty Rahama, Aunty Rahama na shigowa parlon ganin Jiddah kwance kasa a hannun mamanta ta xaro ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me ya faru mama, me ya sameta?" A rikice Hajiya Fatima tace "Ban sani ba wllh Rahama, ki dauko makullin mota mu tafi asibiti, Ali baya nan, quickly get the car key mu tafi asibiti kawai plss" Alhaji Ishaq dai na tsaye yana kallon ikon Allah, gaba daya mamaki ya gama cikasa, Da gudu Rahama ta tafi sama dauko makullin mota sai ga ta ta dawo har da mayafinta jikinta na rawa tace "Na dauko mu tafi Mama" Hajiya Fatima ta mike da sauri tana ce ma mai aiki tayi maxa maza ta dauko mata Hijab dinta, Aunty Rahama na daga Jiddah suka ga jini kwance a kasanta, Da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kin ga mama" Hajiya Fatima ta kwalo ido a tsorace tana kallon jinin tace "Na shiga uku na lalace, meye haka??" sai kuma ta fashe da kuka tana salati tace "Meye haka ni Fatima, me ya sameta" Alhaji Ishaq da shi ma hankalinsa ya tashi ya ajiye jakarsa da sauri yace "Ku fito da ita mu wuce asibiti, hurry pls" Juyawa yayi da sauri ya bar parlon. Hajiya Fatima na xaune a bakin emergency room tayi tagumi, ta dade bata shiga irin wannan tashin hankalin ba, ta ma rasa wani tunanin xata yi in particular, astagfirullah wannan kuma wani irin jarabawa ne a parlonta, sai a parlonta Jiddah xata fara bleeding? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Rahama na jingine da bango ita ma dai duk hankalinta a tashe fatan ta kada ace Jiddah tayi miscarrying cikin nan, Allah kada ya sa hakan, ko don yanda taga Captain ya kwallafa rai a cikin, don time to time ta kan shiga gidan idan ta dawo daga aiki, tunanin miscarriage ya dinga aika mata da wani goosebumps a jiki, she is so afraid, Alhaji Ishaq da Son dinsa Ali na can reception a xaune all disturbed also, bayan kusan minti talatin wata babban likita ta fito tana kallon Hajiya Fatima tace "Kece mahaifiyarta ai?" Hajiya Fatima ta mike da sauri gabanta na faduwa tace "Ni ce doctor, fatan dai babu matsala" Tace "Ki sameni a office" daga haka ta wuce, Rahama na kallon mum dinta sanin ba komai wani lkcn take iya dauka ba a ranta, ta dakatar da ita da sauri tace "Mama ki bari ni in je ko Ali, ke ba sai kin shiga ba ke" Hajiya Fatima tace "Aa babu komai xan je ni..." Daga haka ta bi bayan likitan da sauri xuwa office dinta, Likitan ta cire glasses din idonta tana kallon Mama tace "Ina shi me gidan nata?" Xuciyar Hajiya Fatima na bugawa da karfi tace "Fatan dai babu wata matsala doctor" likitan tace "Da akwai, don ta samu miscarriage, and she is still unconscious...." Da karfi Hajiya Fatima tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, miscarriage likita? Na shiga uku, yanxu cikin ya xube?" Sai kuma ta fashe da kuka, likitan tace "Kamata yayi kiyi fatan tayi gaining conscious Hajiya ba ki karkata kan miscarriage ba... Did she just slouch down, fall accidentally, or an gaya mata wani labari ne da ya girgixa ta ta fadi?" Kuka kawai Hajiya Fatima take ta ma kasa cewa likitan komai, ta furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ya fi a kirga, likitan ta ajiye pen din hannunta tace "I need to talk to her husband, a turo min shi yanxu..." Cikin kuka Mama tace "Baya asibitin likita... Yanxu shkkn cikin ya 6are?" Likitan ta buga table din gabanta a hankali tace "Kiyi tunanin halin da er ki ke ciki tukun ba ciki ba Hajiya, kiyi hakuri ki d'an fita ki turo min wanda aka yi komai a gabansa, u aren't answering any of my questions Hajiya" Mama ta mike da kyar tana kuka ta fita, Rahama dake tsaye tana jiran fitowar mahaifiyarta ganin ta fito tana kuka a ranta ta shiga furta Innalillahi, shkkn abinda take ta gudu ya faru, Mama na kuka tace "Tayi miscarriage kuma wai she is still unconscious" Ita ma hawayen ta shiga yi tace "Mama ki kira mijinta kawai muna ta yin abubuwa gaban kanmu, a kirasa mama a sanar masa ya taho" Mama ta nemi waje ta xauna tana rusa kukan miscarriage din nan da aka yi a parlonta, Ali ya kasa cewa komai bayan yayarsa ta sanar masa abinda ke faruwa, Alhaji Ishaq dai na tsaye shi ma he is so Speechless, Rahama na goge idonta tace "Call him immediately Ali" daga haka ta juya ta bar wajen, Ali ya ciro wayarsa ya shiga neman number Abuturrab, ba karamin courage yayi gathering ba kafin yayi dialing number, yana fara ring Abuturrab ya daga, Ali yayi karfin halin cewa "ermm Captain dama Jiddah ce bata ji dadi ba, so we rushed her to the hospital immediately" Abuturrab ya mike tsaye daga xaunen da yake xuciyarsa na bugawa yace "Jiddah????" Ali ya runtse ido ya bude yace "Ehh" daga haka ya sanar masa da asibitin da suke ya katse wayar. Tun bayan da Abuturrab ya iso asibitin aka sanar masa abinda ake ciki, ya kasa cewa kowa komai, he was more than shock, yana xaune kan kujera a reception ya rike kansa ya kasa kallon kowa cikinsu, lkci daya idanuwansa suka kada, he was so hurt namijin kokari kawai yake, Alhaji Ishaq yace "Kayi hakuri, haka Allah ya kaddaro, ita kuma sai mu yi fatan Allah ya tashi kafadunta, ya bata lafiya" Hajiya Fatima dai na can gefe ta kasa kallon Abuturrab, tayi kuka har ta gaji er ta na taya ta, Ali yayi patting Shoulder din Abuturrab cikin kwantar da murya yace "U need to be strong Captain, Allahn da ya baku shi xai sake baku..." Abuturrab yayi karfin halin mikewa da kyar, gathering much courage yace "I want to see her plss" Ali yace "Likitan ta sanar min she is sleeping now, amma mu je office dinta mu ji ko xa a iya shiga ward din yanxu" kama hannun Abuturrab yayi xuwa office din likitan, likitan na kallon Abuturrab tace "Kai ne mijin nata?" Kai kawai ya iya gyada mata, tace "Ohk dama da akwai wani abu dake damun matarka ne, or did they break any shocking news to her?" Ya girgixa mata kai a hankali ya kasa cewa komai, tace "Toh Allah ya kiyaye, idan ta samu kanta sosai sai ayi mata wankin ciki, Allah ya kiyaye gaba" Ali yace "Doctor plss xa iya shiga a ganta yanxu?" Likitan tace "Alright shi dai mijin nata ya shiga ya dubata, amma yana dubata ya fito, she need much rest now" Ali yace "Toh mun gode Dr" ta fada masu ward din da Jiddah take, daga haka shi da Abuturrab da ya kasa cewa komai suka fita office din... Shi ya raka Abuturrab har dakin sannan ya xauna kujeran dake ajiye bakin ward din, Abuturrab ya tura kofar a hankali ya shiga ciki, yana isa kusa da gadon ya daura kansa saman pillon, he was really hurt, can ya dago kansa a hankali yana kallonta da idanuwansa da suka kada, cike da karfin hali yace "Get well soon wife, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi" Xaunawa yayi kan kujeran dake ward din ya jinginar da kansa yana jin wani xafi da xuciyarsa ke masa bai ta6a xaton haka ba, can ya ciro wayarsa yayi dialing number Ummi, tana dagawa ya gaisheta, jin voice dinsa tace "Lafiya??" A hankali yace "Ummi muna hospital, Jiddah tayi miscarriage" a rikice Ummi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wani hospital din" Ya sanar mata ta katse wayar tana nanata furta Innalillahi a xuciyarta, can tayi dialing number Umma tana dagawa ta sanar mata sannan ta mike ta fita xuwa dakin Hajja, kwalema ta sameta tana yi da su Nafisah wai taga gilmawan kyankyaso a dakinta, Ummi tayi karfin halin cewa "Hajja yanxu Aliyu ya kirani wai Jiddah tayi 6ari suna asibiti" Hajja ta saki Tsintsiyar hannunta da karfi tace "Li eelafi quraysh, meye kuma 6ari?" *Sorry for the silence yesterday, jiki da jini... Kuma aski in ya xo gaban goshi...* Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppKwanansu daya a hospital aka yi discharging Jiddah bayan an mata Dilation and Curettage, Aunty Rahama na rike da hannun Jiddah suka nufi motar Abuturrab, tuni ya fita da basket na abincin da aka kawo da safe daga gidan Umma, Hajja ta bi Aunty Rahama da kallo sai kuma ta kalli Umma dake yi ma nurses din reception sallama, tayi kasa da murya tace "Ita kuma wannan narkekiyar daga ina? Naga sai wani kai wa take tana komowa, a ina ku ka samo ta?" Umma tace "Makociyarsu ce" Hajja ta rike haba tace "A kasar nan dai naga kamar an maida kiba wata abar ado... Ita Jiddah ina ita ina wannan jigbegiyar mata da ta kusa haihuwanta, wnn ai ta fi ta wayewa da duniyanci, salon taje ta kwace mata miji mu shiga uku? Ai ba wani kiban a xo a gani ne da matar ba balle ace Aliyu baxai iya aurenta ba, tsaff xai aureta su xauna, sannan naga fuskarta na da kyau kamar dai yar yarinya, jikinta kuma luwi luwi alamar hutu ya xauna, to ni dai ba ruwana kilan baku xaunar da Jiddar kun koya mata karatun duniya ba ne ku ka kaita gidan miji, ai ba a yarda da mata yanxu barin irin wa ennan da idanuwansa ya yage har kunne" Umma dai bata ce da Hajja komai ba tana ta tafiyarta, Hajja ta ta6e baki tace "Ni dai bata min ba wllh, wa ya sani ma ko mayya ce ita ta lashe d'an a ciki? banda haka mu kaff xuri'armu babu wanda ya ta6a barin ciki yana karaminsa wllh, kana samun cikinka sai ka haifesa lafiya da izinin Allah, toh sai kuma a fara 6ari a kan matar Aliyu? Aa wllh ni dai na dasa ayar tambaya a kan wnn mata dake shisshige masu, to naga mata tun jiya tana ta sintiri cikinmu kamar wata er uwarmu, wa xai yarda da haka banda ku da baku san ciwon kanku ba, ni don dai kada ace ban kyauta bane na cika fitina, banda haka wllh da na koreta nace imu imu ya isa ta koma gida kawai" A haka har suka isa mota Umma uffan bata ce mata ba, Hajja na kallon Rahama da murmushi tace "Toh mun gode yarinya Allah ya saka da alkhairi, yanxu tafiya xaki yi daga nan dai ko? Don mu gidan ubansa muka nufa" Rahama tace "Ehh Kaka ga motata can, nima gida xan wuce" Hajja ta juya ta kalli motar da ta nuna mata tace "Au haba, toh Allah ya saka da alkhairi, dama don naga ba can anguwan naku xa mu bane shi sa nace bari dai in gaya maki inda xa mu... Naka ma ya samu me kula da shi idan bai da lafiya a wannan xamanin ai abun farin ciki ne, don gaskiya yanxu ba a ba ma makotaka hakkinsa kamar xamaninmu" Aunty Rahama dai murmushi kawai take, can ta kalli Jiddah tace "Toh Allah ya kara lafiya Jiddah, sai na kawo mama can gidan in sha Allah, Allah ya kara afuwa" Jiddah tayi murmushi tace "Ameen Nagode Aunty" Aunty Rahama ta kara masu sallama ta tafi gun motarta, shi dai Abuturrab na xaune driver seat ya kulle, Hajja ta bude bayan motar tana kallon Jiddah tace "Toh shiga" Jiddah ta shiga motar Hajja ma ta shiga, Umma ta xaga xata shiga ta daya side din murya can kasa Hajja tace "Yanxu xata shigo duk ta matsi mutane malam" Kamar kuwa Umma ta ji abinda Hajja ke cewa ta bude front seat kawai ta shiga, a hankali Hajja tace "Toh Alhamdulillahi" Bayan sun d'an yi nisa Hajja tace "Yanxu ina muka nufa naga kana ta wani xagaye xagaye Aliyu" Umma tace "Can gidana xa mu tafi" Hajja tace "Me?? Aje gidanki a kan me? Anya kina tsoron Allah kuwa Ramlah ga dai gidan uwarsa a kai mata yarinya ta kula da ita tana yi nima ina yi xaki wani ce a tafi gidanki? To ni nace gidan Usman xa mu kai ta, ai matar Aliyu ce ba matar wani ba, mata kawai neman fitina yayi maki katutu, me xaki yi ma Jiddan wanda mu bamu iya ba, ni dai wllh kin cika wahala, to gidan Usman xa a kai ta in ji ni, mata duk kin shanye yayarki sai yanda kika yi da ita kina ta mulkanta yanda ranki ya so? To ni dai ba ruwana" Shi dai Abuturrab driving yake a hankali, Umma tace "Idan kaje can bus stop din ka ajiye ni Aliyu" ya d'an kalleta yayi kasa da murya yace "No Umma u just have to ignore her, don't take this personal, as if u don't know who she is" cike da damuwa Hajja tace "Toh wai meye kake bata baki kamar warce aka yi ma laifi dai daga fadan gaskiya, ni fa ba wani abu nace ba, ko kaji na xageta ne?" Umma tace "I said drop me Aliyu" yace "Then let me drop u home kawai, bai kamata kiyi dropping a hanya ba" Ta kallesa tace "Ba ni nace maka haka ba" parking ya nemi waje yayi ganin how serious she was ya juya yana kallonta ta bude motar ta sauka, sai duk Jiddah bata ji dadi ba taji kamar ta sauka motar ta bi Umma, shi dai Abuturrab ya bi Umma da kallo har ta kulle motar tayi gaba, Hajja ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh ba shkkn ba... Yanxu da fada nayi mata ai baxata sauka ba, kaga yanxu da nayi mata bayani cikin nutsuwa tayi wucewarta gida abunta baki alekum" Abuturrab bai tanka ta ba ya ci gaba da driving dinsa, Hajja tace "Kai kuma sai wani cika kake kana batsewa kamar dai mu muka kashe maka jariri Aliyu, toh kai arnene da baxa ka dau tawakalli ba, ita kanta warce d'an ya lalace a cikinta ma ta hakura tana ta fara'a abunta tun a asibiti amma kai sai wani nukurci kake yi kana ba ma banxa ajiyar mu, a hakan kake so Allah ya baka wani? Ai ba a ma Allah haka, da kasan xai baka ne?" Wani harara Abuturrab ya watsa mata ta madubi, Jiddah ta d'an yi murmushi ta sunkuyar da kanta. Da daddare Jiddah na kwance kan gadon Hajja bayan tayi wanka tayi shirin kwanciya, bude kofar dakin aka yi ta daga kai Abuturrab ya shigo dakin ya kulle, ta mike xaune tana kallonsa har ya iso ya xauna gefenta ya kamo hannunta yace "How are you feeling now?" Tace "Alhmdlh naji sauki" Gyada mata kai kawai yayi, da damuwa tace "Are u still sad" ya kalleta amma bai ce komai ba, cikin lallashi tace "Kayi hakuri plss, Allah ya rubuta hakan xai faru... And there is a reason for everything..." Ya d'an yi murmushi slowly yace "Sure wife" Ta rungumesa tace "Cheer up pls dear" Ya marairaice mata yace "Xa ki samar mana wani da wuri plss???" Er dariya tayi tana shafa chest dinsa tace "Sai in ka bani da wuri ae, sai in samar mana da wuri" yayi kasa da murya yace "Yanxu fa??" Xaro ido tayi dai dai nan aka bude kofar dakin, ta dinga kokarin kwace kanta amma ya ki saketa, Hajja tace "Kun ga jaraba ko? Ni dama sai da na innata a raina kawai dai na bi son rai ne na laka ma matar mutane maita, amma can kasan xuciyata ina tunanin kilan takuranka ne ma ya sa cikin nan ya lalace, banda haka yarinya daga 6ari ko kwana biyu ba ayi ba ka xo ka sa ta gaba a daki ka makaleta, yanxu meye ma'anar haka Aliyu? Ke kuma kin wani sakar masa jiki kamar kyanwa, ai kya bari ki murmure yanda ya kamata tukunna dai ko" Tashi Abuturrab yayi daga kan gadon ya nufi kofa, Hajja ta bi sa da wani kallon takaici, can tace "Tirrr, wannan ai jaraba ce kawai ba wani abu ba..." Jiddah dai ta koma ta kwanta ta ki yarda su hada ido da Hajja, don sai ta ji kunya sosai... Washegari da safe Hajja na kada mata shayi me kauri Abuturrab ya shigo dakin, ya xauna saman kujera yana kallon Hajja yace "Ina kwana" tace "Lafiya lau, basu baka kumallon bane a can ka yo mana nan?" Yace "Aa, Abba ne ke kiranki" Tace "Usman din?" Yace "Ehh" ta mike da sauri tana cewa "Dama nayi wani mugun mafarki a kansa wllh, shi sa yau da sassafe na fita na ba mai gadi kudi yaje can anguwan da almajirai suke ayi min sadakan kosai na dubu daya" Abuturrab dake kallonta yace "Mafarkin me kika yi?" Tace "Aa sai kace wata jahila xan xauna ina gaya maka mafarkin da nayi bayan naji ance babu kyau, er benue fa nayi mafarki tana kokarin tura mun shi a teku ta basa apple yana ci dadin apple na dibansa yana kakkanne ido, ni kuma sai gani na taho a guje ta bayanta kafin ta turasa ni nayi maxa na turata cikin ruwan sai ruwa ya tafi da ita ta dinga kurma ihu da karfi, ni dai na kamo hannun yaro na muka dawo gida" murmushi kawai Abuturrab ke yi Hajja ta fice daga dakin, Abuturrab ya mike ya dau shayin Jiddah da warmer din masa da miya yace "Tashi mu je" Ta xaro ido tace "Ina?" Ya sha kunu yana kallonta, mikewa tayi ya fita ta bi bayansa, bedroom dinsa ya tafi da ita bayan sun shiga ya kulle kofar, ta marairaice masa tace "So kake in ji kunya don Allah?" Yace "Ehh shi nake so ki ji" Xaunawa tayi saman carpet din dakin ta rasa ma me xata ce masa, ya ajiye mata shayinta da waina yace "Eat now" Abincin ta fara ci yana kallonta, taji ya kira sunanta, ta kallesa, yace "Tell me how everything happen pls" Ta ajiye wainan hannunta tace "Me yasa baxa ka cire wannan abun a ranka ba and move on pls?" Yace "Na cire wife, just that i am still wondering what happened all of a sudden on that day, tunda lafiya muka rabu da ke ai, and i even escorted you to the gate" Sai kuma ya jinginar da kansa da gado a hankali yace "I wish na raka ki har cikin gidan may be hakan da bai faru ba" cikin sanyin murya tace "Ko da kai ko babu kai dole hakan xai faru tunda Allah ya rubuta hakan" Yace "But pls tell me how it happen" Tayi shiru kamar baxata ce komai ba, ganin yanda yake kallonta a hankali tace "I saw someone just like my father...." Abuturrab yace "Ur father?" Ta gyada masa kai, yace "Where?" Ta sauke idonta tace "Gidan mama" Da mamaki yake ta kallonta yace "U mean ur father?" lkci daya hawaye ya kawo idonta tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Yes, i saw someone just like him" Abuturrab yayi kasa da murya da damuwa yace "Amma ai baba ya rasu Jiddah, wani baban kuma kike nufi" Ta fashe da kuka a hankali tace "Eh na san ya rasu, but they look so much alike, ni nasan abinda nake fada ai, i saw my father's duplicate" Abuturrab yace "Ikon Allah, bak'o su maman suka yi ne?" Tace "Nima ban sani ba, ina xaune parlon ya shigo and i was shock sbda nayi tunanin Abbana ne a lkcn at first, kallon Abba na kawai nayi masa...." Abuturrab ya dinga kallonta a bit confuse, knocking din kofar dakin aka yi, ya mike ya bude kofar, Jiddah ta goge idonta da sauri, Umma ya gani tsaye bakin kofar ya gaisheta ta amsa ta shiga dakin tana kallon Jiddah tace "Ya jikin?" Jiddah ta gaisheta ita ma sannan tace "Na ji sauki Umma" Umma tace "Toh maa sha Allah, sannu" juyawa tayi ta fita Abuturrab ya bi bayanta cause he need to talk to her about this. Karfe sha biyu saura na safiyar Hajiya Fatima ta iso gidan da Rahama bayan sun kira Abuturrab ya tura masu address din gidan, a lkcn da suka iso gidan Jiddah na bacci a dakin Abuturrab, Hajja na kyalla ido taga Rahama da Hajiya Fatima ta bi su har parlon Ummi, Umma sai wani hararanta take, Hajja na washe baki tana kallon Rahama tace "Ashe uwarki ce wannan mata me kirki haka?" Rahama na murmushi tace "Ehh" Hajiya Fatima suka kara gaisawa da Hajja cikin fara'a, Hajja tace "Ai ni na haifi Uban Aliyun, da yake dai ni ba mai shige shigen gidan yara bace shi sa tun ranan da aka yi wannan yakin a gidan baki sake ganina ba, balle an saki fitinanniyar gidan, kinsan fa halin banxa aka kamata tana yi dumu dumu, toh dai ba ruwana gwara ka rufa ma wani asiri kai ma Allah ya rufa maka naka" Hajiya Fatima tace "Haka ne kam Baaba, kinga rashin xuwan da baki yi ne yasa bamu sake haduwa ba don kuwa ina yawan leka masu duk bayan sati" Hajja tace "Oh oh dama nace Jiddah na murmurewa idan ta koma gidan mijinta nima sai in tattara in koma can din in sa mata ido da kyau don kada aje a samu wani cikin ya lalace a banxa, ai ba abu bane mai kyau er yarinya karama kamar ta cikin fari ace ya lalace, kwata kwata ba kyau haka idan ba a saka ido a kanta ba tayi ta samun ciki yana xubewa kenan, amma dai ni nasan da akwai wani abu a kasa ba banxa ba, da kyar idan wannan kishiyar tata ta barta a haka, don kaf xuri'armu babu wanda ya ta6a 6ari mu dai" Hajiya Fatima na murmushi tace "Toh Allah dai yayi mana mai kyau, ita kuma Allah ya bata wanda xai tsaya" Hajja tace "Ameen dai, to a kawo masu abinci mana, me lemo da ruwa xai yi ma mutum???" Ganin su Mama xasu wuce bayan Azahar Umma ta tafi dakin Abuturrab ta taso Jiddah ta fito su gaisa, Jiddah ta shigo parlon Ummi ta gaida su da murmushi fuskarta, Hajiya Fatima tace "Ya jikin Jiddah?" Jiddah tace "Na ji sauki Mama" Hajiya Fatima tace "Alhmdlh, Allah ya kara maki lafiya" Ummi na kallon Jiddah da ta rakube waje daya tace "Shiga ciki ki kwanta to..." mikewa tayi ta shiga dakin Ummi, Hajiya Fatima ta sauke ajiyar xuciya tace "Tsautsayi dai kawai, ni fa na shiga gidan nasu da safe yace tana bacci..." Da sauri Ummi ta dakatar da ita don kada ma Hajja ta ji kan xancen tace "Allah sarki, Allah shi yasan dai dai ai Hajiya" Hajiya Fatima tace "Wllh abun ya tsaya min har yanxu a rai, ji nayi ta kwala ihu kawai..." Hajja ta gyara xama tace "Ta kwala ihu a ina?" Hajiya Fatima tace "A parlor na" Hajja ta hangame baki tace "Wai a parlonki cikin ya lalace dama?" Hajiya Fatima tace "Ehh wllh Baaba shi yasa abun ya dameni" Umma tayi saurin cewa "Aa babu xancen saka damuwa a rai Hajiya, sai kace ba musulmai ba, Aa mu kam mun yarda da kaddara wllh, ai ko ba a parlon ki ba tunda Allah ya kaddara sai cikin nan ya xube dole xai xube ko ma a ina ne, in ma dakina, dakin Ummi, ko ma dakin Hajja" Hajja dai aka rasa abun cewa, sai kallon kowa take ta gefen ido, Hajiya Fatima tace "Haka ne kam, Allah yayi mana me kyau" Umma tace "Amma kun yi wani bako a ranan da ya sameta a parlon naki ko?" Hajiya Fatima tayi shiru, sai kuma ta kalli Umma tace "Mai gidana ne, dawowarsa kenan ma daga Abuja" Umma tace "Ikon Allah... To ce ma Aliyun tayi taga yana kama da babanta ne...." Hajiya Fatima ta gwalo ido tace "Babanta, amma ai tace min babanta ya rasu" Umma tace "Kwarai ya rasu, amma tace wai suna kama sosai" Hajiya Fatima ta kalli Rahama da ta saki baki ita ma, Hajja tace "Me kama da babanta kuma??" Hajiya Fatima tace "Toh ni kam na rasa ma me xance kuma" Ummi tayi murmushi tace "Ai kam abun da mamaki, kuma dama irin haka na faruwa ai sai ka ga wani wanda ke kama da wani naka da ka sani" Hajja tace "Aa to ko dai uban nata mutuwan karya yayi masu, wato ya gaji da wahalan su da talauci a hayi" Umma da ta bude baki ta kalli Hajja tace "Toh sai kuma aka yi yaya?" Hajja tace "Atoh, ya gudu mana, so nawa muke samun irin wannan labarin daga karshe ace ai ya gudu birni ya auri wata mai kudi sun hayayyafa, ku ka san ko haka yayi shi ma" Salati Ummi ta dinga yi a ranta, Umma kuma ta dinga ma Hajja wani irin kallo, ita kam Hajiya Fatima sai kirkiran murmushi take, Hajja tace "Xancen gaskiya fa, idan kuwa har sun tabbata ya mutu din to duk yanda aka yi wanda ta gani din d'an uwan ubanta ne, tunda ba daga sama ta fado ba... ayi mutum ace bai da dangi ko daya" Hajiya Fatima da kanta ya gama daurewa don ita dai a iya saninta duk familyn mijinta ta sansu na kauye na birni da ma wa enda suke wasu kasashen, ta dinga kallon Hajja ta ma rasa abun cewa, Hajja tace "Da xa a samu hoton shi uban nata da aka ce ya rasu sai a kai ma mijin ki ya gani kawai" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Ina ga hakan xai fi, idan anyi hakan kilan Jiddan xata fi samun nutsuwa ta kara sakawa a ranta cewar ba mahaifinta bane kawai me kama da shi ne" Hajja tace "Toh ba shkkn ba, amma idan nayi magana a dinga min kallon ta6a66iya, kawai abinda xa ayi kenan yanxu a samo hoton ubanta mu kai ma mijinki shi kuma mu ji me xai ce, sannan idan kin lura er ki na da wannan nakasan na gefen kumatu ita ma jiddah na da shi, wannan lotsewan nan" Hajiya Fatima dai tayi shiru, Hajja tace "kawai abinda xa ayi kenan" Sai wajen karfe biyu da rabi Hajiya Fatima da er ta suka bar gidan, amma gaba daya a sanyaye take da wannan lamari har Allah Allah take ta tafi ta sanar ma mijinta dake gari har lkcn. Abuturrab na kallon Umma yace "Xan gane gidan, wancan lkcn ma ai da Hajiya Fatimar muka je" Umma tayi shiru, sai kuma tace "Toh Allah ya kyauta, xuwa bayan la'asar sai mu tafi can din, nasan ita matar uban ai baxata rasa hoton marigayin mijin nata ba" Abuturrab yace "Haka ne, amma fa tana fita bara sai dare ake samunta a gida" Umma ta rike ha6a tace "Bara kuma? Allah me hikima, bara take yi?" Yace "Ehh" Umma tayi shiru sai kuma tace "Kar a biye halinta Aliyu, idan da taimakon da muka ga xa mu iya rendering mata we should do so, ta ci albarkacin Jiddah" Abuturrab ya girgixa kai yace "Bani da wannan halin Umma" Umma bata kuma ce masa komai ba, ya mike yace "In kina nan har magrib din sai mu tafi can gidan, idan kin koma gida kuma sai in je in daukeki a can gidan mu tafi" Tace "Shkkn" Bayan magrib Abuturrab ya tafi can gidan Umma ya dauketa xuwa can gidan Hansai, yau kam bai yi mistake din xuwa anguwan ba nose mask ba, tunda yayi parking Umma ke kallon layin da gidan yake, suka sauka daga motar ya nuna mata gidan, Umma ta shiga ciki ya tsaya daga waje ya ki shiga, da ya tuna irin abubuwan da Hansai ta dinga ma Jiddah a hayi da irin axabar da ta dinga gana mata tana amfani da ita tana making kudi shi kansa dubi irin karyan da ta dinga lafta masa ya bata kudinsa yayi dubu dari biyar sai yaji wani bacin rai ya xo masa, and he believes the situation she is right now serves her right, don haka ko digon tausayinta baya ji wllh, Umma na shiga dakin ta rasa wajen xama ga wani doyi da dakin yake, Hansai dake xaune kan darduma da wani rubabben fitila da ya d'an haske dakin ta amsa sallamarta cikin sanyin murya sai kuma ta mike ta shimfida mata buhun cement a kasa tace "Sannu" Umma ta daure ta xauna tace "Yauwa nagode... ya gida?" A hankali tace "Lafiya lau" Umma ta kunna wayarta ta ajiye sai kallon Hansai take ganin yanda idanuwanta suka wani kumbura tace "Amma in ji dai lafiya baiwar Allah" Kamar jira take ta fashe da kuka tace "Yau kwana uku Allah yayi ma 'ya ta rasuwa..." Sai ta dinga rusa kuka, Umma tace "Hasbunallah, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah ya gafarta mata" cikin kuka Hansai tace "Ameen" Umma ta girgixa kai tace "Nasan baki san ni ba, ni ce uwar rikon Jiddah sannan kuma kanwar uwar mijinta" Hansai ta dinga kallon Umma sai kuma ta sunkuyar da kai, Umma tace "Na xo neman wata alfarma ne a wajenki" Cikin rawar murya Hansai tace "Ina jin ki Hajiya, Allah ya sa bai fi karfina ba, ni ma kuma ina son rokon wata alfarka a gareki" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "In sha Allah" a hankali Hansai tace "Toh wacce alfarman kike so wajena Hajiya?" Umma tace "Hoton mahaifin Jiddah xaki bamu idan har kina da shi don Allah" Hansai ta goge idonta tace "Baxa a rasa ba" Tana fadin haka ta mike ta bude Ghana must go da ta ciro hoton kakar Jiddah da mahaifiyarta, ta dubo hoton mahaifin Jiddah wajen kala shidda ta ajiye ma Umma har da wanda yake saurayi, Umma ta dau hotunan tace "Toh nagode kwarai da gaske, ki fadi ta ki alfarman..." Hansai ta xauna a sanyaye tace "Alfarma daya nake so Hajiya don Allah a bar ni inyi xumunci da Jiddah, ko da sau daya ne a shekara in dinga ganinta xanyi farin ciki wllh, nasan na xalunceta na ci amanarta da na mahaifanta amma na roketa yafiya kuma tace ta yafe min yau wata hudu kenan tun xuwansu gidan nan, in ci albarkacin ubanta kada a rabani da ita don girman Allah" Hawaye kawai take tana shessheka, Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh in sha Allah, xa ku yi xumunci" Godiya Hansai ta dinga yi ma Umma kamar xata ari baki, Umma ta bude jakarta ta ciro dubu biyar tace "Kiyi hakuri da wannan sai mun sake dawowa, duk da gobe ko jibi xa mu xo din tare da Jiddah ta yi maki gaisuwar yar uwarta in sha Allah" Har bakin mota Hansai ta raka Umma duk jikinta a sanyaye, har ranta take son rayuwa tare da Jiddah gatan da bata gwada mata ba tun ubanta na da rai har ya rasu tana son ta gwada mata yanxu duk da bata da komai, so take kawai ta ja ta a jiki tamkar bibalonta, tana ganin Abuturrab ta duka tana gaishesa, ya amsa a takaice ya xaga ya shiga driver seat ta bi sa da ido, Umma ta bude gaba ta xauna tana daga ma Hansai hannu har suka bar anguwar, sosai taji tausayin matar, lallai kam ita taga kamun Allah tun a duniya. Suna komawa gida da hoton Abban Jiddah Hajja tace Inaaa ai hoton baxai kwana ba aje a nuna ma mijin Hajiya Fatima kawai, haka suka shirya da ita da Umma, da Jiddah da Abuturrab xuwa gidan Hajiya Fatima bayan isha..... Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsApp💖💖 *Jiddatul Khair**💖💖 _By khaleesat Haiydar_📚✍🏻 94...Parking Aunty Rahama tayi a kofar gidan Abba, Hajja dake bayan motar tana washe baki tace "Allah ya maki albarka, in sha Allahu nan da kwana biyu xan dawo anguwan naku gaba daya kin ji?" Aunty Rahama na murmushi tace "Toh Allah ya kawo ki lafiya kaka" Jiddah dake gaban mota tace "Mun gode Aunty" Aunty Rahama na mata murmushi tace "In kun shiga ki gaida su mama kin ji" Hajja tace "Au ni da nake xaton xaki shigo ku gaisa" Aunty Rahama tace "Aiki xan tafi kaka, na makara wllh" Hajja tace "Aa kin makara gaskiya gashi har tara saura, to ke mijin naki ba a kasan yake bane?" Tayi murmushi tace "Allah ya mashi rasuwa kaka" Hajja ta saki wani salati tayi tagumi cike da damuwa tace "Allah sarki, Allah ubangiji ya gafarta masa, to baki da 'ya ya da shi ne?" Tace "Ina da, su biyu ne, suna gun yayansa a Abuja, sai hutu ake kawo min su" da sauri Hajja tace "Aa ki amshe yaranki, ce masu kika yi baxa ki iya kula da su ba ko salon kar yaran su ji kanki su san ciwonki" Ita dai murmushi kawai take, Hajja tace "Wllh amshe abin ki, ni ban yarda da rikon d'a ba..." Daga haka ta bude motar ta sauka, Jiddah ma ta sauka tana kara yi ma Aunty Rahama sallama suka shiga gidan da Hajja, tun daga parlor Hajja ke kwala ma Ummi kira, Ummi na fitowa tace "Toh dai Jiddah ba yar matsiyata bace, kuma kakarta na nan da ranta sai kin ga abun arzikin da aka mana a wannan gari na gombe, mutanen kirki mutanen arxiki suka cika garin, sun karrama mu sun daraja mu sun mutunta ba, wllh basu so mu taho ba amma wannan yayan baban nata Alhaji Sani naji ana ce masa ko wa? Wannan dai da ya mana jagora xuwa garin shi ya axalxala mu taho, in don ta nine da bamu dawo ba wllh, jiya da daddare muka dawo to yau naga wnn yarinya Jiddah sai wani nukurci take taki kulani nace to ko kewan mijinta take shine dai nace su maido mu gida da safe, amma wllh dangin ubanta en arxiki ne babu talaka ko kwaya daya a cikinsu, ke kin ga gidan ma kuwa, wllh yayi biyar din wannan, kuma kinsan gidan waye, gidan uwarsu ne, su suka gina mata gwanin ban sha'awa, ai ita kam ta more rayuwa wllh...." Ummi tace "Toh Alhmdlh, nayi murna sosai, Allah ya bayyana dangin mahaifiyarta haka" Hajja tace "Allah gidan yayi ukun wannan kuma tsohuwar kadai ke rayuwa a ciki, duka duka fa bai fi ta girmeni da shekara uku ko hudu ba, amma sai kin ga abinda yaranta suka kera mata, tana xaxxaune ta mike kafa sai dai ayi mata komai" Ummi ta amsa gaisuwar Jiddah da ta duka kasa ta gaisheta, Ummi tace "Ya hanya, fatan kun dawo lfya, ya kuma ku ka bar mutanen can din" Hajja ta amshe tace "Alhmdlh, babu abinda basu mana ba, yanxun ma fitowa muka yi ba shiri ita kuma warce ta kawo mu tana ta sauri xata aiki, banda haka in gaya maki ai tsarabanmu da yanxu haka ba a gama shigowa da su ba, to sunce anjima da yamma xa a taho mana da shi, ke dai ki bari kawai Hauwa, karramawa da mutunci na inda yake, ni kam bani da abinda xance ma mutanen nan" Daga haka ta wuce dakinta, Ummi da ta bi ta da kallo tace "A kawo maki kumallo Hajja" Hajja tace "Meye kuma kumallo? Aa mu mun yi lafiyayyen kari, kawai a bani makullin d'an kuturun dakina" Ummi ta tafi dauko mata makullinta ta kai mata, ta bude ta shige ciki tana kyabe baki, Ummi ta dawo parlor ta xauna tana kallon Jiddah tana murmushi tace "Kin je kin ga kaka da kawunnanki ko?" Murmushi Jiddah tayi ta gyada mata kai, Ummi tace "Toh Alhmdlh, Alhmdlh, i am so happy for you daughter" Jiddah dai ta sunkuyar da kanta kawai, Tashi Ummi tayi ta tafi parlon Abba, Jiddah ta dinga kallon hanyar dakin Abuturrab amma ta kasa tashi, ta fi minti biyar sai ta kalli dakin sai ta dauke kai, can dai ta mike a hankali ta nufi dakin kamar munafuka muryan Ummi taji tace "Ai bai nan ya koma aiki Jiddah" kunya ta ji kamar ta nutse, ta kasa juyowa ta kalli Ummi, jin shiru sai kuma ta juyo a hankali, gani tayi Ummi bata ma wajen, da sauri ta wuce dakin Hajja. Washegari da safe Jiddah na dakin Hajja, Hajja na cewa "Kin ga ai ni bana kai kaina inda Allah bai kaini ba kuma bana takura ma yarana ince sai sun min abu dole, da wata ce yanxu duk sai ta kwarzabi yaranta tace sai fa an mata gini irin na wannan kakar taki, amma ni kam Allah ya kiyaye inyi haka sai kace wata er banxa, ni ko burgeni gidan bai yi ba balle inji sha'awa ince a min irinsa" Jiddah dai kallonta kawai take amma bata ma san me take cewa ba, kewan Abuturrab kawai take, ji take kamar ta fi wata daya rabon da ta gansa, she's a kind of sad, gaba daya ta ji gidan ya isheta, gashi bata san sanda xai dawo ba, ga surutun Hajja dake sa mata ciwon kai, tayi mata xancen gidan Dada ya fi sau ashirin daga jiya xuwa yau, har Umma da ta xo jiya ta bata labari, Hajja ta ta6e baki tace "Ba ruwana da sa ma wani ido wllh, nagode Allah da inda ya ajiyeni, shege ne kawai xai dinga hangen abun wasu" Bude kofar dakin aka yi Ummi ta shigo tayi ma Hajja sannu, tana kallon, Jiddah tace "Ur husband said he will be back in the evening of today, so get ready after Zuhur, i will instruct the driver to drop u home" Tace "Toh Ummi" Juyawa Ummi tayi ta fita, Hajja ta ta6e baki tace "To ko matansa ma basa hanasa ya min kantamemen gini ba don bakin ciki, ai kai dai kawai ka haifar ma mace yaro kawai, bayan haka baka da sauran martaba a wajensa" Tun da Ummi ta fita Jiddah ke counting agogo sai taga baya sauri, wai karfe goma da rabi, har bacci tayi ta tashi wai karfe sha daya, kawai daga karshe ta mike ta fita daga dakin Hajja ta tafi part din Ummi... Ummi ta ajiye littafin hannunta tana kallonta tace "Ya aka yi Jiddah?" Kunya taji ya rufeta, Ummi tace "Ko har kin shirya?" Tayi karfin halin cewa "Ehh Ummi ina son xanje inyi girki ne" Ummi tace "Eh gaskiya kam, bari in kira driver din, shiga ki dauko jakarki to" Kanta a kasa ta shiga dakin Ummi ta dau jakarta ta fito dama da Hijab dinta a jikinta, bayan Ummi ta kira driver ta mike ta tafi daki ta dauko mata makullin gidan nasu, tana mika mata tace "ki je ki ma Hajja sallama kice mata xaki gidan Umma ne" Jiddah tace "Toh" Ummi tace "Idan kin mata sallaman ki samu driver din yana waje" Jiddah tace "Ummi ina son in siya wasu abu a kasuwa ne..." Ummi tace "Kina da kudi wajen ki ne?" Girgixa mata kai tayi, Ummi tace "Toh bari in baki Atm card, idan ya dawo sai ya maido min da card din nawa" Atm card din ta dauko ta mika ma Jiddah ta gaya mata pin din tana kara nanata mata kar ta manta, Jiddah ta risina ta amsa tayi mata godiya ta fita, kallonta Hajja ta dinga yi sai kuma tace "Me ake yi a gidan Umman?" Jiddah tace "Kawai xan je ne" Hajja tace "Toh sai mijin naki ya dawo xamu koma can gidan kin dai ji abinda nace ma dangin ubanki kar su daukeni makaryaciya idan basu gan ni ba" Jiddah tace "Ehh sai ya dawo" Hajja tace "Toh ki gaida Ramlan" Jiddah ta juya ta fita, sai da driver ya fara ajiyeta kasuwa ta siya ingredients din fried rice da zobo drink, tunda suna da nama a deep freezer bata siyi komai ba banda liver, daga nan driver ya ajiyeta gida tayi masa godiya ta shiga ciki bayan ta gaida mai gadi. Tana shiga cikin gidan ta kai kayan girkin kitchen ta tafi sama ta canxa kaya xuwa kanana sannan ta fara gyaran gidan, ta tsaftace ko ina tayi mopping da goge goge ta kunna turare a burner, sai da tayi azahar sannan ta shiga kitchen.... Kafin la'asar ta gama hada lafiyayyen fried rice dinta with zobo drink, ta soya kajin tayi pepper chicken da shi, sai farfesun offals da tayi kadan, duk ta jera abincin a dinning, ta koma ta tsaftace kitchen din kamar bata yi komai a ciki ba ya dawo fes fes, sama ta wuce dakinta ta shiga wanka, da alwalanta ta fito sai da tayi salla snn ta fiddo da kayan da xata sa, ta dau kusan minti talatin tana shirya, ta saka wasu ubansun English wears masu daukan hankali, ko ina na jikinta wani sanyayyan kamshi ne ke tashi, tayi packing gashinta da ribbon leaving it that way, she look just like a princess, tayi kyau sosai, bude gate taji anyi ta karasa window tana kallon waje yaga Abuturrab ne ya shigo da motarsa... Sauka tayi downstairs ta tafi bakin kofa ta tsaya, she is just so happy, ta labe a gefe daya har ya bude kofar, wani kara tayi da nufin basa tsoro, ya jawota jikinsa yana kallonta daga sama har kasa yana murmushi, 6ata fuska tayi yayi kasa da murya yace "Jirgi bai bani tsoro ba sai matata?" Dariya tayi ta boye fuskarta jikinsa a hankali tace "Welcome my Man" Ya lumshe ido ya bude yana shafa bayanta yana kare ma dressing dinta kallo yace "U look sexy in this wife..." Sai kuma ya kankameta yace "Wllh i have missed u so much wife, Hajja bata kyauta min" amsar jakan hannunsa tayi tana murmushi tace "I missed u more dear... Abinci ko wanka?" Ya girgixa kai yace "Sallah" Tace "Toh mu je" Sai da yayi sallah sannan yayi wanka bayan ta hada masa ruwan wankan a bedroom dinsa, kafin ya fito ta ciro masa kayan da xai sa, sannan ta sauka downstairs ta dauko girkin da tayi xuwa parlonsa, xata shiga bedroom bayan ta gama hayowa da abincin suka kusa cin karo, sai taga ko kayan da ta ciro masa ma bai sa ba sai short, daukanta yayi kamar baby xuwa bed din dakin, ta marairaice masa tace "Dear ga fa abinci can..." Bai bata daman ta karasa ba, ya dinga ce mata yayi missing dinta so much, kamar yanda ya tara mata gajiya ita ma dai hakan tayi masa, bai ta6a tunanin da akwai sanda jiddah xata sake haka da shi ba balle har ta maida masa martani.... Sai bayan ya dawo magrib ta xuba masa abincin da ta girka masa, yana kallonta ta gefen ido yace "Ke dai fadi gaskiya Baby wannan abincin daga gidan Ummi kika taho da shi ko?" Murmushi tayi tace "Ae wannan ma da na ta6a xuba ma Colleagues dinka da dadewa ka kusa cinyewa baka sani ba... Shi ma ai daga gidan Ummi...." jawota yayi jikinsa ya matseta ya buda idonsa yace "Ni xa ki ma sharri?" Dariya tayi tace "Kai ka fara min sharri ai" ya lumshe ido yana murmushi yana shafa dogon gashinta yace "U are really a good cook wife, i know i am blessed... tun daga wannan ranan da kika xuba ma Colleagues dina abinci na dandana na san haka, i was stunned after tasting ur food that day, how possible i thought to my self many times" Tana murmushi tace "Saboda i am too local then ko?" Ya dago kanta yace "Daga sanda na raba ki da hayi kika bar locality dinki a can, u left that locality behind... Ban ta6a tunanin xaki fahimci abubuwa ki koyi abubuwa lkci daya ba jiddah, u were a fast learner... A iya xamanmu na farko I can't say ko na ta6a maki wani correction kan abubuwan da na koya maki" Ita dai murmushi kawai take, yayi kasa da murya yace "Tun daga sannan kika fara burgeni, when i notice u were always clean" Ta d'an saci kallonsa tace "Ashe ina burgeka" He couldn't help it but laugh, sai kuma ya rike kansa yace "Sosai Jiddah, in dai na barki a gida na tafi aiki bani da sukuni up in the sky sai na dawo gidan nan, i hate seeing u sad or worried hakan na karyar min da xuciya..." Ta kwantar da kanta kan shoulder dinsa tace "Kawai dai so na ne baka yi a lkcn ko??" Jin yayi shiru ta daga kai ta kallesa, kallonta taga yana yi babu ko kiftawa, sai kuma ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "Na kan yi sha'awanki a lkcn" Ta d'an buda ido tana kallonsa tace "Wani iri" Ya lumshe ido yana shafa laps dinta yace "Irin wannan but i always try hard to fight it away, i always put in the back of my mind that i am just ur guardian" ita dai Murmushi kawai take, ganin ya ki daina abinda ya ke mata a kafa ta turo baki tana kallonsa, tuni taga idanuwansa suka canxa, ta marairaice tace "Ni wllh na gaji ko abincin fa ban ci ba..." Wannan fried rice din dai sai wajen karfe sha daya na dare aka ci sa, Abuturrab ne ya fara tafiya sama bayan ya wanke baki ya kwanta cause he is so very exhausted, ta gama wanke duk abubuwan da suka 6ata, ta sa turaren wuta ta jira yayi a parlon sannan ta kashe komai ta wuce sama, bedroom dinta ta tafi ta sake wanka ta wanke baki sannan ta saka kayan baccinta ta kashe wutan dakin ta kwanta, nan da nan bacci ya dauketa, can wajen karfe biyu Abuturrab ya koma dakinta ya kwanta because he can't resist sleeping without her close to him... Haka rayuwarsu ya ci gaba da gudana cike da so da kaunan kamar su maida junansu ciki, in dai yana gari bata da sauran sukuni har ma ta sa6a da kwarzabanta da yake, ya kuma yi programming dinta a yanda yake, ya maidata irinsa, shi yasa bata wani wahala ko gajiya da shi, kusan inda Abuturrab ya tafi wajen aiki ta kan shiga gidansu Hajiya Fatima har ma ta yini, Hajiya Dada kuwa duk bayan 2 days ko ita bata kirata ba ita xata kirata don Abuturrab ya siya mata exactly irin wayar da ya siya mata wanda Aneesah ta hade da kayan daki ta dagargazar, hka sauran Uncles dinta da aunt duk suna gaisawa a family group da aka sakata a ciki, she felt belong now, ko ba komai yanxu tana da wa enda xata nuna tace ai wa ennan dangina ne na jini, kowa a familyn ji yake da ita, sau dayawa idan Alhaji Ishaq ya shigo kaduna komai ya kawo ma su khaleesat sai ya raba dai dai da Jiddah ya bada a kai mata, hakan na yi ma Jiddah dadi sosai, jinsa take kamar mahaifinta na gaskiya, Hansai kuwa ta kusa sati uku yanxu a gombe wajen Hajiya Dada.... Yau duk da tasan Abuturrab na hanya sai duk ta kasa tashi tayi abinda ya kamata a gidan gaba daya wani kasala take ji tun da ya tafi ya bar ta, da ta yunkura xata yi aiki sai taji ta kasa sai dai ta koma ta kwanta, gashi gaba daya appetite dinta na cin abinci babu, ko a waya kuma bata sanar masa yanda take ji ba, ganin dai ya kusa shigowa ta mike da kyar tayi karfin halin shiga bandaki ta hada ruwan wanka tayi wanka sannan ta fito ta saka turare sama sama ta shirya, kwanciya ta koma tayi don taga alamar fa baxata iya ta6uka komai a gidan ba, tana jin shigowar motarsa bayan la'asar, ta daure ta kara mikewa ta sauko downstairs, dai dai nan ya shigo parlon karasawa tayi ta shige jikinsa kamar yanda ta saba in dai ya dawo, rike breathing dinta tayi sbda wani hautsine mata ciki da kamshin turarensa yayi, ta sa hannu ta rufe bakinta da hancinta, da mamaki yake kallonta yace "Baby me ya faru" Ta fara masa alamar amai na taho mata, da sauri ya ja ta xuwa bathroom dake parlorn, ganin yanda take aman yace "Oh my God baby dama baki da lafiya ne?" Ta kasa basa amsa sai sauke numfashi take, fitowa yayi da ita daga bandakin, ko minti biyar basu kara a gidan ba ya tafi da ita hospital, tun da suka shigo Aneesah dake xaune reception ta dinga rurrufe fuskarta tana kallonsu kasa kasa, shi kam ko lura da ita bai yi ba haka jiddah dake fama da kanta, bayan an duba Jiddah Abuturrab ya kasa boye farin cikinsa bayan likitan ya sanar masa tana dauke da ciki na sati uku, he felt like kissing and caressing her in public, he was so very happy, kasa daurewa yayi daga karshe ya rungumeta gam a office din likitan ya dinga sa mata albarka, sai bayan kusan 30 mins suka fito haraban hospital din yana rike da hannunta da few drugs da aka bata sbda amai da kasalan da take, gently yake tafiya da ita don bai son anything that will stress her, don ma cikin mutane ne da daukar abarsa xai yi baxata taka kasa ba, tun shigowarsu asibitin da minti goma aka sallami Aneesah amma ta kasa tafiya ta xauna karkashin bishiya a haraban asibitin tana jiran taga fitowarsu, tana ganin sun nufi mota ta mike a hankali ta nufesu, da farko Abuturrab bai ma ganeta ba sai da ya sake kallonta da kyau, ta dan yi murmushi tace "Good evening captain" Sosai gaban Jiddah ya fadi ta juya tana kallonta, yana bude ma Jiddah back seat yace "Evening Aneesah how are you doing, longest time" Tace "Alhmdlh" Jiddah ta shiga motar Aneesah na kallonta tace "Kwana da yawa Hajiya Jiddah" Jiddah tace "Alhmdlh" Rufe motar Abuturrab tayi dai sai kallonsu take ta cikin glass, ya bude driver seat yace "Toh ya aka yi Aneesah?" Tace "No dama gaisuwa ne" Yace "Toh nagode, baki da lafiya ne kika xo ganin likita?" Tace "Ehh" Hannu ya sa a aljihu ya ciro kudi masu yawa yace "Ohk take this little token" Ta dinga kallon kudin amma ta ki amsa, sai ta daga kai ta kallesa hawaye cike idonta tace "I just want to ask u for forgiveness..." Yace "Nahh I've done that long ago Aneesah, na yafe maki wholeheartedly, me yake damun ki kika xo gun likita?" Tace "Xaxxabi nake" Yace "Toh Allah ya sauwake... Allah ya kara lafiya, i need to leave now" Kai kawai ta gyada masa ya bude front seat ya shiga ya tada motar suka bar asibitin ta madubi yake kallon Jiddah ya ga yanda ta wani hade rai, yayi kasa da murya yace "Baby" ko kallonsa bata yi ba ta kauda kanta. Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you _Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_ Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake..... *tested and trusted* If interested contact 👇🏻 08052466875 via WhatsAppJiddah ce xaune dakin bak'i tana yanka fruit din kankana a tray, xaune daga gefe daya kan darduma Hansai ce, Hansai tace "Ina ta son xan maki wata magana Jiddah" Jiddah ta daga kai ta kalleta ta dau tray din watermelon din ta ajiye a gabanta tace "Ina ji Baabarmu" Hansai tayi kasa da murya tace "Shekarun baya da dadewa akwai wata aminiyar mahaifiyarki ana ce mata Sadiya, baabarki tace min tun bata yi aure ba take tare da Sadiya hasalima Uwar sadiya ta san kakarki sosai ina jin kamar sun ma yi kawance, to a da dai Sadiya ta auri wani me rufin asiri a unguwan sanusi, don lkcn da Mahaifiyarki ma ta rasu wllh xuwan Sadiya uku tana son xata daukeki ta rike ki amma duk na hana, a xuwan karshe ma ba ta dadin rai ta bar gidana ba, nace kada ta sake dawo min gida, to wannan dalili ne yasa har yau bata sake waiwayo inda muke ba, to a lkcn har gidanta na sani a can unguwan sanusi don mun je sau uku da Baabarki a lkcn da take da rai, yanxu dai ban san ko tana nan har yanxu ba, ni nasan ko kadan ne Sadiya baxata rasa sanin wani abu a kan mahaifiyarki ko kakarki ba, xai iya yiwuwa ita Baabar sadiya sun ta6a wani hira da kakarki ta fada mata wani abun game da asalinku, shine nace kiyi ma mijin ki magana ko xa mu je gidan Sadiya idan yaga da halin yin hakan" Jiddah dake ta sauraronta tace "Toh Baabarmu xan masa magana in sha Allah" Hansai tace "Toh maa sha Allah...." Xaunawa Jiddah tayi don dama a durkushe take a dakin, Hansai tace "Aa tashi ki tafi gun mijinki ai dare yayi kuma haka" Jiddah tace "Xan jira idan kin gama in kai tray din kitchen" Hansai tace "Xan kai da kaina, ki tashi ki tafi sai da safe" Jiddah tayi mata sai da safe sannan ta mike ta fita... Xaune ta tarda Abuturrab yana operating laptop Little Jiddah na jikinsa tayi bacci, Ta cire Hijab din jikinta ta linke don dama tayi shirin bacci, ta xauna gefensa ta jinginar da kanta da shoulder dinsa tace "Dee" Jawota yyi jikinsa yace "Baby kina stressing kanki da yawa fa, u need housemaid seriously, kullum cikin gyara gidan nn kike ba dare ba rana" Tayi murmushi tace "Sai kace wani aikin duniya?" Kashe laptop din yayi ya kwantar da little Jiddah, ya jawota jikinsa yana kissing lips dinta, bata yi sanya wajen biye masa ba.... bayan an idar da sallan Asuba ya dawo masallaci ta basa d'an labarin da Hansai ta bata, ya d'an yi shiru sai kuma yace "Alright in the evening sai mu tafi tunda tace ta san gidan" Jiddah tace "Allah ya kai mu" A hanxarce Jiddah ta gama wanke few plates da aka 6ata a kitchen ta goge ko ina sannan ta fito tana kallon agogo, Abuturrab na xaune parlorn yana kallon wrestling ta nufesa ta xauna kusa da shi tace "Dee baka kira ayi fill din gas din ba till now" Ya jawota jikinsa yana kallon agogo yace "Sai mun dawo Baby, hope u are done now?" Tace "Eh na gama, ince ta sauko??" Yayi kissing din lips dinta yana murxa hannunta yace "Yeahh Baby" Mikewa tayi ta wuce sama, bude dakin da Hansai take tayi ta shiga ciki, Hansai na xaune kan carpet da Little Jiddah tana daure mata dogon gashinta da colorful ribbons, babu abinda wannan yarinyar ta mance bata dauka ba na ubanta, ko kadan bata kama da Jiddah ta ko ina sai ta beauty point da haskenta da ta dauko... Kyakkyawa ce yarinyar ta karshe, kamar er india, Tana ganin Jiddah ta 6ata fuska xata yi kuka, Hansai tace "Lah ji min yarinya wai ta 6ata fuska daga ganinki, lafiya fa nayi mata wanka na shiryata babu ko tari" Dariya Jiddah tayi tace "Baabarmu wai ki sakko mun gama" Hansai tace "Toh gani nan fitowa, dauketa ku tafi sai ki karasa daure mata gashin tunda ta fara haka baxata yarda ba kuma" Jiddah ta karasa ta dau daughtern nata ta fita daga dakin, dakinta ta fara shiga ta dauko Veil dinta da handbag sannan ta sauka kasa, Little Jiddah na ganin Abuturrab ta fara mika masa hannu tana masa dariya, she looks so happy seeing him, mikewa yayi ya amsheta yayi kissing Cheek dinta affectionately yace "I love u cute Mamina" rungumesa yarinyar da bata wuce shekara daya da wata bakwai ba tayi, Abuturrab ya mika ma Jiddah dake kokarin yafa veil dinta car key yana kallonta, ta xumburo baki tace "Aa ni baxan iya ba, kullum sai ka dinga min wayo kana bari na da tuki" murmushi yayi yace "Toh amshi er ki sai inyi driving din" Little Jiddah ta makalkalesa xata yi kuka, Jiddah ta rike ha6a tace "Dama idan xai koma aiki sai dai ya tafi da ke, baxai bar min ke ba..." Dariya Abuturrab yayi yace "Salon kiyi kuka idan na tafi da ita" Yana fadin haka ya jawota yayi mata side hug yace "Na lura kishi kike yi da Ummi na fa" Jiddah tace "Toh ba gashi baka da time dina yanxu ba sai dai nata" A tare suka fita parlon yana cewa "Ni ko nake da time dinki, during d day dama time din Mami ne, ke kuma throughout the night time dinki ne kinga equation balanced" Jiddah tayi murmushi kawai ta amshi car key din a hannunsa, Hansai ce ta fito daga parlor ganin makulli jikin kofa ta kulle sannan ta cire makullin ta nufi motar ita ma, duk da ba da sanda take tafiya ba amma har lkcn bata tafiya dai dai... Abuturrab na kallon Hansai ta madubi yace "Wani anguwan ma kika ce?" Hansai tace "Unguwan Sanusi" Suna isa gidan luckily har lkcn Sadiya bata tashi ba don gidan mijin nata ne, wanda shi ma ya rasu ya bar mata 'ya ya, duk da Sadiya bata ganesu ba, haka ta shimfida masu tabarma a tsakar gida tana bin su da kallo tace "Sannunku da xuwa" Hansai na murmushi tace "Hansai ce fa Sadiya naga kamar baki gane ni ba" Sadiya tayi shiru tana kallon Hansai, sai kuma ta mike da sauri tace "Hansan Amina?" Hansai na murmushin karfin hali tace "Ni ce Sadiya, kinga ga Jiddah nan" Sadiya ta saki wani salati tace "Jiddah er wajen Marigayiya Amina?" Sai kuma ta fashe da kuka ta dago Jiddah ta rungumeta tace "Allah sarki rayuwa, sannunku da xuwa Jiddah, ashe da rabon xamu sake ganawa Hansai, sannunku da xuwa, Allah sarki rayuwa" Hansai dai sai kirkiro murmushi take, Sadiya tace "Toh ina bibalo?" A hankali Hansai tace "Allah yayi mata rasuwa" Sadiya ta saki salati ta nemi waje ta xauna tace "Yaushe ni Halima?" Hansai tace "Yau kusan shekara uku kenan da rasuwanta" Sadiya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah ya gafarta mata Hansai, Allah ya ji kanta, wayyo rayuwa" Hansai dai ta sunkuyar da kanta, Sadiya tayi tagumi tana jimamin mutuwan Bibalo, Hansai ta dago tace "Dama mun xo gunki ne Sadiya tare da fatan Allah dai ya sa kinsan wani abu game da kakar Jiddah da mahaifiyarta" Sadiya tayi shiru, sai kuma tace "Toh, amma dai duk abinda ni na sani baxai kai wanda mahaifiyata ta sani ba, idan kun ga babu damuwa to mu tashi mu tafi gidan Mamanmu yanxu, tana nan anguwan ita ma" Hansai tace "Wannan ba damuwa bane" Fita suka yi gidan gaba daya suka shiga motar Abuturrab, Abuturrab ya gaida Sadiya dake gaishesa a back seat sannan ya nufi hanyar da tace masa ya bi, bai yi niyyar shiga gidan ba amma haka Sadiya ta matsa ya shiga ayi komai a gabansa kawai, babu yanda ya iya haka ya sauka ya kulle motar yana rungume da little Jiddah, duk da ba wani tsufa mahaifiyar Sadiya tayi ba amma yanayi na rashi da halin rayuwa ya sa duk ta wani yakune kamar warce ta shekara tamanin a duniya, bayan sun gaisa Sadiya ta gaya ma mahaifiyar tata abinda ke tafe da su, Mahaifiyarta ta dinga kallon Jiddah tace "Yanxu kuna nufin jikar Maijiddah ce wannan Sadiya?" Sadiya tace "Ita ce Inna" Inna ta girgixa kai tace "Allah me iko, ikon Allah ya fi gaban haka, Allah sarki rayuwa, Allah ya gafarta ma maijidda, Allah ya Rahama mata, Allah ya raya xuri'ar da ta bari" Duk suka amsa da Ameen, kamar yanda Hansai ta sanar ma Sadiya abinda ke tafe da su a can gidanta haka ta sanar ma Mahaifiyarta abinda ya kawo su, Inna tayi shiru sai kuma a hankali tace "Toh, ita dai Maijiddah nasanta a lkcn tana aikatau a gidan Alhaji Labaran, tace min asalinsu yan kasar Nijar ne, amma bata ce min ga garinsu a Nijar ba gaskiya, ni kuma bata ta6a ce min ai ga abinda ya kawo ita da er ta Amina Nigeria ba, sai amsa daya da ta bani a lkcn da nayi mata tambayar, tace min ita kawai tana son nisa da yan uwanta da garinsu ne ta rike er ta har Allah ya raya mata ita, wato Amina kenan, ko a lkcn da kudinsu na Nijar da yawa a jikinta tayi ta ajiya bata komai da su wllh, ni idan ban manta ba har zinarai maijidda na da su a jaka, ni kuma ban gaya maku dalilin haduwarmu da kawancen mu ba, to a lkcn nima ina aikatau a gidan aminin shi Alhaji Labaran din wato Alhaji Sama'ila, don haka wani lkcn na kan yi ma matarsa Hajiya Kande rakiya xuwa wajen matar Labaran ita kuma ana ce mata Hajiya Bilki, to kun ji dalilin sabawar da muka yi da Maijidda kenan har muka dawo kamar yan uwa, ni kuma a lkcn aurena ne ya mutu, mata me kirki da gaskiya da amana, wnn dalili yasa Hajiya Bilki ta rike ta da kyau, don su suka aurar mata da er ta Amina ga Isuhu, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a gidan kuma Allah yayi mata rasuwa don tana ta ciwon da ba a san daga ina ba, sun kashe mata kudin asibiti bayin Allahn nn ba na wasa ba, amma har ta koma ga mahaliccinta ba a gano kan ciwon nata ba, Allah sarki yanxu xancen da nake maku daga matar har mijin babu su suma duk sun rasu, sai dai ya 'yansu da jikoki, basa ma garin kaduna ynxu gidan ma na samu labarin sun siyar, to ni shkkn iya abinda na sani a kan Maijidda kenan, er mutan Nijar ce dai" Hansai ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh mun gode sosai Inna, Allah ya saka da alkhairi" Tace "Allah ya maku albarka" Jiddah dai duk jikinta yayi sanyi sosai, Inna tace "Kawai ku je kuyi ta addu'a in da rabon Jiddah xata gana da dangin uwarta xata gana da su wataran, Allah kadae yasan dalilin da Maijidda ta baro kasarsu da yar ta da bata wuce shekara goma ba ta dawo Nigeria" Godiya Abuturrab ya kara yi ma Inna ya ciro dubu biyar ya ajiyeta mata, sannan suka bar gidan nata, bayan sun ajiye Sadiya a gidanta suka koma gida. Da daddare Jiddah na kwance jikin Abuturrab tayi lamo, tun bayan dawowarsu ya lura she is moody ya shafa fuskarta a hankali yace "Not again wife, akwai wani abu da kika nema kika rasa ne a rayuwa yanxu? U have ur fathers relative that are firmly there for u always, tunda gashi sun canxa min ra'ayi ba wai don na so ba, u will be starting ur higher institution next month in sha Allah, non of my penny was used, they paid for everything, isn't that for the sake of the love they have for u?" Kasa ce masa komai tayi wasu hawaye masu xafi na sauka idonta, ya rungumeta sosai yace "bana son haka Wife, kina daga min hankali sosai" Cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" Yace "Definitely one day, one time, u will meet with ur Maternal relatives in sha Allah, xa mu tafi Umra soon sai ni dake muyi wannan addu'an a can, sai ki ga Allah ya amsa.... In sha Allah" Cikin sanyin murya tace "In sha Allah" Washegari Karfe goma saura Jiddah ta gama duk abinda take, bayan Hansai tayi breakfast ta shiga gidansu Hajiya Fatima, ita kuma Jiddah suka fita tare da Abuturrab, shi ke driving din, tana xaune front seat rike da Little Jiddah a kafarta, motoci ne sun kai biyar anyi parking kofar gidansu Abuturrab, Abuturrab ya nemi waje shi ma yayi parking ya sauka, Jiddah ma ta sauka, ya amshi little Jiddah a hannunta suka shiga cikin gidan, ganin guards din palace din bauchi ya gane uncle dinsa ma na gidan, Tun daga nesa yake kallon El-Basheer dake tsaye tare da Ahmad, ya karasa suka fara gaisawa da Ahmad sannan ya mika ma El-Basheer hannu yana kallonta, El-Basheer yace "And i am hoping u will be unblocking me this very moment" D'an murmushi kawai Abuturrab yayi yana patting shoulder dinsa yace "I neva did block you brother" Jiddah ta sunkuyar da kai ta gaishe su, El-Basheer na ganin little Jiddah ya wara ido yace "Waow, and at last, my wife is born..." Karasawa tayi ya amshi yarinyar a hannunta yace "Waoow she is so cute" Jiddah na kallon Ahmad tana murmushi tace "Aunty Ramlah fa yaya Ahmad?" Yace "Tana ciki" Juyawa tayi ta karasa cikin gidan, Maimoon ta taso da sauri ganin Jiddah ta rungumeta cike da murnan ganinta tace "Mrs Aliyu" Jiddah na murmushi tace "Mrs Yusuf" Dariya kawai Maimoon tayi, Jiddah ta janye jikinta ganin su Ummi a parlon tace "Bari in gaida su Ummi" xaunawa kasa tayi gefen Ummi ta gaisheta, Ummi ta amsa da fara'a, ta mike ta tafi kusa da Umma tana jin kamar ta rungumeta tana murmushi tana kallonta tace "Umma ina yini" Umma tace "Lafiya lau Daughter, ina Ummin?" Tace "Tana wajen yaya Bashir" Ramlah dake xaune ta daga ma Jiddah hannu tana murmushi, Jiddah ta daga mata hannun ita ma smiling at her, gaida few visitors dake parlon tayi, sai ga Hajja ta fito daga dakinta sanye da kaya na alfarma ta sha gwal a wuya da kunne tana taku dai dai, Akwatunanta uku fal da kaya ana biye da ita da shi.. Wai ashe Masar Hajja xata koma shine yan rakiya xuwa airport suka cika gidan Alhaji Usman, yan kano ne, yan Bauchi ne, har ma da yan zaria, Umma na murmushi tace "Hajja kuma sai Masar" Hajja na daga shoulders ta nufi kofa tana cewa "A bi min akwatuna a hankali kar su yi ko kwarzane a cuce ni, mu a Masar a nutse ake jan akwati" Dariya Maimoon ta dinga yi har da saukowa daga kan dining, Ummi ta mike da su Umma suka bi bayan Hajja suna murmushi, Abba da Mai martaba da sauran brothers dinsu duk suka fito compound jin Hajja ta fito bayan awa daya da ta dauka tana shiri a dakinta, kace wani karamin biki ake yi a compound din gidan saboda mutane, a haka duk suka nufi airport don a private jet xa a kai ta kano sannan ta hau jirgi xuwa Masar..... Waige waige ta dinga yi a airport tana neman Jiddah tana ganinta ta yafito ta, Jiddah ta nufeta Hajja ta jawota kusa da ita tace "Toh Allah ya kaddara saduwan mu Jiddah ni xan koma Masar kuma ban jin xan sake dawowa kasar nan" A hankali Jiddah tace "Aa xaki dawo Hajja" Hajja ta girgixa kai tana kyabe baki tace "Lala, abubuwan kasan nan duk ba tsari, toh me xan dawo yi?? ni dai ina 'ya ta ta ke?" Jiddah tace "Tana hannun Yaya Bashir" Hajja ta d'an waiwaiga ta tabbatar babu idon kowa a kansu ta kamo hannun Jiddah ta saka mata gold na dankunne tace "Gashi ki ajiye ma 'ya ta, tana shekara biyu cif cif ki saka mata kuma kada kice ma ko wani shege ni na bata balle a kullaceni suce ban ba ma yaransu ba to me na hada da su? ko shi gantallalen Aliyun kar ki gaya masa don babu abinda na hada da shi ma din" Rungumeta Jiddah tayi cikin sanyi tace "Mun gode Hajja Allah ya kara girma, Allah ya kai ki lafiya, in Allah ya yarda mu ma muna nan xuwa wataran" A haka suka rabu da Hajja ana ta daga mata hannu har ta hau matakalan jet din tare da mai martaba da Abba da Alhaji Umar, sai ta juya tana fuskantarsu kafin ta shiga jirgin ta daga masu hannu gaba daya sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tace "To a yayyayafe.... mu dai mun koma Masar!!!" Me Abuturrab xai yi banda dariya little Jiddah dake hannunsa na tayasa. *kada a manta littafin Jiddatul Khair na kudi ne, ba kyauta ba, a xo a sauke hakki a xauna lafiya sisters and brothers* It's 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!😃 A nan kam na ajiye alkalamina✍🏻 na kawo karshen littafin _Jiddatul Khair_ darussukan dake ciki Allah ubangiji ya sa mu amfana da shi, kura kuren ciki kuma Allah ya yafe min....😰 Na sadaukar da littafin nan xuwa ga beloved Dad dina, Alhaji Bello Ahmad.... Ur daughter Jiddoh is always proud of u Papa, Allah ya baka kwanciyar hankali na har abada, ya kara maka budi da daukaka, ya kareka sharrin masu sharri, ya kara maka lafiya da duk sauran musulmai Ameeeen🥰 Gaisuwa ta musamman xuwa ga mahaifiyata Hajiya Hajarah, she is my first love, my world, my role model and my everything, Allah ya bar min ke Hajiya yaya, Allah ya kara maki lafiya ya karo arxiki me albarka, My Siblings Ahmad, Maryam, Yahaya, Fatima, Khadija, Aliyu, Ilham, Sudais, Fadeel, Papi auta, Lil Khaleesat, Baby, Haneef, Ashraf, Jamcy, Humaira, Yusuf Black, Mujaheed, Big Ilham, Aneesah, i love u all!! Allah ya albarkace ku gaba daya, ina sonku har raina, small mummies...., Aunty Rukky, Anty Didi, Uwar Ashraf ur daughter Jiddoh is greeting with respect, Allah ubangiji ya jibanci lamuranku.... Hajiya Pc (Sadiya Chamo) ga gaisuwan ku dake da tawagar Khaleesat's palace, duk na gaisheku ina sonku fisabilillah, Hafsat Ado i greet and appreciate you sis...🥰😘 And finally my lovely fans, words alone isn't enough to express my feelings toward u guys, billah ina sonku, ina alfahari da ku, ina maku fatan alkhairi da fatan gamawa da iyaye lafiya Ameen!!! Taku har ko da yaushe, Hauwa Bello Jiddah A.K.A Khaleesat Haiydar📚✍🏻 Na bar ku lafiya😊